Showing 114001 words to 117000 words out of 168002 words

Chapter 39 - Buzu Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

674

?irjina ya fara nauyi" da sauri ta saka bayan hannunta, tana goge hawayen fuskarta.

"Yauwwa dama ina so mu yi wata magana, mai muhimmanci da ke"

Ta tattara hankalinta, gabanta na dukan uku-uku cike da wasi-wasin wace maganar zai yi da ita haka?.

Ayshercool
08081012143
Ayshacool
Ya yi mata alama da hannunsa, a kan ta nutsu ta kwantar da hankalinta. Ta jinjina masa kai, duk da gabanta na ci gaba da faWuwa.

"Amm na san kina ha?uri a kan abubuwan da suke faruwa, duk da kin ce mini ba kya so na din ga irin wannan maganganun, amma sun zama dole na yi. Ina ?ara yi miki godiya da nema miki yardar Allah, na san ba ni da abin da zan biya ki da shi a wannan Duniyar. Ke ce komai nawa da ki ka rage Asmy. Sannan Sangaren abin da ya shafi auratayyarmu, shi ma na san...

Ta katse sh6ta hanyar cewa "Amm ni dai a bar wannan zancen, bari na je na Wora wakena"

"A'a ki tsaya mu yi magana"

"A'a ba sai mun yi ba"

"To kar na sake jin kin bi dare ki na taSa ni" Kamar ta yi tsuntuwa ta Sace, saboda azabar kunya, ita a zatonta ma ya manta gaba Waya. Cikin azama ta mi?e ta Wauki robar wakenta, ta nufi inda take girki. Tana tashi ya kashingiWa yana dariya.

Nana tana ta fifita wuta, yana daga zaune yana kallonta. Wani irin abu ne yake yi masa yawo a jikinsa, a game da ita.
Yana jin zai iya yin komai, dan tabattar da ci gaba da zamanta mallakinsa, shikaWai.
Juriyarta, sadaukarwa da kuma tsananin tausayinta, ya sanya yake jin ina ma yana da wani abu da zai iya kamanta faranta mata rai, kamar yadda take ta wannan Wawainiyar da shi. Ya san in dai a wannan Duniyar ne ba shi da abin da zai biya ta. Duk da matsananciyar damuwar da ya kan shiga, da jin cewa ya zama silar nakasta rayuwarta, ta zama tana rayuwa ba tare da tunanin wani abu da take so ta cimma ba. Kullum tunaninta a kan sa ne kawai.
Tana Wagowa suka haWa ido, ta murguWa masa baki, ta ci gaba da fifitar wutar gabanta.
Ya tako zuwa gaban murhun ya tsuguna.

"Dan Allah ka tashi, saboda numfashinka fa"

"Kawo na yanka miki salak Win"

"A'a kar ka yanke hannu"

Ya ce "Ki kawo zan iya" Ta tsuke fuska ta kalle shi ta ce "Saboda sau?i ya samu, kana iya fitowa da kanka yanzu, shi ne za ka din ga damuna ko?"

Ya yi murmushi, ya zauna a gefe yana kallon ta, da ta Waga ido, sai su yi ido huWu da shi, sai ya yi mata murmushi.

Su na cikin cin abinci, ya ce "Ki na kiran Ummi?"

"Ba na samun ta, ita ma ta kira ni wayar ba na ji. Uwani ta ce haka garin nan yake babu network, sai a yi kira fiye da sau goma ba ka samu mutum ba.

"Idan na ?ara jin sau?i, zamu je mu gaishe ta, mu yi mata godiya"

Ta ce "Alhamdillah, lallai sau?i ya samu."

Ya ce "Eh, ina jin hakan a jikina nima. Mu je waje na Wan tattaka na ga gari"

Nana ta faWaWa murmushinta ta ce "Allah abin godiya, wallahi Sayyid da har na fara fitar da rai da kai, na karaya sosai wallahi" Cikin murna ta saka hijjabinta, suka fita. Su na tafe a hankali ta kalle shi ta ce "Gaskiya na yi mamaki, ashe da gaske magungunan sarkin Baka yana yi"

Ya tsuke fuska ya ce "Na gaji da jin zancen Sarkin Bakar nan"

Nana ma ta yamutsa fuska ta ce "Sayyid ka yi ha?uri, amma na yi farin cikin yadda maganin da na gani a gurinsa ya yi maka aiki. Ina yi masa fatan idan a kan daidai yake, Ubangiji Allah ya ?arfefe shi ya dafa masa, ko dan saboda yadda yake taimakon mutane. Idan kuma a kan kuskure yake Ubangiji Allah ya ganar da shi, ya ba shi ikon tuba kafin lokaci ya ?ure masa."

