Showing 276001 words to 279000 words out of 307403 words
Chapter 93 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete
na wani lokaci,Kafin yace"Ya jikin Mommyn naki"?
"Da sauƙi,Ae jiya munyi waya da ita,ta kirani da layin ɗaya daga cikin likitocin dake kula da ita,tama faɗamun cikin satin nan za'a sallameta,"
"Jiki yayi kyau kenan,To Allah ya ƙara mata Lafiya,".
"Ameen daddy,mungode ssai,Allah ya saka da alheri,"
Sun jima suna waya,kafin su kayi sallama,Ta kira Layin Hayaam......'
Tana fara ringing Hayaam ta ɗaga kiran,bayan sun gaisa Hafsat tace"Aunty hayaam,tunda safe nake ta kiran Layinki tana ta ringing baki ɗaga ba,"
"Na sanya wayar silent ne,dayake naje makaranta ne,"
"Dama inaso na sanar dake cewa,Mommy na nan zata dawo gida,An kusa sallamarta,"
Muryar hayaam da alamun farin ciki tattare da ita tace"Alhamdulullah,Amma naji daɗi sosai,nayi farin ciki,Ya mutanan gidan?
"Suna nan cikin ƙoshin Lafiya,Ae zakuzo bikinsu yaya Omar ko,"_
Shiru hayaam ta ɗanyi kafin tace"Anya!"
"Dan Allah aunty hayaam kuzo,Gagarumin biki za'ayi,Kuma hada fa Amal ma,Kodan ita yakamata kuzo,tunda ƴar uwarku ce,"
"Allah ya bamu ikon zuwan,"
"Ameen,in sha Allah ma zakuzo,"
Sun jima suna waya kafin daga bisani,Sukayi sallama,
*Boss Bature*
Wuraren ƙarfe shida na marece,Ya mu'allim yazo gidan domin duba jikin junaid,tun bayan da yayi parking ɗin motarshi,adai dai lokacin Kanal Yusif da Abba suke ƙoƙarin fitowa daga entry din falon,Suka yi arba dashi,Yana sanye cikin shigar nan tashi ta Larabawa,sai ƙamshi ke tashi daga jikinshi,fuskar kowannansu ɗauke da murmushi,
Mika mashi hannu abba yayi suka gaisa tare da rungume juna,"Nayi farin ciki sosai da zuwanka,Dama junaid ya addabe ni da tambayarka,Har cewa yake yi shi dai ayi mashi kwatancen gidanka Yaje ku gaisa"yayi maganarne bayan sun raba jikinsu,
"Allah sarki,junaid Ya jikin nashi,wlh nima nayi kewarshi sosai,Shiyasa na gaza hakura,"Ya kai ƙarshen maganar,tare da miƙawa Kanal yusif hannu suka gaisa"sannu zuwa,ya gida ya aiki,"
"Alhamdulillah,Yusif Ya mai jiki"!yayi tambayar yana kallonshi,
Yusif yace"mai jiki da sauƙi,Yana nan yanzu ba inda bai zuwa da ƙafafunshi,don da ace yana da mota da ba abunda xai hana ka ganshi ƙopar gidanka,"
Dariya suka saki gaba ɗayansu,Abba yace"bismillah mu shiga daga ciki,"
Atare suka nufi falon Ya mu'allim na a tsakiyarsu,lokacin da suka ƙarasa cikin babban falon,mutun uku suka samu zaune suna fira,Major general osman tare da Adam da Najeeb,miƙewa sukayi ganin abbansu,Gaishe dashi suka yi kafin suka miƙa ma Ya mu'allim hannu ɗaya baya ɗaya ya gaisa dasu,daga bisani kowannasu Ya zauna suka ci gaba da firarsu
Hannu abba yasa cikin aljihun wandon jikinshi ya lulubo wayarshi,Mommy ta dannawa kira,tana fara ringin mommy ta ɗaga kiran,
"Kina ina ne"?
"Na shiga wurin azeema ne,"
"Okey,Ya mu'allim ne yazo,muna buƙatar abunsha,"
Amsa mashi tayi da toh"Gani nan zuwa,"daga haka yayi rejecting kiran,tare da mayar da hankalinshi kan Ya mu'allim
"Yakamata ka gayyace mu zuwa gidanka,tunda mun zama ɗaya,ko ba haka ba"?yayi tambayar yana kallon su Yusif,
"Hakane daddy,abunda na lura dashi,baya son sakewa acikin gidan nan,kuma kullum zaizo shikaɗai yake zuwa,banda ya'yanshi,"acewar yusif,
Murmushi ya mu'allim ya ɗanyi kafin yace"Bani da ya'ya,"
Abba yace"Karfa kace mun baka da aure"?
