Showing 45001 words to 48000 words out of 182919 words

Chapter 16 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

609

min abinda ya faranta raina ba “haka ne kasan baby da shiga rai ai na lura tunda aka haifi yaron nan kake son shi kai ma allah ya baka naka masu albarka shafa fuskar babyn ya cigaba dayi yana murmushi “babana ,my prince ,my averything cikin murmushi ya kalli mami “sunan babana hisham yasa bansan yadda zan misalta farincikina ba.”



nan take fuskar nana hauwa’u data sauran yanuwata ta bayyana tsantsar farinciki daman burinta kenan sunan babanta amman duba ga shi kad’ai iyayensa suka haifa yasa tayi tunanin sunan abbansa zai sa allah sarki ashe ita zai wa suprise
ta kalli yaya hisham tana masa kallo mai dauke da murna da godiya“maryam kuwa ji tayi jikinta yayi mugu mugun sanyi sai taji inama ace nmj zata haifa ba mace ba kai wannnan mutumin ko me zata haifar masa bazai nuna farincikinsa haka ba “ta fad’a a kasan rabata “hisham ya tsallake sunan kowa a dangi yasa na babana bansan yadda zan kwatata murnata ba yau “. hankalin mami gabadaya ta maido kan ata dake zaune rike da baby “lallai wannan abu yayi kyau Allah yayiwa rayuwar ishaq albarka koni naji dadi sosai kuma nasan hajiya zulfa’u ma zataji dadin wannna alamarin kai kowa ma nasan zai ji dadi yaya hisham ya mike ya fita yana dariya byn Kmr second biyar nana hauwa’u ta kwashe kayan baby daaka kawo wa mami tabiyo mijinta d’akin da take jego suka shiga tare ta nufi wordrobe din baby ta bude ta soma qoqarin ajiye kaya .”


Ahankali ya tako zuwa inda take ji tayi kawai ya hadeta da jikinsa ta baya ta juyo a tsorace suka hada ido fuskarsa a sake “meye na wani tsorata bayan kinsan mu kadai ne a dakin “ ?a ganinka bai dace naji tsoro ba?ya daga mata girasa daya lumshe masa idanunta tayi tace “yau ne fa na cika kwana shida da haihuwa “matsota ya sake yi sosai ya hadeta jikinsa “an só !? sai akace kar naji dumin jikin matata ?numfashi ta sauke alokacin da taji ya zame hular kanta ya fara shafa sabon kitson daaka mata kamar wata sokuwa haka ta dawo yayi kamar zai warware mata zani tayi saurin rikewa tana kallonsa ganin yadda ta tsorata ya saki murmushi yana cewa “malama babu abinda zan miki wani naunayen ajiyar zuciya ta sauke “nayi missing dumin jikinki da lip’s dinki bari na rungumeki na rage zafi yana gama fad’ar hk ya hadeta da jikinsa ya kai hannusa ya taro byn kanta ya hade bakinsu waje daya .”



***
Da misalin karfe shad’aya na daren ranar bayan maryamta taga ma komai nata ta dawo parlour’n ta zauna akan kujera hannuta rike da littafin zane tana aikin mr ata duk da tace bazataje aiki gobe ba saboda wulakancisa amman zatayi iyakar qoqarinta taga ta zana masa abinda yake so sai ta mikawa yusura gobe da sassafe ta mika masa ta jima tana zane sai dai bata gama ba acikin biyar uku kawai ta samu damar yi masa a qarshe ta tattara taje ta kwanta washegari karfe bakwai a gidan su yusura tayi mata alokacin yusura na qoqarin futa zuwa aiki bayan maryama sun gaisa da iyayen yusura ta maida hankalinta kanta “ya naga kin biyo ta nan kuma cikin wata irin shiga “?bazani aiki bane yau nazo ne na kawo miki wadan nan zane ki kaiwa mr ata “what ?haba maryama so kike ya tasheni aiki kawai kije ki shirya ki kai masa da kanki ?ai ban gama bane shiyasa nake jin tsoron zuwa ,shine ni zaki tura ni dai gsky Kiyi hakuri gara kije da kanki “yanzu dai bazaki kai masa ba?” gsky ba wai bazan kai masa bane tsoro nake ji maryama ta dauki lokaci tana fama da yusura as ending dai da kyar ta karba da zumar zata bawa madam some sukai sallama




Taron suna akayi a gidan mami mai cike da tsantsar farinciki dan tsabar murna ma mr ata bai je koina ba yayinda duk wanda ya kalli fuskarsa zai san yana cikin farinciki da annashuwa sannan duk wanda yaji sunan da baby yaci sai yayi murna tare da yiwa marigayi alhaji ishaq addua kowa ka kalli fuskarsa farinciki yake banda maryam da gabad’aya tayi wani iri kallo daya zaka mata kasan akwai damuwa atattare da ita duk da mami tana cikin hidima amman hankalinta na kan maryam bini bini zata nemota taga yanayinta ,baby ishaq wanda aka masa lakabi da ashraf ya samu kyaututtuka ta bangaren dabam dabam ta bangaren yan’uwa da kaninsa da kuma bangaren qawayen hajiya zulfa’u dana mami ata ma kyauta yayi masa ta mussaman inda ya bashi takardun gidajensa biyu dake acikin runin gidajensa dake banana estate .”



