Showing 108001 words to 111000 words out of 307403 words

Chapter 37 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

yau naga dama zan iya barin gidan nan,kuma baka isa ka dawo dani ba,dana so tuntuni wlh dana tafi nabar gidan nan,Ƴanci nane,"
.. Tana magana hawaye na shararowa asaman fuskarta,with confidence takeyin maganar,batare data girgixa ba,
   "Zan tafi kuma kada kayi tunanin cewa idan na kammala ƙazantar zan dawo part ɗinka da sunan aiki,Bazan ƙara zuwa ba,kuma kada kayi tunanin cewa zanji tsoranka in gudu daga gidan nan ko inzo in baka haƙuri,Wlh bazan ta6a karaya ba,ka yi duk abunda kaga dama,ƙarshe kace zaka hukuntani ko,Idan ka tashi dan Allah kada kabarni da raina,ka kashe ni,"
  Ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki,a fusace ta juya tabar cikin bedroom ɗin nashi,
   Sai lokacin sgr ya runtse idanunshi,la66ansa sae kerma sukeyi kaf kaf,saboda tsabar 6acin rai,Hannunshi ya cusa acikin sumar kanshi ya shiga cakuɗata,gaba ɗaya ya hargitsar da gashin kan nashi,Cizon la66ansa ya shiga yi,nan take le6en ya fashe jini ya soma ɗiɗɗigowa daga jikinsu,Zuciyarshi har wani boiling take tana burning,wani irin zafi ne ya taso mashi gadan gadan,jiri ya dinga gani acikin idanunshi harya fara tangal tangal zai faɗi ƙasa,
  Daƙyar ya iya takawa izuwa gafen gadonshi ya zube ƙasa saman guiwowinshi tare da aza kanshi saman gadon,Tashin hankali Ran manya ya 6aci sosai,ƙoƙari yakeyi ya dakatar da bad temper ɗinshi saboda gudun karya aikata kisan kai,don muddin yakai matakin ƙarshe zaibi bayanta ne kuma sai yayi mata mummunar illa,
  A hankali ya shiga furta"Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un"!ya ambaci hakan kusan sau talatin,

Sehrish kuwa bayan ta fita daga part ɗinshi,daƙyar take ɗaga ƙafafunta saboda matsanancin ciwon marar da takeyi,Gaba ɗaya duk wannan maganganun da ta gaya ma Sgr ba'a cikin hayyacinta tayi su ba,batasan ma ta furta mashi su ba,Zafin raɗaɗin ciwo ne yasa ta zazzaga mashi masifa,dama kuma a ƙule take dashi saboda ya ƙuntata mata sosai,kuma ya kira jinin da takeyi da ƙazanta abun yayi matuƙar ƙona mata rai,hada ƙarin hakan yasa ta balbaleshi da faɗa,
Tun tana tafiya da ƙafafunta har suka gaza ɗaukarta,ƙarshe a bakin shiga corridor ɗin ɗakinsu,ta yanke jiki ta faɗi ƙasa saman tiles tana birgima,hannunta dafe da mararta,gashi babu wani a kusa balle ya kawo mata agaji,

Kamar yadda sehrish ta kwana waje saman tiles,haka sgr ya kwana zuƙunne saman guiwowinsa,kanshi na asaman gadonshi,Aranar bai runtsa ba,bacci ya ƙauracewa idanuwanshi,

