Showing 156001 words to 159000 words out of 182919 words

Chapter 53 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

382

,abinda ya faru kuma tsaitsayi ne kuma zai iya faruwa da kowa bisa qaddara sam sam kada ki d’auka tana zubar da mutuncinta ne.”
“ ba wai ina tunanin haka bane umma amman ni uwa ce fa abun da ciwo ace maryamata ce na gani kwnace ajikin wani “ta fad’a tana goge hawayen numfashi umma ta sauke yayinda nan take kwalkwal warta ta shiga tariyo mata abinda ya faru a shekarun baya “nasan kema uwa ce a yanzu amman kiyi hakuri ki bar kukan hk sai dai a yau nake son kisan wani abu bilkisu ba wai zan dawo miki da abinda ya wuce bane a’a kawai dai ina son ki gane irin so da qaunar dake tsakanin uwa da d’a ne”Kinsan mai yasa zanyi mgnr tun kafin tayi mgnr kukan aunty ya qaru “bilkisu kina fushi da iyayenki especially mahaifiyarki akan rayuwarki ta baya to kisani taji zafi da radadi fiyye da wanda kike ji a yanzu .kisani ba kiyayya bace tasa mahaifiyarki ta dinga miki abinda ta miki abaya illa so ne da kuma gata da take son tayiwa rayuwarki amman soyayya da qaddara ya rufe miki ido ya hanaki fahimtarta abinda take gudar miki shi kika tsinta kanki ciki ,duk uwa ta gari baza só diyarta tayi rayuwa irin wanda kikayi da hussein ba wahala take gudamarki kuma kin shata har yau kina kan shanta , bazan tillastaki dole ki koma garesu ba amman kisani lokaci yayi da zaki je ga iyayenki ki nemi yafiyarsu da wannna kawai zan kawo qarshen maganata .”nasani umma nasan ban kyauta masu ba, ban kuma san cewar illa nayiwa raywuta ba sai a yanzu” umma ta numfasa sanna ta mikawa maryama dake rakube hannunta alamun tazo gareta “durkusa ki bawa mahaifiyarki hakuri “cike da sanyi jiki ta durkusa tana sheshekar kuka tare da riko hannun aunty cikin nata bilkisu ki yafewa diyarki ki kuma cigaba da yi mata addaua Allah ya shirya mana gabad’aya kasa cewa komai aunty tayi illa ta rike hannun maryama da cike nata sun dade suna kuka umma na rarrashinsu kafin daga bisani umma ta fito ta basu waje”


Kwanciya lamo maryama tayi a saman gwiwowin aunty yayinda ahankali aunty take jin zubar hawayenta ,ta yadda har ta fara jika zanenita duk da har lokacin aunty najin haushi da bakincikin abinda ya faru amman data tuna abinda tayiwa iyayenta sai taga kamar maryama rama masu tayi wani dogon numfashi tare da zubawa bayan maryama ido .”
”aunty kiyi hakuri bazan sake ba, ahankali aunty ta kai hannunta saman kanta tana sheshekan kuka wanda yasa maryama ta d’ago kanta “I’m very sorry aunty !tayi maganar adaidai lokacin da aunty ta mike tsaye cike da sanyin jiki ta juya tana tafiya tamkar wacce bata da laka ajikinta da sauri maryama ta biyo bayanta tana ta faman bata hakuri atare suka shiga dakin aunty inda aunty ta samu waje ta zauna tana sauke numfashi maryama ta qaraso ta zube gabanta cikin tsananin damuwa ki hukuntani aunty ko zuciyarki zatai sanyi domin kuwa na cancanci haka “ta fad’a tana riko hannunsa ta zuba mata ido kawai babu abinda take gani illa maryamar ta kwance ajikin wani kato hannuwansa zagaye da kugunta “dan Allah aunty kiyi hakuri ki daina kukan nan muddin ba so kike rayuwata tafi haka muzanta ba ,dan allah kice kin yafe min ko zuciyata zata samu sausauci “ta fad’a tana hade hannuwnta waje wani numfashi ta sauke sannan ta goge hawayenta “na yafe miki amman abinda nake so dake ki fidda miji aure maryama bazan iya zuyar ganin rayuwarki haka ba, ina miki addua Allah ya baki mijin na kwarai wanda zai duba lamarinki .”bakinta na rawa tace am ..”ameen “amman aunty bani da wanda yake sona da au..” ki nemoshi.” ta fad’a mata haka ta hanyar katseta yayinda fuskarta ke a hade tmkr wacce bata ta’ba dariya ba .”


