Showing 90001 words to 93000 words out of 307403 words
Chapter 31 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete
Sgr ya zaunar da ita,cikin lokaci ƙankani Sgr ya kammala yi mata dressing ɗin itama,
"Ita kuma hosana ya zamuyi da ita?kodai asibiti zamu kai ta?Acewar Abusufyan,
Omar yace"Rafayet zai iya duba mana ita anan gida ma"
"Omar am not a psychiatric doctor,though i've experience about their work,zan iya duba ta,Amma a ƙa'ida,psychiatric doctor ya kamata yayi checking ɗinta,bazan shiga aikin da banawa ba,"kaji turawa,ƴan bin ƙa'ida,
Jinjina kai Omar yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,ya juya tare da kallon Dr harris dake tsaye ya goya hannayenshi saman ƙirjinshi yace"Bismillah,"yayi maganar yayin da yake yi mashi nuni da hosana wadda ke kwance ajikin hafsat,idanunta sun birkice sae farar kwayar idon kawai,yatsunta kuwa sae faman kerma sukeyi,hada na kafafunta,
Kallonta kawai Dr harris yayi batare daya ta6a jikinta ba,ya faɗi sunan allurar da take buƙata ayi mata,
Da sauri Omar ya ciro wayarshi tare daddana wasu numbobi,ya kira Dr Emran na asibitin Sgr,kiran na shiga emran ya ɗauka,don haka Omar ya miƙa ma Dr harris wayar don suyi magana,
Bayan sun kammala wayar,ya dago tare da kallon Marshal yace"Ya sanar dani cewa within 15 mins zaizo tare da allurar da kuma medicine ɗinta,"
Omar yace"Okey,Allah ya kawo shi lafiya,
"Ku kwanta saman gadon,itama mara lafiyar a kwantar da ita before doctor din yazo,Azmee ki shirya masu breakfast dinsu,yanzu haka ma Yunwa ce ke Cinsu,shiyasa su kayi wannan damban," sae yanzu ammi ta tanka masu,saboda tsabar gatanci maimakon asamu wanda xaiyi masu faɗa da tsumagiya a Zane su, amma kowa ya rufe ido,sae lalla6a su akeyi,diyanso kenan,shalelen abusufyan,
miƙewa sgr yayi daga zaunen da yake,sannan yayi masu nuni da su kwanta,a hankali kowaccensu ta kwanta yadda kasan waɗanda suka yi wata suna Jinya don sunji jiki,a hankali Hafsat ta janye Hosana daga jikinta ta kwantar da ita,har lokacin bata dawo hayyacinta ba,sae faman fari takeyi da idanuwanta,yatsun hannunta dana ƙafafunta sae kerma suke yi,
Haɗa baki su fawan su kayi wurin yi masu ya jiki,kafin daga bisani matasan suka fita daga ɗakin nasu tare da Ammi da hajiya saratu,Ya rage daga Sgr sae Marshal Omar,Hajiya azeema da kuma abusufyan da kuma gwaggwon katsina sae hafsat,Azmee ta wuce kitchen don ta shirya masu breakfast ɗinsu,within 15 mins,Dr Emran ya ƙaraso gidan,a cikin motarshi yazo,tun a waje ya haďu da dr Harris tare da kanal Yusuf a tsaye,dama shi suke jira,fitowa yayi daga cikin Motar hannunshi dauke da Ledar maganin Hosana da kuma injection din da xa'ayi mata,gaisawa suka fara yi fuskar kowannansu dauke da murmushi,canal Yusuf ne ya kar6i Ledar da Emran din yaxo da ita,sun so ya shigo daga ciki suyi breakfast atare dashi,Amma ya sanar dasu uzurinshi,hakan yasa suka ƙyale shi,sallama sukayi da juna sannan suka koma ciki da sauri,
Cikin bedroom din nasu,Dr Harris ya shigo ganinshi yasa Omar da Sgr suka bashi wuri donya ƙarasa gaban gadon,batare da 6ata lokaci ba,ya ɗura ruwan allurar acikin syringe,aikuwa kamar akan idon Hosana yana kai hannu zai ruƙota ta zabura,tashiga yan buge²,ganin haka yasa sgr da Omar matsawa kusa dashi,sae da suka rurruketa dakyar aka samu yayi mata allurar,yana kammala yi mata allurar,nan take zufa ta Shiga tsastsafowa daga jikinta,Kafin wani lokaci tuni bacci yayi awon gaba da ita,hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yayi ba,
