Showing 12001 words to 15000 words out of 168002 words

Chapter 5 - Buzu Book One Complete Hausa Novel

27 Oct 2025

642

ba ta dawo ba. A take hankalin Baba ya tashi, ya fara tunanin ko dai ta gudun ne?
Sai a lokacin ya fara binciken ina ne gidan da Nana take aiki, tun da take zuwa bai taSa bibiyar ina take zuwa aikin ba.
Gaddafi baya nan, dan haka ya Wauki Nasiru, suka fita neman Nana.

Gurin ?arfe tara na dare, Gaddafi ya dawo gida, ya shigo cikin gida zai wanke kayansa, yana neman Nasiru zai aike shi. Suwaiba ta gaya masa halin da ake ciki. Ya yi saroro ya ce "Yanzu har ?arafe tara ba a san inda take ba? Kuma babu wanda ya san gidan aikin nata?"

Jamila ta ce "Ni dai ta taSa kwatanta mini, can wajen quarters Win markaz ne, wai gidan Alhaji Zailani"

"Sako hijjabin ki mu je, mu duba"

Mama ta ce "Ku je ina? Babu inda za ta je"

Ya haWe rai ya kalli Jamila ya ce "Ba magana nake yi miki ba, sai na taka wuyanki tukuna?" Ba Jamila ba ita kanta Mama sai tsuke bakinta ta yi, dan iya ashariyar Gaddafi ta ishe su.

Sam ba su sha wahalar gano gidan ba, kasancewar Alhaji Zailani sanannen mutum, saboda yawan kyautar da yake yi da taimakon al'umma.
A tsatstsaye suka tarar da mutane a ?ofar gidan, buzaye sai magana suke yi da yare???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?n su.

Kai tsaye Gaddafi ya kutsa suka shiga cikin gidan, mutane ne a tsaye a ?ofar Wakin masu gadi, ga matar gidan a tsaye fuskarta Wauke da damuwa.
Ayshacool
Gaddafi ya nufe ta, suka gaisa ya ce "Dan Allah ni yayan yarinyar da take yi muku aiki ne, Nana tun da ta fita tun safe bamu ganta ba, shi ne muka zo nan ko ta zo?"

Hajiya Amina ta ce "Alhamdilillah mu na ta tunanin yadda za a yi, tun bayan la'asar muka yi sallama, ta tafi gida. yanzun nan yarona ya shigo yana gaya mini wai masu gadi sun ganta a Wakinsu a sume, su suna waje, mutum Waya suka bari a Wakin, shi kuma ba shi da lafiyar ?wa?walwa, ya ?i magana an rasa wanda zai taSa ta ma. Yanzu nake tunanin ya za a yi a samo wani daga gidansu, dan ni ban san gidansu ba"

Gaddafi ya ce "?akin masu gadi kuma?" Ya juya ya nufi Wakin.

Nana na sume a tsakar Wakin, gefe guda shi kuma yana zaune yana kaWa ?afafuwan sa, tamkar ba ya jin hayaniyar da ake yi.

Gaddafi ya nufi Nana da sauri, ya Wago ta, yatsun hannunta da na ?afarta duk sun ?andare kamar wadda ta daWe da mutuwa, ga jikinta sanyi ?alau.

Ya Waga kai ya kalli Buzun nan da duk abin da ake yi, sabgar gabansa kawai yake yi, ya kalli Nana. Duk da ba shiri suke yi da ita ba, amma ya san Nana ba ta cikin jerin yara marasa ji, amma me ya kawo ta Wakin masu gadi?.

Hajiya Amina ce ta saka Yusuf ya Wauki su Gaddafi ya tafi kai su gida.

Cikin damuwa Habu yake dubansa ya ce "Buzu, ya aka yi yarinyar nan ta shigo Wakinmu, me ya same ta? Me yasa kuma ba ka kira wani daga cikinmu ba?" ?aga idanunsa ya yi ya kalli Habu, a dole Habu ya ja bakinsa ya tsuke, duk da tarin tambayoyin da suke bakinsa.

Cike da takaici, da matsananciyar tsana da damuwa, Baba yake kallon Nana yake maimaita a Wakin masu gadi ka gano Nana?"

"Idan an yi magana a ce aljanu ne suka hanata aure, ga ha?i?anin abin da ya hanata aure nan ai" Mama ta din ga faWar maganganu. Jamila ta ce "Mama ba lallai abin da ki ke tunani ba ne ba, kin san ba ta da cikakkiyar lafiya"

"Eh ban sani ba sai yanzu da ki ke gaya mini, rashin lafiya ne za a ganta a Wakin masu gadi da wani?"