tun tasowar maryama wannan shine karo na uku data ga damuwa mai tsanani atattare da mahaifiyarta “wata biyu kawai na baki maryama ki fidda mijin aure dan bazan juri ganin a ta’ba min ke ba …”ji maryama tayi gabanta yayi mummunar faduwa sakamakon jin abinda mahaifiyarta ta fad’a “dan Allah aunty ki taimakeni I promise you I will be..”banason jin komai daga bakinki mryama ni dai kinji abinda nake da bukata dake ,ki tabbatar kin fito da miji a wata biyu kuma bance kije ki fad’awa umma ba dan na canza maganata ba idan kikayi haka zanyi fushi mai tsanani dake ,ki tashi kije”. inna ilaihi !”ana wata ga wata dame zataji ina zata samo wanda zasuyi aure dashi nan da wata biyu tana kallon aunty ta mike tsaye ta canza waje ,tabita da wani kallo hawaye na kwarara akan kuncinta da kyar maryama ta yunkura ta mike tsaye haka ta fito daga bangaren aunty zuciyarta cike da mummunar tashin hankali daf da maryama zata fita sukai karo da habib wanda shigowarsa kenan ta tsura masa ido tana kallonsa hawaye nabin kuncinta wani irin tausayi da qaunar yaruwarsa ya mamayesa dan yaji duk matakin da aunty ta dauka akanta riko hannunta yayi cikin zafin nama suka dawo wajen aunty .”



“aunty …..”karka ce min komai habib domin maryama bata canci ta cigaba da zama damu haka ba data dinga janyo min magana gara tayi aure kowa ya huta daman yarda da kalar tarbiyar dana mata ne yasa taga na barta tana yin yadda taso bansan shashancin banza da wofi zata dinga yi a wajen aiki ba “nasani aunty hakika heartbeat bata kyauta miki ba ni kaina naji ciwo abun har cikin raina amman ya zamuyi dole hakuri zakiyi ?wani dogon numfashi aunty ta sauke kana ta cigaba da magana “maryama ta manta tsatsonta, ta manta halin da muke ciki acikin gidan nan ,ta manta irin rayuwar da muke ciki acikin gidan da abu kad’an ake jira akanmu ya zama abun mgn ta manta bata da galihu sai nã allah duk ilar da mutumin nan yyi miki yaci bulus tunda shi yana takama da kudi mufa ?bamu da kowa bamu da gata sai Allah shine gatanmu shi yasa wata biyu kawai na bata ta fito da miji tayi aure “.
“Naji tace babu komai tsakanin su amman sau tari idan ta dawo daga aiki ta shigo wajena Ina Jin qamshin turare ajikinta wanda ba nata ba kuma turare ne mai qarfi sai dai yarda da nayi mata yasa naji kunyar tmbyrta sai da wannan abu ya faru na fahimci daga wannan mutumin ne idan ma bai ta’ba yin komai daita ba zata iya rantsewa kafin wannan abun ya faru bai ta’ba sanyata ajikinsa da sunan runguma ba .”



