Showing 105001 words to 108000 words out of 307403 words

Chapter 36 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

Gaban sehrish ne ya faɗi rasss!lokaci guda jikinta yayi wani irin sanyi,yayin da idanunta suka ciko tab da kwalla,
   Ita kanta jahad,bataso ta faɗi hakan ba,ranta ne ya 6aci saboda ta tsani a kushe mata baby Junaid ɗinta,Wannan ne yasa har ta faɗi maganar da tayi,
  "Jahad!ni kike faɗa ma haka"?
Da sauri jahad tace"dan Allah kiyi haƙuri,wlh bansan na faɗi hakan ba,raina ne ya ɗan sosu,"
  "Kinayi mun fatan aurena ya mutu kenan"? Tayi tambayar hankalinta aɗan tashe
  "Dan Allah rishi kidaina faɗin wannan maganar,nace maki ba a son raina na faɗi hakan ba,"tayi maganar tare da ƙarasawa wurin sehrish ɗin,ta ruƙo hannunta,
   "Pls kada ki bari hawayen nan sun fito daga cikin idanunki,kinsan cewa bazan ta6a yi maki fatan aurenki ya mutu ba,kuma wlh ban faɗi hakan ba donna 6ata maki rai ba," fuskar jahad tamkar zatayi kuka saboda tausayin sehrish,
   Tuni hawaye sun shiga wanke mata fuskarta,cikin sanyin murya ta wanda ya karaya tace"kin faɗi gaskiya jahad,bai kamata inyi prouding da aurenshi ba,Ni sam na manta ashe yau saura 2 month babban yaya ya sake ni,ni nama ƙosa ya sake ni in huta,'
   Hannu jahad tasanya tana share mata hawayenta"in sha Allah Babban yaya bazai ta6a sakin ki ba,banayi maku fatan rabuwa da junanku,Nafison ku kasance atare na har abada,Daso samu ne kawai wani abu ya shiga atsakaninku,Ana saura sati daya auren ya mutu,aga kina amai kinga shikenan babu zancen saki,Sae dai a fara tanadin suna,"cike da zolaya jahad tayi maganar,aikuwa nan take sehrish ta fashe da dariya,
  Ganin tafara dariya yasa jahad taci gaba da tsokanarta"gaskiya naƙosa in ganki da ciki,cikin ma na babban yayanmu,Wayyo Allah na bansan wani irin farin ciki zanyi ba aranar,zanso naga babynku,wlh ba ƙaramin kyau zaiyi ba,idan ya biyo kowannanku,"
  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Najima ina burin wannan ranar,bazan 6oye maki ba jahad,inaso inga nima na haifi ɗan babbyna,Amma nasan ba yanzu ba,"
   "Dont worry ur self,Very soon zaki haifa ma babban yayanmu twins ko triplet,tunda muma triplet ne,nasan acikinmu baza'a rasa wadda zata haifi ƴan biyu ba ko ƴan uku,"Acewar jahad,
  Shiru sehrish ta ɗanyi tana murmushi,duk da tasan abune mai wuya amma taji daɗin maganar nan ta jahad,
   "Inaso naje naci abinci,yunwa nake ji,"
   Ta ƙarasa maganar tare da kama hanyar fita daga ɗakin,Bin bayanta jahad tayi da sauri tare da ruƙo hannunta cikin nata,
   "Mu tafi atare,nima ae banci abincin ba,"
  Dining suka nufa,Wuri suka samu asaman dining chairs ɗin kowa ya zauna,Tray ne mai faɗi azmee ta ajiye masu asaman dining ɗin,Warmers ne guda biyu babba da ƙarama ta miya ajiye asaman shi tare da plate,sae drinks data ɗauko masu,
   Da yake mutanen gidan duk basu nan shiyasa bata girka abinci dayawa ba kamar yadda ta saba,ita kanta ta ɗan samu hutu yanzu,
   "Munyi waya da daddy,"sehrish ce tayi maganar a yayin da take ƙoƙarin buɗe warmer ɗin,
   "Ya faɗa maki ranar da zasu dawo ne"?_
  "A'a bai faɗamun ba,sai dai yayi mun albishir mai daɗi,"
  Cike da zumuɗi jahad tace"Wani albishir kenan"?
   Murmushi ta ɗanyi a lokacin ta kammala buɗe warmer ɗin,wainar shinkafa ce acikinta,
   "Ya sanar dani cewa da zarar sun dawo daga damaturu,A washe garin ranar zasu tafi kano,wurin nemo oumman mu,"
  Maimakon taga farin ciki akan fuskar jahad,sai taga idanunta sun ɗan ciko daa kwalla,

