Showing 222001 words to 225000 words out of 307403 words

Chapter 75 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

ne yace"don Allah Aunty kidaina,kina ƙara tayar masu da hankalinsu,keda yakamata ace kina lallashinsu,"hannu tasa tana share hawayen fuskarta,juriyarce bazata iya ba,ita kaɗai tasan yarda take ji acikin zuciyarta,

Fitowa Doctor emran yayi daga cikin ɗakin da aka kwantar da Abbansu,Aikuwa da sauri suka tunkareshi,kowa yana tambayar ya jikin nashi,
  "Ku kwantar da hankalinku,Yana samun sauƙi,Addu'ar ku kawai yake buƙata,"yakai ƙarshen maganar tare da aza idanuwanshi kansu Sgr da Marshal"ina son ganinku a office,"
  Tunda suka ji haka sai jikinsu ya ƙara yin lakwas,gaba Dr emran Yayi suka bi bayanshi,har izuwa Office ɗinshi,Wuri ya samu ya zauna,kafin suma suka zauna suna fuskantarshi,
  A tsanake ya soma yi masu bayani"nasan kunsan meke damun mahaifinku,damuwa ce akan rashin Junaid,Yanzu haka dana baro ɗakin,Sambatu yake yi yana ambaton sunan shi,"dakatawa ya ɗan yi da bayani yana kallonsu,jikinsu sai tsuma Yake yi,
  "Jinin shi ne ya hau sosae,Ga kuma Ciwon zuciya dake barazanar kamashi..."
  Tunkan emran yakai ƙarshen maganar,Omar ya dafe kai jikinshi na kerma,jikinsu Ya gama mutuwa,
  "Yanzu ya zamuyi kenan?menene solution"?Sgr ne yayi tambayar,
  "Akwai matsala fa,saboda ya ƙwallafa ranshi akan son yaron,Idan har ba ganinshi Yayi ba,tofa sai dai abishi da addu'a,"
  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un"miƙewa Sgr yayi da sauri ya fice daga Office ɗin,gaba ɗaya sun rasa inda zasu tsoma ransu suji daɗi,

Miƙewa Sehrish tayi daga zuƙunnan da take abakin ƙopar palourn,Hannu ta zura acikin aljihun rigarta,ta curo wayarta don ta kira Jahad taji Ya jikin Abban nasu,
  Tana kunna wayar,ta shiga Call log anan ta samu missed calls da baƙuwar number,har kusan sau 10 aka kira,Batasan number ɗin wanene ba,Har jaraba kiran Layin tayi wayar nata ringing ba'a ɗaga ba,
  Bayan kiran ya katse ne,ta lura da message ɗin da aka turo mata,Da sauri ta buɗe saƙon ta soma karanta shi kamar haka,
__Sehrish na kira layinki baki ɗaga ba,Amrish ce inason magana dake game da ɗan uwan nan naki,dan Allah idan kinga saƙon nan ki kira ni_
  Abun ya ɗaure mata kai,tunani ta shiga yi wani ɗan uwanta ne Amrish ke magana akai,sake kiran Layin tayi wayar ta dinga ringing amma ba'a ɗaga ba,
  Katse kiran tayi,tana ƙoƙarin juyawa ta koma cikin gidan kira ya shigo layinta da baƙuwar number,da sauri ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta,tunkafin tayi sallama muryar Amrish ta katse mata hanzarinta,
  "Sehrish kina ina ne!ina ta kiran Layin wayarki amma baki ɗaga ba,magana ce akan Junaid na tura maki Address ta message,kibar komai kikeyi kizo ki same mu"tana kai ƙarshen maganar ta katse kiran,
  Wani irin faɗuwar gaba Sehrish taji,Abun ya matukar ɗaure mata kai,musamman data ambaci sunan Junaid,
 
Hannunta na kerma ta shiga duba message ɗin da aka turo mata,kwatancen inda zata same su ne,

Tarasa ya zatayi,ita dai ba mota gareta ba,gashi babu wanda ya rage acikin gidan balle ya kaita,kama hanya tayi ta miƙi titin da zai sadaka da babban gate ɗin gidan,Sae faman zumbula sauri take yi,Sai da tasha wahalar zuwa babban gate ɗin,Sojojin dake tsaron gidan suka hanata fita,kamar ta fashe da kuka,

