Showing 123001 words to 126000 words out of 194715 words
yana bawa Romeo hakuri, dan yasan halin Romeo sarai duk yadda yake son sunnan idan suka ɓata masa rai ya zuciya to dukan mutuwa yake musu, gashi kuma da alama yaji haushin abun da Tga ɗin yayiwa James sosai, dan da alama ya ɗan ɓata rai ka ɗan, shiyasa ma ya murɗe wa Tga ɗin hannu kuma ya dake sa har sai da ya zube kan gwiwowin sa, kwata kwata Michael baya son yaga suna samun matsala da juna.
Su kuwa su daddy sai godiya suke dan yau Romeo bai ɗauki zafi sosai ba, da ya ɗau zafi yadda Tga ya bugi James ai da yanzu wani zance ake.
Ganin yadda Romeo ya ɗagawa Tga wuya sama sosai ne, gashi kuma Tga na shan wahala wajen jan numfashi, hakan yasa murya na rawa daddy ya kariso wajen ya ɗan tsaya daga ɗan baya, cike da kaunar ƴaƴan nasa yace "Please my lion leave him" shiru Romeo ya musu yana ta kallon face ɗin Tga kamar mai karantar wani abu
daddy zai sake magana, Romeo ya dakatar da shi ta hanyar ɗaga masa hannu alamar bai son jin wata magana kuma, shiru daddy yayi ya koma gefe ya tsaya
jin kukan Michael ya fara yin yawa ne kuma gashi Michael yana da matsala yasa Romeo ya juyo da dara daran blue eyes nasa kan fiskar Michael ɗin, a hankali ya saki gashin kan Tga ɗin tare da nunawa Michael hanyar bedroom nasa da hannu ba tare da yayi magana ba, dan bai son Michael ya shiga damuwa, kuma yasan halin sa sarai yanzu zai sa kan sa cikin damuwa,
matsowa Michael yayi da rarrafe ya kariso gaban Romeo yana faɗin "Please lion for giv....bai kai karshen maganar ba, Romeo ya daka masa wata gigitatchiyar tsawa wadda ya razana duk wata halitta mai rai dake cikin palon "I said get in!!!" Saboda tsorata Michael bai san lokacin da ya tashi da gudu ya haye sama ba ya razana sosai, yasan halin Romeo idan ya ɗau zafi ba wanda ya isa ya tinkaresa shi yasa su daddy duk suka tsaya a baya, shima Michael ɗin dan yafi su sanin halin Romeo ne, ya san bai ɗauki zafi sosai ba shi yasa ya tinkaresa.
Goya hannu a saman kirjin Romeo yayi gently ya fara magana "what is happened?" Yayi maganar yana tsare Tga da dara daran blue eyes nasa nan, da kyar Tga ya iya buɗe baki saboda wahalar yadda Romeo ya muɗe masa wuya ya sanya shi kallon sama, ba dan Romeo ne ya masa tambayar nan ba da ba zai iya magana ba, amma tun da Romeo ne ba yadda zai yi dole ya amsa Maganar ko ma tayaya ne, a hankali yace "please help me with water, i need water!!" kallon Romeo daddy da Uncle Herry sukayi suna jiran Romeo ya bada izinin su kawo wa Tga ɗin ruwan, amma sai sukaga Romeo yayi shiru alamar ba za'a kawo ruwan ba kenan, dan shi Romeo shirun sa ma magana ne, wani lokaci da shiru yake magana da Mutane, gaba ɗaya jama'ar gidan sun san ma'anonin shirun Romeo, idan anana magana da shi yayi shiru to akoi abun da yake nufi baya shiru haka kawai, sannan baya magana sai da kwakkwaran dalili, shima kafin yayi maganar sai ya ɗauki lokaci kuma ba wai dan bai ji me kace ba, yana ji, wani lokaci ka masa magana kana sauri sai yafi 5mins bai baka amsa ba, wata zubin ma har sai ka cire rai da zai yi magana sai kuma gaji ya baka amsa a nitse da sassayan murya, idan kuma bai game sa ba da wannan shirun zai baka amsa in ka gane to ruwan ka, idan ma baka gane ba nan ma kai ta shafa shi dai ya gama nasa.