Maryama ta sake rudewa ta gigice tana zazzare ido jikinta na wani irin rawa umma da habib suka zuba mata ido alamun tunhuma ita kuma Maryama alamun rashin gaskiya ya bayyana atare daita “kagani habib duk ta rude alamun rashin gaskiya nan take maryama tayi kasa da kanta tana zubar da kwalla numfashi habib ya saki yana cewa “duk abinda kika fad’a aunty da alamun gsky ne amman dai kiyi hakuri ki yafe mata ki barta har zuwa sanda allah zai kawo mata miji idan kika matsa mata taje ta shiga wata rayuwa fa sam sam zuciyata bazata lamunci haka ba dan haka ki janye maganarki akanta .


ido aunty ta zuba masu ganin yadda yanayin habib ya canza one time ahankali maryama ta d’ago kanta idanunta cike da ruwan hawaye “aunty kiyi hakuri bazan sake ba,kuma babu abinda ya shiga tsakanina da mr ata kawai dai nasan tsautsayi ne yasa na sakar masa jikina amman shima mutumin Kirk ne “aunty ba tace masu uhm bare uhm uhm ta fice daga dakin ta barsu.”
tana fita maryama ta zube jikin habib tana wani irin kuka tana cewa “habib karka qara saka bakinka cikin maganar nan kar laifina ya shafeka ka dai ka tayani da addua Allah ya kawo min mafuta na rabu da mahaifiyarmu lafiya.” sun dade a dakin suna tautaunawa inda maryama ta zayyane masa komai daya faru a wancan ranar wanda ya zamo silar ganin da suka mata da mr ata sai bayan ishai maryama ta dawo bangaren umma tana shiga d’akinta wayarta na soma alamun kira ta qarasa ta d’auka idanunta ya sauka akan screen din wayar sunan mr ata tagani yana yawo akan screen din wayar numfashi ta sauke tare da d’auke idanunta ta samu waje ta zauna bakin gado tai shiru tana tunanin halin da take ciki aure kuma nan da wata biyu “wa take dashi da zata kawo a matsayin miji ?”ta sauke naunayen ajiyar zuciya tana bleming din kanta akan duk abinda ya faru daita itace sila da bata nace akan sai tasan wani abu akan nadia ba da tabbas da yanzu bata tsinci kanta cikin halin da take ciki ba .”



Bangaren mr ata kuwa tsaye yake acikin d’akinsa sanye cikin farar riga mai gajeren hannu da gajeren wondo blue black iya gwiwarsa kanshi sanye da facing cap golden colour ya hard’e hannuwansa waje akan qirjinsa yana kallon hotunan da mami ta zube masa agabnasa “me zakace akan wannan ?akan me zakayi min haka adamcy? a she daman irin sha shancin da kake yi kenan a wajen aiki yasa ka kasa zama da matarka sannan ka kasa yin wani auren ?”wallahi adamcy kayi matukar bani mamaki sam banyi tunanin wannan shashan cin banza daga gareka ba wallahi ka bani mamaki.”


shiru yayi kawai yana jin mami shi sam ba hotunansu rungume da juna da mami ta gani ne damuwarsa ba kmr yadda yaga hankalinta ya tashi matuka da kuma son sanin halin da maryama take ciki ,yana son yasan a wani hali maryama take ciki adaidai wannnan lokacin domin kuwa bai san dalilinta na rashin zuwa aiki ba gashi ya kikkirata wayar bata shiga ba sai yau kuma shina taki d’auka.”


sosai yaga mami ta firgice masa tanata zuba ruwan fad’a “wallahi adamcy ka cuceni .”kuka mami take sosai numfashi ya sauke sannan ya isa wajenta ya zaunar daita akan kujera alokcin kukanta ya ragu” mai yasa sweetheart?” mai yasa zaki min haka kinfi kowa sanin koni waye “mai zan tsinta a isknaci kuma idan ma shashan ci zanyi a irin wannan wajen zanyi ,”ki kalli hotunan nan da kyau zaki fahimci anyisa ne cikin yanayi na damuwa ba wai anyisa dan son rai bane .”akwai guraarr da dama acikin ma’aikatan da zanyi komai da nake so batare da wani yasan halin da nake ciki ba mai yasa sai irin wannan wajen zanyi wani abu .yarinyar nan kamar yadda na fad’a miki tana da matsla a kwakwaluwarta sakamakon abinda ya faru da mijinta ahankali mr ata ya faiyacewa mami komai babu abinda ya rage mata aciki kuma ta fahimcesa” ni bazan cuci rayuwar diyar kowa ba idan kuma har shashncin zanyi wallahilzim bazan yi da maryama ba”. ya fad’a a zuciye yana gama fad’ar haka ya tashi ya shiga d’akinsa cikin tsannain fushi.”


