Showing 234001 words to 237000 words out of 307403 words
Chapter 79 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete
masu wuta,ta ko'ina sautin bindigu kake ji,Sunga tashin hankalin da basu ta6a gani ba,Anan Suka kashe ubaid da kuma Uba,Daga ciki hada iyayensu mata,domin sunyi ƙoƙarin Ɗauko makamai a cikin ɗakunansu da niyyar su taimaki Mazajensu,wannan ya tabbatar masu da cewa suma matan suna da sa hannu a aikata ta'addanci tunda har sunsan suyi harbi da bindiga,aikuwa suka kashesu gaba ɗayansu,A ranar an zubda jini kamar kamar mi,Daga cikin waɗanda tsautsayi Ya ritsa dasu,Hada Jabeer bawan Allah baiji ba bai gani ba,Suka kashe shi,A lokacin yazo duba jikin Azmee yaga in ta sauka lafiya,Shigowarshi keda Wuya,Sojojin suka harbeshi saitin zuciyarshi,Anan Ya yanke jiki ya faɗi matacce,
A ƙarshe mutun uku suka tsira,Azmee data 6oye a ƙarkashin gadon mahaifiyarsu,hannunta ruke da jaririnta, itama Saratu Ta tsira a wannan Lokacin,Sae kuma Gali tare da Ya sayyadi da basa acikin gidan abun Ya faru,
Azmee bata tashi sanin Jabeer ya rasu ba,Sae a washe garin ranar,ta fito daga ƙarkashin gadon hannunta ruƙe da jaririnta,jini duk ajikinshi domin ba'ayi mashi wanka ba,haka ta fito dashi rungume a hannunta,ta tsorata da ganin yadda sojoji suka wanke gidan da jinin Iyayenta,Tasha kuka kamar ranta zai fita,A lokacin Allah ne kawai Yayi zata rayu,A nan tsakar gidan taga gawar Jabeer yashe a ƙasa,ga gawawwakin Sauran Ƴan uwanta,nan take ta yanke jiki ta faɗi kasa a sume,jaririn hannunta ma Ya faɗi wanwar yana ta tsala kuka,
Bayan wasu kwanaki da yin wannan Tashin tashinar,Azmee ta farka a gadon asibiti,bayan ta shafe sati biyu kwance bata acikin hayyacinta,
Tasha kuka kamar ranta zai fita,ita sam bata damu da iyayenta da aka kashe mata ba,Mijinta tafi ji,shi da baisan komai ba,Bai aikata laifin komai ba,Amma an haɗa dashi an kashe,
Hamma Ghali ne Ya kawo ta asibitin,Lokacin data farka tare da sayyadi da saratu tagani tsaye akanta,sune ke jinyarta tun daga wannan lokacin rayuwarsu ta tagayyara,mutane suka ƙyamace su,kowa gudunsu yake yi,saboda sanin Abunda iyayensu suka aikata,Idan suka biyo hanya har jifarsu akeyi da duwatsu ma,Dole suka daina shiga cikin jama'a,
Tundaga wannan Lokacinne,Hamma ghali Ya tunzurasu akan su ɗauki fansar kisan wulakancin da Family ɗin SALAHUDEEEN HOSSEIN suka Yi masu,Kunji silar shigar Azmee ƙungiyarsu,Wadda bayan Su salahuddeen sun ruguzata a karo na biyu,Ghali kuma Ya tada ƙungiyar ta hanyar wasu abokanan Iyayensu da suka rage ba'a kamasu ba,A lokacin ne kuma Salahuddeen yabar duniya,Saboda ɗaukar fansa Azmee ta jefa kanta cikin halaka,duk don saboda Mijinta da aka kashe,ko lokacin bataso shiga ƙungiyar ba,Hamma ghali ne Ya tunzurata sosai har saida ta amince Ta tsunduma tsulundum,Da ita da Ya Sayyadi da saratun dukkansu,Jinjirin da Azmee ta haifa ba kowa bane,Face Haroon shine ɗanta da take dashi ɗaya tilo,
Shiri na musamman sukayi domin ganin sun tarwatsa Family ɗin salahuddeen,Wannan yasa suka raba kansu,Ya sayyadi yabi Ta 6angaren Abusufyan dake zaune a kano,Da biyu ya shiga rayuwar abu saboda kawai Ya cimma burinshi na Ƙuntata rayuwar Abusufyan,Azmee kuma ta hanyar hajjaju ta biyo masu,Sai da tayi bincike sosai ta gano cewa hajjaju tana da kusanci sosai da mutanan gidan kuma itace ke kai masu ƴan aiki duk in suka buƙata,Wannan dalilin ne yasa taje har gidan hajjaju ta nemi da ta taimaka mata ta samo mata aiki a gidan Abban sojoji,
Ganin yarda take roƙonta,Ga ƙaramin yaro yasa hajjaju ta tausaya mata,har dai ta amince zata sama mata aiki a gidan,kuma cikin sa'a Batare da ta sha wahala ba,ta samu aiki agidan duk da dama sai da tayi ma hakan shiri........"
*Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*
*Masu cewa Basu son littafin abban sojoji na kuɗi bane,Littafina na kuɗi ne,Book one ne kawai nayi shi kyauta,Amma 2 da 3 Na kuɗi ne,Dukansu 300 ne duk maiso yayi mun magana kaitsaye Amma message ta whatsapp 08103884440*
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋
𝑗𝑜𝑖𝑛 𝑡𝒉𝑖𝑠 𝑙𝑖𝑛𝑘 𝑡𝑜 𝑓𝑜𝑙𝑙𝑜𝑤 𝑚𝑦 𝑇𝑖𝑘𝑡𝑜𝑘 𝐴𝑐𝑐𝑜𝑢𝑛𝑡👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت❤🤍❤
𝐹𝑎𝑡𝒉𝑒𝑟 𝑂𝑓 𝑆𝑜𝑙𝑑𝑖𝑎𝑟𝑠
*🔥𝕋𝕒𝕜𝕦𝕟 𝕂𝕒𝕣𝕤𝕙𝕖🔥*
_Ga masu karanbanin haɗa mun document,koda gigin wasa kada wanda ya kuskura Ya ƙara haɗamun document,kuma bazaku ta6a samun Complete document na takun ƙarshe ba,saboda ba yanzu zan haɗa shi ba koda na kammala littafin,Dole sai a wurina za'a same shi from page one to the end,if not babu wanda zai baku shi cikakken shi,Sannan Zan canza Lokacin posting_
Lokacin dana fara aiki acikin gidan nan,mahaifinku ya mayar dani tamkar ba ƴar aiki ba don alokacin ya tambayeni game da mahaifin yarona,na sanar dashi cewa ya rasu dalilin hadarin mota,daga haka kuma na kulle bakinshi don kar ya nemi jin wani bayani agame da dangina,Ya ɗauki Haroon ɗansa,Kuma Ya nuna yana so inbar mashi haroon ya kasance acikinku,baya son Ya taso a matsayin bare,Ba ƙaramin daɗi naji ba,Duk da mummunan ƙudirin da nake dashi,
Tsawon Lokaci da fara aikina cikin gidan nan,na fara shirya maku maƙarƙashiya,da niyyar tarwatsa farin cikin gidan nan,Amma silar kyautatawar da mahaifinku keyi mun da kuma wasu daga cikinku yasa na ɗan dakata,Akwai wani hadithi da manzon Allah (SAW) yake cewa"Jubilatul ƙulubu ala hubbi man ahsana ilaiha,Wabugudi man Asa'a ilaiha,(An halicci zuciya da Son mai kyautata mata da kuma ƙin mai munana mata),Wannan kyautatawar da kuke Yi mun ita ta Jani har izuwa tsawon lokacin nan Batare dana Aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ba,a lokacin banyi tsammanin zan faɗa tarkon son wani acikinku ba,Sai gashi na kamu da tsananin Son mahaifinku,Saboda yafi kowa kyautatamun,Ya yarda dani sosai Kuma ya damu dani akan kowa na cikin gidannan,Da yake ita zuciya ba ƙashi ne da ita ba,bansan lokacin dana afkawa Sonshi ba,sai kuma na fara kishi da Alexandra,don nasan cewa muddin tana acikin gidan bazan ta6a samun soyayyar mahaifinku ba,Wannan dalilinne Yasa nayi Amfani da sihirina wurin Ƙuntata mata,ta fara jin ƙunci acikin ranta,Zaman Nigeria ya gagareta,babu arziƙi ta tattara tabar ƙasar nan,batare da ta ƙarasa shayar da Junaid ba,ta barshi cikin tsummanshi yana ɗan jinjirinshi.......... "
Bata ƙarasa maganar ba,Sakamakon wani irin kukan Kura Da Mommy tayi takai mata damƙa a wuyanta,Muryarta adisashe take magana hawaye na zuba"Amma kin cutar dani Azmee,Kin cuci rayuwata,Da kuma rayuwar Junaid,Ashe kece silar dana tafi nabar mijina da ƴa'ƴana,I will neva forgive you....."kasa ƙarasa maganar tayi,nan take ta fashe da kuka,Daƙyar Abba ya samu ta saki wuyan Azmee,har tangal tangal tayi zata faɗi da sauri Jahan ya ruƙota,Ya taimaka mata ta zauna saman hannun kujera tana kuka"matar nan tajima tana cutar da rayuwarmu,Dama ance makashinka Yana tare dakai"Sosai take kuka,Ita kanta Azmeen kukan takeyi,Su Sehrish da Jahad dukkansu kuka sukeyi,Oummansu ma idanuwanta cike tab da kwalla,