Komawa yayi saman sofa ya zauna yayi shiru yana kallon Tga yana jiran amsar tambayar sa, dan shi baya mai mai ta magana idan yayi, idan baka ji bama dole dai ka bashi amsa, already Tga ya san da wannan dan haka sai ya rarrafa ya koma kusa da kafafun Romeo cikin nitsuwa da shakakiyar murya yace "I'm sorry lion it's was a mistake" shiru Romeo ya masa kamar bai ji me Tga ɗin yace ba, ganin haka yasa Tga ya gane, bayani abun da ya haɗasu faɗa da James kawai Romeo yake buƙatar ji, cike da tsoron, murya na rawa ya fara bawa Romeo labarin abun da yafaru tum daga farko har kashe.
Slowly Romeo ya kai kallon sa kan mutumin, sannan ya kalli James dake ta faman juyi a wajen yana numfashi da kyar da kyar, dawo da kallon sa kan Tga yayi yana mamakin, wai ace James ya samu accident dan bai ji ciwo ba ya dawo gida kuma Tga ya masa irin wannan dukan, nan take yaji wani ɓacin rai ya rufe masa zuciya, a fusace ya miƙe rai a ɓace ya fara dukan Tga, daddy na bashi hakuri ya kyale Tga haka ai ya daku amma ina ba wanda ya saurara dan Tga ya bashi haushi, ace James yayi accident Allah ya tsare bai ji ciwo ba ya dawo sannan Tga ya kama sa ya masa irin wannan duka dan yazo da wanda ya buge da mota gida.
Sosai Romeo ya bugi Tga har sai da yaji ya ishe sa, yayin da shi kuma Tga ya sume baya ko motsi, yayi lilis a hannun Romeo, dan ma yayi Sa'a Romeo bai ɗau zafi sosai ba
Cike da jin haushin Tga Romeo ya wuce ya nufi in da James ke kwance yana mai da namfashi da kyar da kyar, ko kallon in da su daddy suke bai yi ba, ya ɗauki James ya saɓa sa a kafa ɗan sa ya haye saman bene ya koma bedroom na sa.
Yana tafiya su daddy sukayo kan Tga, dan bashi taimakon gaggawa kasan cewar daddy likitane.
Shi kuwa Romeo saman katafaren gadon sa ya kwatar da James kusa da Michael dake kwance yana kuka.
Ko kallon in da Michael ɗin yake Romeo bai yi ba, ya wuce ya ɗauko kayan aiki ya fara duba James.
Sai bayan James ya dawo hayyacin sane yace "Please lion ka taimaki mutumin nan da na buge da mota" shiru Romeo ya masa kamar bai ji me yace ba, shi kuma Michael wai yayi fushi da shu shi yasa ya kwanta shiru yana hawaye.
After 40mins
Sai bayan Romeo ya gama duk abun da ya dace yayiwa James ne sannan yace su kira likita ya duba mutumin, amma shi ba zai duba kowa ba, da sauri James ya miƙe, jikin sa ba kwari ya fito ya nufi wajen daddy, dan ya rokesa ya duba mutumin, abun mamaki ko da ya fito palon sai bai ga mutumin ba, yaji tsoron ko dai sunje sun jefar da mutumin ne kamar yadda suka faɗa, da sauri ya nufi hanyar fita daga palon dan yaje ya tambayo security waya fita da mutumin nan
Yana kokarin fita muryan dad ta dakatar da shi "James where are you going" a sukwane ya juyo ya kalli daddy cikin sauri yace "Please dad where is the man I brought" murmushi daddy yayi kafin ya sanar da James mutumin yana ɗakin duba marasa lafiyar su, da sauri James ya nufi wajen dan alhakin kula da mutumin na rataye ne a wuyar sa.