"To ai an ce mahaukaci ne, har fa muka taho yana kallon dandazon mutane, bai yi magana ba, kuma bai fito ba" cewar Jamila, dan ta ?i yarda zuciyarta ta bata wani mugun abin Nana take aikatawa.

Kawai Baba ya tafi Waki, Mama ta bishi tana faWin "Yanzu baban Jamila, baka gudun a zo a ji kunya? Wallahi tun da ta fara haka, ko an yi auren nan ba za ta zauna ba, kunyata ka za ta yi, tun da ta furta maka ba ta son auren nan, take ta wannan iskancin. Maza nawa ta ce ba ta so? ko dai ka san abin yi ko kuma abin da za ta yi a gaba sai ya fi na yanzu muni"

Wata irin tafasa zuciyar Baba ta din ga yi, tafasar da tun da yake bai taSa jin zuciyarsa ta yi ba, wata irin matsananciyar tsanar Nana ta mamaye zuciyarsa.
Kamar mahaukaci haka ya fito fiuu ya yi waje.

Ayshercool
08081012143
Ayshacool
*AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA 08162859027*

*INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK WANI DATTIN MARA SANYI MAI HANA HAIHUWA SA WARIN GABA RASHIN NI IMA JIN ZAFI YAYIN MU AMALAR AURATAYYA FITAR FARIN RUWA MAI WARI KAIKAYIN GABA TUSAR GABA KURAJEN GABA TUSAR GABA BUDEWAR GABA CIWON JIKI RASHIN GAMSUWA*
*Maganin sanyi 5k*


*Maganin sanyi*
*5k*


*Maganin ciwon Qoda 10k*



*Maganin HepatitisB ASHA NA TSAWON WATA DAYA MUNBADA ANWARKE DA YARDAR ALLAH 40k*


*MAGANIN MATA KALOLI DABAN DABAN INGANTATTU MASU LAFIYA DA KARA KUZARI AKWAI NA MATA AKWAI NA MAZA UWARGIDA DA AMARE KU GARZAYO WURIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA*


*INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO MAI TADA KOMADAR NONO DA DUK WATA TAMOWA TA NONO ZAI CIKO DA TUWON NONO YA TADA KOMATSEWARSU BANCE ZASU TASHI BA ZADAI SU CIKO SUYI KYAU*
*Maganin gyaran Nono 8k*



*MAGANIN RAGE TUMBI KODA YAKAI GIRMAN CIKIN YAN BIYU INSHA ALLAH KI GWADA MAGANIN AUNTY ZEE DA YARDAR ALLAH ZAKI GODE*
*Maganin Rage Tumbi 7k*



*MAGANIN BASUR KODA YAKAI GA YIN TSIRO INSHA ALLAH AGWADA ZA ADACE*
*Maganin Basur 5k*



*MAGANIN CIWON SUGAR CIKIN IKON ALLAH MUNBADA ANRABU DASHI*
*Maganin ciwon Sugar 10k*


*08162859027*
*09070027627*

*Location*KATSINA STATE*

*ACCOUNT NUMBER*

*8162859027*
*ZAINAB SHU AIBU*
*OPAY*

*OR*
*3968303018*
*FCMB*
*ZAINAB SHU AIBU*

*DAN ALLAH IN KINSAN BAKI SHIRYA BA KARKI YI MAGANA DAN ALLAH KIBARI KI SHIRYA AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA TAKUCE SAI KUNZO*




Page 25


Ko da Baba ya fita Gaddafi ya nemo, a gurin masu shayi.

Gaddafi ya ce "lafiya kuwa?"

"Ofishin 'yan bijilanti zaka raka ni"

"Amma a daren nan? Me ya faru?"

"Mu je za ka gani"

Gaddafi ya bi Baba zuwa gurin 'yan bijilanti.

Baba ya shigar da ?orafi, a kan zargin yin lalata da yarinyar sa.

Gaddafi ya ce "Baba, babu tabbacin abin da ka ke faWa fa?"

"Babu tabbaci, aka same ta a Waki tare da shi sama da awanni?"

Gaddafi ya ce "Amma ai ka san ba cikakkiyar lafiya ce da ita ba"

"Ka rufe mini baki Gaddafi" Gaddafi ya yi shiru, 'yan bijilanti suka bayar da mutum biyu, tare da Gaddafi aka tafi taho da Buzu.

