Showing 219001 words to 222000 words out of 307403 words

Chapter 74 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

da kuka tana faɗin"Baba mai gadi kashe mu zatayi,In har bamu bar gidan nan ba,"
  A hanzarce Baba mai gadi ya buɗe mata ƙopa suka fita,har zai tsaya ya tuna cewa Shine yaba Amrish Labarin Yaron,kenan shima Yana cikin hatsari,aikuwa da gudu ya bi bayan Amrish suka miƙi hanya suna neman Abun hawa,A ƙarshe daya ga ta jigata shi ya kar6i Junaid ya ɗaura shi a kafaɗarshi,Babban tashin hankalin tunda suka fito Unguwar babu kowa wayaam dama haka unguwannin ƴan gayun nan suke,Da ace irin geto ne da tuni jama'a sun agaza masu,ɗaiɗaikun mutanan dake wucewa duk wanda yayi arba dasu Amrish saiya watsa da gudu kamar sunga Aljanu,saboda ƙurar da ta 6ata masu jiki,

Da iya ƙarfinta Na ƙarshe ta daddage ta miƙe,ɗago kan da zatayi keda Wuya haƙorinta ɗaya ya 6allo jaga jaga da jini,qugunta ya ruƙe sosai,wani irin azababben raɗaɗi,daƙyar ta samu ta fara jan jiki a galabaice ta nufi wayarta dake ajiye saman sofa,jikinta sai tsuma yake yi,daƙyar ta iya cire password ɗin wayar,Call log ta shiga ta kira wani layi da akayi mashi saving da ƙare kukanka,Daƙyar take magana saboda ciwon bakinta,
  "Duk yarda za'ae karku bari yarinyar nan tabar cikin unguwar nan,Nasan zaiyi wuya su samu abun hawa,da ita da yaron Gawarsu kawai nakeso ku kawo mun...."tana magana tana goge zufar goshinta,ga wani irin huci dake fita abakinta,. 
  "Akwai ƙaramar nokia ɗita a hannunta,Zan tura maku Lambar wayar kuyi tracking ɗinta,"ta ƙarasa maganar tare da yin rejecting ɗin kiran,Gaba ɗaya Amrish ta ɗaure mata kai,saboda ta ɗauketa Shashasha,A irin rainon da tayi ma Amrish irin sangartattun nan ne,bata da wayau haka,Sai gashi yau ta bata mamaki,wai har tasan ma inda suka 6oye shi,koya akai duk tasan wannan?

Lokacin da Su Amrish suka haura saman titi,suna neman abun hawa,duk mai motar da suka tsaida sai yaƙi tsayawa,Baiwar Allah duk tabi ta ruɗe gashi sam taƙi tunanin yarda nokia ɗin Hajiya sarat data ɗauko,kuma ta hanyar bin diddigin layinne kaɗai za'a san Location ɗin da suke,

Suna cikin wannan tsayuwar,wata danƙareriyar mota ta shawo kwana da gudu,bata tsaya a ko'ina ba sai agabansu Amrish,mutuwar tsaye tayi lokacin,shi kanshi baba maigadi ya firgita da ganin motar,Jim kaɗan mamallakin Motar ya fito jikinshi sanye da fararen kaya hatta takalmanshi,Facemask ɗin fuskarshi Ya hana Amrish ta gane shi,

Yayi mamakin ganinsu cikin wannan halin,bai tsaya tambayarsu Lafiya ba Kawai ya buɗe masu bayan motar,badon ta yarda dashi ba hakanan dai kawai suka shiga cikin Motar tunda ba yarda zasu yi,a back seat na motar ta shiga baba mai gadi ya jinginar da junaid a tsakiya kafin shima ya shiga,Mai motar ya fusgi motar da gudu,a dai dai Lokacin motoci guda uku masu blank tunted ƙirar Range rover suka bi bayan motar shi,da wani irin mahaukacin gudu mutumin ke tuƙa motarshi,yarda kasan filin ƴar tseral haka motocin nan suke gudu asaman titi,

Amrish sai kuka takeyi tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin tashin hankali ba irin na ranar,ba komai ya ƙara tsoratar da ita ba fa ce Harbin bindiga da taji a bayan motarsu,Ya salam!gashi hanyar da suka biyo babu ƴan sanda balle su samu taimako,