Wuraren sallar asuba,Jahad ta fito daga ɗakin azmee tana ƙoƙarin shiga bedroom ɗinsu,idonta suka sauka akan sehrish dake kwance a ƙasa,gashin kanta duk ya rufe fuskarta,da ƙarfi ta ambaci Sunanta SEHRISH,da gudun gaske ta ƙarasa tare da zubewa saman guiwowinta agaban sehrish ɗin,
  "Innalallahi'wa'innalairrahiji un,Sehrish!meya faru dake ne!nashiga uku!Aunty Azmee!!!"duk tabi ta ruɗe,musamman data ga jini ya 6ata wandon sehrish ɗin,sai tayi tsammanin kodai taji wani mummunan rauni ne,Jijjiga jikinta tashiga yi tana cigaba da kwalama Azmee kira,
   "Aunty azmee!Hosana!dan Allah kuzo ku dubamin!meya faru da sehrish ne!"
   A ruɗe ta miƙe tare da tunkarar ɗakin azmee,tura ƙopar tayi ta faɗa ciki a hargitse,Adai dai lokacin Azmee ta kammala sallar asuba,juyowa tayi tana kallon jahad ganin hawaye asaman fuskarta yasa ta miƙe da sauri ta tunkareta tana tambayarta
   "Jahad lafiya meya faru ne"
  Muryarta har shaƙewa takeyi wurin ambaton sunan sehrish"Aunty azmee sehrish!bansan meya faru da ita ba,gata can kwance a ƙasa bata motsi,ga jini a jikin wandonta....."tunkan taƙarasa maganar Azmee ta zabura da gudu ta fita daga ɗakin,itama jahad ɗin tabi bayanta da sauri,
  Ƙarasawa azmee tayi wurin da sehrish take akwance,ta zuƙunna tana ƙare ma jikinta kallo,tsananin tausayinta ne ya kamata,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin cikin halin ha'ula'e,
   Hannu tasa tare da shafa fuskarta,busassun hawayene asaman fuskarta,la66anta duk sun bushe ƙamas dasu,
ɗagowa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tana kuka,
   "Ki kwantar da hankalin ki,ina tunanin suma tayi ne sakamakon Ciwon cikin da tayi,Jinin dake ajikinta na al'ada ne,"
  Jin haka yasa jahad ta tsagaita da yin kukan,har hankalinta ya ɗan kwanta duk da akwai sauran damuwa atattare da ita,
  "Aunty azmee duk laifin mu ne ni da hosana,da ace bamu tafi mun barta a ɗaki ita kaɗai ba,da duk hakan bata faru ba,Allah kaɗae yasan tun yaushe take kwance a wurin nan,"
   "ɗaukomin ruwa,in yayyafa mata,"
Da sauri jahad ta nufi fridge dinsu,hannunta har kerma yakeyi wurin yin saurin ta buɗe,bottle water ta ɗauko,sannan ta dawo wurin azmee ta miƙa mata,kar6a tayi ta 6alle murfin ta ɗan kur6i ruwan abakinta sannan ta fesar dashi asaman fuskar sehrish,
  Dogon Numfashi taja,tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,muryarta ƙasa ƙasa tashiga fadin"Cikina zafi,Ciwo yakeyi mun!dan Allah abani magani nasha,kada na mutu,"
  "Jahad dauko mata magani,yana nan ajiye saman drawer ɗina,"juya jahad tayi da gudu ta nufi ɗakin azmee,
    Hannu azmee tasa tare da ɗago da kan sehrish ta azata asaman laps ɗinta,kafa mata ruwan tayi abakinta,a hankali tashiga kwankwaɗar ruwan,dama makoshinta a bushe yake,
   Dawowa jahad tayi hannunta ɗauke da maganin ta miƙa ma Azmee, bayan ta kar6a ta curo mata shi guda biyu ta sanya mata abakinta,tare da ruwan ta haɗiya,
  Bayan ta kammala sha,ta mika ma jahad robar ruwan"ki mayar dashi a fridge,bari na taimakata mu shiga daga ciki,"
   Dakyar ta cuccu6i sehrish,don ma ba wani nauyi ne da ita ba,cikin bedroom ɗin nasu ta shiga da ita,Jahad tabi bayansu,
  Toilet tashiga da ita,jahad sae faman zirga zirga take yi acikin bedroom ɗin nasu,duk wannan budurin da akeyi hosana nacan ɗakin azmee naɗe cikin bargo tana bacci,
   Muryar azmee tajiyo daga cikin toilet ɗin tana yi mata magana"Pad zaki miko mun,tare da pant ɗinta,"_
  Jiki na rawa jahad,ta ƙarasa gaban wardrobe ɗinsu,wurin kayan sehrish ta ɗauko mata pant,sannan ta haɗo mata tare da pads,
   Abakin ƙopar toilet din ta tsaya tare da ɗan knocking kopar,zuro hannu azmee tayi ta kar6i kayan,
  Komawa jahad tayi saman gadonsu,ta zauna tana jiran fitowarsu daga cikin toilet ɗin,
  Within mins,Azmee ta fito daga cikin toilet ɗin,hannunta dafe da sehrish,duk ta rurruketa gudun karta faɗi,Waist dinta na ɗaure da farin towel,sae faman cizon la66anta takeyi,saboda raɗaɗin da take ji har lokacin bata dawo cikin hayyacinta ba,
  Asaman bed ɗinsu Azmee ta kwantar da ita,jahad ta yafa mata bargo asaman jikinta ta lullu6eta,
  "Sannu sehrish,Allah ya baki lafiya," acewar jahad,
   Dama ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne,su da suka son zafin abun gashinan sun taimaka mata,saboda suma sunayi kuma sunsan cewa lalurace,sannan sunsan irin raɗaɗin da takeji ajikinta,dayawa Wasu mazan basu son ya abun yake ba,tunda bayi sukeyi ba,shiyasa har suke ganinshi amatsayin ƙazanta,kuma basu yi ma mata uziri,aduk lokacin da sukayi kuskuren da jini ya bayyana ajikinsu,Wasu mazan nake nufi ba duka aka taru aka zama ɗaya ba,Haka matan ba,bakowa bace ke taimakon ƴar uwarta ba,acikin irin wannan yanayin na period,
   "Sannu Allah ya baki lafiya,"azmee ce tayi maganar,yayin da idanuwanta ke akan sehrish,wadda ta runtse idanunta tana ta faman ciccije la66anta,
   Bata bar ɗakin nasu ba,har saida bacci ya ɗauki sehrish sannan tayi masu sallama,
  Kwanciya jahad tayi agafenta,suna fuskantar juna,zuba mata ido tayi tana kallonta,cike da so da ƙauna,
   A haka har bacci ya dauketa,