Dariya yayi batare daya ce komai ba,Osman yace"Haba ya za ace baida aure,Yadda yake malamin nan kyau ace yana da mata huɗu cuf,Ya cike sunnah kenan,"
Sunnar dakai ƙasa ya mu'allim yayi yayin da yake wasa da key ɗin motarshi,
Abba yace"Kayi shiru bakace komai ba?
Najeeb yace"duk kunsa yaji kunya,kunsan fa bakowa keso ayi mashi maganar iyali ba,musamman idan ya kasance baidasu,"
Jin wannan maganar yasa Ya mu'allim ya ɗan ɗago tare da kallon Captain najeeb da yayi maganar,domin kuwa ya canko dai dai,
"Ae ni tun rana ta farko dana fara ganinshi,raina ya bani cewa,duk irinmu ne,"adam ne yayi maganar,fuskarshi dauke da murmushi,
Abba yace"wai dagaske ne?kaima irinsu ne"?
Daƙyar Ya mu'allim ya iya amsa mashi"hakane abba,"
Tafa hannu abba ya shiga yi yana Faɗin"Subhanallahi!An shiga uku!haba Ya mu'alim,Ni duk a tunani na ka cike sunnah,ashe ko ɗaya baka ajiye ba,"
Murmushi kawai Ya mu'allim keyi batare daya ce uffan ba,Saboda kunyar abba da yake yi,
"To dai ga junaid ɗinka nan,In sha Allahu cikin sati mai zuwa zai angwance,"
Cike da mamaki Ya mu'allim yace"junaid zaiyi aure"?
Jinjina kai abba yayi"ƙwarai kuwa,Ae bashi kaɗai ba,Suna dayawa,kusan dukansu zan aurar a lokaci ɗaya,Ina fata kaima kafin lokacin zaka fiddo da mata inyi maka aure,"
Murmushi kawai ya mu'allim yayi,
Fitowa mommy tayi daga cikin kitchen hannunta ɗauke da tray,wanda ta shirya masu abunsha mai sanyi acikin glass cup,hada snacks ta haɗo masu,
Adai dai Lokacin hafsat ta nufe wurinta,jikinta na sanye da arab gown white colour ta yafa mayafi akanta,
"Mommy,"da sauri takai idanuwanta kan hafsat data ambaci sunanta,
Fuskarta asake tace"Hafsat,ina zuwa haka"?
"Ba ko'ina,nagaji da zama cikin ɗakine,Shine nace bari na fito in ɗan zagaye gidan,"
Kafin mommy ta kuma cewa wani abu,hafsat ta nuna tray ɗin hannunta"Wannan fa"?
"Abbane yazo da baƙo,wannan malamin dake duba junaid,shine ya buƙaci in shirya masu drinks,"
"Bari nakai masu,"
Ba ƙarami daɗi mommy taji ba,Miƙa mata tray ɗin tayi,ta sanya hannu biyu ta kar6a,kafin ta wuce cikin palourn,Mommy kuma ta juya zuwa ɗakinta,
"Assalamu Alaikum"cikin sanyin murya tayi masu sallamar,gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta,cikin girmamawa ta shiga gaishe dasu,fuska asake suke amsa mata,
Abba ta fara mika mawa ya ɗauki kofin ɗaya,
"Ga ya mu'allim nan ki miƙa masa,"juyawa tayi wurin Ya mu'allim ta miƙa mashi cup ɗin,a hankali ya sanya hannunshi ya ɗauki cup ɗin,har zata juya taji yace"kina mace kike shafa turare har haka"?ƙasa ƙasa yayi maganar
Gabanta ne ya faɗi rass,dama sai da ranta ya bata cewar zaiyi wuya in bai tanka mata ba,saboda tasan halin malaman nan,kuskure kaɗan sai sunyiwa mutun wa'azi akanshi,'ƙasa ƙasa da murya tace"Za'a gyara,'bata jira amsar da zai bata ba,tayi saurin yin gaba wurin Su osman ta miƙa masu,
Murmushi abba ya ɗan saki bayan ya kur6i lemun yace"Nasan bakasanta ba,Jikata ce,sunanta hafsat,"
Murmushi Ya mu'allim ya ɗan saki kafin yace"Masha Allah,"