Bayan ta tsagaita da yin kukan taci gaba da cewa"A lokacin mahaifinku Ya ɗauki Junaid ya bani shi don inci gaba da shayar dashi,babu yarda Hajiya azeema batayi ba akan Ya bata Junaid ta shayar dashi,Amma ya nuna cewa yafison na shayar dashi,Ba don komai ba Sae don baison Junaid Yayi nisa dashi,tunda ita a lagos take zaune,bayan ya damƙamun Amanar Junaid,naci gaba da shayar dashi,Allah shine shaidata,Inason Junaid sosai,Fiye da son da nake yi ma haroon,Sai na dinga ji kamar ni na haifeshi,har banso su Fawan suzo ɗaukarshi,gashi lokacin haushina suke Ji saboda ina ƴar aiki ƙasƙantacciya an bani Ƙaninsu ina shayarwa,ni kuwa daɗi na dinga Ji,Saboda ina tunanin ta hanyar Junaid zan samu soyayyar mahaifinku don tsakani da Allah nike sonshi hakan yasa banyi mashi wani sihiri ba wai don ya so ni,babu wanda yasan Inasonshi,Sae Laila matar Ishaq da yake ƙawatace duk da ba wani shiri nake da ita ba,Amma ina neman shawara awurinta,haka Hajjaju ma muna mutunci da ita,Dukkansu babu wanda yasan Ainihin wacece Ni,Duk irin son da nake yi ma Abbanku bai ta6a lura ba,Naso na sanar dashi amma ina tsoron Yace baiso na,bansan wani hali zanshiga ba,Lokacin da Junaid Ya fara tasawa,abunda Ya bani tsoro dashi irin wayon dake gare shi,Kullum agabanshi nake yin waya cikin harshen fulatanci,kwatsam wata rana,bayan na kammala waya,sai yake ce mun ae Yaji duk abunda nace,A lokacin na ɗauka da wasa yake yi don nasan baijin fulatanci,Sai cewa nayi toh ya faɗamun me nake cewa acikin wayar,ba zato ba tsammani Yaron nan Ya fassara mun maganganun da nayi acikin wayar,hankalina yayi mugun tashi,Ko makaranta ba'a sanyashi ba,na ruƙe shi ina tambayarshi a ina ya koyi harshen fulatanci,Sae ce mun yayi a wurina yaji ina yi,duk in zanyi waya,tunda naji haka saina tsorata dashi,tabbas wata rana zai iya tona mun asiri,tunda har ya iya yaren da nake yi wanda a waya kawai nake magana da harshen,Kawai na yanke shawarar In juye mashi tunaninshi ta yadda bazai ta6a fahimtar komai ba,Tun daga wannan lokacin Junaid Ya zama soko,Bai ɗaukar karatu ko mis'ƙala zarratin,Nasan na cuci Junaid,Da ace Yayi ilimi da ina da tabbacin cewa zai kasance ɗaya daga cikin ƴaran da duniya zatayi alfahari dasu saboda baiwarsu,A kwana a tashi,Rana ta farko dana fara Yin tozali da Rafayet,Bazan ta6a mantawa da wannan Lokacin ba,dawowarshi kenan daga U.S,Ya soma tambayar ina Babyn da Mommynsu ta bari,Su fawan ke sanar dashi cewa Yana a wurin mai aikinsu har suke bashi labarin cewa ni na shayar dashi,Ranshi yayi mugun 6aci Yasa su kirani,Na fito ɗauke da Junaid a hannuna,ya rufesu da faɗa don me za'a ba mai aiki ta shayar da ƙaninsu,sun tabbatar da tsaftar jikina ne,A karshe ya kar6e Junaid daga hannuna,Ya wuce dashi dakinshi,