Yaji daɗi sosai ganin yadda daddy ya bawa mutumin nan kulawa, har da karin ruwa daddy ya masa, sannan mutumin ya farka, kafar sa da ya karye kuma daddy ya sanya kafar cikin wata na ura na aikin su likitocin.
Karisawa cikin ɗakin James yayi, ya zauna a gefen mutumin yana faɗin "Sorry" kallon sa mutumin yayi kafin ya ɗan ɗaga masa kai kawai, "What is your name?" James ya tambayi sunan mutumin, a hankali mutumin yace masa "Musharraf" jinjina kai James yayi kafin yace "are you an Arab from saudia?" Gyaɗa masa kai mutumin yayi kafin yace "Yes" shiru James yayi kafin ya sake cewa "Are you a Muslim?" Nan ma eh mutumin yace masa "Okey how is your body now" James ya faɗa yana kokarin mikewa ya nufar hanyar fita "Alhadulillah" Musharraf ya faɗa yana bin James da ido kawai amma shi kaɗai yasan azaban da yake ji.
Ficewa James yayi daga room ɗin yana jin daɗi da mutumin bai mutu ba, a palo ya isko daddy, da fara'a ya yiwa daddy godiya, shima daddy ba karamin daɗi yaji ba, dama kuma ya kula da mutumin ne dan James yaji daɗi, yana son yaga yaran sa suna nuna masa soyayya kamar yadda yake son su amma basa hakan sai dai tsawa da faɗa, shi yasa yanzu yake kokarin yin duk abun da suke so dan ya jawo su jikin sa.
Wannan kenan ku koma Nigeria muga meke faruwa
💞NIGERIA💞
💞KATSINA💞
kallon Sadiq tayi idon ta a bushe, dan yanzu gaba ɗaya ta dai na jin kuka zuciyar ta ya bushe, cikin sauri tace "Sadiq ka nemomin masu sayan gidan nan" sannan ta dawo da kallon ta kan gwaggo dake ta faman kuka tace "Gwaggo bamu bukatar mu fitar da Mum waje kuɗin aiki kawai zamu nema mu wuce babban asibiti, na san dai kuɗin gidan nan zai isa ai mata aiki, daman kuɗin jirgin fita wajen shi ne mai tsada, dan haka a sayar da gidan nan a mata magani daga baya zamu san abun yi bayan ta samu lafiya" ta kai karshen maganar tare da miƙewa ta nufi cikin ɗaki.
Jim kaɗan ta fito sanye da abaya a jikin ta tana faɗin "Gwaggo ki koma hospital ni da Sadiq zamu nemo mai sayan gidan" kasa magana gwaggo tayi dan ta jinjinawa Jehan wannan shine dalilin da yasa a kace ilimi na da amfani yau gashi ilimin Jehan ya taimaka musu, dan kwata kwata bata kawo zancen sai da gida ko kuma karsu fita waje da mum ba sai gashi Jehan ta kawo musu mafita.
Jiki ba kwari gwaggo ta miƙe ta wuce hospital wajen mum, su kuma Jehan da Sadiq suka wuce nemam dillalai.
Babban tashin hankali shine duk wanda su Jehan suka kira dan ya sayi gidan idan ya fahimci kuɗi suke buƙata ruwa a jallo, sai yayiwa gidan kuɗin wulakanci, a wannan karon ba karamin tashin hankali Jehan ta shiga ba, dan abun da take tunani shine mafitar su shima yana neman ya gagara, ga mum kuma kwance rai a hannun Allah kowani lokaci daga yanzu tana iya mutuwa, dan da gaggawa ake buƙatar a mata aiki saboda ciwon yaci jikin ta sosai, dan likitan yace ciwon ya jima a zuciyar ta tun bata kai haka ba, cikin watan nan ne kuma ciwon ya kara tsanan ta saboda tashin hankali da ta shiga na rasuwar daddy da kuma ɓatan Rimsha.