Sayyid ya yi mata banza, suka ci gaba da takawa a hankali su na zagayawa.

Wani irin sanyi ne ya fara ratsa Nana, ganin Sayyid ya durfafi wata hanya, ta kuma kasa ce masa uffan, balle ta hana shi. Su na tunkarar gurin, ?irjinta na bugawa da sauri da sauri.

Wata irin narkekiyar bishiyar kuka suka tarar a gurin mai ban tsoro. Yanayin yadda take Wauke da wasu irin murWaWWun rassa, da yadda murtuka-murtukan jijiyoyinta suka huda ?asa suka mamaye gurin. Ga wani irin ?aton kogo a jikinta, hakan ya nuna daWewar da bishiyar ta yi da wanzuwa a gurin.

"Asma'u" ya kira sunanta kai tsaye. Ta kalle shi cikin matsanancin mamakin yadda ya kira sunanta na yanka kai tsaye.
"Ji nake yi kamar na san gurin nan"
Ayshacool
Jiki a sanyaye Nana ta ce "Nima haka, amma ni dai na san ban taSa zuwa gurin nan ba, amma ina jin kamar na san gurin, amma dai... Sai kuma ta yi shiru bayan da gurin ya gauraye da duhu aka yi wata irin wal?iyya, haske ya mamaye gurin. Tsohon nan ta gani a tsaye, ri?e da sandarsa ya zubo wa Nana idanunsa marasa kyan gani. Jikinta ne ya Wau kyarma, ta ?ara rikicewa bayan ganin a hankali wasu halittu da take kyautata zaton ire-iren su ?aisar ne su na bayyana a bayansa.
Tsohon ya kalle ta, ya buWe baki ya fara magana. "Ina sake yi miki barka da zuwa, garin da kakanin kakaninki su ka dur?usa suka haifo matsalar da har abada ba za ta daina bibiyar zuriyar su ba. Zan ci gaba da azabtar da rayuwarki, za ki ci gaba da biyan bashin nan, ko bayan ranki, muddin aka ci gaba da samun haihuwar masu irin tauraronki."

Yana rufe bakinsa, Waya daga cikinsu da Nana take kyautata zaton jininsin mace ce, saboda yanayin wani irin tsohon mayafi da ta yafa a kanta. Ta tunkaro Nana gadan-gadan.
Tana zuwa matar, ta hankaWa Nana ?asa, sauran suka rufu a kan Nana, su na zira hannunsu a mararta, su na ciro gudan jini.

"Ya hayyu ya ?ayyum ya Allah. Allah ka kawo mini Wauki, Sayyid, Sayyid, Sayyid ka tashi"? Ta yi maganar tana jijjiga Sayyid da yake kwance a gefen ta yana bacci.

Ya ja jikinsa ya tashi ya ce "Ma viee lafiya kuwa?"

"Sayyid marata ciwo take yi. Sayyid marata. Sayyid babyna. Ba na son na rasa jaririna a wannan karon, Dan Allah ka taimake ni"

Cikin rashin fahimta ya ce "Meyafaru ne?"

"Marata ce take ciwo, Sayyid ba na son cikina ya zube, ina son jaririna Sayyid ciwo marata take yi sosai" Ta yi maganar tana zubar da hawaye. Ya saka hannunsa a mararta, ta saka hannayenta ya dafe hannunsa tamkar hakan ne zai hana cikin zubewa.

Ya ce "Ki yi Addu'a" Kawai ta jinjina kai, amma Addu'a kam, ko Waya ba ta zo kanta ba, dan ta manta komai daga cikin kanta.

Cikin rauni Nana ta ce "Sayyid fitsari nake ji, ya matse ni"

Ya ce "To mu je ki yi"

Ta girgiza kai ta ce "A'a ba na son na je na ga jini ya zubo, cikin ne zai zube"

Ya ce "A'a ba za ki gani ba" . Ta mi?e ya kama hannunta, ya haska fitila har banWaki, su na zuwa a tsorace ta yi fitsarin, sai dai tana yi sai ga jini. Wani irin kuka ta fashewa da Sayyid. Ta mi?e jikinta yana rawa.

