Showing 114001 words to 117000 words out of 307403 words

Chapter 39 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

taji ance"Madam,barka da warhaka"
  gabanta ne ya ɗan faɗi rass,amma ta dake tace"yawwa,dan Allah wanene ke magana,"
   "Babu bukatar ki sani,dama na kira ne don in yi aikin lada,Nasan kina ta neman hayaam ido a rufe,to hayaam dae a halin yanzu addu'arki take buƙata,idan kina son sanin inda take,yanzu zan turo maki da message na address ɗin inda take,sae ki hanzarta zuwa don ki kai mata agaji,Allah ya bata lafiya,idan ta samu ciki dan Allah a ajiyemun abuna,inaso" yana faɗin haka,yayi rejecting kiran,"
  Waro ido waje Aunty babba tayi,a hargitse ta saukko daga saman gadon hannunta riƙe da wayar,jikinta har kerma yakeyi,zarya ta shiga yi acikin ɗakin tana jiran shigowar saƙon,
  A fili tace"Allah yasa dae hayaam ba wani taje taba ma kanta ba yayi amfani da ita,Sae da naja mata kunne akan ta daina kula maza,amma da ya ke karya ce gaya nan tana son ja mun bala'e,ina zaman zaman lafiyana,"

Tana cikin wannan zullumin,taji ƙarar shigowar message da sauri ta duba top of the screen ɗin wayar,
  "Vip,Room 34,"shine abunda taga an rubuta acikin message ɗin,kuma babu numbar wanda ya tura,anyi hidden number,
   Sai da tayi zurfin tunani sannan ta gane cewa numbar ɗakin hotel ne aka turo mata,hakan na nufin cewa hayaam tana acikin hotel ɗin,
   Jiki na rawa ta ƙarasa wurin trolley ɗin kayansu dake ajiye,gefen wardrobe,buɗe wa tayi ta dauko mayafi ta lullu6a asaman kanta, 
  Sannan ta tura kopar ɗakin ta fito,tafiya takeyi cike da zullumin abunda zai biyo baya,sae bin ɗakunan dake a wurin takeyi tana bin numbobin jikinsu,cikin sa'a batare da tasha wahala ba tazo kan numbar ɗakin da aka turo mata,sae da ta duba dakyau taga Room 34 ne,Hada key aka ajiye mata ajikin ƙopar,wannan ya tabbatar mata da cewa da gangan aka sanya key ɗin,saboda in tazo ta buɗe ta shiga,
   Gabanta sae faɗuwa yakeyi,a hankali ta sanya hannunta ta ɗan murza key ɗin ɗakin ya buɗe,cike da fargaba ta tura ƙopar ɗakin a wani slow kopar ta soma buɗewa ƙiiiiiii,tun kafin ma ta sanya kafarta acikin ɗakin ta hango pant yashe a saman tiles,Rass taji gabanta ya faɗi,wani irin wahalallan yawu ta haɗiya,dakyar ta shiga cikin ɗakin,karaf Idanuwanta suka hango mata Bra din hayaam dake sagale ajikin mirror,tun daga nan tasha jinin jikinta,wurga idonta tayi gefen hagunta,Handbag ɗin hayaam ta hango yashe a kasa,da alama wurgi akayi da jakar kayan cikinta suka watse akasa,hada wayarta ma duk screen ɗin ya fashe,
..arazane Aunty babba takai idonta saman gadon,mutunne a kwance an lullu6e shi da bargo,
  A tsananin tsorace ta ƙarasa gaban gadon,sanya hannunta tayi tare da zame bargon a hankali,tana buɗe bargon da sauri ta mayar ta rufe,saboda tashin hankalin da ta gani,hannu ta aza akai ta fasa ihu tana faɗin"Nashiga uku!Wayyo Allah na,Hayaam wani marar imanin ne yayi maki wannan aika aikar!hayaam waye ya yashe ki haka!La'ila ha'illallahu muhammadur rasulillahi!Amma kowaye wannan anyi haihuwar asara,Uwarshi ta haifo mana Bala'e" ta inda take shiga bata nan take fita ba,Muryarta har shaƙewa takeyi saboda tsabar baƙin ciki,tamkar ta haɗiyi zuciya ta mutu,
..a karshe ta fashe da matsanancin kuka,tare da hayewa saman gadon,tana cigaba da sambatu,da alama ta fara zaucewa,