Abba da ɗumi sai cewa yayi"itama bata da aure kamar kai,sai dai bansani ba,ko tana da saurayi,"
A sukwane hafsat ta juyo tana kallon Abba,hankalinshi kwance yake magana,
Ƙumshe dariya kanal yusif yayi ganin yadda hafsat ta gumtse fuska,taji ana ƙoƙarin yin tallatarta,da sauri ta juya tabar wurin,sai da tayi nisa,takaici ya isheta,juyowa ta kuma yi don ta kalli Ya mu'allim,karaf suka haɗa ido dashi,watsa mashi harara tayi,duk don saboda yayi complain akan turarenta,abun ya bashi mamaki,hakan da tayi kuma ba ƙaramin burgeshi tayi ba,har yayi tunanin yin magana da abba akanta,idan sun ke6e,
Bayan ya kammala shan lemun,Abba yayi mashi jagora zuwa bedroom ɗin junaid,Lokacin da suka shiga zaune suka same shi,tare da Talal suna kallo acikin laptop ɗinshi,
Cike da zolaya ya mu'allim yace"kaida zan sameka kana karatun qur'ani,sai in sameka kana kallon drama?haka mu kayi dakai"?
Saukowa junaid yayi daga saman gadon ya ƙarasa da sauri ya rungumeshi,ba ƙaramin daɗi Ya mu'allim yaji ba,ganin yadda junaid ya samu lafiya sosai,har ƙiba yayi sa6anin da,
Shafa sumar kanshi yayi"Masha Allah,jiki yayi kyau junaid,Naji daɗi sosai,Allah ya Albarkanci rayuwarka,"Abban ya amsa mashi da Ameen
Ɗagowa junaid yayi fuskarshi ɗauke da murmushi yace"I really missed u,meyasa bakazo ba,2 days banganka ba,"ya ɗanyi maganar shagwa6e
Waro ido abbansu yayi ganin junaid na shagwa6a,
"La haula masalli ila!Junaid me nake gani haka?Dama har yanzu akwai sauran shagwa6ar"?
Dariya ya mu'allim yayi"A jininshi take,shiya sanya har yanzu bata rabu dashi ba,kuma hada ƙarin autane shi,dole yayi shagwa6a,"
Abba yace"amma yaci ace ya daina,Nan fa da wani lokaci zai zama ango,"jin wannan maganar yasa junaid,Jin kunya da sauri ya koma saman gadonsu,Ya janyo pillow ya kifa kanshi asama yana dariya,Talal ma dake a gefenshi dariyar yake yi,
"Yana da kunya sosai,"acewar Ya mu'allim,
Abba yace"hmmmmm abar kaza cikin gashinta dai,kar atona,"
Dariya sosai su kayi,Sun jima a wurin Junaid sai da aka fara kiran Sallar magrib tukunna,suka fuce atare,
*Sehrish*
A hankali ta turo ƙopar toilet ɗin,jikinta sanye cikin bathrobe fara ƙyal,ta ɗaure igiyar rigar,wani irin ƙamshine ke fita daga jikinta,kamar wadda tayi wanka da ruwan turare,lallausar suman kanta tayi mata rumfa a bayanta,mai yawan gaske,jiƙe take lemar ruwa,tun bayan sallar Azhar,ta dawo ɗakin Azmee,gudun kada hajiya azeema taga tabaro shi,
Gaban mirror ta zauna,zugudum bakomai keyi mata yawo aranta ba,face maganganun da oummansu ta faɗa mata,sun tsaya mata aranta,
A hankali ta furta"Ya rafayet sona yake yi,ko jikina yake so?taya za'ae na gane haka?,tana tsoran tayi irin kuskuren da Oummansu tayi,Nayin watsi da damarta,
Hand dryer ta fara ɗaukowa,ta jona ajikin socket,busar da gashin kanta tayi,bayan ta kammala ta kashe ta,jikinta ta soma gyarawa,ko'ina ta shafe shi da mai,
Turo ƙopar ɗakin Hajiya azeema tayi da sallama abakinta ta shigo,Sehrish ta amsa mata,fuskarta adan sake ta amsa mata,
'Ina yini aunty azeema,"
"Lafiya Lou daughter,Ya jikin naki"?