Hankalin Habu ya yi mummunan tashi, ganin wai an zo a tafi da Wan uwansu gurin hukuma.? Cikin damuwa ya ce "Wallahi ina da tabbacin babu abin da ya yi mata, ba shi da cikakkiyar lafiya ?wa?walwa ne, amma ba wani abin ya yi mata ba, ai mutane sun ga a yadda muka tarar da su"

Jami'in bijilanti ya ce "To ka Waukko takardar shaidar ba shi da hankalin, ka haWo da ita mu tafi, ko ce maka aka yi mahaukaci ba zai iya wani abun ba" sauran buzayen ma duk hankalinsu a tashe.

Haka aka tasa Buzu da Habu, da wasu daga cikin buzayen, suka tafi ofishin 'yan bijilanti.

Shugaban gurin ya ce "Waye daga cikin su, aka tarar da su a Wakin? Ina kuma ita yarinyar?"

Baba ya ce "Tana gida a sume"

"A sume kuma? Shekararta nawa?"

"Shekara ashirin da Waya"

"Ikon Allah, to waye a cikin su?" Gaddafi ya nuna Buzu.

"Kai malam ya aka yi aka tarar da kai daga kai ita a Waki, tsawon awanni, sauke rawanin nan na fuskarka ina magana kana kallona"

Habu ya ce "YallaSai ba shi da cikakkiyar lafiya fa, wallahi taSin hankali ne da shi, ina da tabbacin babu abin da ya haWa shi da yarinyar nan"

Sule ya ce "Ba ma sa shiri da ita, wallahi rashin fahimta aka samu, na ga kwanon abinci a Wakin, ina kyautata zaton ma abinci ta kai mana, akwai dai abin da ya faru tabbas"

"Ba da ku nake magana ba, ka buWe baki ka yi mana bayani, ko kurma ne?" Shugaban bijilanti ya yi maganar yana kallon Buzu. Amma bai ko motsa ba, balle ya yi magana.

Ya sake tsuke fuska ya ce "Sauke rawanin nan kafin na saka a sauke maka shi yanzun nan, ka ?unshe fuska kamar Wan taliban" ?ura masa ido ya yi bai yi magana ba.

Habu ya ce "Ka cire rawanin dan Allah, ka yi maganar abin da ya faru"

Sule ne ya kai hannu zai sauke masa rawanin, amma ya ri?e masa hannu.

"Dattijo, alamu sun nuna fa mutumin nan da gaske mahaukaci ne"

Baba ya ce "Wallahi ko dawanau ce a kansa sai an bi mini hakkina, dama 'yan kwanakin nan shi ne yake hure mata kunne, sai ta kai bayan magariba a waje ba ta dawo ba. Ta ?i aure fafur kowa ya zo ba ta so"
Ayshacool
"To kai Baba ya ka ke so a yi? Kana gani ya ?i magana, ita yarinyar ba ku zo da ita ba, ni wannan case a bari gobe in Allah ya kaimu ku tafi gurin 'yan sanda".

Baba ya ce "Duk fa wata shaida da ake nema, ta tabatta tun da abin da suke yi kenan, sai ya aure ta ya je su ?arata" gaba Waya suka kalli Baba. Cikin tashin hankali Habu ya ce "Dan Allah dattijo ka yi ha?uri, wallahi ba su saba yin komai ba, wannan karon ma rashin fahimta ne, Nana mutuniyar kirki ce, shi kuma ba shi da cikakkiyar lafiyar ?wa?walwa, dan Allah ka yi ha?uri"

"Wallahi ba zan ha?ura ba, daga nan har kotun ?oli mu je, a karSa mini hakkina na ci mini mutunci ta hanyar yin lalata da 'ya ta, ana daf da Waura mata aure" Gaddafi dai ya yi shiru yana kallon ikon Allah, bai ta taSa tunanin Baba zai Wauki irin wannan matakin ba.

"Dan Allah ka yi ha?uri, ka ga nan ba ?asarmu ba ce ba, idan aka kai mu gaban shari'a wahalar da mu za a yi, dan Allah ka yi ha?uri" Sule ya yi maganar cikin magiya.? Baba ya fututtuke ya din ga bala'i, buzayen nan su na ba shi ha?uri.

"Payer la dot" ya furta cikin harshen faransanci yana kallon Habu. Habu ya waro ido, shi ma ya juye harshe, suka koma magana da french.

Jiki a sanyaye Habu ya kalli Baba ya ce "Nawa ne sadakin?"

