Showing 57001 words to 60000 words out of 307403 words

Chapter 20 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

da wata irin matsananciyar kasala ajikinta,ita kanta batasan lokacin da ta zagaye waist ɗinshi ba da hannayenta duka,ta ƙankame shi sosai kamar zata koma cikin cikinshi,yana jin yadda numfashinta ke fita da zafi zafi,tausasan la66anta sai gogar masa fatarsa suke,sosai sehrish ke shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi,tana jin kanta a wata irin duniya,wadda ba kalar tamu ba,just like in the dream haka take kallon lamarin,ta rasa gane wai shin SGR sosa mata kanta yake yi ko kuwa,saboda daɗin dake ratsa jikinta yafi ƙarfin a kirashi da daɗin susa kawai,tamkar zata zauce haka take ji,ga wani irin abu dake yi mata yawo a jikinta tamkar zufa,'

Duƙar da kansa ya ɗanyi tare da kai hancinsa ya cusa sa shi acikin sumar kanta,ƙamshin man da take shafama kanta ne ya daki hancinsa sosai ya shaƙe sa,lumshe idanunsa yayi tare da ɗan ware su a hankali ya buɗe su,kafin ya mayar da la66ansa asaman fatar kunnanta,tamkar mai yin whispering haka ya shiga yi mata magana"tell me What did you do in the kitchen when you entered"? Yayi maganar tare da raba jikinshi daga nata,idanunshi tamkar na mai jin bacci,
  "Cornflakes na haɗa,saboda in sha,"ta bashi amsa a yayin da idanunta ke kallon yatsun hannunta data haɗesu wuri guda tana wasa dasu,.
  "Okey,ɗaukomin cornflakes ɗin,inaso nasha nima,"
  Batare da musu ba,ta juyawa da sauri da sauri ta sauka downstairs,a nan saman table,ta ɗauko cup ɗin da ta ajiye,sannan ta dawowa upstairs ɗin ta kawo mashi,miƙa mashi tayi,ya sanya hannu tare da kar6ar kofin,spoon ɗin ya ɗauka tare da ɗan jujjuya shi,kafin ya ciko cokalin yana ƙokarin kaiwa bakinsa yaji tace"Kamar yayi yawa,'ɗan ɗagowa yayi da idanunshi ya kalli fuskarta da sauri ta kawar da nata idanun gefe,saboda taga ya ɗebo da yawa ne kuma mouth ɗinsa is too small shiyasa tayi mashi magana,a ganinta cokalin bazai iya wuce wa ba,ta cikin bakinsa,amma sai gashi ya shanye abunsa,bayan ya tauna cornflakes din,ya ɗan dakata tare da cewa"Bana shan sugar sosai,sannan milk ɗin ma tayi yawa acikinsa,meyasa kika sanya da yawa har haka"?
. shiru tayi tana faman wurga ido,
Miƙa mata cup ɗin yayi tare da cewa"Kar6i kayan ki"hannu tasa ta kar6a,sannan tace"Zan iya tafiya,"?
  Hanya ya nuna mata tare da cewa"na ruƙe ki ne"?
  Ajiyar zuciya ta sauke,kafin ta juya da sauri da sauri ta sauka donwstairs,duk yana binta da kallo,kitchen ta shiga a tsaye ta ƙarasa shanye cornflakes din ta ajiye cup ɗin,sannan ta fito tare da kai idanunta Upstairs taga in yana nan,a tsaye ta same shi,idanunshi a lumshe,
  Juyawa tayi ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinsu,adai² corridor din ta kuma tsayawa tare da ɗan waiwayawa don taga in yana nan koya tafi,Again ta ƙara ganinshi a tsaye kuma da alama ita yake kallo,ranta ne ya bata cewar kodai tayi masa bye bye da hannunta,may be ya mayar mata da martani,
  ɗaga hannunta tayi tare dayi mashi bye bye,abun mamaki sai gashi ya ɗaga mata hannu yana yi mata bye bye din shima,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,har batasan lokacin da ta fashe da dariya ba,da gudu ta juya tare da faɗawa bedroom dinsu,
   Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya koma cikin part dinsa,bayan ya shiga bedroom ɗinsa,toilet ya fara shiga,bada jimawa ba,ya fito tare da hayewa saman shimfiɗeɗen gadonshi ya kwanta,tare da janyo pillow ya rungume shi asaman wide chest dinsa,yayin da blue eyes ɗinsa ke kallon haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakinsa,ya rasa gane meke damun shi,amma tabbas yana jin missing ɗin wani abu sosai atattare dashi,yana tsananin buƙatar wani abu,wanda baisan menene shi ba~~~~~~~
[3/19, 2:56 PM] +234 810 388 4440: *💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*