"Alhamdulillah,ina samun sauƙi sosai,"
"Naga gashin kanki,Yayi tsayi sosai,ga yawa,yakamata ku shirya in kaiku wurin Saloon dake da ƴan uwanki,amma fa idan kinji sauki,"_
"Ae nama ji sauƙi,warwarewa kawai zan ƙarasa yi,"
Hararar wasa Azeema tayi mata"A haka din,kina ɗan gyasa ƙafa shine kinji sauki?
Dariya sehrish ta ɗanyi"bari nayi maki make up,"acewar hajiya azeema,
Ba don taso ba,Saboda yanzu bata buƙatar yin kwalliya,tunda wanda take yi dominshi,Rabuwa zasuyi,
Within mins hajiya azeema tayi mata make up,fuskar ta fito sosai,jan bakin data shafa mata red ne mai ƙyalli ajikinshi,daga sama ta shafa mata lip gloss,fuskar ta lindu da foundation mai kyan gaske,ga eye brows ɗinta natural amma ta ƙara mata da brown eye pencil,
"Masha Allah my daughter,Allah yayi maki kyau,ki godewa Allah,Son kowa ƙin wanda Ya rasa,"
Murmushi sehrish ta ɗan saki,
"Bari na ɗauko maki,kayan da zaki sanya,"ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta nufi wardrobe ɗin kayanta,
Can ta hango wata Atampa,Golden glitter,Brown Colour,Riga da skirt ne,ɗinkin ya haɗu over,
Juyawa tayi tare da kallon Sehrish"Har na hangoki acikin wannan,"
"Sunyi kyau sosai,Amma dare yayi,koda na sanyasu,zan cirene in na tashi kwanciya,"
"Duk da haka,ki sanyasu,in yaso daga baya kin cire,"
Gyaɗa kai tayi"shikenan,"ta ambaci hakan tare da mikewa,taje ta kar6i atampar daga hannunta,
"Bari naje,na kawo maki dinner dinki,"tayi maganar tare da nufar hanyar fita daga dakin,Harta ruƙe handle ɗin kopar ta juyo ta kalli sehrish"Munyi magana da Amrish,tace tana so taje gidansu ta kwaso kayanta,bansani ba kota fada maki"
"Bata faɗamun ba,"
"Okey,in Allah yakaimu,Zuwa gobe zanyiwa wani magana cikin matasan gidan nan,yakaita gidan ta dauko kayanta,"
"Allah yakaimu Lafiya,"
"Ameen"ta amsa mata tare da juya ta fuce daga ɗakin,
Shaf shaf ta shiga zura kayan ajikinta,sun zauna mata sosai sunbi dirin jikinta,bata ɗaura ɗankwalin ba,don bata iyaba,zama tayi gaban mirror ɗin tana jiran dawowar,Hajiya azeema don ta ɗaura mata shi,
After some minutes hajiya azeema,ta shigo hannunta dauke da tray mai fadi,Asamanshi food stuff ne,Saman table ta sauke tray ɗin,kafin ta nufo Sehrish,
"Banta6a ganin budurwar da atampa keyi mata kyau ba irinki,yadda kasan donke companyn suka ƙerata,"fashewa sehrish tayi da dariya,don ba ƙaramin nishaɗi ta sanyata ba,
Bayan ta kammala ɗaura mata ɗan kwalin,style me kyau,tace"Aikina ya qare,ga abincinki can kije ki zauna ki ci,"
"Nagode sosai,"tana kai karshen maganarta,ta fuce daga dakin,
Murmushi sehrish ta ɗan saki tana kallon kanta ta cikin madubin,miƙewa tayi daga gaban madubin ta dawo gefen gadon ta zauna,sae ƙamshi ke tashi ajikinta,
Tsaf Ya kammala Shiryawa cikin shadda Ash colour,wa'iyazubillah,kyau iya kyau,a tsaye yake gaban mirror yana gyara agogon diamond ɗin hannunshi,
Omar dake zaune gefen gadonshi sai faman sakin murmushi yake yi,yayin da yake kallonshi,
"Kasan Allah duk macen data mallake ka ba ƙaramar me sa'a bace,cos you're expensive,komai naka Extraordinary ne,wlh mace koda Ilminta koda kyanta koda arzikinta sai da rabonta,"Sai faman zuzutashi Omar yake yi,Shidai baice mashi uffan ba,a hankali yakai hannu tare da ɗaukar turaren nan nashi,Yabi ko'ina na jikinshi ya feshe,
"just ka bayyana mata irin son da kake yi mata,ka ƙaddara cewa yau zaka fara dating......"