A dole ta shiga kiran layin matasan gidan,Duk wanda ta kira bai ɗagawa,har Abusufyan ta kira shima bai ɗaga kiran ba,
 
Sai da ƙyar ta samu Hosana ta ɗaga kiranta,da sauri ta kara wayar a kunnanta,
  "Hosana Ya jikin Abban"?
  "Nima bansani ba,Sun shiga dashi ciki,"
  "Dan Allah idan akwai wani kusa ki bashi wayar,"
  "To"ta amsa mata,jim kaɗan taji muryar Kanal yousouf,
  Sai da ta fara tambayarshi jikin Abban nasu,Ya sanar da ita cewa da sauki,tukunna tace"Gani nan zan fito gida an hanani,dan Allah ka taimaka kasa su barni na fita,nima asibitin zanzo,"
"Ki basu wayar,"Cire wayar tayi daga kunnanta ta miƙa ma ɗaya daga cikin sojojin,ya kar6a su kayi magana dashi sannan ya miƙa mata wayar,"Zaki iya tafiya,amma yace kada abarki ki fita ke kaɗai,don haka wani daga cikinmu zai ɗaukeki a mota ku fita,"
  Ba ƙaramin daɗi taji ba,dama ƙarfin hali ne kawai,ko kuɗin abun hawa bata dashi,

Anan ta tsaya,wani sergeant ya ɗauko mota ta buɗe ta shiga ciki ya tashi motar,saida suka hau saman titi sannan yace"Madam ina zuwa"?
  Karanto mashi Address ɗin wurin tayi kamar yadda Amrish ta rubuto mata a saƙon,

Wani private hospital ne suka shiga,sojan ya fito ya buɗe mata ƙopa ta fito daga ciki,a bakin ƙopar shiga ciki ta samu Amrish a tsaye hannunta ruƙe da waya,wani irin farin ciki ne ya lullu6e Sehrish da gudun gaske ta nufeta,rungume juna sukayi nan take Amrish ta fashe da kuka,
  Ɗago da ita Sehrish tayi tana tambayarta lafiya,
  "Amrish dama kina nan?layinki kona kira bana samu,meya sameki ne?me kike yi a asibitin nan ne"?
  Cikin shessheƙar kuka Amrish tace"mu shiga daga ciki ki gane ma idanuwanki,"
  Ta ƙarasa maganar tare da janyo hannun Sehrish suka shiga asibitin,A A&E aka kwantar dashi,a bakin ƙopar ɗakin Sukayi kici6us da Ya Mu'allim malamin da take ta nema,
  Cike da mamaki ta ambaci sunanshi"Ya mu'allim,"fuskarshi da alamun damuwa atare da ita,Ya amsa mata"Na'am,kina ta nemana ko"?
Jinjina mashi kai tayi alamar eh
  "Naga saƙon da kika turomin,idan muka samu natsuwa zamuyi magana,Yanzu dai ga ɗan uwanki can kije ki duba jikinshi,"
  Gabanta ne ya faɗi rasss!,kawar da idanuwanta tayi daga kallon fuskar Ya mu'allim ta mayar da idanuwanta kan ƙopar ɗakin,mutun ta hango kwance an sanya mashi oxygen a hancinshi,yayin da hannunshi ke sanye da robar ƙarin jini,zuciyarta na harbawa a haka ta nufi cikin ɗakin,lokacin data ƙarasa gaban gadon tayi arba da fuskar Junaid,Sai ta yanke jiki ta faɗi a sume.......