A 6angaren Sgr kuwa,ko sallar asuba bai samu ya halarta ba,Acikin bedroom ɗinshi yayi sallar,komawa yayi saman katafaren gadonshi ya kwanta yayin da blue eyes dinshi ke kallon Ceilling,Kalaman sehrish ne suka shiga dawo mashi acikin zuciyarshi,bakomai ne yafi tsaya mashi aranshi ba fa ce kalmomin nan guda biyu da ta kirashi dasu,MARA TAUSAYI MARA IMANI!sannan kuma tayi comparing ɗinshi da wannan fasiƙin mutumin, yaji raɗaɗin abun sosai acikin zuciyarshi,tayi matuƙar ɗaure mashi kai,Ko a ina tasamu ƙwarin guiwar gaya mashi magana?duk irin yadda take jin shakkarshi?yarinyar da ko cikin idonshi tsoran kallo takeyi,balle har ta ɗaga mashi yatsa,
    Gyara kwanciyarshi yayi,ya koma yana fuskantar right hand ɗinshi,sannu a hankali bacci ya dauke shi batare da ya shirya yin shi ba,

  Wuraren ƙarfe Takwas na safe,jahad na cikin bacci,taji shessheƙar kuka acikin kunnuwanta,buɗe idanuwanta tayi tare da wurgasu wurin da take jin sautin kukan,Sehrish ta gani zaune ta jingina bayanta a head board ɗin gadon,sae kuka takeyi kamar wadda ta rasa wani mai mahimmanci arayuwarta,
  Da sauri jahad ta miƙe zaune,tana kallonta tace"Sehrish!lafiya kike kuka?ko haryanzu ciwon cikin ne"?
  Girgiza kanta tayi alamar a'a,
"To ki faɗamun meke damunki ne"?da damuwa a fuskarta tayi maganar,
  Cikin shesshekar kuka Sehrish ta soma magana,
   "Jahad!na shiga uku!najama kaina bala'e,Jiya nayi ma babban yayanmu rashin kunya,batare da sanina ba,wlh sai yau da safe na tuna duk abunda ya faru,nasan cewa bazai ƙyaleni ba,Dole ya hukunta ni"ta karasa maganar tare da sa hannu tana matsar hancinta,
  Hankali atashe jahad tace"Sehrish!kodai mafarki kikayi ne?ae babban yayanmu bai dawo ba,kin manta sun tafi damaturu ne"?tayi maganar tana ƙoƙarin fahimtar da ita,
  "Wlh jahad ba mafarki nayi ba,jiya ya dawo acikin gidan nan,yana nan a part dinsa,"
   Hannu jahad tasa tare da dafe saitin zuciyarta adan tsorace tace"Munshiga Uku!garin yaya har kikayi mashi rashin kunya?kuma kina acikin hayyacinki babu magagin bacci atare dake"?
  "Bana acikin hayyacina jahad,zafin ciwone yasa na balbaleshi da masifa,har ina nuna shi da yatsa..."kaf ta kwashe duk abunda ya faru a tsakaninsu ta sanar ma jahad,
   Hannu jahad tashiga tafawa tana faɗin"wlh babu ruwana!sehrish kin shiga uku,mai kwatarki a hannunshi yau sai Allah,hukuncinki yafi ƙarfin ayi maki shi acikin gidan nan sai dai yakai ki can headquater dinsu,"
Jin wannan maganar,ya ƙara ɗaga hankalinta,fashewa ta kuma yi da kuka,
  Lallashinta jahad ta shiga yi"Am sorry,zolayarki nakeyi,amma gaskiya sehrish Anya baki sha Codine ba?Yo ni ko giyar wake nasha,ae bazan iya tunkarar babban yayanmu ba,balle har in gaya mashi irin zafafa kalaman da kika yada mashi,"
