Showing 105001 words to 108000 words out of 182919 words
“maryama fad'a min me yasa kike son tsohon mijinki sosai haka ?tayi shiru qirjinta na bugawa fiyye da kaida ,tell me me zakiyi da mutumin da baya raye ?
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 30
Shiru ne ya ratsa office din ,domin kuwa maryama ta kasa bashi amsar tambayarsa ,yadda ba tace masa komai ba haka shima bai sake cewa komai ba har tsawon mintuna shabiyar yana zaune yana kallonta shiru ko bata fad'a masa ya karanci tunani kala kala take acikin zuciyarta ,har ga Allah bata son yasan komai akan rayuwarta, ba dan komai ba sai dan tsare mutuncinta amman kuma idan sanin nashi yana cikin taimakon da zai mata ta samu ganin nadiya bata da option zatayi "maryama !ya kira sunanta da kasalalliyar muryarsa mai tsananin kashe sansar jiki da tsuma zuciyar wanda akayi dominsa"bana maimaita magana d'aya domin kuwa baya daga cikin d'abiata ,amaman akanki kullum sai na aikata haka why ?."still shiru tayi tana nazarin abinda zata fad'a masa wanda zai gamsar dashi "ki amsa min tamabayata akwai abinda zuciyata take bukatar sani" tana can tunanin abinda zata fad'a masa kawai sai taji ya matso ya dawo daf daita sosai yasa hannunsa d'aya ya sake riko hannunta mai ciwo yana kallo "karki ga na damu da son sani kiyi tunanin ina yin shishigi ne acikin abinda bai shafeni ba "no sanin dalilin shine kwanciyar hankalina "."
"maryama a karo na qarshe ki fad'a min me yasa kike son tsohon mijinki sosai ?"ya qarasa maganar yana lumshe tsumammun idanunshi "hallaci ne !"ta fad'a hawaye na zubo mata akan kuncinta, ajiyar zuciya mr ata ya sauke sannan ya bud'e idanunshi sosai akanta yana jin wutar soyayyarta na sake ruruwa acikin zuciyarsa yayinda qaunarta mai zafi ke nacin zuciyarsa, baya qaunar ganin damuwarta bare kuma zubar hawayenta. ya kai hannunsa d'aya ya ciro hanky acikin gaban aljihunsa mai azababben qamshi ya soma share mata hawayen dake gangaro wa akan kuncinta, qamshin turarensa mai sanyi ya cika hancinta ta shaqa ahankali tare da lumshe ido nã second biyu sannan ta bud'e tana kallonsa tana jin wani irin yanayi a gabad'aya ilahirin jikinta ."kasa daina kallonsa tayi dan hk gabad'aya tsigar jikinta suka dinga mikewa tsaye ." kallonta ya sake yi a tsanake yana d'an cizan gefen lip's dinsa ahankali ahankali!!""hallaci mahaifiyarsa tayi min tun kafin nazo cikin duniyar nan ,haka shima yaya sadam yayi min hallacin ,kuma hallacin ne yayi sanadiyyar dasa soyayyarsa mai qarfi acikin zuciyata wanda nake ji muddin ba dashi ba bazan iya qara rayuwa da ko wani namiji ba ."saurin runtse idanushi yayi daga tsura ma marayama idanu da yayi zuciyarsa cigaba da bugawa fiyye da kaida ."
Ahankali yayi baya kad'an da kujera da yake zaune akai yana jin wani irin tattukin bakinciki mai had'e da zazzafan kishi ,ji yayi gabad'aya ya muzanta a gabanta "ashe rashin furta mata soyayyarsa taimako kansa yayi, kuma shine abinda yafi zama alkhairi atare dashi ,shiyasa a kullum manazarta suke cewa duk mutun mai yawon surutu tabbas wata rana sai yayi nadama ,shi kuma mutun shiru shiru kullum cikin nasara yake sakamakon hangen nesan shi "na sani dukkanin rayuwar da nayi abaya rubutaccen qaddara ne ban isa na canzawa kaina ba cike da faduwar gaba ta fara bashi labarin abinda ya faru daita daga kan masu zuwa neman aurenta har zuwa sanda umma ta yanke hukuncin had'a aurenta da yaya sadam da abinda ya faru dasu akan hanyar dawowarsu daga ogun state ta qare maganr tana zubar da kwalla mai zafi tana jin zafi a qirjinta"nasan umma tana rayuwa ne kawai amamn har ta koma ga allah zuciyarta na d'auke da rad'ad'in rashin tilon d'anta wanda nice silar faruwar haka ."
