Showing 3001 words to 6000 words out of 194715 words
take faɗe idan Hausa ta wuce zo tafi zauna ina zuwa zansha ruwa da sauran kananan word to ba wani ganewa take ba. Da kyar mum ta iya cewa Sadiq "Bawan Allah ya sunan ka? kuma inane gidan ku dan gobe nazo muje neman nata tare" Murmushi Sadiq sarkin murmushi yayi kafin yace "Ga gidan mu can mai kofar kwanon nan sunana Sadiq wayan nan biyun kanne nane Yusuf da Sha'aban Yusuf Maman mu ɗaya Sha'aban kuma ɗan kanin Baban mu ne" "Na gode kwarai da gaske Babana dan sunan babana gare ka Allah ya biyaku da gidan Aljanna" murmushi Sadiq yayi yana faɗin "Ba komai Mama sai da safe" ya kai karshen maganar tare da juyawa suka bar wajen, Hannun Jehan Mum ta riko dan su koma cikin gida "Where are we going mum?" harara cikin duhu Mum ta wurga mata kafin tace "cikin gida" "Mum which kind cikin gida kuma? Where is Rimsha what about her?" Shiru Mum tayi dan bakin ciki ji take kamar ta wanke Jehan da mari haka Allah ya kaddara amma ko mai ya faru Jehan da Goggo ne sila "Mum please talk to me now" "Jehan wallahi ki fita ido na idan zaki rabu da wanna shegiyar yaren turawan ki kama Hausa gara miki ki kama yaren ki kina yar fulani shuwa arab Daddyn ku cikakken bafulatani ni cikakkiyar shuwa arab amma dan iskanci baki iya yaren mu ko ka ɗan ba sai aron yare ki bi ki addabi mutane to wallahi tun wuri ki fita harkan yaren yahudawan nan ki kama yaren uwar ki da uban ki kai kaji min ƴa" "Mum what are you saying? why are you shouting anytime everyday" Dogon tsaki mum taja ba tare da ta sake magana ba ta ja hannun ta suka wuce cikin gida dan tasan idan ta biyewa Jehan haukata ta ta zatayi.
A tsakiyar gida suka isko Goggo na alwala sallar issha sakin hannu Jehan Mum tayi tare da wucewa ɗaki abun ta kallon Goggo Jehan tayi tace "My Goggo please where is Rimsha" da sauri Goggo ta ɗago kai tana faɗin "What are you saying Jehan? You mean up til now they didn't see Rimsha?" gyaɗa mata kai Jehan tayi ba tare da tayi magana ba ta nufi cikin ɗaki "Jehan kizo kiyi alwala" cewar goggo "No goggo ba yanzu zan yi sallah ba sai an jima" daga cikin ɗaki mum tace cikin harshen turanci "Wannan ne kuma wane uwar ki baki isa ba wallahi ko ki wuce kije kiyi alwala kizo kiyi sallah a gaba na ko kuma na fito na same ki a wajen" Shiru Jehan ta tsaya ta kasa cigaba da tafiya dan mum bata taɓa mata magana a irin wanna sigar ba juyowa tayi ta kalli goggo "Ni ma dai Jehan awan nan gabar ba zan bi bayan ki ba duk wanda baya sallah bai da wata amfani a duniya da kuma lahira sanna idan baki sallah a kan lokaci idan kin mutu kunama da maciji ne zasu yi gadin ki a cikin gabari ki kuma wutar jahannama zaki tafi saɓanin mai sallah akan lokaci da Mala'ikun rahma ne zasuyi gadin sa a kabarin sa su buɗe masa kofar aljanna ya rinƙa shakan kamshin aljanna sanna ya shiga aljanna" Ta kai karshen maganar tare da mikewa ta wuce ɗaki.