Ɗaya daga cikin Ƴan ta'addan da suka biyosu wanda ya buɗe murfin motar ya miƙe a tsaye hannunshi ruƙe da irin wannan bingidar mai fitar da bullet kamar bomb,kwakkwaran Saiti Yayi ma Motarsu,Yana sakin Bullet ɗin mai girman gaske nan take Ya hau saman motarsu Ya fashe gaba ɗaya Wuta ta kama ci a bayan boot ɗin Motar,Hakan yasa motar ta dakata da tafiya,ganin sun ci nasara akansu yasa suka tsayar da motocinsu,Suka diddiro daga cikinta kusan Su takwas ne,Ƙirar jikinsu gwanin ban tsoro,babu ɗigon imani akan fuskarsu,kowanne hannunshi ruƙe da manyan makamai,

Suna ƙarasowa gaban motar,ɗaya daga cikin samudawan nan ya damƙi murfin motar ya 6alleshi,hannu yakai tare da damƙo rigar mutumin dake acikin motar ya wurgoshi waje,basu tashi ankara ba,Sae da Mai tuƙin motar ya fito yana faman ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,Leƙa cikin motar sukayi Wayaam basu ga Amrish da yaron ba,Ashe Ba motarsu bace,Sunyi mistake Saboda mai wannan motar da suka kama iri ɗaya ce da motar da suka bi su Amrish,

Da sauri Suka koma cikin motocinsu,A guje suka ja motar,Sunbar bayin Allah da aikin neman taimakon kashe masu wutar motarsu,don ma Allah yasa babu wanda ya raunata acikinsu,


A 6angaren Su Amrish kuwa,mutumin dake tuƙa motarsu ne ya umarce ta data jefar da wayoyin hannunta gaba ɗayansu,nan take ta zuge glass ɗin motar ta wurgar dasu waje,Bayan ta jefar dasu sai ya Canza hanya da wani irin gudu yabar titin,Su kuma waɗannan miyagun da suka fara yin tracking ɗin Layin wayar Hajiya sarat na ƙaramar nokia ɗin da aka basu,Ta hanyar laptop ɗin dake a hannun wani kwararre acikinsu,Sae location ɗin ya dinga nuna masu hanyar da Amrish ta jefar da wayoyin,Nan fa suka miƙi hanyar cike da sa ran zasu kamasu,Lokacin da motarsu ƙare kukanka ta ƙarasa inda Location ɗin Ya basu,Sai suka tsayar da motocinsu,A zafafe suka fito suna waige waigen neman inda suka ajiye motarsu,Sai da suka gama shan wahalar nemansu a Area ɗin wurin abun takaici sai ga wayoyin sun tsinta yashe a ƙasa,Rai a matuƙar 6ace suka hanzarta komawa cikin motocinsu batare da sun ɗauki wayoyin ba,Nan fa suka ruɗe saboda hanyoyi ne guda uku,Ta hannun dama da kuma ta hannun hagu,Ga kuma wadda ta mike straight,To fa sun ruɗe a wannan lokacin,Basu san ta wace hanya su Amrish suka bi ba,A ƙarshe kawai suka raba motocinsu dama guda uku ne ɗaya tabi straight,ɗaya tabi Left ɗayar kuma tabi Right,Don sunsan Dole a ɗaya daga cikin hanyoyin suka bi,


*Boss Bature*

Wuraren ƙarfe 2 na rana,

Wayar Ishaq ta soma ringing,A lokacin dawowarshi kenan daga wurin aiki,Buɗe mashi mota sergeant Yayi Ya fito daga cikin motar hannunshi ruƙe da wayarshi,picking call ɗin Yayi tare da kara wayar a kunnanshi,