mr ata ya kalleta cike da tsarewa da tausayawa "kin tabbatar a gabanki aka binnesa da ranshi ?"wasu hawaye ne suka sake biyo kuncinta sakamakon tuno da tashin hankalin ,nan take jikinta ya kama rawa tamkar alokacin alamarin ya faru domin kuwa tashin hankali ne da bazata ta'ba mantashi arayuwarta ."
"idan zata manta komai daya faru a past dinta ban da wannan al'amari mai firgici "No !ni ba kuka nace ki min ba "ya fad'a yana dafe kanshi sannan ya sake kai hanky ya goge mata hawaye sai daya tsareta da tsumammun idanunshi sannna ta d'aga masa gira tace "yes a gabana suka haqa rami suka binnesa ta bashi amsa ."ya sauke numfashi yana dora qafarsa d'aya akan nata batare daya san yayi haka ba duk da qafarsa sanye take da safa amamn sai data ji yadda ya sauke wata naunayen ajiyar zuciya wanda tasa hawaye ya gangaro daga idanunta sannan a can qasan makoshi yace "amamnan maryama idan aka yiwa mutun haka me kike tunanin halin da mutun zai shiga?" ko a minti goma né bare an d'auki sama da kwanaki sannna kuma ke karon kanki kin kasa gane inda abun ya faru "?naunauyen ajiyar zuciya ta sauke kana ta motsa labbanta tace "babu tantama mutun bazai rayu ba ." yayi saurin matso da kujerar da yake zaune still tafin qafarsa na saman nata yace "okay anyi haka a gabanki but what are you still waiting "tayi shiru ta kasa cewa komai "mutumin nan baya raye maryama me yasa zaki dinga imagenation dinsa over?"
na sani nasan baya raye amman na rasa dalilin da yasa nake jin kamar yana raye "wallahi bana jin daidai arayuwata sakamakon rashinsa atare damu domin kuwa bani kad'ai nayi rashinsa ba hatta yanuwa gabad'aya sunyi kewarsa amamn basu kai ni ba"tsakninki da allah kina jin soyayyarsa ko tausayin mahaifiyrsa ne ke dawainiya da zuciyarki "?kamar yadda na fad'a maka a farko hallacci ne amamn a yanzu ina son shi har ina jin bazan iya rayuwa da wani namiji ba idan bashi ba I really love him son shi da qaunarsa sun mamayeni ."yayi mata wani irin kallo yana mai jin zafin mgnarta aransa amman sai ya dane tare da d'auke qafarsa akan nata ya juya tare da janyo laptop dinsa gabansa ya soma da daddana laptop din da qarfi a yadda yake operating din laptop din kasan acikin zafi zuciya yake ,yana daddanawa yana fitar da zazzafan numfashi yana jin wani azababben kishi from know where na shigarsa ."