   "mun shiga uku mu yau,Wllh dana san haka zata faru da bamu zauna a hotel ɗin nan ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,Hayaam kowaye wannan ya gama damu,ɗan jarin da muke taƙama dashi ya kwashe komai babu,ya yashe ki,ya karya mana tattalin arziƙin da yayi mana saura,Ya takaita mu don ubanshi,wlh koma wani jarababben ne,Sae Allah ya toni asirinshi,Ni na ta6a ganin jaraba irin wannan,bai bar komai ba,yayi mata wanwar ɗan jakar uban,haihuwar asara haihuwar titi,haihuwar kwararo...."kasa ƙarasa maganar tayi,wani irin ƙululun baƙin cikine ya tokare mata maƙoshinta,nan tashiga yin kakarin amai,ta saukko daga saman gadon agalabaice ta nufi toilet ɗin cikin ɗakin ta shiga,Sosai tayi amai tamkar ƴan hanjin cikinta zasu fito waje,ta jima acikin toilet ɗin kafin ta fito,tana tafiya ƙafafunta na harɗewa,
  Fitowa tayi daga ɗakin ta koma ɗakinsu,Trolley ɗin kayansu ta buɗe,Jallabiya ta ɗaukowa hayaam tare da Mayafi,Sannan ta koma can ɗakin,taci wahala haka ta kinkimi hayaam ta shiga da ita toilet,wani wurin ma ajikinta,baya ta6uwa sae dai anje asibiti duk ya jagule babu kyan gani,hatta la66anta duk sun faffashe hada busasshen jini,nipple ɗinta na right breast kuwa,sai jini yake yi,ƙiris ya rage ya 6alle,haƙika haroon ya cutar da ita,ya zalunce ta,Da mugunta yayi mata hakan,Dama babu Imani aranshi,duk ya faffasa mata skin ɗinta da Nails ɗinshi,saboda baya yanke akaifa,doguwar ƙumba ne dashi,
  Aunty babba tasha kuka,Tuntana kukan fili har ta koma yin kukan zuciya,wanda yafi ciwo,Sai da ta nemi taimako a hotel ɗin,sannan ta samu aka ɗauki hayaam,Suka kaita wani private hospital saidai sam bata sanar dasu haƙiƙanin abunda ya sameta ba don tasan karshe reporting za'ace ayi wurin yansanda ita kuma bata son asirinsu ya tonu har abun ya kai kunnan su Ishaq,tafi son in hayaam din ta farfado ta fadi wanda yayi mata hakan don ta tabbatar ba da karfi aka jata dakin ba don wanda ya kira ta ya sanar da ita halin da take ciki har sunan hayaam din ya ambata hakan kuma na nufin ya santa ne,

 Tunda aka shiga da ita ciki,Likitoci suka taru akanta,Aunty babba na zaune zugudum saman waiting seat,tashin farko sae da suka fara kar6ar kuɗin gadon kusan Naira dubu 50,Sannan za'ayi mata aiki ciki da waje a ƙalla za'a cajesu kuɗi kusan Dubu ɗari biyar,Bayan haka akwai alluran da za'ayi mata ajikinta kuɗinsu ya kai kimanin dubu 20,
  Abun yayi matuƙar girgizata,ita babbar damuwarta,ba halin da hayaam ke ciki ba,Kuɗinsu da suke tattalawa zasu je wurin boka,Har an yashe kusan rabinsu,wasu mutanen dai ba imani aransu,ɗaya daga cikin halin ɗan adam kenan,Duk yadda take da hayaam same parents,Amma harta fara tunanin guduwa ta barta a asibitin saboda gudun kar su talauta ta,Kuma ta yanke shawarar zata yi ma Abra magana tazo su tafi wurin bokan tare da ita,Tunda ita hayaam ta gama lalacewa,babu wani amfanin da zata yi mata,ƙarshe ma taja masu asara,yini tayi a asibitin tana zirga zirga,Yayin da zuciyarta ke saƙa mata,ta gudu tabar asibitin,tun da ta samu ta biya mata kuɗin aikin Can su ƙarata,

Har wuraren ƙarfe Goma na dare,lokacin an kammala yiwa hayaam aikin,Amma bata farfaɗo ba,tsayawa Aunty babba tayi abakin ƙopar shiga ɗakin tana kallon hayaam dake kwance,hancinta na sanye da Oxygen,
  Komawa tayi saman waiting seat din,inda tabar handbag ɗinta,ɗaukar jakar tayi ta buɗe ta,biro ta curo tare da memo,aza takardar tayi saman kujerar sannan ta soma rubutu Kamar haka