Ɗaki Jehan ta shiga ta ɗauko wayar ta kirar iPhone 14 ta kunna wutar wayar ta dawo tsakar gida ta ɗauki buta tana bin butar da kallo aranta tana faɗin "Disgusting gaskiya ba zan iya wannan rayuwa ba dole na koma asalin gidan mu" kitchen ta nufa ta ɗebo ruwa a butan ta dawo wajen da goggo tayi alwala, ita ma tayi alwala ta wuce ɗaki tana turo baki kamar biro tana kunkuni.
Tana shiga ɗaki ta ajiye wayar saman yar gadon su ta ɗauki ɗan karamin hijabi ta shifiɗa dadduma ta tada Sallah abun mamaki a nitse tayi sallar tare da karanta manya manyan surori a Qur'ani irin su suratul Yusuf da Aaraf a nitse tayi sallar nata sai dai hijabin nata ne bai gama rufe mata hannu ba a haka tayi Sallar.
Bayan ta idar ta ɗaga hannu sama tayi addu'a mai tsawo sanna ta shafa ta mike ta cire hijabin ta mai da saman trolley ta tare da naɗe daddumar ta ajiye saman hijabin nata ta ɗauki wayar ta, ta fito waje nan tsakar gida ta isko mum da goggo sun tasa abinci a gaba sun kasa ci dukkan su sun buga uban ta gumi suna tunani ga wayar mum a gefen ta kirar I phone 13 ta kunna wutar wayar tana haska musu wajen. Kallon Abincin Jehan tayi shinkafa'ce da miyar steew da naman rago yaji ganye irin su lettuce cucumber cabbage da dai sauran su dogon tsaki taja ta nufi hanyar fita gidan babu hijabi" Jehan ina zaki je? Cewar mum "mum I'm feeling hungry kuma ni gaskiya i can't eat this dirty food I want to go and withdraw money from my Account to buy something that I will eat" "Jehan karki kashe kuɗin cikin Account na kin nan saboda bamu san me gobe zata haifar ba kiyi hakuri ki ci abincin nan yau kam kinji? Cewar mum kallon goggo Jehan tayi tana faɗin "ni gaskiya I can't wallahi" "Ok naji bazaki ci ba na yarda amma karki fita da daddaren nan kinga yanzu ma bamu ga Rinsha ba ko? Ki bari na je na ciro kuɗin na sawo miki ko me kike son ci" girgiza kai Jehan tayi kafin tace "No mum bana so, ki zauna i will go by myself" tana kai karshen maganar ta fice da sauri mum na faɗin "To ki dawo ki sa hijabi" ina kan mum tayi magana ma Jehan ta fice abun ta kallon mum goggo tayi tace "Maryam kiyi hakuri kici Abincin ki kinji ko?" girgiza kai mum tayi tana faɗin "Aunty Aisha ba zan iya cin Abincin ba bakina ba daɗi ina Rimsha take? Wani hali take ciki? Hannun su wa take? Mutane na gari ne ko na banza? Taci Abinci ne? ko bata ci ba? Wanna tunani ba zai barni na iya cin Abinci ba Aunty A'isha" dafa kafaɗar ta goggo tayi cikin tausayin uwa da ƴa tace "Na sani Maryam dole ki shiga tashin hankali muma muka shiga tashin hankali bare ke amma ki daure ki ci Abinci nan In Sha Allah babu abun da zai samu Rimsha zata dawo gare mu cikin koshin lafiya" da kyar mum ta iya cewa "Aunty A'isha ina ji ajikina duk in da Rimsha take bata lafiya tana cikin tashin hankali da damuwa" "A'a Maryam ki dai na faɗin hakan ki mata Addu'a domin Addu'ar Uwa bata faɗuwa haka kasa banza kinji? Yanzu dai dan Allah kici abincin" miƙewa Mum tayi ta nufi ɗaki tana faɗin "Aunty A'isha sai da safe ba zan iya cin komai ba" ta kai karshen maganar tare da shigewa ɗaki dafe kai goggo tayi tana salati da ambaton sunan Allah a ranta. Tana kokarin miƙewa Jahan ta shigo gidan babu ko sallama, kusa da goggo tazo ta miƙa mata ledoji biyu farare masu ɗauke da takeaway da drinks a ciki ta wuce da leda ɗaya ɗakin ta