Juyawa dr Harris yayi tare da kallonsu Omar yace"in sha Allah,Zata ji sauƙin jikin nata,sannan idan ta farka,ga medicines ɗinta nan,bayan taci abinci,akwai direction ajikin kowani magani sae a duba,idan za'a bata,"
Amsa mashi sukayi da toh,Omar yace"aikin ka na kyau dr,"sannan ya mayar da idanunshi kan hajiya azeema tunkafin yayi mata magana tace"Zan kula dasu,idan tafarka zan bata maganin da yardar Allah,"murmushi ya saki tare da juyawa ya kalli sgr,"Muje ko?time karya ƙure mana,naga yanzu har 12 ta kusa,nan da wani lokaci xa'a shafa fati.....'bai ƙarasa maganar ba ganin irin kallon da rafayet ya jefa mashi,Dariya Omar yayi yana faɗin"Sorry bro,kada ranka ya 6aci mana,Yau fa ranar farin ciki ce agaremu,murmushi yakamata a gani akan fuskokinmu,ɗanyi murmushi mana,cike da zolaya Omar keyi mashi magana,shi kuwa Namijin sae faman tamke fuska yake yi,daga bisani suka fita daga ɗakin atare da dr harris,
Komawa hajiya azeema tayi tare da samun wuri gefen gadon ta zauna tana kallonsu,duk sun rufe idanunsu kamar masu yin bacci,
"Bismillah gwaggo ku zauna mana,"azeema ce tayi maganar tare da yi mata nuni da saman bedside drawer dinsu,jiki asanyaye gwaggon katsina ta karasa ta zauna saman drawer din,ita dae har yanzu bata yarda Cewar Hosana ce ta ciccijesu ba,
"Azeeme yanzu kema kin yarda cewa yarinyar nan itace da kanta ta gartsa ma ƴan uwanta cizo har haka?Ni nafi tunanin cewa Ya Sayyadine yazo da suffar kura yayi masu wannan aika aikar,mutumin nan fa ba ƙaramin Taƙadari bane,banbancinshi da shaiďan kaho ne kawai da babu,"wannan maganar da gwaggon katsina tayi ba karamin dariya tabasu ba,
Girgiza kai hajiya azeema tayi fuskarta ɗauke da dariya tace"gwaggon shagali,ae in ma shine to ta Allah ba tashi ba,ki kwantar da hankalinki,Sayyadi yake kowa,ba abunda ya isa yayi masu bi'iznillahi,"
Washe Baki gwaggo tayi da alama taji dadin abunda Azeema tace mata,
"Allah yayi mana maganin la'ananne,"
Azeema ta amsa mata da ameen,
Sae wuraren karfe sha biyu da rabi Hosana ta farka jikinta da sauki sosai,kuma tana bude ido ta fashe da kuka tana ambaton sunansu sehrish da jahad,sae da aka nuna mata su sannan hankalinta ya kwanta,
Tuni azmee ta kawo masu breakfast ɗinsu acikin dakin,da taimakon Hafsat da kuma hajiya azeema suka ci abincin,bayan sun kammala cin abincin,Hajiya azeema da gwaggo suka bar dakin,ya rage saura hafsat ita kaɗai,gyara masu bedroom din nasu ta Shiga yi,komai yadawo normal Ba kamar daba da suka hargitsa dakin,bayan ta kammala gyaran ɗakin,wuri tasamu saman side drawer dinsu ta zauna tana kallonsu,
"Hosana ki ji tsoran Allah,jibi yadda kika raunata mu sae kace ba yan uwanki ba,"jahad ce tayi maganar ranta a6ace,
A kule hosana tace"ae laifin ku ne,saboda me zakuyi mun rashin kunya?ni ba yayarku bace?oumma tace ni ce babba acikin ku,saboda majnun ya faɗa mata cewa ni ce na fara zuwa duniya,sae da na shaƙi iskar duniya da minti biyar sannan ke kika zo daga ke kuma sae waccen uwar tsiwar" "dakyar take magana,saboda har yanxu jikin nata da sauranshi,
Guntun tsoki sehrish taja"karki kara ce mun uwar tsiwa,in ba haka ba zan nuna maki kalar nawa haukan,mara mutunci kawai,kuranya mai cin naman ýan uwanta..."