Shigowa Cikin ɗakin Ya mu'allim yayi tare da Amrish,ruwan dake ajiye saman drawer din dake gefen gadon Ya ɗauka,Ya cire murfin ya tarfa ruwan a tafin hannunshi Ya watsa mata akan fuskarta,Nan take ta farfaɗo tana faman Sauke ajiyar zuciya,Yayin da take ambaton Sunan Junaid abakinta,Miƙawa tayi agaban gadon ta zube saman guiwowinta,kamar a mafarki haka take ganin Junaid,bazata Iya jurewa ba,fashewa tayi da matsanancin kuka yayin da take kallonshi,Dama sai da ranta ya bata cewa Junaid bai mutu ba,Yana araye,Ashe dagaske ne,tasha kuka ta gode ma Allah,Cikin shessheƙar kuka ta soma magana tana kallon Ya mu'alim da amrish dake a tsaye,
"Taya akai junaid daya mutu ya dawo?a ina kuka same shi,A iya saninmu junaid yayi hatsarin mota Ya ƙone ƙurmus"
  Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim da Amrish suka kalli Junaid,har suna haɗa baki wurin cewa"Junaid Yayi hatsarin mota'?
  Jinjina kai Sehrish tayi"Babbar motace tabi takan Motarsu,Wuta ta kamaci,ba'a samu komai daga sassan jikinshi ba,wannan Shi ne abunda muka sani a game dashi....."tana kuka ta Zayyana masu Komai daya faru har 6oye mutuwar junaid dasu Marshal Su kayi,Da kuma Halin da abbansu ke ciki na rashinsa,. 
  Amrish tasha kuka hada majina,Shi kanshi Ya mu'allim jurewa kawai yake yi,rashin imanin Yayi yawa
  "In sha Allah komai Yazo ƙarshe,duk wanda keda sa hannu a wurin cutar da family ɗinku,Zai gane kuskurenshi,don wannan karan da shirina nazo,"Babu wasa a fuskarshi yayi maganar,
  "Dan Allah ku faɗamun ya akai kuka samu junaid"?tayi maganar yayin da take share hawayen fuskarta,
  Anan Amrish ta kwashe dukkan abunda Ya faru daga farko har ƙarshe

Miƙewa Sehrish tayi tana kuka,Ta rungume amrish tana Yi mata godiya,bawan Allah ashe shine Yake tura mana saƙo da layinki,muka kasa gane wanene,da yake ni ina da numberki,Shiyasa saƙon Ya bayyana da sunanki,nayi tunanin ko kin yada wayarki ne,Ashe junaid ne ya ɗauketa,Bawan Allah,wlh da ace zan iya mayar da ciwonshi jikina da nayi hakan,junaid bai ta6a shan wahala rayuwarba,Sae wannan karan da ƙaddara ta rutsa shi....."
  "Mu gode ma Allah junaid yana raye,duk yarda suka so su cutar dashi,basu ci nasara akanshi ba,domin kuwa junaid kainuwa ne dashen Allah,badai mutun ba,lokacin da muka kawo shi asibitin nan,jinin jikinshi Yayi ƙanƙanta,cikin sa'a likita ya gwada jinina,kuma aka dace yayi dai dai da nashi,gashi nan ana ƙara mashi,Amma yana bukatar jini sosai,"

*ƙarin Bayani*

Abunda ya faru lokacin da Sehrish ta tura saƙonnin nan cike da saran Ya mu'allim zai gani,malaman da ta tura ma saƙon daga ciki akwai numbar Ya mu'alim,Yaga Saƙonta saƙonta sai kuma Aka kirashi a waya ana sanar dashi cewa ɗalibarsa na nemanshi,Sauran malaman data tura ma sakone suka sanar dashi,An turo masu saƙo ana nemanshi,Wannan dalilin ne yasa Ya mu'alimm Ya shirya zuwa gidan,tun lokacin baya ya ta6a zuwa gidan security guards ɗin gidan suka hanashi wuce wa,baisamu shiga ba a wannan lokacin,Sai yau daya samu saƙonnin nemanshi da sehrish keyi,Shi ne ya yanke shawarar Ya fara zuwa gidansu Amrish don tayi mashi jagora zuwa gidansu sehrish ɗin su tafi atare,Da yake ya ta6a zuwa gidansu Amrish lokacin da tayi jinya,kuma cikin sa'a ya zo adaidai lokacin da suke buƙatar taimako,Kunji yarda akai Allah ya hadasu dashi Har ya ɗauke su,

Saboda halin da Abban junaid ke ciki,Ya mu'allim Ya basu shawarar su ɗauki junaid su koma dashi Can Sgr hospital ɗin,Don A haɗashi da mahaifinshi in yaso sai acigaba da jinyarshi acan asibitin,Sai da suka tsaya Jinin ya ƙare sannan Likita ya sallamesu,Suka ɗauke shi a back seat ɗin motar Ya mu'alim Aka shigar da junaid,Sehrish ta shiga ta ruƙoshi ajikinta,bawan Allah ya zama tamkar lagwanin filita jikin sae kerma Yake yi sam baya acikin hayyacinshi,Mazaunin driver Ya mu'allim Ya shiga,Amrish ta zauna gefenshi,Ya tashi motar,a tsanake yake driving ɗinsu,Amrish sae faman zabga murmushi take yi,burinta Ya cika,junaid zai koma wurin ƴan uwanshi,Sehrish kuwa ba'a magana,Bakinta yaƙi rufuwa,Kamar wadda akayi ma Albishir da gidan Aljanna,Tsabar farin ciki ne kawai,Ta ƙankame junaid ajikinta kamar ta mayar dashi cikin cikinta,Saboda tsabar ƙaunar da take yi ma ɗan uwanta,A ranta tana ayyana irin farin cikin dasu Babban Yaya zasu yi idan suka ga junaid bai mutu ba,

Slowly motarsu ta ƙaraso cikin katafaren asibitin SGR................