"wato duniya juyi juyi ne yau gareka gobe ga d'an uwarka ,abinda ya baka dariya wata rana shi zai sakaka kuka ,dan girgiza kanshi yayi yana zance zuci wato shi kuma haka qarshen soyyarsa ta zama yana son maso wani ,ina ma mafarkinta ya cigaba da yi da wannan lukutar matseefar da ta samesa .wai kamar shi yau soyayya take kutimememiya dashi haka ?""karkaji komai aranka adam, sannan karka manta ita soyayya allah ne yake sakata acikin zukatan wad'an da yaso ,kuma babu wanda ya isa ya rabata ko kuma ya hana faruwar abinda allah ya had'a kai kanka da kasan haka rayuwar soyayyarka zata zo a qarshe da duk yadda zakayi ka goge shi dakayi amman dake had'in Allah ne har ma yake jin babu abinda zai iya sawa ya juya mata baya ko kuma ya daina sonta dan a yadda yake jin soyayya da qaunar da yake mata babu wani abu a duniyar da zai firgitashi har yaji zai iya hakura daita to kuma ai ita zuciyarta ta tsundu ma acikin tafkin son wani ?"zuciyarsa tayi saurin tunatar dashi "uhm ai kuwa akwai bala'i dan kuwa ta qarfi da qarfafa zai shigar daita tsundum cikin kogin sonshi har ta manta ta ta'ba son wani a duniya yayinda ita kuma maryama sai goge hawaye take wasu na sake gangarowa muryarsa a tsarke yace "kiyi hakuri banyi miki wad'an nan tambayoyin dan na 'bata miki rai ba." karka damu sir dan nima banji komai ba"ni dai ina bukatar nadiya ina son nasan wani abu dan gabadaya a tsorace nake tana bani tsoro matuka bansan me yasa take bibiyar rayuwata ba ."
"nima abinda yaketa bani mamaki Kenan ko me yasa zata shigo har office byn ta rufe fuskarta "na samu wayarta ina ganin akwai abinda yake tare da wayar mai mahimanci ,ta kira taji muryata kuma tana ganin idan batayi hanzari ba zan iya sanin wani abu akanta idan na koma gida dan kwata kwata bana jin dan wayar kawai tazo domin zata iya samun wata wayar kuma tasan bazan tsinci komai da wayar ba tunda a kulle take idan ma nace zanyi flash din wayar dan na bude bazan ga komai ba saboda wayr zata dawo empty akwai dai abinda ta biyo "okay zanga abinda zanyi akai dan dole na nemo nadiya."
" kana ganin zaka iya nemo min ita ?tunda nace miki zanyi zanyi ne" taya kenan ?tana matukar bukatar aiki damu a yanzu zan tura mata sako mun d'auketa aiki ,zanyi qoqari na had'uku sannna akwai binciken da zan yi still akanta in sha allahu .matsa war haduwarki daita zai sa kisamu kwnaciyar hankali I wil try my best ya fad'a yana cigaba da aikinsa maryama ta mike tsaye da kyar tace "na gode sir ni zan wuce gida "."koma ki zauna na gama mu kaiki gida ."haka ta koma ta zauna jiki a sanyaye dan gara ta jirasa din su kai gida ta sake cewa "na gode sosai."bai kulata ba illa ya cigaba da abinda yake ."
Bayan kamar minti shabiyar ya mike ya tattara wayoyinsa ya nufi hanyar fita yana cewa "muje ko".mikewa tayi tabi bayansa yana gaba tana biye dashi har suka sauka qasa yaja ya tsaya tare da zura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa inda masu tsaronsa suka taso da sauri duk suka zagayesa cike da girmamawa ,a natse ya ciro hannunsa daya daga aljihunsa ya soma keyarsa sannan ya soma magana cike da kamewa "a ruwa zai kai ni agege so ku zaku iya wucewa ."iyakar abinda ya fad'a kenan dan bai son ya shiga unguwar da jami'an tsaro."
tana tsaye tana kallonsa ya bud'e gidan baya tayi shiru tana jin mummunar faduwar gaba gabad'aya daga securities din bakin get din har na cikin ma'aikatan da masu tsaronsa babu wanda bai yi mamaki ba dan basu ta'ba ganin haka daga garesa ba har gara ma masu tsaronsa zasu iya cewa suna ganin yana yiwa mahaifiyarsa amman wata mace daban wannan ne farko ."ki bar wannan banzar tunanin naki ki shiga"ya fad'a yana hura hanci jiki a matukar sanyaye ta shiga ta zauna ya maida kofar ya rufe mata sannan ya soma qoqarin zagayawa inda kafin ya qarasa tuni a ruwa ya bud'e masa ya shiga ya zauna yana ware qafafuwansa wanda ya zame masa jiki sannan a ruwa ya shiga mazaunin direba ya tada motar suka nufi get ."