Tunkan ta ƙarasa maganar,da Sauri jahad ta toshe mata bakinta,"Dan Allah ya isa haka,da alama baki ji jiki ba,shiyasa kike ƙoƙarin tsokanota,salon Kija mana jinyar ta koma a gadon asibiti,"
Hafsat dake zaune tana sauraronsu,sae faman kunshe Dariya takeyi,
*Boss Bature*
❤🤍❤
Gaba ďaya matasan gidan,kowa ya Shiga yin wankan juma'a,Kafin wani lokaci duk sun shirya halarta Sallar Juma'a tsaf,kowa ya ɗauki wanka na mutunci wankan shadda,abun sai wanda ya gani,bakowa ne yasan da zancen ɗaurin auren babban yayan nasu ba ko acikin matasan gidan,manyan su ne kawai suka son da ɗaurin auren,sauran kuwa koda zasu san da auren sai dai suji a masallaci a yayin da ake sanarwa.
Zuba mashi ido Alexandra tayi ganin yadda yake ta rawar jiki,yaci uban ado cikin farar shadda,ya zura malunmalun,ya sanya sabuwar hula akanshi,ga agogo sabuwa ya Sanya a hannunshi,ga haɗaɗɗun takalma masu tsadar gaske ya zura a kafafunshi,sae faman sakin Fara'a ya keyi kamar wani sabon ango,yana tsaye agaban mirror hannunshi dauke da kwalbar Turare sae bin jikinshi yakeyi ko ina yana feshe shi saƙo da lungu na jikinshi tamkar zai ƙarar da turaren dukansa,
Abun ya ɗaure mata kai cike da mamaki tace"Darling,irin wannan daukar wanka haka?kaji tsoran Allah kodai kishiya Zaka ƙaromin ne"? dariya abbansu yayi tare da ďan juyawa ya kalli wurin da take zaune gafen gadonsu,ta kura mashi ido ko kyaftawa batayi,
"Ni da nake da Alexandra,Me zanyi da wata ya' mace?Ni na isa ma nayi maki kishiya?kefa ta dabance ko acikin mata,shiyasa lokacin da kika tafi kika barni nagaza samun natsuwa,kuma naqi kula kowa,saboda son da nake yi maki,"
ƴar hararar wasa ta jefa mashi tare da cewa"daɗin baki zakayi mun ko?
"No,ba haka bane,am serious fa,taya zanyi aure baki sani ba?kamar dai wani munafuki,wannan fa wankar sallar juma'a ne,ko kin manta cewa Yau juma'a ne"?
Shiru ta ɗanyi tana kallonshi,kafin ta ɗan ta6e bakinta tare da cewa"Okey,natuna,nidae duk da haka ban yarda dakai ba Allah,ji nake kamar na bika masallacin nan,"
Dariya sosai abba yayi,bayan ya tsagaita da yin dariyar yace"Ashe kina kishi ne?shine kuma kika tafi kika barni,ba kiyi tunanin cewa zan iya ƙara aure ba,a bayan idonki ba"?
"Ae nasan cewa ba zaka iya ƙara aure ba,that's why ban damu akan haka ba,nasan wanene mijina,kuma na yarda da irin son da yake yi mun,bazai haɗa ni da wata ba," acikin zuciyarta kuwa cewa takeyi"Mutun ma ya kuskura yayi mun kishi,da kuwa na tashi gidan nan da bomb,kowa ya rasa,"
Suna cikin magana,sae ga junaid ya faɗo cikin ɗakin,jikinshi na sanye da farar shadda,sae ƙamshi ke tashi ajikinshi,hannunshi na ruke da hularshi,mommynsu na ganinshi ta miƙe jiki na rawa,ta rungumoshi tana shafa sumar kanshi,
"My baby boy,U look so beautiful,Har ma kaso kafi daddynku kyau,"ta ƙarasa maganar a yayin da take raba jikinta daga nashi,
Ashagwa6e yace"Mommy,yanzu kina nufin Abba ya fi ni kyau?kallar ni fa dakyau ki gani tun daga ƙasa har sama,son kowa ƙin wanda ya rasa,"
Dariya sukayi gaba ɗayansu,Abbansu yace"To fa!junaid kishi kake dani"?
