Showing 96001 words to 99000 words out of 307403 words

Chapter 33 - Abban Sojoji Takun Karshe Hausa Novel Complete

banyi kuskuren aura ma rafayet ita ba,kasan cewa inason ka sosai,kowa ma yana sonka,kuma zamu iya yin komai saboda farin cikinka,hatta rayukan mu ma zamu iya badawa domin ceto rayuwarka,balle kuma ƴar uwarka?sae ita zata gagara?"
  "Amma..uncle..meyasa ku ka ɗaura mata aure da babban yayan mu?maimakon ni"?daƙyar yake magana,
   "Kayi haƙuri junaid,dama Allah ya ƙaddara cewar ita ba matarka bace,Matar babban yayanku ce,"
   ɗagowa yayi daga jikin Abusufyan din fuskarshi jaga jaga da hawaye hada majina,yana kallon uncle ɗin yace"yanzu kuna nufin cewa,babu ni babu rishi?in haƙura da ita kawai?kun za6i ku rasa ni kenan"?
  ruƙo hannunshi abusufyan yayi tare da sassauta muryarshi yace"haba junaid,in sha Allah ba zamu rasa ka ba saboda sehrish,ae ba ita kaɗai bace ba,Ko ka manta cewar su ƴan ukune?kuma kamanninsu ɗaya,Idan kayi haƙuri zan baka auren ɗaya daga cikinsu,"
  Da sauri Marshal Omar ya katse mashi hanzarinshi da cewar"Wacce acikinsu,"?
  dariya abbansu yayi ganin yadda omar ya ɗan tashi hankalinshi,
  Abbas yace"Uncle,kada fa kayi mashi alƙawarin auren ɗaya daga cikinsu,saboda junaid bai da wayau baisan wasa ba,kuma koda za'ayi mashi aure ba yanzu ba,sae yayi hankali nan da in ya kai shekara talatin,"yana kai ƙarshen maganarshi,Ishaq ya ɗaura da cewar"Bazai yiwu ba ayi ma junaid aure a yanzu,bayan ga yayyensa nan duk sun manyanta kowa na bukatar aure,yayi haƙuri dai akwai matar abokina na nan,yanzu haka tana dauke da ciki,idan ta haifi jinjirin muka ga mace ce,sae ayi masu magana,su ajiye mashi ita,in ta girma lokacin yayi hankali sai a aura mashi ita,"
  Suna cikin maganar nan,Junaid ya sume,a jikin Abusufyan,a ruɗe abusufyan ya shiga jijjiga shi yana kiran sunanshi"Junaid!Junaid!!"
  Hankalin Abbansu atashe yace"Duk laifinku ne!meyasa bazakuyi shiru da bakinku ba,gashi nan ya ƙara sumewa,kuma ina da tabbacin cewar maganganun da kuke gaya masa ne suka ƙona mashi rai,"
  Hannu Omar yasa tare da ɗauko bottle water ɗin dake ajiye saman side drawer dinsa,ya cire murfin tare da mika ma abusufyan,A hannu ya tar6o ruwan sannan ya watsa mashi a fuskarshi,
  Dogon numfashi yaja tare da sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya,
  Shafa fuskarshi Abusufyan yayi tare da cewa"Junaid,"
   Tunkafin ya buɗe idanunshi yace"Uncle mutuwa zanyi,"
  "Junaid dan Allah kadaina kira mana mutuwa,Indai kan sehrish ne,NI NAYI MAKA ALƘAWARIN CEWA ZAN AURA MAKA ƊAYA DAGA CIKINSU IN HAR TANA SONKA,"
  Muryarshi a kasalance yace"Uncle nasan wasa kake yi mun,kada kayi mun alƙwarin da bazaka iya cika mun ba,Zan haƙura kawai in rungumi ƙaddarata,"_
   Wannan maganar da junaid yayi ba ƙaramin kashe masu jiki tayi ba,
Tuni hawaye suka cicciko a idanuwan Abusufyan,muryarshi na kerma yace"meyasa kace haka junaid"?
  "Uncle,bani da wayau,ni yaro ne har yanzu,kowa yana yi mun kallon sakarai,kuma bani da aikin yi,a haka zaka bani auren ƴarka""?
   A hankali wasu siraran hawaye suka shiga gangarowa a saman fuskar Abusufyan,daƙyar ya iya buɗe baki yace"Junaid!duk rashin wayonka baka kaini ba lokacin da ina yaro,bana jin magana har sa'insa nake yi da Mahaifiyata,na iya rashin kunya saboda ni bana jin kunyar kowa,ni ina mu'amala da mata muje party,muje night club,Ka faɗamun ɗaya daga cikinsu wanne kake yi?