Fuskarshi ɗauke da murmushi ya soma magana"Mutanan Damaturu,Sai yau ake jinku"?
On the other hand Hafsat tace"Wlh Daddy fushi nake dakai,you forgot about me,"
  "Nima ae fushi nake dake,tunda na baro damaturu kin ƙara kirana ne?Ko irin Morning message ɗin nan babu ko,Yanzu da ace ban kiraki ba da shikenan bazaki neme ni ba,"ya ɗanyi maganar yana ɗaure fuska kamar tana agabanshi,
   "Shikenan na ɗauki laifin,Am so sorry,Amma daddy meyasa ka canza Layinka?in na kira wancen Mtn ɗin bana samun shi"
  "Kinga yanzu na dawo daga wurin aiki,Agajiye nake,bari na ɗan samu natsuwa I will call u later,"
A ɗan shagwa6e tace"dan Allah Daddy,idan ka huta kada ka manta ka kirani akwai maganar da nakeso nayi dakai,"
  "Toh,"ya amsa tare da kashe kiran Ya nufi cikin gidan aranshi yana faɗin"yanzu haka saboda Mommynta ne yasa ta kira ni,lokacin daya shiga gidan ya yi mamakin yarda aka gyara mashi ko'ina fess,murmushi ya dinga saki don ya san cewa aikin hajjaju ne,wani irin ƙamshi ke tashi acikin palourn,

Ga lafiyayyen abinci An jera mashi asaman dining,Dama da wata matsiyaciyar yunwa ya dawo,A hanzarce ya haura upstairs ya shige Bedroom ɗinshi,Bayan ya rage kayan jikinshi ya faɗa cikin toilet,Within mins Ya fito Ya kimtsa kanshi cikin jallabiya,Saukowa Downstairs Yayi kaitsaye ya nufi dining ya zauna,Da kanshi Yayi serving ɗin abincin ya zauna yana ci yana murmushi kamar wani zautacce,Sai da ya kammala cin abinci,tukunna ya koma saman Sofa ya zauna tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,

Wayarshi ya ɗauko ya lalubo Layin Hafsat ya danna mata kira,Kamar jira takeyi ta ɗaga kiran,
  "Daughter ina sauraronki!maganar menene kikeson Yi dani"?
"Daddy dan Allah ka taimaka,Nasan zaiyi wuya ka fahimceni,wlh Mommy tana cikin mawuyacin hali,Ta zama abun tausayi,ta kira ni da wani layi jiya tana kuka tana rokona cewa inyi maka magana ka yafe mata,Ta gane kuskurenta,Rayuwarta ta wulakanta Daddy a gefen bishiya take kwana zaune ba bacci,dare da rana a wurin nan take Yini......."
Tunkan Hafsat takai ƙarshen Maganarta,Ishaq ya katse ta"ke yanzu kin yarda da maganarta?Kodai kun haɗa baki ne da ita?
  Da sauri hafsat tace"Wlh daddy da gaske take,Ae nasa ta ɗauko mun video ɗinta,Wayarma fa aronta takeyi don ta kiramu,Zan tura maka video ɗin ta whatsapp yanzu,zaka shaida abunda nake faɗa maka,"
  Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"its okey,Am waiting for the video,"yana kai ƙarshen maganar ya katse kiran,Kafin Ya kunna wifi ɗinshi ya shiga whatsapp,Messages ne suka fara shigowa cikin wayar,can sai ga saƙon hafsat ya shigo,

Chat ɗinsu Ya shiga,Anan ya samu video ɗin data tura mashi,yatsanshi yasa ya ɗan ta6a video ɗin nan take Ya soma loading,ƙura ido Ishaq yayi akan Screen ɗin wayar yana kallon video ɗin,
   Bai ta6a tunanin zaiga laila a irin wannan ƙasƙantacciyar rayuwarba,a gefen bishiya take zaune,gefenta kwanon bara ne,ƙafarta ɗaya ta lalace babu kyan gani wani irin ruwa ke fita acikinta,Sae kuka takeyi tana magana
  "Don Allah Ishaq ka taimaki rayuwata,ba don halina ba,dan Allah da manzonsa zakayi,Nasan nina jefa kaina cikin wannan halin,Ku kalli irin wurin da nake rayuwa,kowa ƙyamar taimakona yake yi,babu mai son zuwa wurina saboda warin da nake yi,"_
  Saboda tsabar tashin hankali,Da sauri Ishaq ya kashe video ɗin tare da yin wurgi da wayar saman sofa ɗin,
Jingina bayanshi Yayi ajikin kujerar,tabbas Yaji tausayinta amma abunda ya ɗaure mashi kai shine taya akai taje Enugu!Uban me yakaita?don a iya saninshi bata da wata alaƙa da garin,Ya jima a haka kafin Ya ɗauki wayar Ya sake kiran Hafsat,
  Tana ɗaga kiran Yace"Naga video ɗin,wlh hafsat ba don zuciyar musulunci ba,babu abunda zaisa na taimaki Laila!ke bari in faɗa maki zan taimaketa ne kawai Saboda Allah!Taci albarkacinki hafsat!Zansa a ɗaukota akaita asibiti,Inyaso ko ƙafarce su cireta A maidata maiduguri,Amma ni bazan sake rayuwa da laila ba,"
  Fashewa hafsat Tayi da matsanancin kuka kamar ranta zai fita,daƙyar ta samu ta tsagaita da yin kukan tace"Nagode sosai Daddy,koma miye laifinta ne,ita taja ma kanta,naji daɗi sosai Daddy Am really proud of u,"
  "Yaushe zaki dawo gida!kinsan cewa hutun aikin da kika ɗauka ya qare ko"?
  "Eh daddy,Ina nan ina shirin dawowa amma yanzu gidan bazaiyi mun daɗi ba,nafison na zauna a wurinsu Abba,tunda ga ƴan uwana acikin gidan inyaso sai ka nema mun transfer na dawo aiki a Abuja,"
  "Idan kika koma Abuja,ni kuma fa?nikaɗai akeso inyi ta zama a kaduna "?
  A ɗan shagwa6e hafsat tace"idan zaka ƙara aure,Sai in dawo nan,"
Murmushi ya saki anzo dai dai inda yafi so,
  "Calm down ur mind,just ki dawo gida kawai,Cikin ƴan kwanakin nan Nima zanyi aure,"
  Yana jiyo sautin dariyarta,alamar taji daɗin maganarshi,sun jima suna waya kafin suka Yi sallama,