Gaba ɗaya Aunty babba idonta bai hango mata su hosana ba,kutsa kai kawai takeyi cikin falon,hafsat dai tana la6e a bayanta,cike da fargaba,
Ƙarasawa sukayi wurinsu,daga bayansu Sehrish suka tsaya,hakan yasa bata samu damar ganin fuskokinsu ba,sai faman washe baki take yi,gaishe dasu Abba suka farayi,fuskar kowannansu awashe,"Ishaq shine baka sanar dani zuwansu ba,"acewar Abba,General ishaq yace"Ni kaina bansan sun karaso ba,nadaisan munyi dasu kan cewa zasu taho,"
Abusufyan yace"masha Allah hafsat ta girma sosai,ba don ina ganin hoton ta ba,da bazan iya gane ta ba,
  Sunnar da kai ƙasa hafsat tayi tana murmushi ƙasa ƙasa,yayin da zuciyarta ke a cunkushe,
  duk su hosana basu ɗauki muryarta ba,amma da zarar tayi magana sai sunji tamkar sun ta6a jin muryar matar dake magana,
    "Muna taya ka murna Abusufyan,ƴa'ƴa har ƴan uku Allah ya albarkaci rayuwarsu,Alla ya.........'bata ƙarasa maganar ba sakamakon juyowar da sehrish tayi,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake daram!!!dararam!!!yadda kasan ana buga ganga,Saboda tsabar kiɗima bata san lokacin da ta furta"Kutumar Uba...."gaba ɗaya hankalin kowa ya dawo kanta,jin ashar ɗin data buga,Hakan yasa Jahad da Hosana juyowa atare,Waro ido waje tayi hankalinta a matuƙar tashe,lokaci guda duk tabi ta gigice ta ruɗe ta rikice ta fita hayyacinta abunda batayi tsammani ba,la66anta har kerma sukeyi wurin nuna su da hannu tana ƙoƙarin tayi magana amma kermar da bakinta keyi ya hanata cewa komai,
  Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin matar da ta azabtar da rayuwarsu,ta ƙuntata masu ta kusa halakasu,hosana kuwa a matuƙar tsorace ta faɗa bayan Marshal Omar ta ƙanƙame shi tana faɗin"Ya Omar,bansan ganinta,tsoranta nake ji,itace matar da ta azabtar da rayuwarmu,itace tasa aje a jefar damu cikin daji,har wannan tsohon mutumin ya kusa cutar dani,don Allah ya Omar ku kureta,azzaluma ce macuciya ce,bata tsoran Allah,bata da tausayi kuma bata da Imani,
Hankalin kowa dake a wurin ya dawo kansu,gaba daya Abba dasu Abusufyan da sauran mutanen dake a wurin duk sun ruɗe sun gaza gane inda zancen nata ya dosa,Ishaq kuwa tun da yaga jikin Aunty babba na kerma,zufa na keto mata,ranshi ya bashi cewar tabbas ta aikata wani abu ne,saboda yasan halinta,muguwace kuma bata da gaskiya,Bashi ba hatta Marshal jikinshi yayi mugun sanyi,musamman da yaji hosana na fadin ta cutar da rayuwarsu nan ya fara tunanin Wasu abubuwa da yake zargi a lokacin baya,da kuma maganar da major ya ta6a sanar dashi na cewar baya son ya shiga tsakaninshi da matar Yayan shi,
hannu Aunty babba ta aza akanta tana faɗin"Shikenan An yanka ta tashi,amaimakon ta mutu,nashiga ukku ni laila,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wani tsautsayi ne da ƙaddara suka kawo ni gidan nan,'
Tunda Abbansu junaid yaji hakan yasan cewa tabbas akwai wani abu daya ta6a faruwa a tsakaninsu,koma dae menene bai kamata,su tuhumeta ba agaban ƙannen mijinta,a bainar jama'a kuma,ko ba komai Matar babban yayansu ce,
  "Ya Omar dan Allah,tabar wurin nan wlh bansan ganinta,kashe mu take son yi,shiyasa ta biyo mu har nan,"gaba ɗaya kukan hosana ya cika kunnuwansu,'
  Wani irin wahalallan yawu Aunty babba tazo haɗiyewa,nan take ta yanke jiki a wurin ta faɗi asume,da sauri hafsat ta tsugunna tare da tallabo ta,tana jijjjigata,