  "Ko ɗaya bana yi"ya bashi amsa,
Murmushi abusufyan yayi kafin ya cigaba da cewa"kana da kyakkyawar zuciya junaid kai mutumin kirki ne,kana son kaga farin ciki a fuskar kowannan mu,saboda me Ni zan gaza sanya ka farin ciki?Duk da banajin magana amma ahaka Mahaifin Oummansu Sehrish ya bani auren ƴarsa,Nima don haka daga yau ka sanya aranka cewar na baka Auren JAHAD!idan ma akwai mai sonta cikin yayyenka sai dai yayi haƙuri yabar maka,
   Wani irin Farin Ciki ne ya lullu6e junaid,lokaci guda ya nemi kukan da yake yi ya rasa,bashi kaɗae ba hatta sauran ƴan uwan nasa dake tsaye a wurin ba ƙaramin daɗi suka ji ba,Musamman Abbansu,Yaji daɗi har cikin ranshi,
   Cike da zolaya abusufyan ya kallesu tare da cewa"Ko akwai mai ja acikin ku ne"?
   Fashewa sukayi da dariya gaba ɗayansu,tare da haɗa baki aurin cewa"Mu mun isa?Uba ya mallaka ma ɗansa auren ƴarsa?waya isa yaja daku?ae magana ta ƙare"
   Sae lokacin junaid ya fashe da dariya har fararen haƙoransa suka bayyana masu ɗauke da matsakaiciyar wushirya siririya,mai kyan gaske,
  "Surukina,fadamun me kakeso yanzu"?
  Cikin shagwa6a junaid yace"Maganin ciwon kai,sannan ina jin yunwa sosai,"
   "Bari inyi ma jahad magana takawo maka,hakan yayi maka"?
  Cike da jin kunya junaid ya rufe fuskarshi da tafukan hannayenshi,yana dariya ƙasa ƙasa,
   Zolayarshi suka shiga yi,har sai da suka sanya shi farin ciki sosai,sannan suka bar cikin bedroom ɗin nashi,ya kasance shi kaɗae ne acikin ɗakin kwance asaman gadon,kamar wani zautacce sae faman sakin murmushi yake yi,bakinshi yaƙi rufuwa,
   Turo ƙopar ɗakin nashi,akayi da sauri yakai idanunshi wurin,Azmee ce ta shigo hannunta ruke da tray,lunch ne ta shirya mashi,ƙarasawa tayi tare da ajiye mashi tray ɗin saman front table din gadonshi,
  Mikewa yayi daga zaune,yana gaisar da ita,
   "Ina yini Aunty azmee,ya aiki,"
  Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Lafiya lou junaid Alhamdulillah,"
Ta karasa maganar tare da ɗaukar plate ta buɗe warmer mai dauke da chicken pepper soup serving spoon ta sanya tana ɗaukar cinyar kazar tana sanya mashi a plate,kallonta yakeyi sae ya dinga ganin kamar jahad ce,saboda tsabar son ya ganta musamman da yaji an mallaka mashi ita,
"Idan ka kammala ci,ga magani nan Uncle ɗinku ne yace na baka kasha,"tayi maganar tana nuna mashi maganin dake ajiye asaman tray ɗin,
"Nagode sosai Aunty azmee,"
"Na lura kamar kana cikin farin ciki sosai yau,"_
Murmushi ya saki tare da cewa"Aunty azmee,Am so,so happy today,Uncle abusufyan ya bani auren Jahad,Ya mallaka mun ita,"
Waro ido waje Azmee tayi cike da mamaki tace"Wai dagaske"?
ɗaga mata kai yayi alamar eh,Hannayenta ta daga sama cike da tsantsar farin ciki tace"Alhamdulillah!Allah na gode maka!ashe dae ina da rabon ganin aurenka junaid,Allah ya nuna mana lokacin,"
"Ameen ameen,"ya amsa mata,
"Dan Allah kaci abincin nan sosai,kaci ka koshi angon jahad,"
Rufe fuskarshi yayi yana dariya ƙasa ƙasa, itama dariyar ce ɗauke akan fuskarta har ta kammala zuba mashi abincin,sannan ta kama hanyar fita daga ɗakin,sae da junaid yaji alamun ta bar bedroom ɗin nashi sannan ya buɗe fuskarshi yana faman sakin murmushi