Kamar zararriya haka Jehan ta dawo lokaci guda ta fita hayyacin ta rasa mada fa.
Da kyar suka samu wani ya sai gidan 2 million haka suka sallama masa ya zuba musu kuɗin a account ɗin mum, haka Jehan taje ta ciro 1.5m misalin karfe 5 na yamma, duk wannan yawon da suke tare da Sadiq suke, haka suka shiga a daidaita sahu suka kama hanyar asibiti dan taje ta ɗauki mum su wuce babban hospital, tana rungume da jakar kuɗin tana tunanin halin da suke ciki.
A kan hanyar su ta zuwa asibitin ne suka samu accident da wata mota, cikin kwata Jehan ta faɗa yayin da shi kuma Sadiq ya faɗi can gefen titi, saboda juyin da a daidaita sahun tayi da su, shi ne ta watsar da su, kan kace me jama'a sun taru sai salati suke yayin da shima mai motar da sukayi accident ɗin da shi ya sume sakamakon buga kan sa da glass ɗin marfin motar da yayi.
Allah ya kiyaye Jehan da Sadiq basu ji ciwo sosai ba, a sukwane Jehan ta miƙe bata damu da kwatar dake jikin taba, ita dai kawai burin ta mum ɗin ta tafita daga haɗari ta samu lafiya.
Kai tsaye bakin hanya ta koma tana neman wani mai a daidaita sahu dan su wuce asibiti, ta ruɗe ta manta da jakar kuɗin ma, haka Sadiq yazo ya same ta, suka ɗan kara gaba da in da sukayi accident ɗin suka samu wani abun hawan, zasu hau kenan Sadiq yace mata "Jehan ina kuɗin kuma" a sukwane ta juyo, tana faɗin "Yana cikin wannan abun da muka hau ɗin" a guje Sadiq ya juya ya koma, da sauri ta bi bayan sa.
Ko da suka zo wajen babu jakar, tsab suka duba cikin mashin ɗin duk da cewa mashin ɗin ma ya faɗi dan sai da sukayi juyi biyu kafin mashin ɗin ya faɗi.
Tsab suka duba cikim mashin ɗin babu komai, a razane Sadiq ya ɗago yana tambayar jama'ar dake wajen, kowa yace masa bai gani ba, mutuwar tsaye Jehan tayi ta kasa motsawa, ta rasa me zatayi, daman ta ciro kuɗin ne a nata tunani dan tana zuwa kawai su wuce babban asibiti ta biya kuɗi kawai a yiwa mum aiki ba sai sun kai gobe ba, a yau zaayiwa mum komai shi yasa tayi sauri ta ciro kuɗin dan kar banki su rufe, gashi a daren nan take son ayiwa mum aiki kuma banki basa aiki da daddare bare tace zata bar kuɗin a bank har sai an buƙata, a takaice dai bata son ɓata lokacin shi yasa ta ciro kuɗin, yanzu gashi wanda ya fisu iya ajiyar kuɗin ya ɗauke,ko in ce mara imani.
Shi ma Sadiq kasa magana yayi dan yasan ba karamin wahala suka shaba, wajen neman kuɗin nan, jiki ba kwari ya kariso wajen da Jehan ɗin ke tsaye, a hankali yace "Ya Zamuyi" shiru Jehan ta masa dan bata da bakin magana, ganin haka yasa ya riko hannun ta suka hau abin hawan da suka tare suka nufi asibiti, cike da tashin hankali da fargaban abun da zasu gayawa gwaggo.
wannan shi ne ba ɗaya kanin biyu, ba gida kuma ba kuɗi sannan ba yiwa mum aiki, tashin sense, muje zuwa yanzu wasan zai fara, karki bari a baki labari.
👹Daular mutuwa👹
Rimsha bata sake fita ba tun ranar da abun nan ya faru tsakanin ta da duna, yau kwana biyu kenan.