Gaba ɗaya duk sun kashe ma ishaq baki yama rasa abun cewa,tsananin baƙin ciki da takaici ya hanashi cewa uffan,jikinshi sae faman tsuma yake yi,burinshi kawai yaji abunda suka aikata ma yaran,da har suka tsorata da ganinsu,tabbas sai sunci Ubansu,muddin yaji wani da ba dai dai ba,don bazai yarda suja mashi tozarta ba a idon ƴan uwanshi,

Aunty Azmee ce ta taimaka wurin ɗebo ruwa suka yayyafa ma Aunty babba a fuskarta,ae tana farfaɗowa kamar wata zautacciya tayi zumbur ta miƙe,ko waiwayonsu ba tayi ba,ta watsa aguje,tayi cikin gidan,Allah kaɗae yasan inda ta kutsa kanta,

A fusace General ishaq zai bi bayanta,Abbansu junaid yayi saurin ruƙo hannunshi tare da cewa"kada ka bita,yakamata mubi komai a sannu,yanzu bamu kaɗai bane a wurin nan ba,akwai ƙannenka kuma akwai bare a wurin nan,"
  Jinjina kanshi kawai yayi ba don ya haƙuri ba,
  Batare da sanin kowa ba,hafsat ta zame jiki daga wurin,saboda wani irin mugun kallo da taga Daddynta nayi mata,bashi kaɗae ba hatta Marshal kallon tuhuma yake yi mata,hakan ne yasata ta sulale tabar wurin,sauƙinta ma basu ambaci sunanta ba,amma tasan dole sunanta ya fito aciki,kuma daddynta in ya tashi yanke hukunci hada ita zai haɗa ya yanke mawa,tabbas tayi dana sanin biye ma mahaifiyarta wurin cutar dasu hosana,gayanan sunja ma kansu,
  Ruƙo hannun hosana yayi tare da janyota,ta dawo ta gabanshi,fuskarnan tayi jawur,sae faman kuka takeyi tana faɗin"ya Omar a koreta tabar gidan nan,bana son ganinta,bata da Imani,itace ta rufe mu acikin store tayi mana horon yunwa,ta dinga bugunmu da bulala,kuma ta dinga samu aiki,har gadon asibiti sai da aka kwantar dani.......'
Cikin sauri Omar ya sanya tafin hannunshi ya toshe mata baki,cikin lallashi yace"its ok hosana,na fahimce ki,zansa sojoji su koreta daga gidan nan hakan yayi maki,"
  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan yace"kada na sake jin kukan ki to,ya isa haka,kalli fa ki gani duk kin 6ata kwalliyarki da hawaye,"
  Curo handkerchief Abusufyan yayi daga gaban aljihunsa,ya ruƙo hosana,tare da sanyashi a fuskarta yana goge mata hawayenta,"Daddy matar can bata da Imani ko kaɗan,taso ta kashe ni,dan Allah ku sakar mata karnuka su rakata bakin gate,tabar gidan nan,"
  Muryar abusufyan tamkar zaiyi kuka yace"Kiyi haƙuri kinji hosanata,zansa a koreta kamar yadda kikeso,amma yanzu kiyi shiru da bakinki,ki daina magana,banason ganin hawayenki,"
  "Daddy bakasan yadda nakeji bane,zuciyata tafarfasa takeyi,raɗaɗi takeyi mun kamar ana rura garwashin wuta acikinta,wlh daddy waccen matar bazata ga Manzon Allah ba,sai ta shiga wuta,'
Hankali atashe Marshal ya daka mata tsawa har saida ta dawo cikin hayyacinta,fuskarshi a daure yace"kar na sake jin kince uffan a wurin nan,surutun ya isa haka!banace za'a kore ta ba,"
  Saboda tsoratar da tayi da tsawar da yayi mata ne yasa ta faɗa jikin daddyn nasu ta ƙankameshi,tana faman sauke ajiyar zuciya,'
  jikin kowa yayi sanyi,musamman Ishaq,bawan Allah duk yabi ya takure kansa,idanunshi sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,