  *Haroon*

Motarshi na qoqarin shiga cikin hotel yaji an ambaci sunanshi"Ya Haroon,"gabansa ne ya faɗi rass jin Muryar mutum mai mahimmanci a wurinshi,da sauri yaci burki tare da zuge glass ɗin motar a slow,

   Tsaye take jikinta na asanye da Uniform,yadda kasan mahaukaciya,gashin kanta duk ya tarwatse ya hargitse,babu gyara,ƙafafunta babu takalma,tayi buɗu buɗu da ita,waro ido waje haroon yayi yana kallonta,tamkar a mafarki,kusan minti 5 kafin ya buɗe motar,ya fito har lokacin kayan jiya ne ajikinshi,a hankali yake tunkararta yana ƙare mata kallo,ita kuwa da gudun gaske ta tunkareshi,faɗawa tayi saman ƙirjinshi tare da zagayo da hanneyenta ta bayanshi,ta ƙanƙame shi sosai,lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka,
  Lumshe idanunshi yayi tare da sanya hannunshi abayanta,yana ɗan bubbuga bayan nata,a hankali ya ambaci sunanta"AMRISH"
   Boss tabarku da tunani,Bashin friday ne na biyaku,kowa yasan cewa weekend banayin posting,Don haka mu haɗu On monday,in Allah yakaimu da rai da lafiya,don jin Yadda zata kaya👍
    *SALON NA DABANNE🔥*
*kada fa ku manta har yanzu muna acikin Littafin Abban Sojoji ne Takun ƙarshe wanda Ni hafsat Bature Na rubuta*







   
[3/19, 2:57 PM] +234 810 388 4440: 💋Boss Bature💋*



Join this link to follow my tiktok acct👇

https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1




قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖*

*Father of soldiers*

*🔥TAKUN ƘARSHE🔥*




_❤Littafin abban sojoji 300 ne,gamai bukata zaiyi mun magana kaitsaye ta layina pls banda kiran waya,bana amsa shi,Just message za'ayi mun ta whatsapp in sha Allah zan amsa,don bana shariya indai ina online 08103884440❤Masu kirana ƙarfe goma na dare kuna son jamun wlh😡_