*dakwai yiyuwar littafin Abban Sojoji yakai farkon march,Ba kamar yarda nace ba ƙarshen February,Amma idan kuna son ayi maku after 3 years,kuyi mun magana,sai mu katse shi,ra'ayinku nakeson ji,littafin yazo ƙarshe masu tunanin zai kai azumi,Aniyarku tabi ku😂*

*masu son karanta Littafin Abban Sojoji su tuntu6i layina,Message za'a tura mun ta whatsapp banda phone call*



 
 [3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋





𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤
𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠

*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*








Members na paid group ɗina Am really Sorry🙏masu cewa ko naje wurin za6e na gaji shiyasa banyi posting ba,Boss ko Voters card bata dashi🤣




Acan cikin asibitin kuwa,Suna cikin matsanancin tashin hankali,Jikin Abba Yayi tsauri sosai sam bai kar6ar treatment din da ake basa,Zuciyarshi tana barazanar bugawa,Kowa yayi zugudum cike da jimami suna jiran Tsammani,Sgr da Omar Sunfi kowa shiga matsananciyar damuwa,Saboda suna ganin sune silar Halin da Abbansu Yake ciki,

Tunda suka fito daga Office ɗin Doctor Emran,a tsaye suke sun jingina bayansu da wall,Sgr Ya goya hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuciyarshi sai tafarfasa take yi,wani irin bugun zuciya yake ji,Omar kuwa idanuwanshi na kallon Ceiling,tsantsar damuwa ce akan fuskarshi,

Mommy tuni ta jima da kifa kanta saman cinyoyinta,tayi kukan harta gaji tayi shiru,Abu na zaune a gefenta,Yayin da Jahad ta kwantar da kanta saman kafadar Oummansu,idanuwanta a lumshe,Hosana na kwance saman cinyoyin Jahad,ta ɗan aza kanta saboda baccin da take ji,

Su fawan kuwa,Duk sun rufe idanuwansu yayin da kwalla ke zuba,Abusufyan dae Ya gaza samun natsuwa Sae faman safa da marya yake Yi a tsakanin Corridor ɗin dakin da Abban yake,

Dirar Motarsu Sehrish keda Wuya,Motar Sergeant ɗin daya ɗaukota daga gida ta faɗo asibitin dama Yana biye dasu,A bayan motarsu yai Parking ɗin tashi,Fitowa Sergeant ɗin Yayi,Sae ga Baba maigadi ya fito daga back seat na motar,Ashe lokacin da suka barshi acan asibitin,Masallaci Yaje don Yayi sallar azhar da bai samu yayi ba yana fitowa motarsu na fita shine sergeant ya taho da shi,

Wayar aljihunsa sai ringing take yi,sam hankalinshi baya a wurin,har sai da Abusufyan ya ambaci sunanshi"Rafayet ka ɗaga kiran mana,"
A kasalance Ya sanya hannu ya curo wayar,Abbas ne ke kiranshi,picking call din yayi tare da kara wayar a kunnanshi,akan rashin lafiyar Abbansu suke tattauna,

Kamar daga sama Sehrish ta faɗo wurin da suke bakinta ɗauke da sallama,jin muryarta yasa Jahad ta ɗago da kanta tana kallonta,kanal Yousouf ma ya ɗaura idonshi akanta,Haka Abusufyan da abu ma duk ita suke kallo,Sauran kuwa duk hankalinsu baya a wurinta,abun ya ɗaure masu kai ganin tana ta faman sakin Murmushi kamar wata zautacciya,
"Anya Sehrish tana da lafiya kuwa?sai kace batasan halin da muke ciki ba,Sai murmushi take ta saki kamar wata zararra,kodai Hosana batayi wannan haukan ba,"Jahad ce tayi maganar acikin zuciyarta,
  "Sehrish!waya kawo ki?dama bada ke muka zo ba"?Oummansu ce tayi mata tambayar,don ita bata lura ma babu ita ba,
"Daughter,"Abusufyan ya kira sunanta yayin da yake tunkaro wurinda take a tsaye,duk wannan abun dake faruwa Sgr bai ankara da ita ba,Saboda Ya juya bayanshi Yana waya da Abbas,
  A hankali ta soma magana"Bani kaɗai nazo ba"tana kai ƙarshen maganarta ta matsa gefe,Sae ga nurses guda biyu sun shigo da Junaid asaman gadon daukar marasa lafiya suna gunguroshi a wani irin Slow,