mami tabi bayansa da sauri tana kiran sunansa tsaye ta iskeshi a juyawa kofar baya ta dafashi tana cewa “kayi hakuri adamcy nayi saurin daukar zafi batare da naji ta bakinka ba .” Mami tayi magana sosai amman sam ata bai ce mata Uhm ba bare uhm uhm tasan halinsa tunda yayi shiru irin haka to fa komai zatace bazai yi magana ba dan haka ta juya ta bar masa d’akin daren ranar mr ata bai runtsa ba duk byn awa sai ya kiran layin maryama amman bata d’auka a qarshe dai ya tura mata text amman babu amsa “.


Sosai zuciyarsa tayi nauyi dan ko ya kwanta da zumar bacci baccin bai zuwa bangaren maryama kuwa ko ajiknta tana kallon kiransa amman taki d’agawa dan tasan qarshe dai ruwan bala’i zai mata ya ma barta taji da damuwarta ba sai ya qara mata wani ba qarfe uku daidai tayi wani juyi ta kai hannunta inda wayarta take ajiye shigowar sakonsa ta gani da kamar bazata duba ba sai kuma tayi tunanin ta bude taga wani irin cin mutunci ya turo .”

_Slm zuciyata na min zugi akan rashin d’aga kirana damuwarki tana maseefar d’aga min hankali ,a yanzu haka ina jin kamar ana zarar raina ne idan kinga sakona ki kirani ina son muyi magana dake ina son nasan halin da kike ciki_


shiru tayi kawai tana sake karanta sakon shi”zuciyata na min zugi akan rashin d’aga kirana damuwarki tana maseefar d’aga min hankali ,a yanzu haka ina jin kamar ana zarar raina ne idan kinga sakona ki kirani ina son muyi magana dake ina son nasan halin da kike ciki ta karanta sakon yafi sau biyar duk da ba sako ne na kwantar da hankali ba amman ta rasa dalilin da yasa taji kalmomin sun tsaya mata arai .numfashi ta sauke sannan ta tashi ta shige bayi ta dauro alwala ta fito ta fara gabatar da nafilflii .”


washegari ma kiransa ne ya soma shigowa wayarta amman taki dagawa sai ma kashe wayar tayi gabad’aya ta fita wajen umma ta cigaba da tsabgogin gabanta sai wajen tara na dare ta kunna wayar tana kunna wayar sakonsa ne ya shigo “maryama zan miki rashin mutunci idan baki kirani ba, ko idan na sake kiranki baki daga ba ko kuma naji wayarki a kashe .”shiru tai tana karanta sakonsa tana mamakinsa rashin mutunci kuma idan dai rashin mutuncika ne wanene sabon abu a wajena kayi duk abinda zakayi tunda ba qarqashinka nake ba mai zai dameni ta fad’a a fili tana yatsuna fuska .”
Ko minti biyar batayi da shigowa ba kiransa ya shigo tsaye tayi tana kallon sunansa qirjinta na wani Irin luguden bugu da qarfi kira uku yayi mata ajere bata daga ba haushi yasa yayi wurgi da wayar yana jan tsaki tare da cewa bazai sake kiranta ba sai dai baya jin zuciyarsa zata iya hakura daita jiki a sanyaye kamar wanda Kwai ya fashe aciki ya samu waje ya zauna yana huci shi kadai yasan yadda yake ji a sansar ajikinsa .”