Turo baki yayi yana faman ƙunƙuni,irin na shagwa6a66un nan,
Alexandra tace"wasa nake nima,kafi shi kyau nesa ba kusa ba,"
Ƙayataccen murmushi ya saki jin abunda tace,
Mayar da hankalinshi yayi kan abban nasu tare da cewa"Abba mu tafi,kada lokaci ya ƙure mana,"
"Toh,Uban sauri,mu tafi," yayi maganar tare da ruƙo hannunshi,
"Madam mu zamu wuce"
Murmushi tasaki tare da ɗaga masu hannu tace"Adawo lafiya,in anje anyi mana addu'a,"
Junaid yace"kada ki damu mommy zanyi maki addu'a akan Allah yasa daddy ya ƙara maki kishiya,"
ɗan zaro ido waje tayi tana kallonshi,da sauri yaja hannun abbansu suka fuce suna dariya,
A main palour Matasan gidan suka hallara ga6a dayansu,sae ƙamshi ke tashi,kowannansu fuskarshi na ɗauke da murmushi,musamman abusufyan,shigowa abba yayi cikin falon hannunshi cikin na junaid,tunkan ya ƙaraso ya lura cewa babu Rafayet acikinsu,
Kowa sai tambayar ina babban yaya yake,saboda sun saba tafiya masallacin juma'a atare,gaba ɗayansu suke hallara a babban falon nasu duk juma'a before su wuce masallaci,shiru babu rafayet,sae Faman duba agogon hannuwansu sukeyi suna kallon lokaci,har sai da Marshal Omar yace"bari naje bedroom ɗinshi yanzu haka bai kammala shiryawa bane,"da sauri ya tunkari upstairs ɗin yana ƙoƙarin hawa saman benen,Suka jiyo sautin takalmansa,
Gaba ɗayansu suka ɗaga idanunsu sama suna kallonshi,Cike da tsananin mamaki,tunda suke arayuwarsu basu ta6a ganin sgr ya sanya shadda ajikinshi ba,this is the first time daya fara sanya shadda ajikinshi,tabarakallahu ahsanul khaliƙin,Getzner ce sky blue mai ɗaukar ido,wadda sehrish ta ta6a ɗauko mashi a kwanakin baya,donya sanya amma yaƙi sanyawa,To yau dai itace ya sanya ajikinshi,Babu hula akanshi amma ba ƙaramin kyau sumar kanshi tayi ba,yayi mata gyara na musamman,hannunshi kuwa na sanye da Wannan diamond watch ɗin tashi,yayin da ƙafarshi ke sanye da penny loafers,tunkan ya ƙaraso down stairs din ƙamshin turarenshi ya gauraye ko'ina,yadda kasan tauraro acikin taurari haka ya bayyana,tafiya yakeyi gently tamkar baisan taka ƙasa,fuskar nan tashi aɗaure babu fara'a ko miskala zarratin,sae kace ba yau zai angwance ba,
A hankali yake tattaka stairs ɗin, yayin da yake manna links ɗin hannun rigarshi,koda ya ƙaraso cikin falon,batare daya kalli kowannansu ba,ya nufi hanyar fita daga main falo ɗin,Murmushi abbansu ya saki aranshi yace"Rafayet kenan"
batare da 6ata lokaci ba,Suka fito waje gaba dayansu,dama already motocinsu na nan a jere,Nan kowa ya buɗe motarshi ya shiga,A jere motocin suka fuce daga cikin gidan ɗauke da jiniya,
*💃💃💃ALHAMDULILLAH, A YAU JUMA'A DUBBAN JAMA'A SUN SHAIDA ƊAURIN AUREN RAFAYET SALAHUDDEEN HOSSEIN,TARE DA AMARYARSA SEHRISH SALAHUDDEEEN ABUSUFYAN💃💃💃*,
bayan kammala sallar juma'a aka ɗaura auren nasu,Sae dai muce Allah ya basu zaman Lafiya atsakaninsu❤
*Finally Rafayet weds sehrish*🥳🥳🥳😘
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*
*Father of soldiers*
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina 08103884440❤_
Fitowarta kenan daga cikin toilet taji gabanta ya faɗi rasss!da sauri takai hannu ta dafe saitin zuciyarta,ƙamewa tayi abakin toilet ɗin batare da ta motsa ba,jahad dake zaune saman darduma,da alama ta kammala sallah,jikinta na a sanye da hijab Maroon colour,ta ɗaga hannayenta sama tana addu'a,tunkan ta kammala ta lura da halin da Sehrish ke ciki,tana shafa addu'ar da sauri ta miƙe ta tunkareta,
"Sehrish!lafiya meya faru ne? A ɗan ruɗe ta tambayeta,
Sehrish kuwa sam ta gaza buɗe bakinta tayi magana,saboda yanayin da ta shiga,gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi,
Ruƙo hannunta jahad tayi tare da cewa"sehrish!wai lafiya?ki amsa mun mana"?