Cikin shessheƙar kuka ta amsa mashi"na..am yaya haroon" raba ta yayi daga jikinshi tare da sanya hannayenshi ya tallabo fuskarta,daƙyar take iya buɗe idanunta waɗanda ke jike sharkaf da hawaye,zuba mata ido yayi yana kalllonta,fuskarta duk ta kumbura tayi haske,gashi ta ɗan yi rama wannan ya tabbatar mashi da cewar tana cikin matsananciyar damuwa,yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana idonshi ya sauka akan hannunta,kanula ya gani,a ruɗe yace"Amrish!Wannan fa?faɗa mun meya faru?Kinyi rashin lafiya ne"?
   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Poison nasha,Saboda na gaji da zaman duniyar nan,Mommy ta 6atamun rai,ba ta sona ba ta damu dani ba......".
  Bata ƙarasa maganar ba,yaja hannunta izuwa wurin motarshi,buɗe mata motar yayi ta shiga back seat ta zauna sannan shima ya shiga mazaunin driver,shiga cikin Hotel ɗin ya ƙarasa shiga da ita,bayan yayi parking ɗin Motar ya fito ya buɗe wurin da amrish take ya shiga daga ciki,
   Cikin sanyin Murya yace"faɗamun abunda ya faru tsakanin ki da ita"?
  Nan ta labarta mashi abunda ya faru tsakaninta da mommynta tun daga farko har ƙarshe,
     "Amrish!ashe baki da hankali?saboda kawai ta gaya maki wannan ƴar maganar sai ki nemi kashe kan ki?suwa kika yi ma asara?
  Shiru tayi yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,
    "So kike narasa ki ko"?da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a,
   "Bazan ƙara ba,yaya haroon mommy ce ta 6ata mun rai,kuma ni bansan zama wurinta,Na tsaneta bata kwanta mun araina ba,dan Allah kada ka mayar dani wurinta,ka kaini gidanku kawai in zauna tare daku,"
  Waro idonshi ya ɗan yi kafin yace"gidan mu!in kaiki a matsayin wa?so kike kija mun?yayyena fa gaba ɗayansu maza ne kuma sojoji ne,bazaiyiwu ba ki zauna acan,"
  Fuskarta tamkar zata yi kuka tace"Ya kake so nayi da rayuwata ne?ni babu wurin da nake jin daɗin zama,Ka kaini kawai gidan ku in zauna,idan ina ganinka sai hankalina yafi kwanciya,amma ni bazan koma wurin mommy ba,in ba so kake ka rasa ni ba gaba ɗaya,"tayi maganar aɗan shagwa6e,
   Shiru ya ɗan yi yana tunanin mafita,don kuwa ya santa da baƙar zuciyar nan ta gado,in har yaƙi yi mata abunda take so to tabbas zata aikata abunda ta faɗa ne,
   Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallonta yace"It's Okey,zan kai ki gidan mu amma kafin nan,Ki fara zama a wurina,Ni abunda ya ɗaure mun kai,taya ya har kika gano inda nake?"
  Sae lokacin ta ɗan saki murmushi akan fuskarta,kafin tace"Ae nasan duk wani wuri da kake zuwa,kaine baka sani ba....". 
   "Wato bibiyata kikeyi ko"? Dariya tayi,tana ɗaga mashi gira,
    "Zanyi maganinki,mai ɗan kumatu,"
  Sosai ya shiga zolayarta,har sai da yaga farin ciki akan fuskarta,atare suka fito daga cikin Motar hannunshi acikin nata,wucewa yayi da ita VIP,inda room ɗinsa daya kama a hotel ɗin yake,bayan sun shiga ciki wanka ya sanyata tayi sannan ya daukko mata kayan da zata sanya ajikinta,dama ɗakin nasa na sharholiyarsa ne,akwai duk wani abu da mace zata buƙata,tunda nan yake kawo ƴan matansa da samarinsa duka dae,bayan ta kammala shirya kanta,order ya bada na abincin da zataci,
  Bayan an kawo mata abincin,taci ta ƙoshi,sannan yace ta kwanta ta huta,Cikin ƙankanin lokaci bacci ya ɗauke ta asaman gadonshi,
  Safa da marwa ya shiga yi acikin ɗakin tunanin shi,taya za'ae yakai amrish gidansu!?Yasan cewa ba wani abun tashin hankali bane,kuma in ya kaita zasu kar6eta hannu bibbiyu,amma bazai bari su ganshi ba da sunan wanda ya kawota,in ba haka ba zai zama abun zargi a wurin ƴan uwansu,
  Sae faman zirga zirga yakeyi acikin ɗakin,lokaci zuwa lokaci yakan ɗan juya ya kalli amrish dake kwance saman gadon nashi,hankalinta kwance sae sharar bacci take yi,bai ta6a ganin yarinyar da ta yarda dashi ba kamar amrish,kwata kwata ba ta jin tsoranshi don ta rungumeshi,ba wani abu bane a wurinta,duk da shi ya koya mata hakan,har kwana saman gado ɗaya suna yi da ita,amma wani abu bai ta6a shiga tsakaninsu ba,sae dai ƙawayenta su Zeenatu,babu wadda bai yi lalata da ita ba acikinsu,kuma har yanzu yana tare da kowaccensu,duk in ya buƙace su zasu kawo mashi kansu ne,

❤🤍❤

After La'asar,

Tsaye take agaban dressing mirror tana ƙare ma kanta kallo yadda kasan wadda za ta je gasar Kyawun duniya,Wedding gown ce a jikinta  fara ƙal,tabi shape ɗin jikinta,hips ɗinta ya fito sosai kamar zai fasa rigar haka daga saman rigar net ne,sosai fatar ƙirjinta ta fito mai matuƙar jan hankali,Daga bayan Rigar lace tattoo ne wanda ya ƙara fito da kyawun rigar,fuskarta na ɗauke da light makeup,ta shafa jan baki red colour,Hannunta na sanye da haɗaɗɗiyar wrist watch ta diamond da Aunty azeeema ta saka mata,mai haɗe da ring da kuma chain ƴar ziririya fara,ga earrings ɗinta,wani irin daddaɗan kamshi ne ke fitowa daga jikinta Kamar wadda aka tsamo daga cikin ƙogin turare,gaba ɗaya bedroom ɗin nasu Ƙamshin turarenta ne ya karaɗe ko'ina,ƙafarta na sanye da stilleto,matsiyacin high heels ne mai shegen tsini,shima launin rigar jikinta ne,ƙafafunta sun fito ɗass acikinsa,