   Cikin shesshekar kuka tace"dan Allah jahad ki bani shawara,kodai in gudu in bar gidanne?kinga su daddy basu nan,zai iya kashe ni,"
   Shiru jahad tayi tana saƙa wani abu aranta,sehrish kuwa ta zuba mata ido tana jiran jin shawarar da zata bata,
  "Kinsan me!kada ki kuskura kije bashi haƙuri,Dama kin faɗa mashi cewa kada yayi tunanin zaki gudu kibar gidan ne,ko kuma zaki zo bashi hakuri,Sannan kuma kince mashi ba zaki ƙara zuwa part dinshi ba koda ace kin kammala ƙazantar ne,Inaso ya tabbatar da cewar dagaske kike mashi bada wasa ba,hakan zaisa abun ya tsaya mashi acikin ranshi kuma zaiji shakkar ƙara faɗa maki irin waɗannan kalaman saboda gudun kar girmanshi ya faɗi,sannan idan yaga kwana biyu baki je yi mashi aiki ba,ina da tabbacin cewar zai nemeki ne,Amma muddin kika je bashi hakuri,wlh sai kinyi danasani ne,"
  "Amma jahad,rashin kunya fa nayi mashi,yakamata na bashi hakuri in ba haka ba Zai gane cewa ina acikin hayyacina na gaya mashi magana,kuma zai dinga yi mun kallon mara kunya ƙarshe ma ya tsane ni gaba daya,"
  Murmushi jahad tayi tare da cewa"indai bazai ta6a lafiyar jikinka ba toh da sauki,ƙwara yayi maki kallon mara kunyar,akan dai kije bashi haƙuri,nasan bazaki fahimce ni ba,A yanzu amma nan gaba zaki ga amfanin yin hakan da kikayi,"_
  Zugudum sehrish tayi tana doubting akan abunda jahad ta faɗa mata,Anya kuwa jahad ba hanyar banza takeson ɗaurata ba?in ba haka ba saboda me zata hana ta zuwa bashi haƙuri,bayan itace mai laifi,A matsayin shi na mijinta kuma yayanta,bai kamata tayi mashi hakan ba,sannan kuma taƙi zuwa bashi hakuri,
Shigowar azmee ne ya katse mata zancen zucin nata,atare suka juya suna kallonta,
   "An kammala breakfast,yana a dining yana jiranku,"
  Ta karasa maganar tare da kai idanunta kan sehrish tace"Ya jikin naki"?
"da sauƙi alhamdullah,nagode ssai da irin kulawar da kuka bani,"
  "Kada ki damu ae duk yiwa kaine,Amma naga kamar hawaye akan fuskarki,Ko haryanzu akwai ciwon ne"?
  "A'a,naji sauƙi sosai,"
Murmushi azmee ta saki,kafin ta juya ta fuce daga ɗakin,
   "Jahad kije kawai kuyi breakfast ɗin,Ni zan zauna a ɗakine,kada mu haɗu da babban yaya,Don nasan bazaiyi mun da kyau ba,"
    "kada kisa damuwa aranki mana,duk kin bi kin tashi hankalin ki,Da yunwa zakiyi ta zama ne?bazaki ci komai ba"?
   Shiru tayi ba tare da tace komai ba,
  "Okey,zan kawo maki breakfast ɗin aɗaki sai kici hakan yayi maki"?
  Ɗaga mata kai sehrish tayi"Eh,ki kawomin anan,zan fi samun kwanciyar hankali,akan in fita wajen,"
  Saukowa jahad tayi daga saman gadon,ta buɗe kopa ta fuce daga dakin,
  Ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunani ta shiga yi ko a wani hali babban yaya yake ciki,Yayi bacci jiya ko baiyi ba,Allah yasa dai kalamanta basu ta6a mashi zuciyarshi ba,