   "Meyasa bakya farin ciki ne"?
"Sehrish farin ciki fa kika ce?Bana Farin ciki,Idan har kika ga nayi farin ciki,toh An samu oummaan mu ne da ranta kuma da lafiyarta,ina fargabar abunda zaibiyo baya,idan suka je nemanta,Kinsan yadda oumman mu take tsananin son mu sosai,Amma lokaci guda aka nemeta aka rasa,tsorona kada ace ya sayyadi ne yayi mata wani abun,dama yasha faɗin cewa zai kashe ta idan har bata daina bin ƙwaƙƙwafin da takeyi mashi ba....."dakatawa jahad tayi da yin maganar,jikinsu duk yayi sanyi,
   "Addu'a yakamata muyi mata akan Allah yasa su samota,Amma nikaina ina fargabar a wani hali zasu same ta,"
    Duk sunsha jinin jikinsu,zuba masu wainar tayi acikin plate,sannan ta buɗe ƙaramar warmer ɗin,Miyar ganye ce,taji ganda lu6u lu6u acikin,Tuni ƙamshinta ya gauraye wurin,
   Daƙyar suke iya cin abincin,kamar waɗanda akayi ma dole suci,

   *HAROON*

Fitowarshi kenan daga cikin bedroom ɗinshi,yana ƙokarin barin wurin,Yaji an ambaci sunanshi"Haroon"!gabanshi ne ya fadi,duk a tunaninshi Amrish ce ta kuma biyo shi,da sauri ya juya don yaga wacece,tun daga ƙasa har sama ya soma binta da kallo,Jikinta na sanye da atampa,riga da skirt ne sun matseta sosai,gaba ɗaya surar jikinta ta fito ɗass,bakowa bace wannan fa ce Hayaam,fitowarta kenan daga ɗakinsu na hotel da Omar ya kama masu,Ashe tun ranar basu tafi ba,Zama suka cigaba dayi acikinshi sun ƙara biyan kuɗin ɗakin,don aunty babba taci alwashin cewa babu inda zasu tafi,daga abuja sai Enugu wurin bokan nan,Yanzu haka kuɗi suke harhaɗawa,duk ta siyar da gold ɗinta,yanzu ma shirye shiryen tafiya sukeyi,
  Sakin baki haroon yayi yana kallonta,da wata irin kasalalliyar Murya yace"Ke!me kikeyi anan"!?
  Cike da kwarkwasa Hayaam ta ƙarasa gabanshi fuskarta ɗauke da murmushi tace"Kayi mamakin ganina ne?nikaina bansan da zamanka anan ba,yanzu kawai ina fitowa na ganka,kana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinka,"
   Lokaci guda haroon ya saki wannan shu'umin murmushin nashi,a wayance yace"Amma nadaina ganinki a gidanmu,nayi tsammanin cewa kin koma gidanku ne?but me kikeyi acikin hotel ɗin nan"?
   Shiru ta danyi tana tunanin abunda zata faɗa mashi,
Shi kuwa gogan gaba daya ya aza kwartayen idanuwan nan nashi akan Ƙirjinta,
   "Naji kin yi shiru,idan ba damuwa mu shiga daga ciki mana,"yayi maganar yana nuna mata ƙopar daƙinshi,
  Gaba yayi tabi bayanshi,buɗe masu ɗakin yayi suka shiga ciki,
   A gefen gadonshi suka zauna,suna fuskantar juna,
   "Kinyi kyau sosai,"yayi maganar yana wasa da harshen shi asaman la66ansa,
  Murmushi hayaam tayi,batare da tace mashi komai ba,
  "Ko kina buƙatar abunsha ne kona ci haka insa akawo maki"?
  Girgiza kai tayi"a'a,a ƙoshe nake,bana jin yunwa,
  ta6e bakinsa ya ɗanyi,kafin ya kuma cewa"Ƙamshin turarenki yayi mun,"
  Dariya tayi tare da cewa"Allah ko"?
  "Da zaki bani dama ko sau ɗaya ne,just inaso in ɗan shaƙi ƙamshinne a hancina,"
   Batasan wanene haroon ba,saboda tasan halayen matasan gidansu,tayi tunanin cewa shima duk irinsu ne,hakan yasa tace mashi"Mezai hana,"