Gaddafi ya ce "Baba wai da gaske aura masan ita za ka yi?"

"Eh mana, tun da haka ta zaSa. Ai wallahi ba za ta zubar mini mutunci a idon duniya ba, dan na san tun da Rabi ta san maganar nan babu wanda ba zai ji a ciki da wajen unguwar nan ba, har a dangi sai ta yi ta yamaWiWi, tun da haka ta zaSa ta samu"

Baba ya mayar da idonsa kan Habu ya ce "Ko ma nawa ne, ku bayar da sadaki da safe ya zo ya Wauke ta".

Habu ya sake kallon Buzu, cike da damuwa ko zai canza magana, amma ya ga babu alamar hakan.

Hatta 'yan bijilantin, sai da su ka ba shi ha?uri, da rarrashi amma fafur Baba ya ?i yarda kamar wanda ake ?ara zugawa.

Habu ya ce kuWin hannunsa ba su da yawa, bari ya kira waya a kawo kuWi.

Shugaban bijilanti ya ce ba za Waura auren nan a ofishin bijilanti ba, sai dai a tafi gidan mai unguwa, a yi a gaban jagororin unguwa.

Haka kuwa a ka yi, abin da Baba bai sani ba, da kansa ya ?ara tagayyara Nana, da yayata maganar.

Naira dubu Wari biyu Habu ya bayar, a matsayin sadakin auren Nana Asma'u ?arfe sha biyu saura na dare.

Gaddafi dai Baba ya ?ure masa mamaki, duk da ya san har da ziga a cikin lamarin na Baba.

Sai dai kuma Gaddafi ya yi mamakin yadda buzaye, masu gadi suka iya biyan har Naira dubu Wari biyu a take matsayin sadaki. Nawa ake ba su kuWin gadin da har su ka ci suka tayar da kan biyan wannan kuWin haka?.

Can gida kuwa Nasiru ne yake ta tattaSa Nana cikin tsoro, saboda sanyin da jikinta ya yi, kamar gawa.
Sai can wajen ?arfe goma na dare ta farka. Ta saka Nasiru ya kawo mata ruwa ?ofar Waki. Da rarrafe ta fito bakin ?ofar ta yi alwala. Ko yin?urawa ba ta iya yi balle ta tashi, saboda wani irin jiri da take yi. Da jikin kaya ta jingina daga zaune ta yi salla. Ta idar ta sake kwanciya.

Nasiru ya ce "Nana ba za ki ci abinci ba? Ga awara na sayo miki mai zafi" amma ya ji shiru. Ya duba sai ya ga ta koma yadda take da farko, hannunta zuwa ?afafuwan ta duk sun ?andare sun lan?washe.

Sha biyu da rabi Baba suka nufo gida, Gaddafi ya ce "Amma Baba ba a yi ganganci ba kuwa? Kawai ka aura mata mutunen da baka san ma wani iri ba ne ba, dubu Wari biyu fa suka bayar na sadaki ba ka tunanin ma ko wasu marasa gaskiyar ne?"

"Gaddafi wannan abin da na yi shi ne kawai maganin abin da yarinyar nan take aikatawa. Sau nawa ana yin?urin aurenta tana ?i? Mutumin nan da ya fito fa cewa ta yi za ta gudu, ko kuma ta kashe kanta a kan auren, amma ta san ta je Waki gurin namiji. Wannan ne kawai hanyar da zan bi na aurar da ita. Muddin za a din ga saka lokaci ba za ta taSa bari a yi ba".

Gaddafi ya numfasa ya ce "Haka ne, amma ba na tunanin za ta bi maza ko makamancin haka."

"Ba a shaidar Wan yau Gaddafi. Allah ya zaunar da ita lafiya"

Gaddafi yana son sake yin magana, amma ya fasa ya yi shiru.
Ayshacool
Mama tamkar ta zuba ruwa a ?asa ta sha, haka ta ji bayan da Baba ya yi mata bayanin abin da ya faru. "Wallahi ka yi dabara baban Jamila, wallahi da haka za ta ci gaba da zubar mana da mutunci a idon duniya, kuma auren ba za ta yi shi ba, duk wanda ya zo haka za ta ci gaba da korarsa. Kuma shi kansa Alhajin idan ya ji abin da ya faru ba zai yarda ya aure ta ba, ba ma ita kaWai ba, duk wanda ya ji maganar nan ba zai yadda ya aure ta ba, amma tun da aka yi haka ka ga an yi maganin kowa ma. Kuma asiri ya rufu, tun da ta yi i?rarin kashe kanta, ko guduwa muddin aka yi mata wannan auren".