shigowa jahad ta kumayi hannunta ɗauke da madaidaicin tray,kayan tea ne sai chips da sauran abunda baza a rasa ba,Asaman drawer ta ajiye mata shi,sannan ta juya ta fuce daga ɗakin,
  Matsawa tayi kusa da trayn,sannan takai hannu ta ɗauki cup of tea ɗin tana ɗan kur6arshi,
   Cikin ƙankanin lokaci ta kammala yin breakfast ɗin nata,
   Zama tayi cike da fargabar abunda zai biyo baya,
   Ranta ne ya bata cewar,ta jaraba kiran aunty azeema ta sanar da ita abunda ya faru atsakaninta da sgr,may be ta samu shawara mai kyau a wurinta,
  Da sauri ta ɗauki wayarta dake ajiye saman gadon,contact ta shiga ta lalubo numbarta,ta danna mata kira,tana fara ringing,Azeema ta ɗaga kiran nata,
  Tunkafin tafara magana hajiya azeema tace"2 days ba hello ba hi ko?har kin fara mantawa dani ko,"
  Murmushi sehrish tayi tare da cewa"ba haka bane,Aunty azeema kusan kullum ne saina nemi layinki,amma baya shiga,"
  Azeema tace"Hakane fa,nifa wayata indai bani na kira mutun ba,da wuya ne a same shi,kullum busy nake,"
  Shiru sehrish tayi tana tunanin ta ina zata fara kora mata jawabi,
  "Ina sauraronki,Har yanzu ba wani cigaba a zamanki dashi"?_
   Nan fa sehrish ta samu ƙwarin guiwar sanar da ita duk abunda ya faru atsakaninsu daren jiya,
  Tayi tunanin aunty azeema zatayi mata faɗa ne,amma da buɗar bakinta sai cewa tayi"Very Good!hakan da kikayi mashi yayi mun dai dai wlh,"
   Sakin baki sehrish tayi tamkar tana agabanta,kusan bakinsu ɗaya da jahad,
  "Kada ki kuskura kije bashi haƙuri!nafi so ya gasgata kalamanki"
  Cike da mamaki sehrish tace"Aunty azeema dagaske kike?kada na bashi haƙuri"?
  "Ƙwarai kuwa,ina goyon bayan hakan ɗari bisa ɗari,kuma kada ki kuskura kije part dinshi da sunan aiki,Ki rabu dashi,dama ae yace kada ki koma mashi har saikin kammala kazantar kibarshi a hakan,kada ki wani ji tsoro,"
  Lumshe ido sehrish tayi tare da ware su fuskarta da dan murmushi tace"Shikenan aunty azeema bazanje ba in sha Allah,"
  "Namanta ban sanar dake ba,nafa dawo nigeria,tun jiya amma na wuce damaturu,bazan samu zuwa nan ba yanzu saboda abunda ya faru na rasuwar modibbo,amma kada ki damu zan bada saƙo ta wurin junaid,naji yace zai biyo Abusufyan idan ya tashi dawowa,zan bashi ya kawo maki har gida,Sannan zanyi maki bayanin yadda zakiyi amfani dasu,koda ta wayane,"
   "Nagode sosai Aunty azeema,Allah yasaka da alkhairi,Amma yaushe zaki dawo nan?don nayi kewarki sosai,"
  Dariya hajiya azeema tayi tare da cewa"Very soon zan dawo,"
  Sehrish tace"to shikenan,Allah ya kaimu lokacin,"
"Ameen my daughter,"
  Sun jima suna waya kafin daga bisani ta ajiye wayar,har hankalinta ya kwanta,duk da akwai sauran fargaba atare da ita,

saukowa tayi daga saman gadon,Wardrobe ta nufa,hannu tasa ta buɗe,Arab gown ce ta ɗauko pink colour,tare da mayafinta shima pink ne amma bai ciza ba,kamar na rigar,zura kayan tayi ajikinta,sannan ta koma gaban mirror ta zauna,zuba ma mirror din ido tayi tana kallon fuskarta,ta cikin madubin,yayin da zuciyarta ke tariyo mata abunda ya faru adaren jiya,