Shiru suna zaune a bayan motan sai driver a ruwa a mazauninshi, haka nan taji hawaye ya ziraro mata a sanda suke hau babban titi , ahankali ta juyar da kanta tana kallon gefen titi tana sheshekan kuka wani dogon tsaki yaja ,tana jinsa kamar zata juya ta kallesa sai kuma ta fasa,ta ci gaba da barin kanta a inda yake ya motsa bakinshi kamar zaice wani abu shima sai kuma ya fasa ya ciro d'aya daga cikin wayoyinsa dake qara mara sauti yanayin yadda taji yayi maganar tasan oga amar ne, bisa dukkan alamu maganar mai mahimanci ne "karka damu dole zan nemeka cikin satin nan "eh duk acikin satin zamuje gurinsa in sha allahu to gsky dai ban gama tantacewa ba, tsarin farko zanbi ko kuwa wani tsarin ne amman dai duk abinda ake ciki zan nemeka sukai sallama kana ya dan tsaya yna kallona"wallahi kukan nan yana maseefar kona min rai ."ya fad'a yana sake jan tsaki mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga” yayi maganar acan qasan makoshinsa ."
shiru tayi tana assessing maganarsa, ta juyo a sukwane taga ita yake kallo fuskashi a hade tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa ."ahankali ta dauke kanta tare da tsaida hawayenta tana lissafi maganarsa "wallahi kukan nan yana maseefa kona min rai ,mutun yayita kuka baya tunanin halin da mutane zasu shiga "bata gama tunanin makomar maganarsa ba taji ya matso kusa daita sosai tare da daura kanshi akan kafad'anta wanda yasa ta sauke naunayen ajiyar zuciya "please maryama ki daina tunanin matacce haka ."numfashi ta sauke kawai .
bata ankara ba taji ya kamo hannunta mara ciwo cikin nashi "ina son ki daina tunaninsa ,ko zaki min wannan alqarin ?"tun kafin tace wani abu ya cigaba "yes I know you can do it for me "kiyi saboda ni bansan dalili ba maryama bana son ganinki cikin damuwar nan zaki daina tunaninsa " anya kuwa zata iya kuwa? Not thinking of yaya sadam dinta bayan a yanzu bata iya kwana ba tare data yi tunaninsa ba ? "Kullum sweetheart dina tana fad'a min yawon tunani yana illata zuciyar dan adam ta kallesa a tsanake tana sauke numfashi ".
"banason ki illata zuciyarki ko babu komai kina da qarancin shekarun ,kinyi kankatar da zaki jefa rayuwarki cikin over thinking haka .ta sake kallonsa taga har lokacin ita yake kallo sai dai fuskar nan tashi a hade take "nasan daga yau zaki daina ko? ya fad'a yana matse yatsun hannunta cikin nashi sai dai ta girgiza masa kanta ,alamun bazata iya ba, sai ya sake langwabe mata ya dawo kamar wani abun tausayi yana murza tafin hannunta cikin nashi .tayi qoqarin zare hannuta ya damke sosai yace "Please maryama wai mai yasa bakya tausayin kanki ne ?"
yayi mata tambayar yana mata tafiyar tsutsa a tsakiyar hannunta tayi saurin zare hannuna daga nasa tana yarfarwa kamar wadda wuta ta kona saboda wani yanayi da taji ya taso daga hannun nashi zuwa cikin nata, cikin kankanin lokaci ya zagaye dukkanin ilahirin jikinta ,cikin sarkewar murya tace "no sir I can't bazan ta'ba dainawa ba yaya sadam fa jinina ne ko babu aure atsananinmu babban yaya ne a wajena .“ina tabbatar maka idan babu baba gali a raye da yaya sadam yana raye shine ma daurin aurena .da mahaifina da mahaifinsa uwa daya uba daya ta yaya kake tunanin zan iya mantawa da wannan dangantar?"