Tunda na koma ɗaki,na kasa runtsawa saboda tunanin Rafayet,Kyawun fuskarshi dana surarshi suka ɗebeni har na Fara kamuwa da sonshi,Maimakon da yayi mun faɗa inji haushinshi,Sai ma sonshi da nake kara Yi,na kasa samun natsuwa kullum in naje kai mashi abinci,ban iya kawar da idanuwana daga kallonshi,shi kuwa bai ta6a ɗago da idonshi ya kalleni ba a wannan lokacin balle insa ran zan same shi........."dakatawa ta ɗanyi da yin maganar,Yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta,
Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,Kallon Sgr kawai take yi,Shi kanshi abun ya ɗaure mashi kai,bai ta6a sanin wannan zancen ba,Mommy kuwa wani irin kallo take binta dashi,
"Daƙyar na samu Sgr ya fara tanka mun in na gaishe shi,Ba ƙaramin daɗi nake ji ba idan na kai mashi abinci yaci,ni kaɗai nayita haukan soyayyata don shi baisan ma inayi ba,A kwana a tashi Ya koma U.s A ranar kamar nayi hauka,bayan tafiyarshi na soma tunanin Me ya kawoni gidan?Me nake jira da ban aiwatar da mummunan ƙudurin daya kawoni ba,Saboda jin daɗin da nake ciki,Na manta cewa ɗaukar fansa ta kawoni gidan,Komai na more rayuwa ina samu,Inci me kyau in sha me kyau in kwana a me kyau,ga Albashin da Abba ke bani harya zarce na wani likitan,ko lokacin bani albashina baiyi ba,Yana yawan dunƙulo kuɗi ya damƙa mun,Yace ga wannan in ina buƙatar wani abu,Insa driver yakaini kasuwa inyi siyayya,Wani irin daɗi nake ji,koba shi ba da yawan lokutta Yusuf Yana bani kuɗi hakanan kyauta yace mun ga wannan Inyi amfani dasu,Ganin irin ƙaunar da suke nuna mun saina fara tunanin kodai in janye batun ɗaukar fansar nan tawa,Tabbas a lokacin na fara tunanin yin tuba in koma Ga Allah,Amma sai Dangina suka taso ni gaba,Musamman Hamma Ghali barazana Ya soma yi mun akan kodai na aiwatar da abunda ya kawoni cikinku ko kuma zai ɗauki mataki akaina,na tsorata sosai,Saboda mugune shi,nasan shi sarai,kuma shine Shugaban ƙungiyarmu ta matsafa,komai nake Yi acikin gidan nan akan idonshi nake yi,Duk da bamu atare amma Yana da madubin tsafinshi wanda yake kallon duk wani motsina,Ba don naso ba haka naci gaba da bin umarninshi,A lokacin Haroon na soma ƙoƙarin janyowa Jikina,Na nuna mashi cewa ku ba jininshi bane,Ya daina shige maku,Fansa muka zo ɗauka acikinku,Amma sai ya kangaremun,Yace shi bazai yarda a haɗa baki dashi ba,Wurin cutar daku ba,Saboda Abba yana sonshi,kuma Yanayi mashi duk abunda Yake so,Don haka inma naci gaba dayi mashi magana zai tona mun asiri ne,Jin wannan magana ta haroon Yasa na fara tunanin ta yadda zan juye mashi tunaninshi,Don na lura ɗabi'unsa da halayyarsa ba irin ta dangina bace,Duk da dama ina kokwanto akanshi,Banda tabbacin wanene mahaifinshi,Ganin yana nema yafi ƙarfina sai na sanar ma Hamma ghali abunda Haroon Yace,aikuwa tun daga wannan Lokacin da mukayi waya dashi,Ya sanar dani cewa In kawar dakaina akanshi zanga me zai biyo baya,tofa aikoda yace haka,cikin ƴan kwanaki ƙalilan Haroon ya canza,Ya zama mugun ƙarfi da yaji,Wata muguntar ma ba saina sanar