"Ai yanzu sai ta yi duk abin da ta ga dama, na yi wa tufkar hanci. Har Gaddafi yana wani cewa ba za ta aikata ba, ba zata aika ta ba uban me ya kaita Wakin masu gadi? ?ila ma Allah ne ya tashi tona mata asiri hakan ta faru"

Mama ta ce "To Allah dai ya kyauta"

Jamila kuwa jikinta ya yi sanyi sosai, sam ba ta taSa tunanin Baba zai Wauki wannan matakin ba. A yanayin yadda suka tarar da Nana, bai yi kama da wadda ta aikata wani rashin gaskiya ba.

****

Cikin matsanancin Sacin rai sule yake magana, "Habu yanzu da ka yarda aka yi wannan auren ya zamu yi da su gaba Waya?"

Habu ya ce "Amma ai ka na ji, da kansa ya ce a biya sadakin ko?"

"A'a ni ya za ayi na sani, tun da ba iya faransanci na yi ba, kuma da ya ce ka biya masa sadakin sai ka biye masa? Mutumin da ba hankali ne da shi ba, kai yanzu idan aka saka maka takobi a wuya, za ka iya nuna danginsa ko ahalinsa ne? Daga taimako sai jajubo mana wahala? Aure ai Wawainiya ne, shekarata nawa a Nigeria iyalina su na can sahara, ban kawo su nan ba, yanzu ya ka ke so mu yi?"

Habu ya kwantar da murya ya ce "Dan Allah Souley ka yi ha?uri, duk ba abin Waga hankali ba ne ba, idan aka samo wani gidan gadin, sai ya fara aikin gafin kafin a san abin yi"

Tamkar ya gaurawa Habu mari ya ce "A haka zai yi gadin? Mutumin da sai ya yi sati bai ce uffan ba, aikin gadi fa ba buWewa da rufe ?ofa ba ne kawai"

"Ai ba hauka yake tuburan ba, kuma ko a nan ai mu na tafiya mu bar shi, kuma ya yi gadin, dan Allah ka yi ha?uri ka daina Waga muryar nan, zamu san abin yi da yardar Allah"

"Ni wallahi har mamaki ka ke bani Habou, daga tsintar mutum sai wahala ka ke da shi, kamar wani tsohonka, na ga yadda za ayi ai da wannan bada?alar"

Habu ya dafa kafaWar Sule ya yi murmushi ya ce "Babu abin da zai faru sai alkhairi in sha Allah, kuma Allah ya na gani taimako muka yi, ba zamu wula?anta ba". Da ?yar Habu ya samu ya shawo kan Sule.

*

Nana ba ta sake tashi ba, sai washegari ?arfe bakwai na safe, shi ma Nasiru ne ya tashe ta, kamar jiya a bakin ?ofar Wakin su ta yi alwala, ta yi sallar asuba a zaune. Yana zaune ta idar, tana idarwa ya ce "Nana kar ki kwanta, ga kokona ki sha ki daina wannan baccin, jikin ki fa sanyi yake yi"

Ta girgiza kai ta ce "Na ?oshi Nasiru, jikina babu ?wari nima ji nake kamar mutuwa zan yi"

Da sauri ya ce "Ba mutuwa za ki yi ba, yunwa ki ke ji, ki sha kaWan" ganin yadda ya damu sosai da sosai, ya sanya ta karSa ta sha kaWan, ta ajiye ta fara ?o?arin kwanciya.

Suwaiba ce ta shigo Wakin, tare da rangaWa guWa ta ce "Amaryar tsakar dare, mai doki ya koma kuturi, ba a auri mai gida ba an auri mai gadi, to Allah ya sanya alkhairi".

Nana ta Waga jajayen idanunta ta kalli Suwaiba, ta mayar da idonta kan Nasiru ta ce "Nasiru mafarki ne wai?"

Ya girgiza kai ya ce "A'a a zahiri ne"

"To me Suwaiba take cewa ne?"

Cike da ?uruciya ya ce "Wai jiya da daddare aka yi auren ki"

"Aurena kuma? Kamar yaya?"

Ya ce "Wallahi nima ban sani ba" Suwaiba ta cigaba da dariya, tana Waukar jakar kayan kwalliyar ta.

Baba ne ya shigo Wakin, ya tarar da Nana a zaune, ga Nasiru a gabanta da kofin koko.

"Yauwwa kin tashi kenan? To ki buWe

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login