   "Wow masha Allah,Tabarakallahu Ahsanul khaliƙin!"hajiya azeema ce ta ambaci hakan,jahad kuwa hannunta na ɗauke da Wayar sehrish ta shiga Camera sae video take yi mata,ita ma hosana hannunta na ruqe da wayar hajiya azeema I phone 13,Sun taru sai video suke ɗaukar sehrish,
Ƙoƙarin juyowa tayi da sauri hajiya azeema ta dakatar da ita"Kada ki juyo yanzu,bari na aza maki net ɗin nan asaman kanki zai ƙara maki kyau sosai,Bayan ta kammala sanya mata mayafin sannan tace"Sannu a hankali zaki juyo ba da sauri ba," a natse Sehrish ta soma juyowa a wani slow,Hosana na kallonta ta cikin camera sai faman sakin Murmushi take yi,
  Hajiya azeema tace"Yawwa My photographers ku ɗaukarmun ita da kyau,ta fito sosai acikin Video ɗin,yadda zanji daɗin ɗaurawa a status ɗina,
  Ƙarasa juyowa sehrish tayi,fuskar nan ɗauke da ƙayataccen Murmushi,ita kanta tasan tayi kyau over,Zuciyarta cike fal da farin ciki,kamar wadda akayima albishir da gidan Aljanna,dama hannunta akwai zanen jan lallen da akayi masu na walima,yana nan raɗau a hannunta bai goge ba,ta ruƙe yar purse ɗinta a hannunta,
  Tun daga ƙasa Hosana ta fara ɗaukarta ta cikin camera ɗin har izuwa saman fuskarta,
   "Turn ur back,yadda zasu ji daɗin ɗaukarki da kyau,"acewar Azeema,
  Juyawa sehrish tayi a hankali suka ɗauki bayan,sannan ta sake juyowa,Jahad sae faman zuzuta ta take yi tana cewa"wlh yadda kasan Amaryar Gaske,Sehrish kinyi kyau sosai kamar dollars"
  Dariya hajiya azeema tayi jin abunda jahad tace,
  tace"Wato kuɗi sune suka fi komai kyau kenan?shiyasa ake kwantanta su da mutumin da yayi kyau ko"?tayi maganar tana kallon Jahad dariya sukayi gaba ɗayansu,
  Suna cikin rahar nan wayar hajiya azeema tayi ringing,sunan Abba ne ya bayyana akan screen ɗin wayar,da sauri hosana ta miƙa mata wayar,hannu tasa ta kar6i wayar bayan ta ɗaga kiran ta kara wayar a kunnanta,
   Tun kafin tayi sallama taji muryar abba yace"Azeema kina ina ne"?
   "Ina a ɗakinsu sehrish ne yanzu haka,na kammala yi mata kwalliya ne harma ta sanya rigar amaren...."
  Katse ta yayi da cewa"Karki kuskura,kice zaki kai yarinyar nan ɗakin Rafayet!". 
   Hankalinta atashe tace"Saboda me Yaya hossein"?tun daga kan muryar Abba ta tabbatar da cewar yana cikin matsananciyar damuwa,
   "Tun farko sai da na faɗa maki cewar wannan auren na sirri ne,kuma na faɗa maki dalilin dayasa ya aureta ba don yana sonta ba fa ce don tayi mashi aiki,.." a ɗan ruɗe hajiya azeema ta dago tana kallon Sehrish,jikinta ne yayi wani irin sanyi har cikin zuciyarta taji babu daɗi,
  Da sauri tace masu"Ina zuwa" tana faɗin hakan ta fuce daga ɗakin,a nan cikin corridor din ta tsaya,Muryarta asanyaye tace"Yanzu yaya kana nufin cewa yarinyar nan bazata tare aɗakin Mijinta ba!"
   "Azeema so nake ki fahimce ni,!ki natsu ki saurare ni,!rafayet wani irin bauɗaɗɗan mutunne mai wuyar sha'ani,Wlh bazai bari yarinyar nan ta zauna a part ɗinsa ba,da sunan amaryarshi,Yanzu haka zancen da nake yi maki,Ya hana uban kowa ya ɗauki hoto tare dashi!gaba ɗaya babu wanda ranshi bai 6aci ba saboda rafayet!"
   Muryar hajiya azeema tamkar zatayi kuka tace"Amma ba'ayi ma yarinyar nan adalci ba!Meyasa tun farko ba'a shawarce ta ba?kafin a ɗaura mata aure dashi!yakamata ace tasan da zancen auren da za'ayi mata da kuma dalilin yin auren!me kuke tunanin zai faru idan har yarinyar nan taji cewar an aurar da ita ne don tayi aiki kawai a ƙarkashinsa"?
  Shiru Abba yayi batare daya ce mata komai ba,
  Jinjina kai kawai hajiya azeema tayi tare da cewa "Shikenan kawai,Zansa ta cire rigar dana sanya mata,Amma dae banji daɗi ba,Kuma in sha Allah rafayet sai yayi danasanin yin hakan da yayi!"tana kai ƙarshen maganarta,tayi rejecting kiran,Tuni idanunta sun cicciko da kwalla,Ranta yayi mugun 6aci,
    "Aunty azeema!"hosana ce ta ambaci sunanta,da sauri takai idanunta ƙopar ɗakin nasu,tsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Munata jiranki,Kince zamu je kai amarya,"
   "Kada ki damu hosana,Yanzu zan shigo ciki,"
  Amsa mata tayi da toh,sannan ta koma cikin ɗakin,Kusan 15 mins hajiya azeema tana tsaye batare da ta motsa ba,sae da zuciyarta ta lafa,sannan ta wuce cikin ɗakin nasu,
    A tsaitsaye ta samesu suna jiran dawowarta,gaba ɗaya duk sai taji ba daɗi,Musamman yadda taga Sehrish sae faman sakin Murmushi takeyi,tsananin tausayinta ne ya kamata,Shin wata irin rayuwa yarinyar zatayi a ƙarƙashin Sgr?mutumin da baisan Soyayya ba,Tabbas zata sha wahala a hannunshi,Domin kuwa zai mayar da ita tamkar baiwarshi ne,su yaya hossein sunyi kuskuren aura mashi ita,da sunan tayi mashi aiki,wannan tamkar ƙasƙanci ne,kuma yarinyar bazata ji daɗi ba,ranta zai 6aci sosai idan ta gano cewar aure akayi mata,auren ma na sirri,tamkar wata mara gata,babu walima babu wani party,babu taron mutane,babu wedding pics,dole abun ya ta6a Zuciyarta,na biyu da sa hannun iyayenta suka aura mata shi da sunan tayi aiki a ƙarƙashinsa ba matsayin matarshi ba,tabbas an gama cutar da ita,