dashi ba,dakanshi yake yi,Ga bin mata da bin maza,Shaye shaye duk wani aiki na shaiɗanci Haroon ya iyashi,nikaina banji daɗin Sauyawar Haroon ba,Iya Cuta dai Mun cutar dashi,Duk da bani bace silar jefa shi cikin halin da yake ciki ba,Amma ni mahaifiyarshi ce,dani akayi amfani wurin Canza mashi tunaninshi,su kuma Su twins Rashin kunyar da suke yi mun ne Yasa nayi masu turen shaiɗanin Aljanu ajikinsu,Waɗanda ke sanyasu suna Neman junansu wanda in har basuyi ba,Aljanun nan ke jibgarsu da bulala,........."sosai Azmee ta fashe da kuka,
Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,wasu ma gaza cigaba da tsayuwa suka yi dole suka zauna,
"About Junaid!Ke da Haroon Waye ya shirya Mutuwarshi"?Sgr ne yayi mata tambayar,
Daƙyar ta tsagaita da Yin kukan ta soma kora mashi bayani,
"Haroon ne Ya shirya mutuwar Junaid,A lokacin Kun fusata shi sosai,dama a ƙule yake daku,saboda bambancin da kuke nuna mashi don ba ahankalinshi yake duk abubuwan da yakeyi ba,Duk da ni naso In kashe Junaid,ko dan in fanshe haushin kisan Mijina da akayi,Nasha Sanya Haroon ya kashe Junaid,Amma sai ya ce mun bazai Iya kashe shi ba,Junaid yana sonshi sosai,Kuma bai aikata mashi laifin da zai kasheshi ba,Har ce mun yakeyi zai iya kashe kowa acikin gidan nan koda kuwa Abbane,Amma banda Junaid,Ni gaskiya aranar bansan maiya ƙona mashi rai ba,Har ya bada Umarnin akashe mashi Junaid,
a ƙa'ida Miyagun dake yi mana aiki,basa Yanke hukunci in ba sun sanar dani ba,Dole sai in ni na basu umarni kaitsaye suke aiwatar da abu,Haroon ya basu Umarni su kashe Junaid su kuma Sun kirani a waya sun sanar dani cewa Haroon Ya basu Umarnin su kashe Junaid,Shin da sanina koba da sani na ba,"!nan take nace masu karsu kuskura su kashe shi,Su san yarda za'ae su ɗauke Junaid daga cikin motar sannan su ƙonata yarda kowa zaiyi tunanin ya mutu,Nayi hakanne saboda banaso Haroon yaji cewa Na hana su bi umarninshi don zai canja wata hanyarne,sannan Kuma Don Junaid Ya zame mun makamin da zan Yaƙe ku dashi,
Ƙarin bayani,
Lokacin da Jahad ta fita daga cikin motar ta tsallaka zata siya masu ice cream,Junaid Ya dinga ƙwala mata kira,Ta dinga juyowa tana kallonshi Yana yi mata bye bye,bayan mai ice cream ɗin ya sallami mutanan dake gabanshi,Yace ma Jahad madam guda nawa za'a baki,Ta juya ta bashi Amsa,A cikin wannan Lokacin kafin Jahad ta lalubo kuɗi acikin jakarta ta miƙa mashi,adai dai lokacin,waɗannan miyagun suka buɗe motar,kafin Junaid ya ankara suka shaƙa mashi cocaine a hancinshi gaba ɗaya ya fita hayyacinshi,janyoshi su kayi daga cikin motar da hanzari suka fitar dashi,wanda ya ɗauki Junaid a kafaɗarshi ya juya dashi ta baya inda suka ajiye motarsu ya tura shi aciki,Shi kuma ɗayan Ya jefa bomb acikin motar,Yana barin wurin,Gingimarin Motar nan Ta shararo da gudu,Dama already sun kira wayarshi yana akan layi suna sanar dashi cewa Babu Yaron acikin motar,Atsiyace Yabi takan motar Junaid Ya rugurguzata,Yana sauka ya antaya da gudun gaske,Nan take Bomb ɗin cikin