Zaune maryam take akan kujera a parlour’n umma ta rungume pillow hannuta rike da littafi wanda ya kasance english novel ne tana karantawa domin so take ta cire damuwar mr ata aranta dan tun safe take cikin tashin hankali da fargaba shiyasa ma ta kasa qarasa masa aikinsa dan batasan wainar daake toyawa ba jira take biyar tayi ta kira layin yusura taji ko ta bawa madam some .”knowking din kofa taji ta ajiye littafin hannunta akan kujera da pillow ta mike ta garasa bakin kofa ta bude wata kyakkyawar budurwa ta gani tsaye abakin kofar lokaci daya taji wani mummunar faduwar gaba from know where ya diram mata “ko zan iya shigowa ? budurwar ta tambaya “sunana anifa friend din sadam ko nace tare mukayi karatu dashi haka ma wurin aikinmu daya dashi bana nan nayi tafiya na dawo naji abinda ya samesa”jin haka yasa maryama ta qara sakin fuska sosai tace sannu da zuwa ki shigo daga ciki budurwar ta shigo ta tsaya tana qarewa falon kallo” ya kika tsaya ki zauna mana babu mutsu ta samu waje ta zauna tana cigaba da qarewa falon kallo .”


“Kece matar daya aura “?maryama ta gyda mata kai alamun “eh!allah sarki wai ya wannan alamarin ya kasance ance anemi sadam an rasa amman kuma ke kina raye ?kuma kin cigaba da rayuwa batare da kin cigaba da nemansa ba ko yana raye ko ya mutu?” ya zakice hk ?kin kuwa san irin nemanshi da mukayi ?” munyi iya qaqarinmu ni alokacin bana cikin haiyacina ni dai nasan an binnesa da ransa daga nan kuma bansan komai daya faru ba “okay budurwa ta gyada kanta tana cewa “allah bayyana shi idan yana raye idan kuma ya mutu allah ya jikinsa dan sadam mutumin kirki ne kowa nashi ne sam bashi da matsala banji dadin abinda ya faru dashi ba allah dai yayi masa rahma.”ameen !maryama ta fad’a .”muryarta cike da runi.”


“Amman dai ya kamata kiyi aure zuwa yanzu tunda baya raye .”maryama tayi shiru tana dubanta hakan yasa budurwar tace “am really sorry shawara ce na baki dan naga ke yarinya ce bai dace kice zaki tsaya batawa kanki lokaci ba saboda rayuwa babu tabbas ko yana raye bare baasan a hali da yake ciki ba a mace ne ko a raye “haka ne banji zafin mgnrki ba amman dai na barwa allah komai .”gsky ne kinyi rashin miji mai hakuri da son mutane kai baqarmin sabo mukai dashi ba alokacin muna karatu koda yaushe muna tare har ma mutane suka fara tunanin ko akwai soyayya a tsakaninmu .”


Maryama tayi murmushi kana tace “Amman kuma bai ta’ba bani labari ki ba ?duk wasu abokan karatusa nasani ,haka dayawa abokan aikinsa nasani kece dai gsky ko sunanki ban ta’ba ji ba sai yau shiru budurwar tayi sannan maryama ta cigaba “bari na kira mahaifiyarmu idan zata dawo yanzu ku hadu watakilla ya taba bata labarinki ?” Oh ! bata nan ne ?eh ta dan fita amman bazata jima ba zata dawo zan so naganta dan hasalima akwai abinda ya kawoni saboda akwai aikin project din da muka fara dashi kafin nayi tafiya in fact maryam document din gabadaya suna hannunsa inda zan samu document din gaskiya da zanji dadi sai na qarasa komai idan aka biyani sai nã kawo masa nashi kason tunda tare muka fara .”