Ya mu'allim na a bayansu tare da Amrish da kuma Baba mai gadi,
Zuba ido Abusufyan yayi yana kallon fuskar mara lafiyan da suka ɗauko,Lokaci guda Ya ambaci sunanshi"JUNAID!!!"da tsantsan mamaki akan fuskarshi,Jin sunan Daya Ambata ne Yasa Su fawan suka ɗago da idanuwansu,Ai ko da sukayi Arba da Junaid kwance saman gadon,A wani irin firgice Suka mike suna ambaton Sunanshi Junaid! Junaid!!,Tuni Jahad ta ƙame a tsaye,gaba ɗaya ta rikice Sai faman zazzare idanuwanta take yi akan fuskarshi gani take Yi tamkar Mafarki ne ba gaske ba,Tsabar razanar da tayi ne Yasa ta Yanke jiki ta zube anan wurin,Gaba ɗaya sun miƙe tsaye cirko cirko agaban gadon,Surutun da suke yi ne Ya jawo hankalin Omar kansu,koda Yayi arba da Junaid nan take kirjinshi Yayi wani irin mugun bugu,Waro ido waje yayi yana ƙare mashi kallo a ruɗe ya ambaci sunanshi"JUNAID"!
Adai dai Lokacin Sgr Ya ɗan juyo a sukwane don Yaga meke wakana Yaji sunata ambaton Sunan junaid,baiyi tsammanin wani abu ba,Juyowarshi keda Wuya idanuwanshi Suka sauka direct kan gadon Da junid yake kwance,Saboda tsabar firgitar da yayi baisan Lokacin daya Saki wayar dake hannunshi ba,ta faɗo ƙasa,
Hannu yasa saman idanuwanshi Ya murzasu dakyau don Yaga in dagaske ne,A sukwane Ya kalli Marshal a lokacin shima Omar ya juya a hargitse suka haɗa ido,Just speechless sun gaza magana sai dai nuni da hannu,Sun zama kurmayen Ƙarfi da Yaji,Girgiza kai Sgr ya shiga yi,Alamar bai Yarda ba,
  "I can't believe it,Wannan bazai ta6a yiwuwa ba,Junaid Daya mutu Ya dawo,how can that be possible?Yaron daya ƙone a mota,dama ana mutuwa adawo ne....its just a dream...."acikin ranshi yake wannan Sambatun,Sae faman motsa la66ansa Yake yi amma ya kasa buɗe baki Yayi magana,sunyi matuƙar razana,Sun gigice da ganinshi,Duk da basu Yarda cewa shi bane,Ido kawai suke binshi dashi,

Su kuwa Sauran Matasan Sae murna Suke Yi baby Junaid ɗinsu Ya dawo,Duk da matsananciyar damuwar da suka Shiga na ganin halin da Junaid ɗin yake ciki,Tuni Fawan ya fashe da matsanancin kuka,haka su Irfan sun tasa shi gaba sai kuka sukeyi sun hana nurses ɗin su wuce dashi ciki,
Koke koken da suke Yi ne ya farkar da Alex,Dagowa tayi fuskarta sharkaf da hawaye,Ganinsu tsaitsaye cirko cirko Yasa ta miƙe tare da nufarsu tana Tambayar Lafiya,Matsa mata su kayi don ta ganshi dakyau,A sukwane Alex ta zube saman guiwowinta agabanshi Tana kallon fuskarshi,Yatsun hannunta Na kerma ta azasu asaman ramammar fuskarshi,
  Lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka tana ambaton Sunan shi"Romeo ɗina ne ya koma haka"?rufe bakinta tayi da tafin hannunta tana cigaba da yin kuka,
  Ganin Suna 6ata Lokaci Yasa nurses ɗin suka nemi alfarmar su basu hanya su wuce dashi ciki,Gungurashi sukayi da sauri Abusufyan tare dasu Kanal Yousouf suka bi bayansu,Ɗakin da aka kwantar Da Abbansu nan suka nuna suna son a shigar dashi,Ko Allah zaisa adace Abba Ya dawo hayyacinshi,shiga ciki Su kayi dashi,anan gefe aka kwantar da Junaid,dandazo likitoci su Kayi acikin ɗakin domin duba Lafiyarshi,gwaje gwaje suka fara yi mashi,Yafi buƙatar blood ajikinshi fiye da Komai,tsabar so da ƙauna har kokawa su Fawan suke yi don a ɗebi jininsu,Kowa so Yake a sanya ma Junaid nashi,One by One aka dinga gwada Jininsu,A ƙarshe aka ɗibi jinin Fawan dana Ayaaan,kusan Leda huɗu za'a ƙara mashi,