*Boss Bature*

*AMANI*

Tana kwance saman gadonta,Amal ta faɗo cikin ɗakin Hannunta ruƙe da wayarta,hawa saman gadon tayi har zuwa inda Amani ke kwance tana sharar bacci,Hannu tasa tana bubbuga ƙafarta,
  "Aunty Amani!ki tashi ana kira,"
Daƙyar ta iya buɗe idanuwanta masu ɗauke da bacci,sun ɗanyi jawur dasu,rai a6ace ta kalleta"Bana hanaki tashi na daga bacci ba in aka kira ni"?
  Sunnar dakai Amal tayi"Am sorry,dama Aunty hayaam ce ta kira tana kuka......"hankali aɗan tashe Amani ta yunƙura tare da mikewa zaune tana faɗin"kuka kuma!Allah yasa lafiya,"ta ƙarasa maganar tare da kar6ar wayarta da Amal ke miƙo mata,
  Call log ta shiga,Anan taga kiran da hayaam tayi mata,
  Calling ɗin layin tayi,bayan Hayaam ta ɗaga kiran Amani ta kara wayar a kunnanta,tun kafin tayi sallama taji shessheƙar kukan Hayaam
  "Subhanallahi!wai meke faruwa ne?hayaam ki buɗe baki kiyi magana mana,"a ɗan ruɗe tayi maganar,
    "Kodai Wani ya rasu ne"?
Sai lokacin Hayaam ta soma magana"Aunty amani muna cikin masifa!munga rayuwa,rayuwarmu ta wulaƙanta a idon jama'a......"anan hayaam ta kwashe dukkan abunda Ya faru bayan komawarsu maiduguri ta sanar da ita,
  Saukowa Amani tayi daga saman gadon tana ambaton"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"tuni hawaye sun wanke mata fuskarta,. 
  "Allah yajiƙan Mammy,Allah ya gafarta mata zunubbanta,Amma banji daɗin irin mutuwar da tayi ba,ƙaddara ta riga fata,da kunsani tun farko baku barota ba,
  Cikin shessheƙar kuka hayaam taci gaba da magana,
  "Munaji muna gani,zama gidanmu ya gagaremu,Mutane sun ɗaura mana karan tsana,Yanzu haka a gidan Malam limam muke,matanshi sun tsanemu,suyi ta tseguminmu suna zaginmu,Abinci basu bamu sai in liman yana acikin gidan,Abra ma sai addu'a domin kuwa ta fara samun ta6in hankali,sai sambatu takeyi tana faɗin duk ita taja,Itace tayi silar mutuwar Mammy...."kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya cuyota,
  Daƙyar Amani ta lallasheta"kuyi haƙuri ku rungumi ƙaddara,in sha Allah komai zai wuce,Yanzu nidai zanyi ƙoƙari wurin ganin na taimaka maku,Ko gidan ne a gyara maku shi,kafin Allah ya kawo maku mazajen aure,don kuwa yin auren shikaɗaine rufin asirinku,in ba haka ba mutane bazasu daina tsangwamarku ba,"
  (Wlh matsalar mutananmu kenan,idan mutun Ya aikata zunubi arayuwarshi yazo ya yi nadama ya shiryu,Sai su dinga tseguminshi suna ƙyamatarshi,Shi kanshi Allah daya halicce mu yana son bayinsa waɗanda suka Tuba daga aikata zunubi,Amma wasu mutanan da ruƙo,shiyasa wasu ko sun shiryun daga baya sai su koma ruwa saboda mutane,Wannan babban kuskure ne saboda mutane ka koma kana aikata barna,Makomarka zaka duba,In zaka tuba dan Allah zakayi,Dan kuma kanka,ba don mutun ba,a karshe ina mai jan hankalinmu da mu kiyaye harshenmu don zai iya jefamu a halaka,aduk lokacin da wata mummunar kaddara ta fada ma wani muyi Addu'a mu nemi tsarin Allah kada mu rinka zundenshi don muma bamu fi karfin Allah ya jarabemu ba,Allah ubangiji ya rabamu da mummunan kaddara yasa mufi karfin zukatanmu,Amin )