  Matsawa yayi kusa da ita,tare da kai hancinshi saman fatar ƙirjinta,yana ɗan shinshinar ƙamshin turaren,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,zagayawa yayi da hannunshi ta bayan rigarta,abu kamar wasa,ya zuge zeep ɗin rigarta a hankali,saboda tafara fita hayyacinta,
  ɗagowa yayi da hancinshi izuwa saman wuyanta kamar wani maye,haka ya shiga shinshina wuyan nata,da wata irin kasalalliyar murya yace,"Wannan turaren na wani company ne"
    Shiru tayi batare da ta bashi amsar tambayarshi ba,dama da biyu yayi mata maganar don yaji idan har lokacin tana acikin hayyacinta,Shirun da tayi mashi ne ya tabbatar mashi da cewar,tafara fita hayyacinta,
   Bata ankara ba,taji hannunshi ta cikin rigarta saman boobs ɗinta,A zabure ta kwace kanta daga jikinshi tare da ja da baya,tana ƙokarin gyara rigarta,ɗagowa tayi tana kallonshi,Murmushi ta gani akan fuskarshi,
   Hakan ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ma,duk a tunaninta mutumin kirki ne shi ashe shima ɗan harka ne,
   Miƙewa tayi da sauri ta nufi hanyar fita daga ɗakin,Hannu tasa ta ruƙo kopar zata buɗe,taji ƙopar adatse,hakan yasa tayi saurin juyawa tare da kallonshi,Nuna mata key ɗin yayi a hannunshi yana dariya,
   Fuskarta aɗan ɗaure tace"pls,ka buɗe mun kopa inaso na tafi,Aunty laila na jirana,"
  Mikewa haroon yayi tare da takawa izuwa gabanta ya tsaya,sannan yace"Ganinki da nayi gaba daya kin tayarmun da sha'awata,na kwaɗaitu da son kasancewa tare dake,kallo ɗaya da nayi maki na gane cewa ke ba ƙaramar ƴar bariki bace,Don haka kada ki 6oye mun true colour ɗinki,kizo kawai muyi harka,"
  Zuba mashi ido tayi tana tunanin ta wata hanya zata 6ullowa haroon don ta samu ta tsere mashi,bakomai take ji ma tsoro ba fa ce aunty babba,saboda ta hanata kula maza,'
    "Koda ace ina kula maza,bazan kula irinka ba,Kuma ni ba ƴar iska bace kamar yadda kake tsammani,Ka buɗe mun kopa in fita,in ba haka ba zanyi maka illa,"a tsiwace tayi maganar hada rufe idanunta,
  Dariya haroon yayi tare da sanya hannushi ya ɗaga wandon jikinshi,ya tura key din acikinsa,sannan yace mata"Zoki ɗauki key din idan kin isa,ƙaramar ƴar tasha kafin kiyimun illa ni zan illata ki idan har baki taimaki kanki ba"
  Tsabar takaici ne ya cika hayaam,tayi danasanin yi mashi magana,da duk hakan bata faru ba,
  
  
  
  
  


   
  
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda phone call just message ta whatsapp,08103884440❤_





*Aunty Babba*

Guntun tsoki taja,yayin da idanunta ke kallon agogon dake manne acikin ɗakin,kusan ƙarfe 6 na marece babu hayaam babu alamarta,har ta fara gajiya da jiranta,tun ɗazu take traying numbar wayarta amma Still Switch off,hakan ba ƙaramin 6ata mata rai yayi ba,tunani tashiga yi ko ina ta shiga?daga zuwa curo kuɗi a banki shiru kake ji wai malam yaci shirwa,
Ruƙe qugu tayi tare da yin ƙwafa,ta koma gefen gadon ta zauna,tana jiran shigowarta,tuntana sa ran dawowarta harta fara fidda rai,lokaci sai gudu yake yi har wurin ƙarfe 7,hayaam bata dawo ba,duk tana azaune har 8 ta buga,
"Allah yasa ba gantalin nata ta tafi ba,daga zuwa curo kuɗi a banki kamar na aiketa wata uwa duniya,tabi duk ta rufe layinta,Mtsww"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,