in da sabo goggo ta saba tun da su kazo garin nan Jehan bata cin Abincin da suke girkawa sai dai taje restaurants tayo musu takeaway kuma bata taɓa saya ita kaɗai guda huɗu take saya kullun goggo tasha ruman mamakin ganin yau ta sayi guda uku sai daga baya ta tuna ashe Rimsha bata nan, jiki ba kwari goggo ta mike taje ta rufe musu kofar gida sanna ta dawo ta wuce ɗakin mum saman gado ta isko mum kwance kamar mai barci ajiye mata wayar ta da kuma leda ɗaya daga cikin ledojin da Jehan ta sawo musu abinci goggo tayi, ta juya ta fita ta nufi ɗakin Jahan kasan cewar ɗakuna biyu ne a cikin gidan mum da Rimsha take kwana ita kuma goggo da Jehan zaune a tsakiyar ɗaki ta isko Jehan tana cin abinci fried rice da pepper chicken ajiye nata Abincin goggo tayi ta haye gadon su ta kwanta dan ita ma bata jin yinwa ko kaɗan ɓatan Rimsha ya tsaya mata a rai sosai, Addu'a tayi ta yiwa Rimsha akan duk in da take Allah ya tsare ta da haka har barci ɓarawo yayi awon gaba da ita. Ita kuwa Jehan sai da taci tayi nak sanna ta kwanshe kayan ta gyara wajen dan ita mace ce mai son tsabta bata son datti ko kaɗan. Sai da ta gyare wajen tsab ta sauya kayan jikin ta izuwa na barci ta haye gado kusa da goggo ta kwanta tare switch off na wayar ta ba jimawa barci yayi awon gaba da ita dayake ba tare da Rimsha suke kwana ba sai bata wani damu da rashin Rimsha ɗin sosai ba.
Misalin karfe 1 na dare duniya duk sunyi barci Mum na zaune tsakiyar gadon ta ta kifa kai da gwiwa tana sharar kuka tana cikin matsanancinyar damuwa da tashin hankali ɓatan Rimsha, sosai take kuka damuwa sun haɗu sun mata yawa ga yanayin Jehan ga ɓatan Rimsha har karfe 2 na dare tana zaune tana sharar kuka.
Sai 2:30 ta mike ta ɗauro alwala a toilet na ɗakin ta tazo ta fara sallah tana kai wa Allah kukan ta.
Kamar yadda ta ga rana haka taga dare dan ta kasa rintsawa gani take kamar Rimsha zata dawo komai dare.
Washegari tun karfe 6 mum ta fita ta nufi gidan su Sadiq yayin da ita kuma Jehan ke sharar barcin ta goggo na fama da Aikace Aikace gida tana kokarin ɗunɗuma musu abincin daren su na jiya da basu samu damar ci ba dan suci da safen.
Da sallama mum ta shiga gidan su Sadiq yana tsaye a tsakar gida shi da maman sa da alama wani magana suke jin sallamar mum yasa suka juya a tare, ganin mum yasa Sadiq ya ɗan saki murmushi yana faɗin "Sannu da zuwa Mama ina kwana?" "Lafiya lou babana" kallon Mum Maman Sadiq tayi cikin mutuntawa tace "Sannu ki da zuwa yanzu Sadiq ke faɗa min abun da ke faruwa na ɓatar ƴarki Allah sarki Allah ya bayyana ta" da sauri mum tace "Amin ya Allah" "Mama bari na kira su Sha'aban muje mu duba gidajen masu anguwanni ko Allah zai sa mu dace muga yarinyar" "To Sadiq Allah Ubangijin yasa ku ganta Allah ya bada Sa'a" "Amin" Sadiq ya amsa da shi sanna ya dubi mum yace "Mama ki koma gida zamu dubata gidajen masu anguwanni da dai duk in da ya dace" girgiza kai mum tayi cikin sauri tana faɗin "A'a babana muje tare ba zan iya zama a gida ba hankalina ba zai taɓa kwanciya ba". Ba yadda Sadiq bai yi da Mum akan ta koma gida ta jira su ba amma taki har Maman Sadiq ta sa baki amma mum taki haka Sadiq ya hakura suka tafi cikin jin kunya ya jera da mum suka fito ya shiga ɗakin su dake zauren gidan ya kira Sha'aban da Yusuf suka fito suka jera a tare suka fice daga gidan.