Ya rungume ta ya ce "Ki yi ha?uri, kin ga dare ne, ki daina kuka. Kuma idan za ki yi Sari, jinin da ki ke zubarwa ya fi wannan kin manta?"

"A'a idan jini ya fara zuba, shikenan ciki zai zube"

Ya ce "A'a, ba haka ba ne, ai bai zuba da yawa ba" Ya lallaSa ta da ?yar, ta gyara jikinta, ta Wauraye jikinta, da banWakin su ka koma Waki.

Karatun Alkur'ani ya kunna a waya, ya ajiye a gefen katifar da suke kai, kamar yadda ya ga tana yi, a duk lokacin da su ka shiga yanayi na tsoro.

Suka kwanta yana Wan shafa ta, cikin sigar rarrashi.

A hankali ta ce "Sayyid"

"Na'am"

"Da gaske mun fita Wazu ko?"

"Eh mun fita"

"Mun je can bayan gari, har ka ce mini kamar ka san gurin?"

"Eh haka aka yi, mun je"

Ta sake cewa "To daga nan meyafaru?"

"FaWuwa ki ka yi, na ri?e ki muka dawo gida. Tun da muka dawo kuma ki ke bacci"

Ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba, ta ?ara lafewa a jikinsa cikin tsoro. Yau ma kwana suka yi, tana gane-gane da jin abubuwa daban-daban masu razanarwa.
Wannan bafulatanar matar ce, ta ?ara zuwa ta tsaya a saitin tagat Nana tana kiran ta, a kan lallai sai ta fito ta ga yadda suke gudanar da bikin girka. Nana ta ?ara rintse idanunta tare da ?an?ame Sayyid.

Da safe ta tashi da wani irin nauyin jiki, ga sanyi da ta kasa daina ji. Ta duba ta ga ba ta kuma ganin jinin nan ba. Ta yi wanka ta rama sallolinta, sai dai Sayyid bai tashi ba. Da ?yar ta samu ya yi alwala ya yi salla.

Ta gaishe shi, amma bai yi magana ba sai kallonta da yake yi. Hakan ya sanya ta fuskanci maganar ta Wauke.
Ta tambaye shi za ta fita, amma bai ko Waga kai ya kalle ta ba. Ta saka hijjabi ta fita ta bi 'yan matan gidan Uwani gona roron gyaWa a gona.

Allah ya taimake ta, ta samo da yawa ta zo tsakar gida ta baje ta domin ta sha iska.
Ayshacool
Ta kai hannu ta janyo hannun nasa, dan ta dam?a masa kofin kunun, amma ta ji hannun a ?ame ?am. Ta sake ?o?arin janyowa, amma ta ji tamkar tana jan itace.

Ta kalli hannun sosai, sai ta ga shanyewa ya yi.

Gabanta ya yi wata irin mummunar faWuwa, ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, Sayyid me ya same ka haka? Me ya samu hannunka? Ya Allah!" Ta yi maganar tana kuma ?o?arin ganin ta mi?ar da hannun nasa, amma hannun yana ma?ale, kamar an tsotse shi.

Ya sunkuyar da kai ya yi shiru, fuskarsa Wauke da damuwa. Ta aro jarumta, ta matsa daf da shi, ta Webo kunun ta kai bakinsa. Amma ya tsaya yana kallonta, bai buWe bakinsa ba.

"BuWe baninka na baka" Ta yi maganar tana ?o?arin danne hawayen da ke ?o?arin ?wace mata.

A hankali ya buWe bakin, sai ta ga shi ma bakin ya karkace, yawu na ?o?arin zubowa. Kawai ya rufe bakin hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanunsa. Ta ajiye kofin kunun ta rasa abin yi. Kawai rungume shi, ta fashe da matsanancin kuka, sai da ta yi iya yin ta.
Sannan ta cika shi, ta share masa hawayensa.
Ta fara ?o?arin ba shi kunun, sai dai tana ba shi, ya haWiye wani kuma ya zubo.
Ta na yi tana goge masa wanda yake zubowa, ta gama ba shi, ta kama hannunsa su ka je waje, ta taimaka masa ya yi alwala. Ya dawo ya rama sallolin da ta gaya masa ana bin sa. Sai dai ba magana ga hannu a ma?ale, da ta kalle shi sai ta ji hawaye ya cika mata ido.
Ganin yana gyangyaWi a zaune, ya sanya ta saka masa pillow ya kwanta, ta saka hijjabi ta fita.