  _Hayaam sae dai kiyi haƙuri,Wlh bazan iya cigaba da zama acikin asibitin nan ba,duk laifinki ne,Sai da na gargaɗeki akan karki kuskura ki ƙara kula wani ɗa namiji,amma da yake ke karyace ba'a raba ki da maza,Gashi nan kin jawowa kanki wanda yafi ƙarfinki,Ya gama dake yayi maki kankat,babu abunda yayi saura ajikinki balle har insa ran zakiyi mun amfani,Shiyasa na yanke shawarar zanyi ma Abra magana,zamuje wurin bokan tare da ita,Don bazan bari burina yaƙi cika ba har su Amani suyi nasara,In dana gode ma Allah bake kaɗai bace ƙanwar da nake da ita ba,Wlh dana ji kunya_
  Tana kammala rubuta short note ɗin,Ta ɗauki handbag ɗinta,Sannan ta shiga cikin ɗakin da aka kwantar da hayaam ɗin,A gefenta ta ajiye wasiƙar,Sannan ta curo bandir ɗin kuɗi dubu hamsin ta ajiye mata a gefenta,a hankali ta furta Allah ya baki lafiya hayaam,Idan kuma kin riga mu gidan Gaskiya,Allah ya jiƙanki da rahama,
  Tana kai ƙarshen maganar,da sauri ta juya tabar ɗakin,batare da 6ata lokaci ba,ta gudu tabar asibitin,
  Rayuwa kenan,

*Boss Bature*

   ❤🤍❤

Tunda sanyin safiya ringing ɗin wayarta ya farkar da ita daga bacci,cikin bacci takai hannu tana laluban wayar harta samu ta cafkota,janyota tayi cikin bargon tare da buɗe idanunta masu ɗauke da bacci,Sunan Mommy Azeema ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri ta miƙe daga zaune,har time ɗin doguwar rigar jiyace a jikinta pink ɗin nan,picking call ɗin tayi ta kara wayar a kunnanta,
  "Assalamu alaikum,"
On the other hand Aunty Azeema tace"Babyn Rafayet,kin tashi lafiya,"
  Murmushi sehrish ta ɗan yi tare da cewa"lafiya qalou Alhamdulillah,"
"Yawwa my Daughter,dama na kira ne about abunda ya faru a tsakaninki da Rafayet,"
  Natsuwa Sehrish tayi tana sauraronta
  Ci gaba da magana tayi,"Jiya na hana ki bashi haƙuri,Saboda nasan cewa yana cikin fushi,kuma haɗari ne ki tunkareshi a wannan lokacin,kafin nan abunda nakeso in sanar dake,duk yadda kike tunanin rafayet ba haka yake ba,mutunne shi mai ƙyanƙyami sosai,kuma yana da zuciya shiyasa a lokacin ranshi ya 6aci ne sosai,har yayi yunƙurin bugunki,kinsan in ran mutun ya 6aci zai iya aikata komai ba'a hayyacinshi ba,sae yadawo cikin hankalinshi kuma yazo yana danasani,Akwai ire irensu,Ni nasan ba ason ranshi yayi maki hakan ba,don ba halinshi bane wulaƙanta mace,Zuciya ce ta fisge shi har yayi wurgi dake,ya kuma yi yunƙurin marinki......"dakatawa ta ɗan yi da yin maganar na wani lokaci kafin ta ɗaura da cewa"Kin riga da kin faɗi abunda ke cikin ranki ba'a hayyacinki ba,ina mai tabbatar maki da cewar yanzu zai yi ƙoƙarin gyara mu'amularshi dake ne,Saboda ki daina yi mashi kallon mugu,Amma fa idan har kina son hakan ta faru dole sai kinje kin bashi haƙuri,sai daga baya na zauna nayi wani tunani,muddin baki bashi haƙuri ba,to akwai gagarumar matsala,tunda bai fara sonki ba,zai iya aikata komai daga ciki hada divorce tun kafin ma lokacin ya cika kin ga mu kuma ba haka muke so ba,Kuma idan kin bashi haƙuri ba hakan yana nufin cewa kin zubda ajinki bane,Darajarki zata ƙara daukaka a wurinshi,zai san cewa tabbas kina da hankali sosai tunda har kinsan kiyi laifi kuma ki nemi yafiya,kawai abunda nake so dake koda kinje bashi haƙuri karki nuna cewa ba'a hayyacinki kikayi maganar ba,"
  Zuru sehrish tayi tana sauraronta,hankalinta yayi mugun tashi,Shin ta yaya zata tunkari Sgr da sunan zata bashi haƙuri?