Yayin da aunty babba ke zaman jiran hayaam,ita kuma tana can rai hannun Allah a ɗakin haroon,Lokacin daya hanata fita daga ɗakin ya zura key a wondonshi yace ta taimaki kanta,tayi tsammanin cewa zata iya kwatar kanta saboda tasa ba gara sofwan saurayinta,hakan yasa cikin salon wayau ta zura hannunta acikin jakarta,batare da ya ankare ba,Ta curo kwalbar turare ta fesa mashi asaman fuskarshi,kai tsaye ya ta6a idanuwanshi,raɗaɗi yasa yayi saurin kai hannu yana murza idanun nashi,ganin ya fita hayyacinshi yasa tayi ƙoƙarin zura hannunta acikin wandonshi,aikuwa batayi wani aune ba yayi mata ƙwaƙƙwarar damƙa,Ya yayyaga kayan jikinta da hannunshi,tundaga tsaye ya fara biyan buƙatarshi da ita,cikin rashin imani haroon yayi mata kaca kaca,Karshe yayi wurgi da ita saman gadonshi,Ya tu6e kayan jikinshi kamar yadda ya cire nata gaba ɗaya,sannan yabi ya danneta kamar wani bakure haka yakai mata Hari,wa'iyazubillah duk yadda taso ta ƙwaci kanta amma hakan ya faskara,Tun tana ihu tana kuka har bakinta ya mutu ƙarshe ta sume....."

*Boss Bature*

❤🤍❤

*SEHRISH*

Wuraren ƙarfe 10 na dare,tana a kwance saman gadonsu,ta ƙudundune cikin bargo,bacci harya fara ɗaukarta,tajiyo ringing ɗin wayarta,a hankali ta zame bargon tare da miƙa hannu ta dauki wayar dake ajiye saman mattress din,daƙyar ta iya buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,ƙurawa screen ɗin ido tayi yayin ta zuciyarta ke bugawa,Sunan My Boss Man ne ya bayyana da manyan haruffa,Gabanta ne yayi wani irin bugu rass!lokaci guda ta miƙe daga zaune tana faman zare ido,hannayenta har kerma sukeyi,Amsa kiran tayi tare da kara wayar a kunnata,Tunkafin tayi sallama Sexy voice ɗinshi ta katse mata hanzarinta da cewa"Am back,"yana faɗin hakan yayi rejecting call ɗin,
   Yadda kasan gunki haka sehrish tayi kasaƙai,fuskarnan tamkar ta fashe da kuka,ɗan hutun da ta samu na kwana biyu ya ƙare,
   Jiki asanyaye ta sauko daga saman gadon bayan tayi wurgi da wayar saman mattress ɗin,Sleeping dress ne ajikinta white colour masu ɗige ɗigen baƙi ajikinsu,sunyi matuƙar yi mata kyau,Riga da wando ne,