    Mamaki abun ya ba su Jahad ganin hajiya azeema tayi tsaye agabansu,kuma ta ƙurawa sehrish ido tana kallonta,Kamar mai nazarin wani abu,
   Jahad ce ta ambaci sunanta"Aunty azeema,"
  Firgita tayi lokaci guda ta ɗan saki murmushin yaƙe tare da cewa"Am sorry fa,wlh na shafa'a ne,Yanzu mai ya rage mana muyi"?
   Hosana tace"Kai amarya mana,ki faɗa mana a ina zamu kai rishi ɗin,"
   Hajiya azeema tace"Ae wannan shirin drama ne!ba dagaske ba,A nan zakuyi wasan ga wayata ma idan kuna buƙatar yin hotuna,Ni yanzu inaso zan wuce ciki ne,"
  Da sauri Hosana ta kar6i wayar daga hannun hajiya azeeman,sallama tayi masu da sauri ta fuce daga cikin ɗakin,
  "Kamar yanayinta ya canza ko"?jahad ce tayi maganar tana kallon sehrish,
   "Nima na lura da hakan,Hosana wanene ya kira ta a waya nasan kinga sunan daya bayyana akan screen ɗin,Zai iya yiwuwa wani abu aka sanar da ita wanda ya 6ata mata rai,"acewar sehrish,
   Hosana tace"Ni dai naga Sunan Yaya hossein,amma bansan wanene ba,"
  "Sunan Abbansu Junaid ne,Allah yasa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login