Tafiya mai nisa ta yi, ta je ta samu wani chemist, bayan sun gaisa ta ce "Dan Allah malam, idan babu damuwa, Bp nake son mu je ka gwadawa mijina a gida"

Ya kalle ta ya ce "A ina ne?"

"Cikin Budu ne, nan unguwar maharba"

"TaS gaskiya da nisa gurin nan ba kaWan ba, ba zan iya zuwa ba sai dai ki je ku zo tare a yi masa"

"Wallahi da zai yiwu, da ba zan zo na ro?e ka ba, yana kwance babu lafiya ka taimaka mini dan Allah"

Ya ce "Gaskiya kin san cajin zuwa gida ma ka yi wa mutum abu daban yake, sai dai idan za ki ba ni dubu biyu"

Nana ta ce "Eh na yarda mu je zan baka in sha Allah" Ya rufe chemist Win ya bi Nana.

Su na zuwa gidan, Nana ta shiga ta tarar da shi a zaune ya tashi, ta ce "Sayyid kar ka ga na fita ban gaya maka ba. Na je na samo wani ma'aikaci ne, ya zo ya duba jininka a gani, idan jinin ne ya hau ya sanya hannunka ya shanye, mu tafi Asibiti. Idan kuma ba shi ba ne, sai mu san abin yi." Bai ce komai ba, ta yi wa mai chemist magana, ya shigo ya gwada jininsa.
Ya gwada ya kalli Nana ya ce "Jininsa bai wani hau sosai ba, 140/90 ne" Ajiyar zuciya Nana ta yi. Ta ce "A ganinka wannan hawan zai iya sanya masa shanyewar hannu?.
Ya girgiza kai ya ce "Gaskiya ba na tunanin haka, amma ban tabattar ba tun da ni ba likita ba ne ba. Amma a shekarunaa bana tunanin jinin 140 zai shanye masa wata gaSa a jikinsa, amma dai ku je Asibiti a ?ara bincikawa"
Nana ta ba shi kuWin sa, ta yi tai masa godiya. Ta koma Waki ta zauna ta yi shiru, tana tunanin ko Uwani za ta tambaya, idan akwai wani mai magani, ta raka su, sai dai ta fasa saboda akwai sauran SurSushin jahilci a tattare su, ba ta son surutu kuma tana tsoron a kai su gurin da ba shikenan ba.

****

Alhaji Fatuhu kuwa kamar yadda ya matsa, sai da aka sallame shi ya koma gida. Gidan nasa ma wani abokin kasuwancinsa ne ya saya, ya bar shi a ciki ya zauna ya bar masa aro.

Sagir yana kwance a kan gadonsa, yana kaWa ?afa ya ?ura wa screen Win wayarsa ido. Yusra ce zaune sanye da doguwar rigar material, kanta ko Wan kwali babu, dogon gashin kanta ya sha gyara. Tana ta zuba masa surutu.
Har mamaki yake yi, yadda Yusra ta zama mai Wan karen surutun tsiya, wanda da ba haka take ba.

"Ya ka yi shiru ne?" Ya wani lumshe ido ya ce "Ina jin ki ai".

"So talk, ka yi magana mana" ta yi maganar tana cika bakinta da guggurun hannunta.

"Ina ga zan shigo Abuja mu haWu very soon in sha Allah" wata irin zabura ta yi ta ce "Are You serious, dan Allah da gaske?"

"Da gaske nake, zan zo na ganki, amma ki na ganin babu matsala a zuwan nawa? Kar a yi miki faWa fa, ba zan ji daWi hakan ba"
Ayshacool
Yusra ta ce "Babu wata matsala, ba za a yi mini faWa ba, ai ba na tare da su Mami, ina gidan Anty Sumayya. Dan Allah ka zo"

Sagir ya yi murmushi ya ce "Kin yi missing Wina ne?"

Ta gyaWa masa kai tana murmushi.

"Shikenan, i miss you too, ban taSa tunanin ma za ki neme ni ba, na za ta ki na jin haushina haryanzu, amma in sha Allah zan shigo, zan sanar miki lokacin da zan shigo na zo na ganki" ya yi maganar yana kashe mata ido.