motar Ya fashe,Dama sun ɗibar mashi adadin mintunan da zai tashi,To masu karatu Kunji yadda akai Junaid Ya tsira,Baya acikin motar lokacin da suka take motar,Ko lokacin da Jahad ke ihu tana kuka,Duk a kunnanshi bawan Allah,Yana acikin motarsu sun rufe shi,Sam baya acikin hayyacinshi sai faman shafa glass ɗin motar yake yi yana kallonta,A haka har suka tashi motar da gudu suka bar wurin bayan sun dauki vedion motar naci da wuta wanda suka tura ma haroon,
Yadda akai Sgr yasan game da abubuwan daya fadi ma haroon kuwa,dama tun farko,ya dawo Nigeria ne da niyyar yin bincike,don Mommynsa tasha fadi masa cewa akwae abubuwan dake faruwa ba daidai ba acikin gidan,kuma ta sanar dashi ita bata yarda da azmee ba,wannan dalilinne yasa yazo da shirinshi,a 6oye ya fara yin bincikenshi ba tare da kowa ya sani ba,ana haka kuma Mommynsu ta kirashi ta sanar dashi game da makudan kudin dasu twins suka bukata awurinta,ta tabbatar mashi akwae abunda yake faruwa dasu wanda suka 6oye don a yadda suka bukaci kudin sam hankalinsu ba'a kwance yake ba,gashi itama ta bukaci sai sun shirya tsakaninta da Junaid wanda tana ganin hakan ba mai yuwuwa bane cikin sauki,amman sai gashi sun aikata hakan duk don ta basu kudin,hakan yasa mata zarginsu,jin hakan yasa Sgr yin amfani da Surveillance Cameras wadanda yasa a wasu bangarori na gidan ba tare da kowa ya sani ba don bai barsu a bayyane ba wasu har a cikin chandeliers(fitilun sama) na parlon gidan aka sa,ta nan yake ganin duk abunda ke faruwa har lokacin dasu twins din suka kaima haroon kudin wanda daga baya yabi ya daukesu,koda ace asirin Azmee bai tonu ba ta hanyar ya Mu'allim ba,Sgr na gab da ganota,atakaice ma kusan ya gane bata da gaskia shiyasa ko lokacin da Abu ta sanar dashi dalilin ciwon Sehrish da kuma inda tasan Azmee yayi murmushin takaici,haka lokacin da Marshal Omar ke lallaba haroon akan ya sanar dasu wanda ke bashi umarni yace Sgr yasan komae,wannan kenan.
Azmee taci gaba da bayani "Tunkafin Afkuwar wannan Lamarin,Akwai sihiri ajikin Junaid,Wanda mukayi mashi turenshi,a duk daren duniya,dunƙulen jini na fita daga hancinshi batare da sanin kowa ba,Saboda bai sanar daku ba,bayan Faruwar Accident ɗin nan ni nasa aka killace mun Junaid,kuma na hana kowa Ya cutar mun dashi,Lokacin da kuka sanar cewa Junaid Anyi kidnapping dinshi,Nayi mamaki sosai,Yarda kuka tsara hakan bayan a iya saninku mutuwa Yayi,Sai kuma nayi tunanin cewa Kun 6oye mutuwar Junaid ne saboda mahaifinku gudun kada ku rasa shi,bakowa ya fara Zargina ba,Sae Sehrish da ta tsinci zoben Junaid a cikin wardrobe ɗina,tundaga nan ta fara sanya mun ido,ni kuma nayi kokarin rikitar da ita har ta fara ƴan gane gane..............."
Tunkan takai ƙarshen Maganar,Omar ya katse ta da cewa"Yanzu ina Junaid Yake,"?yayi tambayar tamkar baisan inda yake ba,
Shuru Azmee Ta ɗanyi kafin tace"daga bayan nan Nasa an kaishi gidan Hajiya saratu,Ɗiyar wan mahaifina wadda ke acikin garin nan,"..
"Innalallahi wa'inna ilahirraji'un!!"