Abun sai ya baka mamaki,Gaba ɗaya sun kasa samun natsuwa sae faman sintiri Suke Yi,da taimakon Oummansu Jahad ta farfaɗo da matsanancin Ciwon kai,Still bata Yarda da abunda idanuwanta suka nuna mata ba,Asaman laps ɗin abu ta kwanta,wani irin zazza6i ne ya rufe ta,duk a tunaninta Fatalwarsa ce aka kawo masu,Mommyn Junaid kuwa tana bakin ƙopar ɗakin tsaye ita da Abusufyan,jikinta sae tsuma Yake Yi,ji take kamar ta faɗa ɗakin,

Ya Mu'allim yana a tsaye tare dasu Amrish,ba ƙaramin tausayi suka bashi ba,sam babu kwanciyar hankali atattare dasu,Tunda Allah yasa su kayi arba da Junaid,hankalinsu gabadaya ya koma akanshi,shiyasa basu nemi ƙarin bayani a wurinsu ba,Wuri Sehrish ta nuna masu suka zazzauna,kafin ta wuce izuwa wurinsu Marshal Omar dake a tsaye,Suna bin kowa da ido,Su da suka san Cewa Junaid Ya mutu,Abun ya matukar jijjigasu,

"Ya Omar,"firgit ya wurga idanuwanshi akan fuskarta,A lokacin Shima Sgr Ya mayar da hankalinshi akanta,
  Da hannu Yake tambayarta taya akai hakan ta faru"?
  Murmushi ta ɗan saki,kafin ta soma magana a tsanake,
  "Nasan zaiyi wuya ku yarda,Amma tabbas Junaid ne,bai mutu ba,Lokacin da hatsarin motar nan ya faru,Junaid baya acikin motar,"a iya nan ta dakata,dan tasan brain ɗinsu a yanzu bazata Iya ɗaukar dogon bayani ba,
  "Idan muka samu natsuwa zamu fahimtar daku komai,Atare da malamin makarantarmu,Da kuma ƙawata Amrish muka kawo shi,"tayi maganar tana nuna masu Ya mu'allim dake a zaune,
Sai Lokacin Sgr yaja dogon numfashi hadi da sauke nauyayyar Ajiyar Zuciya,runtse idanuwanshi Ya ɗanyi yana tariyo abunda Ya wakana a lokacin da suka je wurin da hatsarin motar ya faru,Tabbas sunyi kuskure da basu kwantar da hankali sun tsananta bincike ba,Shi kanshi Yajima yana ji aranshi cewa Kamar Junaid Yana araye,Koba don haka ba,Yayi mamakin Yadda akai ba'asamu ƙashi ko ɗaya ba na jikinshi,wata irin zufa ce ta wanke mashi fuskarshi,Ganin Yadda ta tsastsafo mashi akan fuskarshi ne Yasa Sehrish ta zame mayafinta,goge mashi zufar fuskarshi tayi,kafin ta mayar da mayafin akanta,
"Alhamdulillah,Junaid bai mutu ba,dama yana raye,Ya salaam!"Omar ne ya ambaci hakan fuskarshi ɗauke da wani irin murmushin farin ciki,
Doctor emran ne ya fito daga Medical room ɗin da aka kwantar dasu,Fuskarshi ɗauke da murmushi,kaitsaye wurinsu Sgr ya nufa yana dariya,Kallo Ya koma Sama,
  "Wonders shall neva end"!Ya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login