Yauma kamar kullun suna zaune cikin ɗakin su, sunyi jugum jugum, ita Rimsha sai faman kokarin ɗaure dark black curly hair ta take, gashin nata na da tsantsi sosai yaki ɗauruwa, ita kuma bata son barin sa a sake haka saboda ƙuran dake ɗakin nasu. Cikin sauri Ayla tace "La Meesha muje mu gaishe da baba, kwana biyu ban je ba" juyo da dara daran sleeping eyes nata Rimsha tayi kan Ayla kafin tace "waye kuma baba?" Miƙe wa Ayla tayi tana faɗin "Zo muje ki gan shi" miƙa wa Ayla hannu Rimsha tayi, Ayla tajata ta miƙe tana faɗin "Meesha kin fini quality fa" shiru Rimsha ta mata ba tayi magana ba, mukowa Ayla hannu itama kausar tayi, Ayla ta kama, ta miƙar da ita.
A tare suka jera suka fita a ɗakin, suna fita suka hango Mustapha a bakin kofar ɗakin sa yana ɗaure takalmin sa da igiya, da yar fara'ar su suka karisa wajen sa, suka gaida shi, shima da fara'a ya amsa musu tare da tambayar ina zasu je, Ayla ce ta sanar da shi wajen baba zasu je "to kuje nima ina zuwa bari na ɗan gama aiki na" to suka amsa masa da shi kafin su wuce su shiga ɗaya daga cikin ɗakunan dake wajen, yanzu sosai Mustapha ke sake musu fuska suyi hira, tun ranar da Rimsha ta masa magana, shi kenan sai suka zama ɗaya.
Kusa da wani tsohon mutumi suka je suka zauna, tsoho ne sosai, ya manyan ta, gashi fari tas kamar bature ga dogon hanci da dara daran ido, duk da tsufa da wahala da yake ciki, hakan ba zai hana kaga kyan saba, ga gashin kan nan nasa da ya zama farin saboda tsufa kwance luf mai tsantsi har goshin sa, Rimsha ta sha mamakin ganin mutumin nan, ji take kamar ta san shi, lokaci guda taji kaunar tsohon ya shiga ranta.
Ayla ce ta fara gaishe sa, ya amsa cike da kulawa yana tambayar ta kwana biyu ina ta shiga ta dai na zuwa wajen sa suyi hira, nan take bashi labarin su Rimsha, sosai ya jajan ta musu, kafin suma su gaishe shi ya amsa, sai kallon shi Rimsha keyi tana tunanin ina ta san wannan fuskar, amma ina ta kasa tunawa, amma dai koma me tabbas tasan wannan fuskar.
Suna zaune suna hira har Mustapha shima yazo nan suka ci-gaba da hiran su, baba na basu labarai suna dariya, a nan wata yarinya tazo ta same su, suka ci-gaba da hira..
Share fisabilillah 👏
To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai🤪
💞Star Lady💞
💞TRIPLET'S💞
💞STAR LADY💞
*Gargarɗi*
_Ban amince wani ko wata yayi amfani da wani sashe na book ɗin nan ba ta kowace siga, ko akaranta mun shi a youtube batare da an nemi izini awurina ba, ko a haɗamun document, ko amin Edit, Idan kunne yaji jiki ya tsira ko da Allah nabar mutun zaibi mun haƙƙina_
WhatsApp me for more information 09162620621
Episode 26
Suna zaune suna hira har Mustapha shima yazo nan suka ci-gaba da hiran su, baba na basu labarai suna dariya, a nan wata yarinya tazo ta same su, suka ci-gaba da hira, nan baba ke basu labarin mutanen da a ha rinƙa kashe wa a gidan, sosai Rimsha ta sha mamaki kuma tafi kowa kuka a cikin su, sai lokacin baba ya ɗago ido yana kallon ta, sosai shima yayi shock da ganin ta, abun ya bashi mamaki sai yaji kamar ya santa kamar ya taɓa rayuwa da ita a wani wajen, ya zuba mata ido, ya ɗan jima yama kallon ta kafin ya fara share mata hawaye