  "Aunty azeema,still akwai matsala,Babban yaya ya hanani zuwa part ɗinshi fa,saboda period ɗin da nake yi,Nasan idan ya ganni zai tuna da jinin da ya gani ajikin wandona ƙarshema yayi mun korar kare in bai bugeni ba,"muryarta tamkar zata yi kuka haka tayi maganar,
  "Kada ki damu da wannan,In sha Allah babu abunda zai faru dake,sannan idan zaki je part ɗin nashi,ki gyara jikin naki sosai,Kuma ki shafe shi da turare"
  Gyaɗa kai kawai tayi tare da cewa"Shikenan zanje in sha Allah,duk yadda mukayi dashi zan sanar maki,"
   "Okey,saina ji ki,"
Tayi rejecting kiran,Ajiye wayar sehrish tayi saman gadon,Saukkowa tayi tare da nufar toilet ta shiga,Cikin mintina tayi wanka ta fito jikinta sanye da undy taja shi saman ƙirjinta,hannunta ruƙe da Short towel,Goge ruwan jikinta tayi dashi,bayan ta kammala,ta zauna gaban mirror tana shafa body cream ɗinta,Bayan ta gama ta shafa powder afuskarta,tare da murza man baki,Comb ta ɗauka tana sharce gashin kanta,
  Turo kopar akayi,ta cikin mirror ta kalli wurin ƙopar don taga wanene,Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da plate meat balls ne aciki tare da Cup na coffee,
  "Allah yasa nawa ne,"acewar Sehrish,
  Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Naki ne mana,nayi tunanin ma baki tashi daga bacci ba," tayi maganar tare da nufar wurin mirror ɗin ta tsaya,hannu tasa ta ɗauki meat ball din guda daya tace"Buɗe bakinki in saka maki,kiji idan yayi daɗi,"
  Buɗe baki Sehrish tayi,Jahad ta tura mata shi cikin bakinta,taunarshi ta shiga yi tana jinjina kai alamar daɗinshi yana kai mata karo,
  "Baby junaid nayi mawa,Ya kika ji ɗanɗanon"?
.Sehrish tace"Bangane ba,wani junaid ɗin bayan basu nan?ko kin manta ne"?
   Jahad tace"Ae munyi waya dashi,Ya sanar dani cewa,Yau ko gobe zasu dawo,Amma basu duka ba,Shi dai yace bazai iya jure rashina ba,In ma basu dawo dashi ba,ko a ƙafa ne sai ya tako,"
..fashewa da dariya Sehrish tayi,itama jahad ɗin dariyar ce akan fuskarta,
  "Gaskiya junaid na dabanne,yaci sunanshi Romeo,ga kuma juliet ɗinshi tsaye agabana,"
  Tayi maganar tana nuna Jahad dake atsaye,
Murmushi jahad ta saki tare da cewa"Oh Ni sehrish,Wlh bansan ya zamu qare da junaid ba,idan munyi aure,Kina ganinshi ɗan ustazi ko,ba ƙaramin jarababbe bane,"
  Sehrish tace"gaskiya sai kin jure don kula da junaid ba abu bane mai sauki,a kwanakin baya can da jimawa,lokacin daya gane cewa ni mace ce,Mun ta6a yi dashi zamu haɗu a garden,Ni kuma na manta,kinsan Allah tun wurin magrib junaid ya zauna a garden ɗin nan yana jiran zuwana,maimakon da ya ji ni shiru ya dawo cikin gida,sae yaƙi shigowa saboda munyi alkawarin haɗuwa dashi,Ni kuma na manta,ɗan tahalikin nan,tsakar dare akayi ta nemanshi aka rasa,ashe yana can garden yana jirana,ga asthma ɗinshi ta tashi,da ace ban tuna ba naje wurin nan ba,da Allah kaɗae yasan abunda zai faru dashi....."