   Abba ne yayi ƙoƙari wurin dawo dasu daidai daga yanayin da suka shiga,daƙyar aka samu hosana ta zauna itama amma duk da haka tana yawan firgita wannan ya ƙara tabbatar masu da cewa ba ƙaramin Abu Aunty laila ta aikata masu ba,wuri kowa ya samu ya zauna agaban table ɗin dake a wurin wanda ke shaqe da abinci kala kala,nan fa kowa ya shiga bama cikinsa abinci,jikin Sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ta gane dalilin dayasa su jahad suka tsorata da ganin matar,wato itace matar da Omar ya kaisu gidanta,wadda ta azabtar da rayuwarsu,kamar yadda jahad ta bata labarinta,kowa ya lura da yanayin yaran,sun kasa sakewa suci abinci sosai,ƙarshe sai dae Abusufyan ya dinga binsu one by one yana sanya masu abinci abakinsu suna ci,a haka har ya samu suka ci sosai,bayan sun kammala cin abincin,Junaid ya ɗaukko Camera ɗinsa,nan fa aka shiga ɗaukar hotuna,abun gwanin burgewa,Happy family,kowa sai da ya fito Hajiya azeema,su gwaggon katsina Saude,Dr harris,hatta ƴan matan da hajiya sarah tazo dasu,sae da suka fito akayi masu hotuna,mutun uku ne kawai babu a wurin Ammi wadda kowa ke fargabar fitowarta,bayan ita sae Haroon wanda ke ƙumshe acikin ɗakinsa,Sgr kuwa baya cikin gidan,tun wuraren ƙarfe uku yabar gidan,
  Anyi masu hoto tare da mahaifinsu sun sanyashi atsakiya,sae wanda akayi masu tare da Abbansu junaid tare dashi kanshi junaid ɗin,kowa saida yayi hoto tare dasu,hatta Su twins da fawan dasu irfan,kowannansu sae da yayi hoto dasu,sun sha hotuna ba ƙadan ba,

Basu suka kammala ba sae wuraren sallar magrib,sannan kowa ya shige ciki domin yin alwala,

Kamar jira jahad takeyi su shiga ɗaki ta rufe hosana da faɗa,tamkar zata bugeta,"Sai yanzu na tabbatar da cewar ke cikakkar zararriyace baki da hankali,meyasa ba zakiyi shiru da bakin ki ba?don me zaki tona mata asiri agaban mutane"?
Fashewa da kuka hosana tayi tana faɗin"kada ki ƙara cemun zararriya,kuma naje na tona mata asirin,Ni bazan ta6a yafe mata ba wlh,kamar yadda ta cutar da rayuwarmu itama sai ta fuskanci sakamakon abunda ta aikata mana,'
"Hosana,karna sake jin kin tada wannan maganar,idan ba so kike ranki ya 6aci ba,"
  "Wlh saina faɗima Daddy da Abba,kuma saina faɗa ma yaya Omar,sai dai duk abunda zai faru ya faru,'
  rai a6ace tayi maganar,cakumar rigarta jahad tayi,tare da yin wurgi da ita,ta faɗa saman gadon tana kuka,fitowa Sehrish tayi daga cikin toilet,ganin jahad na ƙoƙarin bugun hosana yasa tayi saurin zuwa tare da ruƙo hannunta"karki kuskura kice zaki hukunta hosana!abunda tayi dai dai ne,koda ace ita bata faɗa masu ba,to ni saina faɗa masu abunda waccan matar ta aikata maku,saboda bata da Imani,muguwace ita,muddin akace za'a cigaba da yafe ma mutane irinta to tabbas bazasu ta6a canza halinsu ba!Suna buƙatar a ladabtar dasu,a hukuntasu,idan suka aikata ba dai dai ba,Ni hakan da hosana tayi ta burgeni,!"
  Shiru jahad tayi,ta wani 6angaren zancen sehrish gaskiya ne,muddin ba'a ɗauki mataki ba akanta taga an ƙyaleta to tabbas bazata ta6a canzawa ba,amma yanzu idan suka hukunta ta dole nan gaba taji shakkar ƙara yin irin kuskuren da tayi abaya,
 