Sosai Hayaam ta shiga yi mata godiya,kafin daga bisani Su kayi sallama,

*Boss Bature*

Wuraren ƙarfe 6 na marece,Sehrish na kwance saman gadonsu abun duniya ya isheta,duk ta shiga damuwa saboda rashin samun kwakkwarar hujjar da zasu kama Azmee,tana cikin wannan zancen zucin taji an banko kopar ɗakin,A firgice takai idanuwanta kan mai shigowa,Jahad ce ta faɗo ɗakin fuskarta sharkaf da hawaye,a ruɗe Sehrish ta shiga tambayarta Lafiya,
  "Bakisan meke faruwa ba,Ga Abba can ya yanke jiki ya faɗi rai hannun Allah,"jin wannan maganar yasa Sehrish ta sauko daga saman gadon jikinta na kerma ta nufi hanyar fita ɗakin,atare da jahad suka fita,

Abunda ya faru,Alex na zaune gefen gado tana jiran fitowarshi daga toilet,tun da ya shiga shiru bai fito ba,tun tana sa ran fitowarshi harta fara tunanin ko lafiya kusan Awa ɗaya da rabi yana acikin toilet ɗin nan,Miƙewa tayi ta nufi toilet ɗin tasa hannu ta kwankwasa ƙopar"Abban Junaid!"ta kira sunanshi da ƙarfi,Shiru bai amsa mata ba,a ƙarshe dai ta yanke shawarar shiga ciki,tana tura ƙopa ta same shi kwance saman tiles,idanuwanshi sun jirkice,jikinshi sai kerma yake yi,Fasa ƙara Mommy tayi anan ta zube tana jijjigashi,Ganin cewa dagaske fa baya acikin hayyacinshi yasa ta miƙe da gudu ta fito daga ɗakin tana kuka,

A lokacin Abusufyan da abu suna zaune a main palour tare dasu Hosana da Jahad,Tun daga kan yarda ta faɗo falon Yasa su miƙewa suna tambayar lafiya,Kasa buɗe baki tayi sai dai nuna masu hanyar bedroom ɗinshi da tayi duk tabi ta ruɗe,da gudun gaske Abusufyan ya nufi ɗakin tare da abu,suna shiga ciki dama ƙopar toilet ɗin abuɗe Mommy tabarta,nan suka sameshi cikin mawuyacin hali,sunyi matuƙar girgiza,Cuccuboshi Abusufyan yayi ya fito dashi daga cikin toilet ɗin,Ya janyoshi zuwa saman gadon ya kwantar dashi,jiki na rawa Ya curo wayarshi saboda ruɗu daƙyar ya iya lalubo Layin Sgr ya danna mashi Kira,Sai daya bi kowannansu Ya sanar dashi halin da Mahaifinsu ke ciki,