Slowly ya juya gefe tare da kallon Omar"how can i do that"?
"Ni zan koya maka,"
Girgiza kai yayi,Omar kasan ban iya soyayya ba,'
Matsalarka kenan,tunda baka iyaba ka bari in koya mata,natsuwa sgr yayi yana sauraronshi
"Kece sanyin idaniyata,bana iya runtsawa in bakya a kusa dani....."
Kwata kwata Sgr baya fahimtar abunda Omar ke koya mashi,
"Na lura baka fahimtata,Zamuyi amfani da bluetooth,zaka manna shi a kunnanka,Idan kaje wurinta,zan dinga karanto maka,kai kuma kana faɗa mata,haka yayi"?
Ɗaga mashi kai yayi"yeah,i can try it,
[3/19, 2:58 PM] +234 810 388 4440: _💋The father Of Soldiers💋_
*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*
Story
&
Written
by
*_Boss Bature_*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
Dedicated to my beloved sisters. 😍
Proud Of My First Novel💋
_Warning banyarda wani yayi amfani da wani sashe na littafina ba, kada a ta6amin komai na littafina,Sannan kar a kuskura a haɗamun document,Ga mai buƙatar karanta Littafin Abban Sojoji from Book one to 3 yayi mun magana ta whatsapp 08103884440_
Canza ra'ayi yayi"Omar,bana buƙatar using the bluetooth Just komai ya dace ka sanar da ni,"
Murmushi Omar ya ɗan saki don yasan cewa Sgr zai iya,A nan ya shiga kwatanta mashi yadda zai bayyanar da Soyayyarshi,bayan Ya Kammala Sgr yace"thanks,sai nadawo,"yakai ƙarshen maganar tare da juyawa ya nufi hanyar fita ɗakin,Yana jiyo muryar Omar Yana faɗin"Wish u all the best,"
A lokacin Sehrish tana zaune ta tasa abincin da Aunty Azeema ta haɗa mata sai ci take yi,bayan ta kammala ta yagi tissue tana goge bakinta,A dai dai wannan Lokacin taji an turo ƙopar ɗakin,dakatawa tayi tana jiran ganin mai shigowar,Natsuwa tayi tana shaƙar daddaɗan kamshin turaren dake kai ma hancinta ziyara,tunkafin ma Ya shigo ƙamshin jikinshi ya gauraye ɗakin saƙo da lugu,
A hankali ya sako ƙafarshi kafin ya ƙarasa shigowa ciki,Har sai da gabanta ya faɗi rass,Saboda razana da tayi da kyawun da Sgr yayi,Kayan hausawa ba ƙaramin kyau suke yi mashi ba,yadda kasan danshi kamfanin shadda suke ƙerata,cikakkiyar surar jikin nan nashi ta ƙara fito da kyan shaddar,
Tunda ya ɗaura idanuwanshi akanta,gaba ɗaya wankanta ya tafi da imaninshi,natsuwa yayi yana kallonta,from head to toe,Atampar jikinta ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,Ya kasa kawar da idanuwanshi kamar yadda itama take Kallonshi,
Sallama yayi mata cikin sanyin Murya ta amsa mashi,kafin ya ƙarasa shiga ciki,gefen gadon ya zauna dab da ita,tuni kasala ta fara baibaye kowannansu,
Almost 15 mins,tsit kake ji ba wanda yace uffan acikinsu,Ajiyar Zuciya ya ɗan sauke kafin Ya soma magana,
"Ya jikinki?"A hankali tace"da sauki" jinjina kai yayi yana cigaba da kallonta,hakan yasa ta Sunkuyar da kanta tana kallon hannuwanta,
"Reesh,nasan nayi maki laifi wanda yasa kika juyamun baya,But Why can't u forgive me?komai ya wuce mana,Idan har bana ƙaunarki serious bazan kulaki ba,kuma abunda ya faru,duk don saboda ƙaunar da nake yi maki ne,Naji fargabar su rabani dake,I thought yi maki hakan da nayi will be the solution,sai dai nayi mistake na kusantarki a lokacin da nake cikin fushi,wanda duk Iyayenmu ne suka jawo hakan,"ya ɗan dakata da yin maganar Yana mayar da numfashi,jin yayi shiru yasa ta dago,yayin da idanuwansu ke kallon cikin na Juna,
"Ina neman alfarma a wurinki,For the Last time,ki bani dama,zan gyara kuskure na,Zan canza maki kamar yarda kikeso,"
Jikinta ya ɗanyi sanyi da jin kalamansa,Amma still tana kokwanto akanshi,gani take kamar Sgr bazai ta6a sonta don Allah ba,sai don ya mayar da ita abun biyan buƙatarshi kamar yadda ya saba yi mata,Zurfin tunani ta shiga,ba zato ba tsammani,taji ya ruko hannuwanta Acikin nashi,sosai ya ruƙe hannun yana shafa lallausar fatar hannun,a hankali ya fara matsawa yana niyyar rumgumeta....