Yau kwana biyu mr ata bai kira maryama ba wanda yayi daidai da kwanaki bakwai kenan bai sakata acikin ko danunshi sai dai yayi balain jin jiki adaddafe mr ata yayi kwanaki nan batare daya sanya maryamarsa a ido ba, jinsa yake kamar wanda yayi shekara ba lafiya har zubewa yayi ya qara zamowa silent kullum tunaninta ne ya zame masa aikinyi ,kullum yaje office idanunshi na kan kofar shigowa ko zai ganta daga sama still shiru dan haka ya tura some gidansu domin ta dubo masa ita babu bata lokaci taje sai dai labarin data zo masa dashi yayi mugun girgiza shi dan haka ya kudurce aransa gobe Jumma’a zai je gidansu maryama ,ya kira m.b yace yazo su had’u gobe yayi masa rakiya zuwa gidansu kasancewar amar baya qasar tun kafin mr ata ya dasa aya yace “kar dai har yanzu baka fad’a ma yarinyar nan kana sonta ba ?
ya gyada masa Kmr yana gabansa “wallahi har yanzu mb yanxu ma wata matsala ce ta tso iyayenta sun hanata zuwa aiki ,to kai mai yasa baka fad’a mata ba ayita ta qare idan aure zai yuwu ayi idan bazai yuwu ba ka saukakawa kanka “bare ma zai yuwu ai maryama bata da wani miji sai ni haka nima bani da wata mata sai ita kasan komai sai lokaci yayi may be akwai abinda Allah ya boye yasa har yanzu ban fad’a ba amman fa ina shan wahala sosai ya fad’a yana dafe goshinsa sun jima suna hira kafin daga bisani sukai sallama.”


******


Wayewar garin ranar jumaa mr ata bai fito daga samansa ba da murna yayi shirinsa kamar wanda akayi masa albishiri da gidan aljanna shigar farin kaya yayi na wani had’ad’den danyen yadi mai azabar kyau wanda tsayawa fad’ar kudinsa ma bata lokaci ne, yasa takalmi da hula baki haka zalika agogon rolex din dake d’aure da hannusa baki ne , kana kallonsa zaka d’auka zashi d’aurin aurensa ne ahankali cike da natsuwa yake qarasa saukowa yana taku kamar baya son taka kasa hannusa d’aya soke acikin aljihunsa sai zuba qamshi yake tunda ya sauko idanun mami yake kanshi babu abinda take sai kallonsa sai kace wanda zashi biki yayi mata kyau sosai cike da farinciki ta soma mgn “kai adamcy nah irin wannan kwaliya ai sai ka firgita yammata “ta fad’a cike da tsigar zolaya d’an murmushi yayi wanda bai wuce iya labbansa ba “ina zuwa ne haka ?kai tsaye yace mata “zanje gidansu maryama ne.”“gidansu maryama !ta furta ahankali ya gyad’a mata kai yana ciro wayarsa ya soma neman layin mb “wai kana ina ne ko d’an na bukaci kamin rakiya shine zaka ‘bata min lokaci daga can bangaren mb cewa yayi “malam karka dameni dan sai na fasa maka rakiya wajen budurwarka ai kafi kowa ‘batawa mutane lokacin ko dan wajen maryama za’aje ka wani shirya da wuri .?”


“minti goma kawai na ba”dan Allah karka dameni idan ma ka dame ni sai naje massalaci na dawo na had’a da ziyara gidan yanuwa da abokan arziki daga nan sai nazo” inji cewar mb “shikenan karka zo ka tafi duk inda zakaje nonsense”mr ata ya fad’a yana cika yana batsewa shi a dole mb ya bata masa rai sosai ransa a ‘baci ya kalli mami wacce Ke zaune tana kallon sarautar allah “sai na dawo sweetheart “yana gamar fadar haka ya juya itama ta juyo tana kallon kyakkywan d’an nata dake faman zuba qamshi kamar shagon turare killama wanka yayi da ruwan turare wayasani


Cigaba da kallonsa tayi yana taku yana gyara zaman hullarsa har sai data daina hangosa sannan ta lumshe idanunta .mr ata yana gama fitowa idanunshi da m.b suka soma cin karo tsaye kamar had’in baki shima farin yadi ne sanye ajikinsa “ya sakar masa murmushin yana cewa “yi hakuri abokina sarkin zuciya ai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login