Gidajen masu anguwanni suka fara zuwa suna tambaya, duk in da suka je ace musu ba'a ganta ba sunje gidajen masu anguwanni 5 amma shiru shiru ba labari mum ta gaji iya gajiya dan bata saba tafiyar kafa ba ga yinwa da take ji tun jiya da rana rabon ta da Abinci amma saboda tana da yakinin za'a iya ganin Rimsha ko da a hanya ne yasa ta danne duk wani abun da take ji ta jure ta cigaba da bin su Sadiq. Duk in da Sadiq yake tunanin za'a ga Rimsha sunje amma shiru daga karshe sai ya yanke shawarar suje su kai wa malamai kuɗi afara yi musu addu'a. Haka kuwa akayi malamai biyar mum ta rabawa dukka kuɗin hannun ta akan ayiwa Rimsha saukan Al Qur'ani mai girma sanna tayi sadaka da ɗan kuɗin da suka rage mata, jiki ba kwari ga gajiya da yinwa suka juya suka dawo anguwar su cikin mutunci da girmama juna sukayi sallama dasu Sadiq ta wuce gida da kyar take jan kafar ta duk kafar nata sun kunbura sun yi ja.
Da sallama ta shigo gidan a tsakar gida ta isko Jehan da goggo suna zaune goggo tayi jugumi tana tunani, ita ma jehan tana zaune gefe ta buga nata tagumin, ganin mum yasa sukayi saurin miƙewa Jehan ta fasa kuka tana faɗin "Mum whare is my Rimsha?" "Maryam ina Rimsha ɗin take?" Cewar goggo wuce wa mum tayi ta zauna saman tabarma tana mai da numfashi kamar zatayi kuka cikin sauri goggo ta koma ta zauna tare da dafa kafaɗar mum tana faɗin "Maryam ki faɗa mana ina Rimsha kar ki sa zuciyar mu ta buga" shiru mum tayi tana mai da numfashi ta kasa magana.
To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai
💋Star Lady💋
Share fisabilillah 👏
💞💕
💕💞💕
💕💞💕💞
💞💕💞💕💞
Mai bukatan karanta book ɗin*TRIPLETS* daga farko har karshe yamin magana ta WhatsApp da wannan phone number 09162620621 ban da kira please
STAR 🌟 LADY..✍️
*💋The beginning💋*
Episode 2
____Komawa itama Jehan tayi ta zauna ta dafa mum kamar zata yi kuka tace "Mum please where is Rimsha?" Har lokacin mum bata samu damar yi musu magana ba hasali ma dukar da kanta kasa tayi tana sauke ajiyar zuciya, hawaye Jehan ta farayi dan duk wan nan rashin shiri da suke da Rimsha tana bala'i kaunar kanwar nata.