ahankali ya lumshe mata tsumammun idanunsa yace "shikenan ba’a bukatar ki daina tunaninsa ki cigaba da tunaninsa idan kina só ma kema kije ki haqa rami ki shiga ki binne kanki “kai a ruwa miko min kwalin sigari "sigari kuma ?"ta furta a razane baqar maganar daya fad’a bai mata ciwo ba kamar abinda yake qoqarin aikatawa yanxu .a ruwa ya miko masa tare layter ja ya kar’ba ya bude ya ciro Karan sigari daya ya rike batare daya kai bakinsa ba duk tana kallonsa yayinda idanunta suka sake ciccikowa da ruwan hawaye ya janyo hannuta mara ciwo ya saka layter ciki "kunna min !"ya fad'a yana miko mata sigarin , zaro idanu tayi waje tana dubansa cike da matsanancin mamaki .hankalinsa kwnace yayi mata wannna banzar maganar aiko sai ganin hawaye yayi sharr suna gangaro mata ." numfashi ya sauke sannan ya sake kamo hannunta ya cire layter sa ya kunna sigari ya fara zuka ahankali ahankali hannu ta kai ta toshe hancinta tana tunanin abun yi ita kam tayi data sanin shiga motarsa mutun kamar mai ajanu sam shi baya son zaman lafiya yanzu daga magana me ya kawo batun ta kunna masa sigari ko shan sigari saboda Allah?"yayinda shi kuma ya kai hannu yana shafa goshinsa zuwa keyarsa .”
ahankali ta juyo garesa still hannunta na rufe da hancinta "sir !” ya kalle a d’age da gefen idanunshi “warin abar nan yana damuna "gara ki saba."gara ta saba kuma ?"wannan wace irin banzar magana ce " tayi maganar aranta “zuwa yanzu yaci ace kin fara sabawa da warin sigari "inna ilaihi "ta furta a fili"ita kam ta rasa gane inda maganganunsa suka dosa me yake nufi da hakan kuma?” tunda ya soma zugar sigarinsa bai kalleta ba sai yanzu da ya wani tsareta da tsumammun idanunshi da suka fara canza kala tare da dage mata girarsa d'aya yace "tsoro kike ji ne ?" cike da jin haushi ta fixge sigarin a hannunsa ta manna a gefen hannunta mai ciwo "kina hauka ne ?"
yayi mgnr a firgice yana cigaba da kallon hannun "kasan illar abinda kake yi kuwa ?muna cikin mota kana sha mana wannan qazantar "ka kuwa ma san yadda nake ji idan naga kana shan wannan abar ?"ta qarasa maganar tana juya masa baya sakamakon kukan daya kwace mata ."
ahankali ya kwanto jikinta tare da juyo daita garesa ya sake makale mata ya janyo hannunta ya tsura ma hannun ido "kalli illar da kika yiwa kanki "?gara wannan rad'ad'in akan zafin sigarin da kake sha a gabana "bai san sanda murmushi ya bayyana akan fuskarsa ba sai dai ya gintse yace "marayam kina da rigima "ai kai ne rigimam me ."tayi maganr a kasan ranta tana zabga masa harara."ni kikewa wannan kallon ?tayi shiru tana qoqarin janye jikinta daga nashi “kince na kuwa san yadda kike ji idan ina shan sigari ?kawar da kanta tayi gefe dan bata ma son kallon fuskarsa sai dai ji tayi ya fixgota jikinsa gbdy ta kwanto jikinsa wani irin bugawa zuciyarta tayi ta sauke numfashi tare da tsuke qaramin bakinta tana kallonsa muryarsa can qasan makoshi yace “fada min me kike ji ?"zuciyata na zafi "tayi maganar kmr zatai kuka “amm da ni ina son ki saba daita "akan wani dalili kenan zan saba ?” ni wallahi bana son warinta yana mugun d'aga min hankali bama warinta ba ni d'an sigari ma banason shi a kusa dani "to ya zakiyi dani kenan ?"ya fad'a yana hura hucin numfashi da iskar bakinsa ya qarasa maganar adaidai lokacin da a ruwa yayi magana “yalla’bai mun shigo agege “nan yayi directing dinsa inda zasu sannan ya sake janyo hannuta yana kallo inda ta