  Jin wannan maganar ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali tayi ba,
  "Kice Majnun zan aura ba Romeo ba,junaid bashi da hankali wlh,"acewar jahad,
  Sehrish tace"yana da hankali mana,Junaid yana da mutunci sosai,ya kyautatamun sosai,bazan ta6a mantawa da halaccin da yayi mun ba,ina taya ki murna jahad,idan har kika auri junaid,babu ke babu yin aikin wahala,zan so naga rayuwar aurenku,tamkar comedy haka zata kasance,Zaki samu nishaɗi sosai,"
  Ba ƙaramin farin ciki jahad taji ba,sae faman sakin murmushi takeyi,
  Hannu sehrish tasa tare da ɗaukar cup ta kaishi bakinta tana kur6ar coffee,sae da ta shanye sannan taci gaba da ɗaukar Meatballs ɗin tana jefawa a bakinta,Duk jahad na atsaye ta ruƙe mata plate ɗin,
   "ki zauna mana,ƙafafunki basu ciwo ne"?
   "A'a,So nake in koma kitchen,Ina taya Aunty azmee aikin gida ne,"
  "Hosana fa?tunda mukayi sallar Asuba,dana koma bacci ban ganta ba lokacin dana farka,"tayi maganar a yayin da takai hannu gaban mirror,ta yago tissue tana goge bakinta,
  Jahad tace"Tana a dining,kinsan ta bata gajiya da ci,Ae ina tausayin Ya Omar,Don hosana saita ƙarar mashi da duk wani tattalin arziƙin da yake dashi,Gashi don ubanta ko girki bata wani iya ba,ci kawai ta sani,"
  Dariya Sehrish tayi sosai kafin tace"Sauƙinta ma,Ya Omar mutunne mai haƙuri,Kuma yana da kyakkyawar zuciya,Shi kaɗai ne zai iya control ɗinta,Amma fa zaiyi fama wlh,"tayi maganar tare da miƙewa ta koma gaban wardrobe,
  Buɗewa tayi tana neman kayan da zata sanya ajikinta,
  Suna cikin magana,Hosana ta faɗo ɗakin tana kuka,bakinta cunkushe da Donuts,Ga wani a hannunta ta ruƙo,ɗayan hannun na ruƙe da wayarta,
  Juyowa sukayi atare suna kallonta,hankali atashe suka tunkareta har suna haɗa baki wurin cewa"Hosana,Me ya faru!me kikeyi ma kuka haka?Wani ne ya rasu"?
  Ɗaga masu kai tayi alamar eh,
Gabansu ya faɗi rass,A sukwane suka kalli juna,kafin suka mayar da idanuwansu kanta,
  "Hosana faɗamun!waye ya rasu!"jahad tayi maganar jikinta na kerma,
  Sehrish tace"ki buɗe baki kiyi mana magana,ko wani ne bashi da lafiya,"?
  Sae lokacin ta taune donut ɗin bakinta tana matsar kwalla tace"Yayi Hatsarin Mota ya mutu"!
  Kallon juna sukayi atare kafin su kuma mayar da idanuwansu kanta,arazane suka haɗa baki wurin cewa"Wa?
..cusa donut ɗin hannunta tayi acikin bakinta,Cikin shessheƙar kuka tace"wani Mai yin comedy,Yanzu nake gani acikin wayata,yayi hatsarin mota ya rasu"
  Sauke ajiyar zuciya su kayi atare,Duk atunaninsu wani ne ya rasu Cikin waɗanda suka tafi damaturu,
  "Hosana ba kuka zakiyi mashi ba,Addu'a yakamata kiyi mashi don ita yake bukata,Allah ya jiƙanshi,Ya gafarta mashi zunubban shi,Allah yasa aljanna ce makomarshi,Amma idan kikayi mashi kuka to ke ba cikakkiyar masoyiyarshi bace,"
  "Nadaina kukan,Idan nayi sallah zanyi mashi addu'a,"
   ta ƙarasa maganar,tana cigaba da taunar donut ɗin dake a bakinta,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,
  Jiki asanyaye Jahad ta koma gefen gadonsu ta zauna,Sehrish kuma ta koma wurin wadrobe ɗin,Tana ɗaukar kayan da zata sanya,
  "Hosana ta tayar mun da hankalina sosai,Jikina duk yayi sanyi,"
  "Kin gane wa take nufi ne"?sehrish tayi mata tambayar,ayayin da take zura skirt ajikinta,
  "Kamal Aboki take nufi mana,Wanda yayi wannan comedy ɗin nan,na matar soja,yana rera waƙar india shi da wani,akwae ma wani wanda yake cewa gayuna kun ga Alert,su kuma sauran sai suce a'a,kin tuna shi"?