Almost 30mins mum ta ɗauka san nan ta ɗago kai ta kalle su cikin karyewar zuciya ta fara magana "Aunty A'isha banga Rimsha ba babu ita duk in da muka san zamu ganta mun duba bamu gan taba" tashin hankali iya tashin hankali goggo da Jehan sun shiga cike da matsanancinyar damuwa da tashin hankali goggo tace "Ai zama bai ganmu ba tashi za kuyi mu wuce police station mu kai Report" girgiza kai mum tayi tana faɗin "Aunty A'isha kin manta abun da Alhaji Shitu yace mana ne?" "A'a Maryam ban manta ba amma ai yanzu ya zama dole ne muje police station dan wan nan ba karamin case bane kin san dai idan Allah yayi Nawazudden ya zo yanzu ba zasu kare da shi ta daɗi ba ko?" "Nasani Aunty A'isha na sani amma to ya zamuyi bamu isa muje police station ba jiya ma da nace muje ido na ne ya rufe gaba ɗaya ban da haka da ban isa in yi wani zancen police station ba" "Maryam yanzu to me abun yi?" "Aunty A'isha sai dai fa mu zubawa sarautan Allah ido mu ci-gaba da yiwa Rimsha addu'a amma batun muje police station ko mu fita neman ta ma ya kare daga yanzu dan gudun ukubar da zamu shiga kin ji dai abun da Alhaji Shitu yace mana ko?" Shiru goggo tayi tana tunani ita kuma Jehan sai ruwan hawaye take wani na bin wani tana mai dana sanin kin zuwa aikan da tayi har a ka aiki Rimsha yanzu gashi yar uwar ta ɗaya tilo a duniya ta ɓata innalillahi wa inna ilaihir rajiun, jugum jugum sukayi dukkan su ba mai iya yiwa ɗan uwan sa magana kowa da abun da yake tunawa a ran sa amma kallo ɗaya zaka musu kaga tsananin tashin hankali a kan fuskokin su.
KANO STATE
Katafaren two storey building gida ne mai matukar kyau da tsada iya haɗuwa gidan nan ya haɗu kai da ganin gidan kasan masu rayuwa cikin wan nan gidan ko dai wani babban kusa daga gomnati ko wani babban ɗan kasuwa gate ɗin gidan kawai abun kallo ne ɓangaren biyu ne a cikin gidan ga wani ɗan ma dai dai cin pool a tsakar harabar gidan daga gefen hagu katafaren parking space ne mai ɗauke da katon rumfa ga dankara dankaran motoncin uku a wajen kirar *Mercedes-Benz* *McLaren solus GT.* *Roll-Royce boat Tail* motocin kawai abun kallo ne daga gefen dama kuma shuke shuken fulawowi ne awajen masu matikar kyau da ban sha'awa launin ja da yellow daga ɗan gefen parking space wani Katafaren wajen hutawa ne dake kewaye da glass wajen ɗauke yake da tampatsa tampatsan kujeru masu numfashi set ɗaya launin sky blue a tsakiyar kujerun wani haɗaɗen sofa table ne mai ɗan girma a wajen da gefe guda kuma ga makeken fridge a wajen dake ɗauke da lemukan sha kai ko ta ina gidan nan ya haɗu ba karya.
Wani kyakkyawan puppy dog ne fari tas mai yalwataccen gashi a jikin sa ya fito da gudu daga katafaren kofar da zata sadaka da babban palo na gidan da
Da gudu wata yar matashiyar yarinya ta fito daga kofar wadda a shakaru ba zata wuci 13 to 14 years ba tana sanye cikin wandon jeans guntu zuwa guiwa da yar riga baki mara nauyi kanta ba ɗankwali ta saki gashi har zuwa bayan wuyar ta, an zuba mata kananan kitso a kan nata kyakkyawace sosai chocolate color tana da dogon hanci da kyakkyawar fuskar ga manya manyan idon farare tas kamar madara yar siririyace ba kuma siririya sosai ba yar ma dai dai ciya,
da gudu ta biyo puppy dog ɗin tana faɗin "My Dolly ki tsaya mana haba Dolly na so ki ke nayi kuka ne" gudu Dolly take sosai yarinyar tana bin ta a baya har sai da suka kai wajen wasa dake gidan waje ne mai girma ga gefen buga basket ball a gefe ga wajen lilo ga wajen hawa dokin wasa da motoci na yara na wasa da dai sauran su wajen ya haɗu iya haduwa. Saman lilo Dolly ta hau ta zauna da gudu yarinyar ta kariso wajen tana haki tana mai da numfashi ta tsaya ta rike kugun ta da hannun ta dukka biyu tana kallon Dollyn ta yayin