A 6angaren Sgr kuwa,wata irin matsiyaciyar yunwa ce ta farkar dashi daga bacci,saukowa yayi daga saman gadon,Jallabiya ce ajikinshi,wuce wa yayi wurin closet ɗinshi,withins mins ya shirya kanshi cikin jeans da t shirt Maroon colour,rigar ta fito da surar jikinshi saboda ta ɗanyi tighting ɗinshi,Ƙafarshi na sanye cikin Canvas sneakers,
   fitowa yayi daga part ɗinsa,Ya nufi downatairs,a natse yake taka staircase din har ya sauko down,Su jahad na zaune ita da hosana saman Sofa mai mazaunin mutun uku,suka jiyo takun takalmanshi,

  ɗagowa sukayi atare suna kallonshi,lokacin da ya ƙaraso wurinsu,da sauri suka haɗa baki wurin gaisar dashi,
  Batare daya kallesu ba,Ya amsa masu gaisuwarta su,fuce wa yayi daga cikin main palour ɗin,Kaitsaye Motarshi ya nufa,Amstrong na ganin shi da sauri ya ƙarasa tare da buɗe mashi motar ya shiga daga ciki,sannan shima ya bude driver seat ya zauna,
   Kafin ya tashi motar,ya ɗan dago tare da kallonshi ta cikon mirror yace"Sir,Where are we going"?
   "Restaurant,"ya bashi amsa atakaice,
    Shiru amstrong yayi batare daya tashi motar ba,Hakan yasa shi cewa"what are u waiting for"?
  Cikin harshen turanci amstrong yace"Sir,kayi haƙuri da abunda zance,Amma zuwa restaurant ba naka bane,da matsayinka aganka a restaurant ka je cin abinci?kaida ya kamata ace a gida ake girka maka,idan ba damuwa zanje nakawo maka,ka koma ciki pls"
   Tunda ya soma magana sgr yayi shiru yana sauraronshi,saboda amstrong yana ɗaya daga cikin waɗanda suke Control dinshi,"
  Amsa mashi yayi da okey,sannan ya buɗe motar ya fuce,
  Duk wannan abun dake faruwa sehrish na tsaye a wurin window tana leƙen motarshi,taga lokacin daya shiga cikin motar,kuma sai taga ya fito daga ciki,
  Aranta tashiga tunanin ko lafiya,
Dawowa cikin gidan yayi,Part ɗinshi ya koma ya zauna saman sofa yana jiran dawowar Amstrong,dan bala'e ga abinci acikin gidan amma yafi ƙarfin yayi ma wani magana ya kawo mashi abincin,tunda ya ƙori mai aikin tashi,
  Cikin minti goma sha biyar,Amstrong ya shigo cikin gidan hannunshi dauke da ledojin,Su jahad na ganinshi suka shiga gaisar dashi,fuskarshi ɗauke da murmushi ya amsa mashi,sannan ya wuce upstairs sashen sgr,
  Yana barin wurin da gudu jahad ta nufi ɗakinsu,tura kopar tayi ta shiga ciki tana faman ƙwala ma sehrish kira,
   tsaye ta same ta hannunta ruke da wayarta,ganin jahad ta faɗo ɗakin babu sallama yasa tace"Lafiya"?
   Jahad tace"Yanzu naga wannan sojan wanda yake yin driving ɗin babban yayanmu,Hannunshi dauke da ledojin kuma na restaurant ne don naga sunan ajiki,"
   Cike da mamaki sehrish tace"to fa!ko meyasa ya aika akawo mashi abinci bayan ga wanda aka girka agida"?
  Jahad tace"Yanzu haka saboda abunda ya faru atsakaninku ne jiya,shiyasa yaƙi cin abincin gidan,"
   Jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,
   "Yanzu haka,saboda yana ƙyamar girkina ne saboda ina yin period,shiyasa bazaici abincin gidan ba,"acewar sehrish,
  Jahad tace"Amma ae bake kikayi girkin ba,Aunty azmee ce ta girka,Gaskiya nafi tunanin cewa wani abunne daban yasa bazaici abincin gidan nan ba,"
   Murmushi sehrish ta ɗanyi tare da cewa"kinsan Allah babban yaya bazai iya cin abincin nan ba,Ina nan dake ƙarshe sai dai azubar da shi abanza"
     Jahad tace"Mu zuba ido mu gani,zaici ko bazaici ba,"

***

Excuse sir!muryar amstrong ce ta dawo dashi daga zurfin tunanin da ya faɗa,
   Muryarshi a kasalance yace mashi"Come


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login