Lumshe ido sehrish tayi a hankali ta shiga sauke ajiyar zuciya,daga bisani ta ɗan ware idanunta tana kallon fuskar jahad,dake tsaye agabanta,
"Ko kin fama ciwonki ne"?
Girgiza kai sehrish tayi alamar a'a,tukunna tace"Jahad,ina fitowa daga cikin toilet ɗinnan,naji gabana ya faɗi rass,kuma naji jikina gaba ɗaya yayi mun sanyi,bansan meya jawo hakan ba,"
"Ki cigaba da ambaton Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un acikin zuciyarki,In sha Allah babu abunda zai faru dake fa ce alkhairi,"ta ƙarasa maganar tare da janyo sehrish ɗin har izuwa gefen gadonsu ta zaunar da ita sannan tace"Ki kwantar da hankalinki,bari na ɗauko maki kayan da zaki sanya,".
Amsa mata tayi da toh,kafin ta mayar da idanunta kan farin towel ɗin dake sanye ajikinta ta ƙura mashi ido tana kallonshi zuciyarta cike fal da fargaba,ita kanta batasan dalilin faruwar hakan ba,
Jin an turo ƙopar ɗakinsu yasa tayi saurin ɗagowa don taga wanene,Hajiya azeema ce ta shigo hannunta ruƙe da shopping bag fara fuskar nan ɗauke da murmushi kamar wadda akayi ma albishir da gidan aljanna,murmushi sehrish ta saki da sauri ta miƙe tsaye tana gaisheta"Ina yini Aunty azeema,"
Bata amsa mata gaisuwar ba sae cewa tayi"me nake gani haka?Amarya sanye da towel,ko baki san cewa an ɗaura ba"?
A ruɗe sehrish tace"Aunty azeema,bangane me kike nufi ba,naji kince an ɗaura"?
dariya azeema tayi tare da cewa"su6ul da baka ne fa,Bansan ma na faɗa ba,inaso ince ko an ɗaura abincin lunch ne,ashe azmeen bata a cikin ɗakin nan,"
"Ina yini Aunty azeema,"jahad ce tayi maganar a yayin da take ƙarasowa wurinsu hannunta ruƙe da wasu riga da wando na turkey,da ta ɗaukko ma sehrish,
"Lafiya lou jahad,in ce ko ke zaki sanya waɗannan kayan na hannunki,"
Girgiza kai jahad tayi tare da nuna sehrish tace"A'a bani zan sanya ba,Sehrish na ɗauko masu don ta sanya"
Cike da Zolaya Aunty azeeema tace"kin ta6a ganin inda Amarya ta sanya waɗannan kayan a ranar ɗaurin aurenta"?
Cike da mamaki suka haɗa baki wurin cewa"AMARYA KUMA!!"?
da sauri Azeema tace"Kai,mantawa fa nakeyi,wani film na kalla yanzu,to yarinyar cikin film ɗince aka ɗaura ma aure,a yau juma'a batare da saninta ba,abunne ya tsayamun arai shiyasa nake ta sako zancen,"
Murmushi suka saki gaba ɗayansu,Jahad tace"Amma gaskiya na tausaya mata Aunty,meyasa za'ayi mata aure batare da saninta ba?To idan ita bata son Mijin da aka aura mata zata iya kashe kanta fa,'?yanayin yadda jahad tayi maganar fuskarta da alamun tausayi,
Sehrish tace"Nima abunda nakeson cewa kenan,zai iya yiwuwa akwai wanda take so,hakan ba ƙaramin illa zaiyi mata ba,"
Murmushi hajiya azeema tayi tana kallonsu,har sai da suka kai ƙarshen maganar tasu,sannan tace"kun ce wani abu anan,amma idan mijin ya kasance kamar babban yayan ku fa?kuna tunanin akwai macen da zata iya rejecting ɗin aurenshi"?