"Kin faɗi gaskiya sehrish,ni banyi tunanin hakan ba,kuma koda nake yi ma hosana faɗa,saboda 6arin zancen da tayi ne agaban mutane,bai kamata ta yi magana akan idon kowa ba,in ma faɗin ne Ya Omar yakamata ta sanar mawa,sae su yanke mata hukuncin da suka ga ya dace da ita,"
Ta ƙarasa maganar tare da ɗauke idonta daga kan sehrish ta mayar dasu kan hosana dake baje saman gadon tana kuka,nan take taji bata kyauta mata ba,hawa saman gadon tayi tare da janyota jikinta,tana lallashinta,daƙyar ta samu tayi shiru,daga bisani suka tashi domin yin sallar magrib,

*Aunty Babba*

Tunda ta watsa a gujen nan,ɗakin hayaam ta faɗa,jikinta sae faman rawa yakeyi,zagaye tashiga yi a ɗakin tana tunanin hanyar da zata bi ta gudu daga cikin gidan tun kafin ishaq ya waiwayeta,tsoranta karya bata takardar saki,don bata shirya yin zawarci ba,hannu ta aza aka tana fadin"Nashiga uku ni laila,na jama kaina masifa da bala'e,Ina zan tsoma raina inji daɗi,"tana cikin zancen zucin nan,hafsat ta shigo ɗakin,kamar jira takeyi nan ta shiga balbaleta da faɗa ta inda take shiga bata nan take fita ba,
"Don ubanki ki faɗa mun taya akai yaran nan suka rayu!nasan kinsan komai munafuka algunguma!"hafsat na ƙokarin buɗe baki,Aunty babba takai mata naushi a kumatunta,har sai da le6enta ya ɗan fashe,idonta jawur ta ɗago tare da kallon Mommyn nata idanunta cike taf da hawaye tace"Mommy!ni kika buga saboda zunubin da bani na aikata ba?
A faɗace Aunty babba tace"Zanci ubanki ko ki rufe mun baki,wlh hafsat kin cuce ni!Allah ya isa tsakanina dake!ae kinsan da zaman yaran nan acikin gidan nan, shiyasa don munafunci kika sanyo nikabi uban meyasa baki sanar dani ba tuntuni don inyi takaina!Kece kika tseratar dasu daga hannun baba alamu,in ba haka ba taya akai har suka kawo kansu cikin gidan nan"!?
Girgiza kai hafsat ta shiga yi yayin da idanunta ke fitar da wasu irin hawaye masu ɗumi,cikin shessheƙar kuka tace"banta6a dana sanin kasancewarki mahaifiyata ba sai yau!Kin jefani acikin masifa kin kuma zo kina neman ƙala mun sharrin cewa ni na tseratar dasu daga hannunshi,wlh Mommy bakiyi ba!duk wasu magayen ɗabi'u da halayen dana ɗauko naki ne,baki ta6a cemun nayi badai dai ba,baki bani tarbiya mai kyau ba,kullum gur6atamun tunani na kikeyi,saboda kar in dauko halayyar mahaifina,Ni banta6a ganin uwa irinki ba,Yanzu gashi nan daga ni harke wa gari ya waya?kuma inaso ki sani mommy,Ni bansan komai agame dasu hosana ba,bansan ya akai suka dawo hannun Ya Omar ba,Na faɗa maki hakan ne ba don ina jin tsoranki ba,sai don kisan cewar Bani na aikata hakan ba,Allah ne Ya Kamaki,ba yadda banyi ba don ki kyale yaran nan karki salwantar da rayuwarsu kika ki,kuma ni ce da hannuna na goge hotunan da hayaam ta tura maki a wayarki,saboda nafi son ki tako da ƙafafunki don ki gir6i abunda kika shuka......"