“Okay wannan ba matsala bane wani suna ne ajiki sai naje dakinsa na duba miki uhm zakiga sunana da sunanshi maryama ta mike itama budurwar ta mike da sauri “ammm ko zan iya biyoki dan ba lallai ki gane document din ba maryam ta tsaya jim tana mata kallon mamaki kafin tace “tunda akwai suna ai komai zai zo da sauki amman dai muje tayi mata alamar ta biyota da hannunta “maryama tana gaba budurwar data kira kanta da anifa ta biyota basu tsaya akoina ba sai a bakin kofarsa .”


Tsayawa tayi cak qirjinta na bugawa a hankali ta tura kofar dakin ta sanya kafarta daya tana mai jin faduwar gaba tunda aka nemesa aka rasa bata qara shigowa dakin ba ta shigo sosai haka ma anifa abubuwa dayawa sun dawo mata yadda a farko kamar bazai karbi soyayyarta ba daga baya ta juye soyayyar gaskiyar daya dawo yana mata sadaukar wa da yayi a gareta aranar daurin aurensu murmushinsa tabbas matar tayi gsky shi din mutumin kirki ne .”a hankali ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana kallon koina a dakin komai nashi yana nan kamar lokacin da yake nan dakin babu dotti da alamun umma na kula da dakin sosai .”


Ahankali suka fara duba wuraren da takardu suke sai dai duk document din da maryama ta nuna mata sai anifa tace bashi bane can ta kalleta “ammmm ko akwai key din wordrobe dinsa a hannunki ?maryama daukowa tayi ta mika mata tare suka bude wani jaka suka gani dan haka suka fito dashi tare suka bude suka fito da takardun ciki gbdy sai dai basu gani ba tarasa yadda zatai can tayi wani tunani dan haka ta kalli maryama “ko zan iya samun ruwa ?ta dafe kanta maryama tayi tana cewa “sorry wallahi na manta ban baki ruwa ba akawo miki juice ko ruwan Kika fi bukata ?kawo min ruwan ma ya isa ok bari naje na kawo miki ta mike ta fita wanda hakan ya bawa budurwa damar kira a waya .”


byn an dauka ta soma magan kasa kasa “na fa duba inda kace amman banga komai ba sai wasu takardun dabam can bangaren data kira akace “ki dai duba da kyau zaki gani anan suke ,wa kika samu a gidan?”
“ wannna sakariyar yarinyar , okay shinkenan naji na daina ta fad’a tana ajiye wayar akan gado ta cigaba da dubawa har tagani naunayen ajiyar zuciya ta sauke da karfi ta dauki abinda ya kawota tana mgnr a fili “ya allah na gode maka da baka bari na sha wahala ba “kin gani ne taji sautin murayar ta cikin waya ?eh ! nagani bari nayi masa kyaywan ajiya ajikina kafin ta dawo ta daga rigarta daman akwai bodyhug data saka domin aiwatar da shirita ta nade takardun ta saka acikin rigarta ta maida rigarta ta sauke da sauri sannan ta cigaba dadduba sauran takardun zuwa sanda maryama ta dawo dakin tana qaqarin mika mata cup din ruwa taji sautin magana “me kik jira ne ?ga ruwa taji muryar maryama a gigice ta dago da sauri ta mike tana duban wayarta da mgn ta fito “kina jina Kiyi sauri mana ina kiranki please “budurwa tayi sauri ta dauki wayar tana rage volume ta gefe “wannan muryar fa ? Maryama ta furta a matukar rikice .”


Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 13


Jikin budurwar na kyarma tace “wani abokin aikina ne wallahi”ta fad’a a rikice tana maida hankalinta ga wayar “kana jina?” okay gani nan zuwa yanzu “daga haka ta kashe wayar gbdy, maryama tayi shiru tare da zuba mata shayayyun idanunta tana kallonta qirjinta na dokowa da qarfi “tabbas wannna muryar da taji yanzu daga cikin wayarta tasanta kuma ba muryar kowa bace face muryar ya sadam dinta ,jikinta a matukar sanyaye ta mika mata cup din ruwa data kawo mata tana cewa”wanan murya kamar ta sadam ?”da sauri budurwar tace “no! d’an dai kina cikin alhinin rashinsa ne kikaji kamar irin nashi ne amman sam sam bashi bane wannna ,tayi maganar a rud’e zufa na karyo mata .”