  Shiru sehrish tayi tana ƙoƙarin tuna comedy ɗinsa,can tace"Nagane shi,ya iya comedy sosai,Na ta6a ganin video ɗinshi a wayar Amrish,dayake ita mayyar kallon Comedy ce,Ni kinsan bancika amfani da waya ba,"
   Jahad tace"naji mutuwarshi sosai,ya tsaya mun araina,rayuwar kenan kana taka Allah yana nashi,shiyasa wasu mutanen in suna aikata abunda suka ga dama har mamaki suke bani,sun manta cewa duniyar nan ba wurin zama bane,Jin daɗinta ƙalilan ne,da zarar ka mutu za'a kai ka grave ɗinka,daga kai sai Halinka,mai kyau ne ko mara kyau,idan na tuna cewa zan mutu in bar duniyar nan,ko inaso ko banso sai inji komai ya fita raina,ina rage duk wani dogon burin da nake dashi akan duniyar nan,Kuma ina ƙara kusanta kaina wurin Allah,...'
   Sehrish tace"Wata rana muma babu mu,masu karanta labarin ma babu su,Mai bada labarin ma babu ita,Allah yasa dae mu cika da kyau da imani"_
  Jahad ta amsa mata da"Ameen" sannan ta miƙe tare da nufar ƙopar fita daga ɗakin tana cewa"Ni zan wuce wurin Aunty azmee,kada mu barta da aiki ita kaɗae,"
  "Nima idan na kammala shiryawar zanzo na tayaku aikin"acewar sehrish,"
   Shaf shaf ta kammala shirya kanta,Cikin Skirt red colour,Asymmetrical Yana da baza ajikinshi,Gaban skirt ɗin bai kai bayanshi tsayi ba,yayi matuƙar yi mata kyau,Halter shirt ta sanya ajikinta white colour tayi tighting ɗinta,Red & white abun ba'a magana,Takalma ta zura a ƙafarta t-strap yana da ɗan tsini amma ba sosai ba,Launin skirt ɗinta ne,komawa tayi gaban mirror ɗin,ta ɗauki kwalbar turarenta tabi jikinta ta feshe ko'ina,saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina,bata sanya mayafi akanta ba,sai gashin kanta da yayi mata rumfa abayanta,
  Fitowa tayi daga ɗakin,ta shiga cikin palour bata samu kowa ba,Suna can cikin gidan suna gyare gyare,
  Tunda ta hau saman staircases(matattakalar bene)gabanta ya shiga faɗuwa,lokacin da ta ƙarasa part ɗin nashi bata shiga daga ciki ba,
Gabanta sae faɗuwa yake yi rass rass!leƙawa tayi ciki babu kowa Sae dae kayan abincin nan daya ci,'
Runtse idanuwanta tayi tare da ɗaga hannayenta izuwa saitin fuskarta,
"Ya Allah Kana ganin baiwarka,acikin wani hali na firgici da tsoro,Allah ka tsare ni,Wllh idan naga ya nufo ni zai bugeni,Sae in watsa da gudu,Amma takalmana masu tsini ne,kada suja inyi tuntu6e in faɗi ƙasa,"
Dakatawa tayi da yin zancen zucin nata,Sannan ta ɗan buɗe idanuwanta tana ƙara leƙa cikin palourn nashi,
Jaraba yadda zata bashi haƙuri ta shiga yi,
_babban yaya,Am sorry bazan ƙara ba,nasan nayi maka laifi,amma banyi hakan da niyyar na 6ata maka rai ba,Ba yin kaina bane,kuma ba hali na


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login