Kallon juna suka kuma yi,kafin jahad tace"Gaskiya zaiyi wuya Aunty azeema,ae babban yayanmu na daban ne shi ko acikin maza,zan iya cewa ma duk macen da ta mallake shi ba ƙaramar mai sa'a bace,ƴar baiwar ce,kuma ita jinin nasara ce,da ƙafar dama ta shigo duniya,"
Dariya sosai hajiya azeema tayi,jin yadda jahad ke zuzuta SGR,
"Duk da ance abincin wani gubar wani,Zai iya yuwuwa ita yarinyar bata ra'ayin namiji irinsa,ba wai don bai kai ba...."
Katseta hajiya azeema tayi da cewa"kamar ya kenan"?
Sehrish taci gaba da cewa"yanzu kamar ace ita yarinyar,tafi son baƙin namiji dogo,sannan wanda baya tara sumar kai,kuma tafi son namiji mai yawan fara'a a fuskar shi,ko kuma ace ita yarinyar tafi son ta auri wanda bai ruƙe da muƙamin soja,Ya abun zai kasance?zatayi farin ciki idan ta samu kamar babban yayanmu,amma ta wani 6angaren baiyi dai dai da ra'ayinta ba,"
Tana kai ƙarshen maganar,Azeema tace"kamar ke kenan!kina nufin bakison namiji kamar babban yayan ku"? Tayi tambayar cike da fargabar amsar da Sehrish zata bata,
Sunnar dakai ƙasa sehrish tayi tana wasa da yatsun hannunta,yayin da fuskarta ke ɗauke da ƙayataccen murmushi,wannan ya tabbatar mata da cewa Tana RA'AYINSA,
Dariya hajiya azeema tayi tare da ɗago da shopping bag ɗin dake hannunta ta miƙe ma sehrish,
"Wedding gown ce aciki,tare da takalmanta,Zuwa bayan la'asar,da zarar an kammala sallar,Zanzo in taimaka maki wurin sanya rigar,sannan da kaina zanyi maki kwalliya,"
A ruɗe sehrish ke kallonta don bata gane inda zancen nata ya dosa ba,ita kanta jahad abun ya ɗaure mata kai,
Ganin yadda suka saki baki suna kallonta,yasa tayi saurin cewa"Oh,na manta ban sanar daku ba,Wani wasan kwaikwayone zamu yi yau acikin gidan nan don nishadi,that's why we choose you to be our bride in the drama,"
Wani irin farin cikine ya lullu6e sehrish,cike da zumuɗi ta kar6i bag ɗin,tana fadin"Amma abun zai ƙayatar sosai,dama inason inga na sanya wedding gown,Ashe da rabon yau in sanyata,
Jahad tace"gaskiya abun zai bada citta,yau kam zamu sha hotuna,"
"Har ma video idan kunaso zaku iyayi,Ni bari na wuce kitchen wurin Azmee,".
Tana ƙoƙarin fita,ta tuna da hosana da sauri ta juyo tare da kallonsu tace"Ya jikin hosana?naga sae bacci take tayi tunda nashigo,da alama jikin yayi sauƙi kenan"?
Jahad tace"eh,taji sauƙi sosai,"
"To,ku ya jikin naku"?
"Ae mu munji sauƙi,"suka haɗa baki wurin bata amsa,
Jinjina kai tayi tare da kama hanyar fita tana cewa"Allah ya ƙaro sauƙi,"
Suka amsa mata da cewa"Ameen,"
A saman gado sehrish ta ajiye shopping bag ɗin,sannan ta kar6i kayan da jahad,ta ɗauko mata batare da 6ata lokaci ba ta zura riga da wandon ajikinta Red colour ne ba ƙaramin kyau suka yi mata