A lokacin dasu Sehrish suka faɗo falon Ya yi dai dai da shigowar Omar da Sgr,da gudun gaske suka shigo kaitsaye suka nufi bedroom ɗin Abbansu,wucewarsu keda wuya Kanal yousouf ya faɗo falon da gudu shima Ya wuce part ɗin,gaba ɗaya sai da matasan gidan suka hallara a ɗakin,wasu tuni sun fara zubar da hawaye,tsoransu kada su rasa mahaifinsu a wannan halin da suke ciki,sae faman ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un suke yi,

Fawan dasu twins kuwa tuni sun fara kuka kamar wasu ƙananun yara,
  "Addu'a zakuyi mashi ba kuka ba,in sha Allah zai samu lafiya,"acewar Abusufyan shi kanshi dauriya kawai yake yi,don kada suga rauninshi,hakan zai ƙara tayar masu da hankali,
   yanke shawarar kaishi Asibiti suka yi,Sgr ne ya ɗauke shi asaman kafaɗarshi,Sauran suka bi bayanshi,
  Suna fitowa entry hall ɗin gidan,da gudun gaske armstrong ya buɗe mashi mota ya kwantar da Abbansu aciki,Sannan ya bude mashi front seat ya zauna,Jan motar yayi da gudun gaske motar Marshal tabi bayansu,Motocinsu Kanal yousouf suka rufa masu baya,hada Oummansu Sehrish aka tafi asibitin a motar fawan ta zauna tare da Jahad da Hosana,Mommynsu Junaid kuwa tana a motarsu Abusufyan sai lallashinta Yake yi,duk ta shiga damuwa alokacin motocinsu suka fita daga babban gate ɗin gidan,mutun uku aka bari a gidan Aunty Azmee dake kumshe a ɗakinta,Sae Haroon dake kulle a medical room dinsu,

Sehrish bata samu tabisu ba,daga komawa ta ɗauko mayafinta sai dai tajiyo tashin motocinsu,kamar tayi hauka lokacin da ta fito waje bata samu motar ɗaya daga cikinsu ba,anan ta zuƙunna gaban ƙopar palourn tana kuka,ga tsoron shiga gidan da takeyi,



Da wata irin jiniya motocinsu suka hau saman titi a jere,Lokacin da suka ƙaraso Katafaren Asibitin Sgr,Sai suka tsaida jiniyar,a hanzarce bayan sunyi parking ɗin motocin nasu,Sgr ya fito Ya ɗauki Abbansu,sauran ma suka fito gaba ɗaya suka wuce cikin asibitin,Zo kaga taron nurses da likitoci,Ai tunda suka ji isowar Sgr kuma suka ji cewa Mahaifinshi ne baida lafiya,nan fa sukayi dandazo domin duba lafiyarshi,

A wani katafaren ɗaki suka kwantar dashi,kusan likitoci shida ne akanshi daga cikinsu hada Doctor Emran,

Sgr baisamu shiga ba,saboda a halin da yake ciki a yanzu bazai iya duba Abbansu ba,yana cikin matsananciyar damuwa saboda yasan dalilin ciwon Abban nasu,dama yace su fara ƙirgen kwanakin mutuwarshi,in har basu dawo mashi da yaronshi ba,

A saman waiting seat suka zazzauna suna jiran tsammani,Omar da Sgr suna a tsaye,Kowa ka kalli fuskarshi gwanin ban tausayi,
  "I can't forgive my self,idan har Daddy ya mutu silar 6oye mashi mutuwar Junaid da mu kayi,"Ya ƙarasa maganar yayin da idanuwanshi suka cicciko tab da hawaye,
  Ruƙo hannunshi Omar yayi"bakai kaɗai ba Rafayet,nima bazan yafewa kaina ba,in har muka rasa shi,wlh i ave regretted already,Da mun sani tunfarko mun sanar dashi gaskiya kawae tunda dama gudun hakan yasa muka 6oye mashi,"gaba ɗaya duk sun sha jinin jikinsu,

"Dan Allah kukan ya isa haka,twins,fawan da irfan,in na sake jin shessheƙar kukan wani acikinku wlh zaku koma gida ne,"kanal yousouf ne keyi masu faɗa,. 
  "Sai kace ba musulmai ba!maimakon ku tayashi da addu'a amma kun dage sai kuka kukeyi,"ya ƙarasa maganar tare da jan guntun tsoki,idanuwanshi cike tab da kwalla,
  Abu kuwa sai faman lallashin Mommy takeyi,ganin yadda take ta shar6ar kuka,
  Abusufyan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login