..saboda tsabar tsuma jikinta har kerma yakeyi,shaƙo wuyan rigar hafsat tayi da ƙarfin gaske,gadan gadan kasheta zatayi,kiciniyar kwace wa hafsat tashiga yi,suna cikin wannan halin,Amani da hayaam suka faɗo cikin ɗakin da gudun gaske sukayi kansu,daƙyar suka kwaci hafsat daga hannun Aunty babba,dafe maƙoshinta tayi tana faman yarfa hannu tana ambaton"ruwa!ruwa'
Da sauri hayaam ta fita waje,sai gata ta dawo da bottle water a hannunta mai sanyi,miƙa ma Hafsat ruwan tayi,jiki na rawa ta cire marfin robar tare da yin wurgi dashi,ta kafa robar abakinta tana kwankwaɗar ruwan,hayaam ce ta zauna a wurinta,tana lallashinta,
Rai amatuƙar 6ace tashiga fadin"ae da kun barni na kasheta don ubanta,wlh hafsat baƙin cikinki bazai ta6a kashe ni ba,Muguwa kawai,nafi kowa dana sanin haihuwarki,Ni ina kokwanton cewar Anya ba'a asibiti akayimun musanyarki ba,"
Fashewa da dariya Amani tayi tana tafa hannayenta,
Nan take Aunty babba ta ɗaure fuska,tana jifarta da harara,
Tsagaitawa tayi daga yin dariyar da takeyi masu sannan tace"Wannan abun daya faru nafi kowa farin cikinsa,tamkar na zuba ruwa a ƙasa na sha,"
"Amani baki da hankaline?kinsan me kike faɗi kuwa?wannan abun fa ya shafi kowannanmu,bai kamata ki dinga yi mana dariya ba,"Acewar Aunty babba,
wurga mata harara amani tayi tare da cewa"yadai shafe ku!karki kuskura ki ƙara mentioning ɗina aciki,domin kuwa bansan anyi ba,lokacin da kuka tsara muguntarku kuka cutar dasu,kunyi shawara dani ne?Kuma ae har shawara saida na baki akan ki daina azabtar da yaran amma kika ƙi ji ke ga shugabar azzalumai,wlh baku da imani zuciyarku ta bushe,kwakwalwarku a toshe take,tamkar ana zuba maku dussa acikin kawunanku saboda ɗabi'unku sak irin na kafuran farko ne,....."
Waro ido waje Aunty babba tayi tare da faɗin"Ni kike faɗama wannan maganar!"
Amani tace"Kwarai kuwa dake nake,Muguwa macuciya kuma Azzaluma,zuciyarku ta ƙeƙashe Zalunci kawai kuka sa agaba,daku da uwarku Mammy,tsohuwar banza me shegen son kuɗin tsiya,wlh kunji haushin rayuwarku,shegen kwaɗayin abun duniya,ga baƙar zuciya,ga dogon burin tsiya ko tsoran mutuwa bakwayi..."
Tunkan amani ta ƙarasa maganar Aunty babba ta kwashe ta da tagwayen maruka,ji kake tasss tatasss!'kafin Aunty babba ta janye hannunta daga kan kuncin Amani,itama ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe ta kikkifa mata maruka a jere kusan uku ji kake fass tasss taaasss!
dafe kumatu aunty babba tayi yayin da idanunta sukayi jawur,tunda take arayuwarta ba'a ta6a yi mata irin marin da Amani tayi mata ba,hasalima Amani shakkarta take ji,amma sai gashi yau ta cire yatsunta guda biyar cuf,ta kikkifa mata maruka,
Koda ganin haka,sae hayaam ta miƙe tare da ɗaga hannu zata sharara ma Amani mari,aikuwa hafsat ta yunkura tare da miƙewa ta damƙo hannun hayaam tana faɗin"baki da hankaline?matar da ta iya ɗaga hannu ta mari mommy har sau uku,itace zaki mara?kina tunanin cewa zaki


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login