Kaitsaye ta nufi wurin windown don ta leƙa taga idan dagaske ya dawo din,hannu tasa ta janye labulen tare da zuqe glass ɗinta,
   daga inda take ta hango motorshi a parkin space,wannan ya tabbatar mata da cewar ya dawo yana a cikin gidan,hannu tasa tare da dafe goshinta a hankali ta furta"OMG!"
  Gyaɗa kawai tayi tare da cewa"Ae shikenan,Za'a koma ƴar gidan jiya kenan,
   Juyawa tayi ta nufi shoe rock ɗinsu,flat shoe ta ɗauko ta zura a ƙafafunta,sannan ta nufi hanyar fita daga ɗakin,buɗe kopar ɗakin tayi bayan ta fita ta datse ɗakin,
   Fitowa tayi daga corridor din ta wuce kitchen,gidan tsit babu kowa,duk babu daɗi,tayi kewarsu sosai,musamman ɗan baby junaid ɗinsu,
   Batasan ko zai buƙaci abinci ba,tun da yanzu ya dawo,Hakan yasa ta hado mashi Coffee kawai don tasan dole ya bukace shi,a cikin plate ta aza cup ɗin,ta fito daga kitchen ɗin,ta nufi upstairs,tunani tashiga yi ko ina su jahad suke,yanzu haka suna a ɗakin aunty azmee dama kwana biyun nan,duk in dare yayi suna zuwa fira ɗakinta,wani lokacin acan bacci yake ɗaukarsu,sae wurin asuba suke dawowa dakinsu,
  A hankali take taka staircase ɗin harta haura sama,wuce wa part ɗinshi tayi,a baƙin kopar shiga falon ta tsaya,kamar yadda tasa ba,sae da fara karanta addu'o'in neman tsari daga sharrinshi sannan ta shiga ciki da sallama abakinta,
  Babu kowa acikin falon,bedroom dinshi ta wuce zuciyarta na ɗar ɗar,sallama tayi mashi,daga ciki taji ya amsa mata,tare da bata Iznin shiga,
Shiga cikin ɗakin tayi cike da fargabar ganin fuskarshi,agaban mirror ta same shi tsaye,yana sanye da bathrobe,jikinshi da alamun danshin ruwan da yayi wanka,bata samu damar ganin fuskarshi ba saboda ya juya mata baya,
  Ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi coffee ɗin saman table sannan tace"Sannu da dawowa babban yaya ya gajiyar tafiya"?
   Tamkar bazai amsa mata ba,har sai da ta fidda rai da zaiyi mata magana sannan yace"Am ok,"ɗaya daga cikin abunda ke ƙona mata rai kenan,Saita saki baki tayi mashi magana mai tsayi ya bata amsa in short,
   "Ga coffee nan,bansan ko zaka buƙaci wani abu ba,bayan wannan,"
    "No,need,"ya ambaci hakan tare da juyowa ya koma daga gefen gadon ya zauna,tsayawa tayi saboda tasan halinshi,in har bashi ya sallameta ba,toh bata isa ta tafi ba,
   Ɗagowa tayi ahankali ta saci kallon fuskarshi,yayi haske sosai la66an nan nashi sunyi pink tamkar ya shafa jan baki,ya ɗaure fuskar tamau kamar wanda aka aiko ma saƙon mutuwa,
   Mayar da idanuwanta tayi akan fatar ƙirjinshi,ganin yana ƙokarin dagowa yasa tayi saurin kawar da idonta gefe guda,
     Hannu yasa tare da daukar Cup of coffee din,sae faman tiririn zafi yake yi,saitin bakinsa yakai cup ɗin a hankali yake kur6arshi,
   ɗan dakatawa yayi da shan coffee ɗin batare da ya ɗago ya kalleta ba yace"Ɗaukomin sleeping dress ɗin da zan sanya,"
  Amsa mashi tayi da toh,Sannan ta juya,kamar ance ya ɗago idonshi karaf ya sauka akan Wandon jikinta,ɗigon jinin daya gani ne yasa shi yin wurgi da Cup ɗin hannunshi ya faɗi ƙasa ya fashe,wani irin tashin zuciya ne yazo mashi,da gudun gaske ya mike tare da tunkarar toilet ya faɗa ciki,
  Hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,batasan meyasa shi jin amai ba,ita dae kawai taga yayi wurgi da cup kuma ya nufi toilet,tuni tasha jinin jikinta,tsananin tsoro ne ya bayyana kan fuskarta,tunkafin ma taji meyasa shi yin amai,
  Gaban Basin ya tsaya,sae faman kakarin amai yakeyi,tamakar ƴan hanjin Cikinshi zasu fito waje,Wani irin ƙyanƙyami ne dashi,gaba ɗaya duk yabi ya burkice,almost 8 mins yana acikin toilet ɗin,tanajiyo sautin aman da yake yi,zugudum tayi tana jiran fitowarshi,