Shukura ce ta turo ?ofar Wakin ta shigo, a burkice ya kif wayar yana kallon ta. ?arara yanayinsa ya nuna alamun rashin gaskiya, amma ta share shi, ta haye kan gadon ta ja bargo ta lulluSe jikinta.
Ya matsa kusa da ita yana Wan shafa ta ya ce "Sweetheart, ya na gan ki kamar a fusace ne? Lafiya dai ko?"

"Lafiya ?alau" ta amsa a ta?aice. ?an shiru ya yi yana tunanin ko dai ji wayar da yake yi ne? Amma a yadda ya santa da azababben kishi, da zargi da ta ji sai ta yi masa magana. Sai dai ya bar abin a haka bai matsa mata da tambayoyi ba gudun kar su yi faWa.

Tana ankare da take-taken Sagir, na rashin gaskiya. Sai dai ita yanzu ba wannan ne a gabanta ba, bin diddigin mutuwar Wanta take son yi. Dan haryanzu zuciyarta ta kasa amincewa da natural mutuwa ya yi. Domin haryanzu tana mafarke-mafarke marasa? daWi da mahaifinta da kuma Doctor Sharif.

****
Aka shiga sati na biyu, Sayyid yana cikin wannan yanayi na rashin lafiya, kuma hannunsa bai saki ba, yana nan a ma?ale.
Ga hauka da yake yi tuburan wasu lokutan, wasu lokutan idan ya burkice sai ya sha?e ta, ko ya hankaWe ta ?asa, sai dai ta yi ?o?arin kare cikinta. Ko kuma Ya ya ta watsi da duk abin da ya ci karo da shi, a Waki ko a tsakar gida. Wasu lokutan ma katangar Wakin yake duka da kansa. Ya ?i cin abinci ya ?i shan magani, ba salla, komai sai dai ta yi masa cikin rarrashi da ban ha?uri. Tun tana jin tsoron ya yi mata wani abin, har ta daina ji, ta zuba wa sarautar Allah ido.
Sannu a hankali ta rage yawan amai, sai dai zazzaSi da rashin son cin abinci da take yi, hakan ya sanya ta tabattar da cikin jikinta bai fita ba haryanzu. Sai dai ba ma ta cikin nutsuwar da za ta nemi inda Asibiti yake ta je, ta tabattar da halin da suke ciki ita da jaririn saboda tashin hankalin da take ciki.
Yanayin yadda uwani ta lura kamar Nana na Soye wani abu, ya sanya ta daina zuwa gidan,ta rage aika yara ma. Sai dai lokaci lokaci, ta kan aika mata da Abinci.
Haka sauran 'yan uwansu na garin ma, su kan aiko mata da sha tara ta arziki saboda su na tausayin Nana, sun san mijinta a kwance yake babu lafiya.
Yawon roro a gona kuwa yanzu Nana ta ?ware, ranar kasuwa ta je ta sayar da abin ta.
Kasancewar ranar Asbar kasuwar garin take ci, sai ta tashi ta yi fanke da sassafe, jikan Uwani Haladu, ya kai mata kasuwa. Ko ta dafa masa zoSo ta ?u??ula ya tafi da shi.
Idan ta gama komai kuma, ta bi yara gona roro.

Dare ya tsala, amma Nana tana zaune tunkurkur, wuni Sayyid ya yi yana wani irin nishi, ga wannan azababben zafin jiki da yake fama da dhi.
Tana zaune tana tunani, tana jin yadda mararta take motsi, cikin jikinta yake motsawa.
Ba ta da sauran wanda za ta kai kukanta bayan Ubangiji. Ta fara tunanin ?o?arin tara musu kuWin mota, su tafi Nijar, neman danginsa, sai dai idan sun je Nijar Win ina za su nufa? Babu tsammani ta ji Sayyid Win ya laluba cinyarta, ya kwantar da kansa.
Ta shafa gashinsa ta ce "Sayyid" bai amsa ba, sai dai ya ri?e hannunta. Hakan ya tabattar mata da ya dawo hayyacinsa ne. Haka ta tashi a cikin daren ta tsiyayo ruwan zafi, ta ba shi shayi ta yi masa wanka suka kwanta, ta lulluSe su da bargo.
Sheshshe?ar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login