"Reesh,I've Fallen for you...... "Tunkan yakai ƙarshen Maganar,Rai a matuƙar 6ace Sehrish Ta ƙwace hannunta daga nashi tare da yin wurgi da hannunsa ta dan ja baya,Abunda bai ta6a tsammani ba,Waro idanuwanshi yayi waje yana kallonta,
A fusace take magana"Wlh ba sona kake yi ba don Allah,Ni nasani don kawai biyan buƙatarka yasa kake so naci gaba da kasancewa dakai,idan har dagaske kana sona,Meyasa tuntuni baka sanar dasu cewa kana sona ka maida ni matarka ba,kuma tun farko kayi accepting aurena don kawai naci gaba da yi maka Aiki,Saboda kafi ƙarfin kayi soyayya dani,bankai matsayin da zan zama Matarka..... "Kasa ƙarasa Maganar tayi sakamakon gigitacciyar tsawar da Sgr ya daka mata,A firgice ta zazzare idanuwanta tana kallonshi,tuni idanuwanshi sun Canza launi sosai,Ranshi yayi Mugun 6aci,Zuciyarshi ta hasala,har ya ɗaga yatsu biyar cuf zai wanka mata mari,Ta fashe da matsanancin kuka,Ta dinga ja da baya har ta ƙurewa kan gadon,ta runtse idanuwanta sosai,'
Yarfar da hannun gefe yayi,wani irin raɗaɗi yake ji acikin zuciyarshi,tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla,takaicin Duniya ya ishe shi,ƙaramar yarinya kamar wannan ce take gaya mashi Magana,gudun kada ya karya ƙasusuwan jikinta ne Yasa yayi saurin miƙewa da saurin gaske har yana tuntu6e ya fuce daga ɗakin,A makance yake tafiya Allah yaso babu kowa a babban falon,A zafafe ya nufi twin stairs ɗin Ya haye,yana taka staircases ɗin wasu Zafafan hawaye suka wanke mashi fuskarshi masu ɗumin gaske,har wani zazza6i yake ji ajikinshi,Sehrish ta hasala shi sosai,
Yana shiga Bedroom Yasa hannu Ya tu6e rigar jikinshi yayi wurgi da ita ƙasa,A haukace Yakai hannu Ya damƙi bedsheet din gadon Ya yayeshi tare da Jefar dashi gefe guda,Dunƙule hannunshi Yayi da ƙarfin gaske Ya naushi Dressing Mirror ɗinshi,gaba ɗaya madubin ya farfashe ya zube,hatta hannunshi sai da glass din ya faffasashi,jini ya shiga tsastsafowa,raɗaɗin da yake ji a hannunshi bai kai raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi ba,lokacin da Sehrish ke faɗa mashi wannan maganganun,Biji biji ya fara gani acikin idanuwanshi,Jiri ya soma ɗaukarshi,tangal tangal yayi zai faɗi,kaitsaye ya faɗa saman gadonshi,numfashin shi na fita da wani irin huci,ga wani matsanancin ciwon kai daya farmasa,
Wuraren ƙarfe 12 na dare,Omar ya faɗo part ɗinsa,fuskarshi ɗauke da Murmushi,Yazo cike da sa ran sunyi nasara,Tun a palour Yake ƙwala mashi kira"Bro!bro!"shiru ba Amsa,har yayi tunanin ko bai kaiga dawowa bane,Acikin ransa har yana cewa"Yanzu haka yana can manne da ita suna shan Soyayya,"ya ƙarasa zancen zucin yana kokarin juyawa kwatsam Idanuwanshui suka sauka akan Agogon Diamond ɗin