“kad’an tasha ruwan ta mika mata cup din tana cewa “na gode sosai da kulawarki sai dai ina ganin zan wuce yanzu dan duk na duba banga document din da nake bukata ba “.ta qarasa maganr cike da damuwa akan fuskarta kamar da gaske “shikenan mun rasa komai na project dinmu amman allah yasa ya zame mana alkairi “Ameen! maryama ta amsa mata da haka .”tana jin wani iri a gabad’aya ilahirin jikinta yayinda kallo d’aya zakawa budurwar nan kasan bata cikin natsuwarta ba kamar sanda ta shigo ba, a yanzu a kallon da maryama take mata tamkar mai laifi ce tsaye a gabanta ji tayi kamar kar ta bari ta wuce har sai umma ta dawo sun hadu da juna ,gyaran murya budurwar nan tayi kana tace “maryama ni zan wuce duk da naso na tsaya mu had’u da umma amman wannan kiran da kika ga na amsa na gaugauwa ne ana bukatar gani na yanzu wani aiki ne ya taso amman in sha allahu zan dawo cikin satin nan muga juna da umma .”



Naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tace “Kamar kin shiga zuciyata tunanin da nake kenan ku had’u da umma amman shikenan sai kin dawo muna zuba ido murmushi ya bayyana akan fuskar budurwa sannan ta soma qoqarin fitowa daga d’aki a tare suka fito .”har bakin part din umma ta rakata inda ta hango baba gali tsaye tare da aunty salma cike da tsinkewar zuciya maryama tai sallama da budurwar ta juyo ta koma bangaren umma kai tsaye dakin ta koma ta maida komai inda yake sannna ta dawo parlour’ madadin ta cigaba da karatunta sai kawai ta kira layin yusura taji yadda ko ta samu damar mikawa madam some zanenta kira d’aya ta d’auka.”


Bangaren baba gali kuwa hankalinsa kacokan ya maida kan aunty salma dake tsaye gefensa yana dubanta”maryama kamar yau bataje aiki ba “uhm ta furta tana dariyar mugunta “ai muddin ina raye kuma malamaina na aiki an dakatar daita kenan dan yadda nida ya’yana bamuji dadin rayuwa ba to wallahi itama bazataji ba muddin ina raye .” baba gali ya gyad’a kai kawai yana gyara tsayuwarsa inda aunty salma ta cigaba da magana “ka duba kaga alamarin yaron nan yusuf gabad’aya ya daina neman inda muke dan ma aikin malam yana tasiri har yanzu ajikinsa ai da dawo zai wajen wannan Shegiyar yarinyar“ai kuwa da ya cucemu kina kallo fa kullum sai na kiran layin mahaifinsa amman magana d’aya ce muyi hakuri .” wannan alamari ya fara damuna matuka dan dai burina auren ya tabbata “kar wannan ya dameka kai dai kayi shiru kawai abunka ka zuba masu ido har zuwa sanda zata fashe “.


“Allah ta wajena akwai shirin da kikeyi kenan akasa ?sosai kuwa shirin kuma babban shiri ne ai na rantse da Allah muddin ya’yana basu fara barin gidan nan zuwa gidan miji ba babu inda maryama zata sai dai bayan raina .”murmushi jin dadi ta subewa baba gali itama aunty salma murmushi take tana kallon fuskar mijinta dake kwance da annuri sosa keya ya hau yi yace “an gaishe da salama uwar gidan gali amman mai zai hana kisa ayi aikin da wannan matar zata damka mana takardun gidan biredin da ma duk wani abu daya zamo mallakin sadam ne .itama murmushi tayi tace “sha kuruminka mijina me kake ci nã baka na zuba ai duk sai sun dawo tafin hannunmu sai yadda mukayi dasu kai dai ka zuba ido kawai zaka sha kallo “an gama ranki shi dade ahaka ya juya ya nufi hanyar fita waje ita kuma ta shige ciki tana zagin maryama da umma .”



Da misalin karfe goma na daren ranar Mr ata yana zaune a tsakiyar gadonsa system ne agabansa yana duba sakonin mutane sai dai duk wani motsi da bugun da zuciyarsa takeyi makale take da tunanin maryama kusan ma yace tunaninta ya hanashi sukuni baya jin zai iya jurar rashinta yau kawai da bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba yana jinsa cikin matsi da takura shiru yayi yana cigaba da aikinsa yayinda ahankali maganganunta suke zuwa masa daki daki babu abinda brain dinsa bai kawo masa ba ,wani yayi tsaki wani yayi murmushi yayinda itama .”bangaren maryama itama ta kasa runtsawa tunani muryar da taji d’azu take .”
muryar sai kuwa take mata acikin kunnuwanta dan koda tasanarwa umma zuwan budurwar itama cikin yanayi na tashin hankali ta hauta da fad’a tace ita sam sam bata san wata mai sunan anifa ba mai yasa zata amince daita dan haka karta sake irin wannan ganganci “.


maryama ta qara da sheida mata muryar data ji nan kuma jikin umma yayi sanyi tace “ haba maryama wai mai yasa bazaki manta komai ba dan dai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login