  Hannu yasa tare da buɗe ƙopar toilet ɗin ya fito,jikinshi sae kerma yake yi saboda tsabar 6acin rai,idanuwanshi har sun canza launi,
   A zafafe ya tunkareta,ganin haka yasa sehrish tashi ga ƙoƙarin ja da baya,tana ƙoƙarin guduwa daga bedroom ɗin nashi, damƙo wuyan rigar jikinta yayi,tare da janyota yayi wurgi da ita,ta bugi bangon ɗakin,
   Raɗaɗin da taji ne yasa ta fashe da matsanancin kuka,ware hannayensa yayi da nufin ya mare ta,runtse idanuwanta tayi da sauri tana kuka,
  Yarfar da hannun yayi gefe guda,tsabar 6acin rai ya hana ya buɗe baki yayi mata magana balle har tasan laifin data aikata mashi,cikin shesshekar kuka tace"Dan Allah kayi haƙuri bansan laifin dana aikata maka ba,"
    Tamkar ya rufe ta bugu haka yake ji,daƙyar ya iya buɗe baki yace"karki kuskura ki ƙara shigomin part ɗina da wannan ƙazantar a jikinki!ki tsaya har saikin kammala"
  a ruɗe sehrish tashiga tunanin wata ƙazanta ce yake magana akai,da sauri ta shiga bin jikinta da kallo,a ƙoƙarinta nata gano abunda ya kira da ƙazanta,
.  hakan ba ƙaramin fusata shi yayi ba,a fusace ya buga mata tsawa wadda tayi matuƙar girgizata,ta zaburar da ita kuma ta tsoratar da ita,Nan take taji zubar jini acan under ɗinta,tare da matsanancin ciwon mara lokaci guda ya farmata,Sae lokacin ta gane cewa period ɗinta ne yazo mata,jinin ne ya fara zuwa shiyasa batayi noticing ɗinshi ba,sae daga baya raɗaɗin ciwon ya taso mata,
  Dogon tsoki yaja,tare da juyawa ya nufi cikin ɗakin,
   Sehrish kuwa tuni ta soma fita hayyacinta,idanuwanta sunyi jawur da su,kamar daga sama yaji tace"AMMA BAKA DA IMANI"_
   gabanshi ne ya faɗi rass,dakatawa yayi da yin tafiyar tamkar antokare shi,
   "Tunda nake arayuwata banta6a ganin mutun mara imani mara tausayi ba irinka!Jinin daka gani ajikina lalura ce bani na ɗaurama kaina ba,nikaina bansan dashi ba,da bazan bari ya zuba ajikin kayana ba balle har ka gani,duk irin ƙoƙarin da nakeyi wurin ganin na faranta maka rai baka ta6a gani ba,Nifa ba tsoranka nake ji ba!Allah kaɗae nake tsoro,Idan taƙamarka ƙarfi kazo ka buge ni,kaga in zan mutu,Na rayu da wanda yafi ka rashin Imani da tausayi,Kuma na jure zama dashi,naga tashin hankalin daya fi wanda nagani a wurinka,kuma duk na jure hakan....."
  Tashin hankali,Sanƙamewa sgr yayi atsaye,hankalinshi yayi matuƙar tashi,a arazane ya juyo don ya tabbatarwa kanshi da abunda kunnuwanshi ke juyo mashi,Jikinshi sae faman tsuma yakeyi,abun yayi matuƙar girgizashi,abun Yayi mugu mugun ɗaure mashi rai,Zuba mata ido yayi yana kallonta cike da mamaki,
  "Dame ka ke taƙama ne?kaifa mutunne ɗan adam,mai hannu biyu mai ƙafa biyu,hancin ɗaya,da baki ɗaya,idanuwa guda biyu kamar nawa,Wanda idan yayi bacci sai yarda akayi dashi,idan ya mutu kuwa duk  kyanshi duk mun dukiyarshi duk ji dakanshi acikin farin yadi mafi arha za'ayi mashi sutura,ƙarshe ya zama abincin tsutsa,"
   Waro ido waje sgr yayi hankali atashe yake kallonta,tunda yake arayuwarshi wata ƴa mace bata ta6a tsayawa agabanshi ba,kamar haka tana gaya mashi magana,Ido cikin ido batare da jin shakkarshi ba,yadda kasan mai iskokai haka sehrish ta rufe shi da faɗa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,har ya fara tunanin kodae Tasha ƙwaya ne?to ae ko wanda yasha ya bugi da giya bai ta6a kallon cikin idonshi ba ya gaya mashi magana,
   "Burin ka kawai ka wulaƙanta rayuwata,shiyasa ka aure ni don in cigaba da aiki a ƙarƙashinka,Inayi maka biyayya ne ba don inajin tsoranka ba,kaima ka sani,ni ba baiwarka bace baiwar Allah ce,Kuma idan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login