Showing 90001 words to 93000 words out of 182919 words
baki tashi aure ba a yanzu kar na qara ganin kin kula sultan magana ma ta fatar baki kar ya qara shiga tsakaninku dashi maganarsa kusan ta qarshe kenan to me yake nufi da hakan shi bai ce yana sonta ba sannan kuma zai ce karta kula wanda ya nuna yana sonta ."
Kwakwalwa maryama ta bude sosai duk abinda mr ata ya fada sun samu kyakkwan mazauni acikin
zuciyarta ta rufe shayayyun idanunta ta jingina bayanta da jikin gado ta sake rungume pillown dake makale a qirjinta tana jujjuya maganganunsa tana kuma yin filla filla da su tana so ta fito da komai daga rami daya shige ya fake a ciki, ta sake tariyo hirarsu da sultan a kanta ta kuma hada da maganar sa, ta so ta fahimci abubuwa da dama a kansa amma wani abu guda daya yafi komai girma, he is smart duk abinda yake yana yinsa da gogewa idan ba mugun karantarshi kayi ba bazaka ta'ba gane inda ya dosa ba , maganar sultan kuma wannan ba wani abun damuwa bane a wajenta saboda a yanzu ba soyayya bace a gabanta kamar yadda ta sheidawa mr ata bare tayi tunanin aure a nan kusa , abu daya yake tsaye a cikin zuciyarta wanda yasa kwakwalwata ya kasa samun kwanciya shine yaya sadam dinta da take jin har yau cewar yana raye ."
Washegari maryama bata samu zuwa office da wuri ba sai wajajen karfe goma da wasu mintuna dan tuni duk wani maaikacin dake aiki a qarshin AGC yana cikin kuma yana kan aiki jiki a sanyaye ta shigo office dinsu bakinta d'auke da sallama ta gaishesu ta cire jakarta sannan ta samu waje ta zauna tare da yin shiru tana kallon sauran abokan aikinta da suka dukufa suna kan aiki madam some ta shigo tace "sai yanzu maryama ?me yasa baki d'aukar aikinki da mahimanci ai shikenan daman idan kana jin mugunta bakayi wa kanka ba ai baka cika mugu ba. "maryama ta kalleta a kaikaice sannan tace "madam please me haka yake nufi ?"ina nufin duk ranar da sir ya gaji da halinki ya dakatar dake kinga ai kanki kika cuta ,"maryama ta numfasa sannan tace "duk abinda Allah ya hukunto akaina daidai ne "ai shi kenan kuma daman muslim’s din nan haka kuke da taurin kai ,ga aikinki gobe zaa kar'ba idan kuma kingama shi a yau mrs ata zai ji dadi maryama tasa hannu ta kar'ba tana cewa me zaa zana? ahankali madam some ta soma mata bayani tana gama mata bayani ta fita ."
Maryama ta mike ta dauki jakarta ta fice daga office din ta koma qasa office din da'aka maida ema.
yayi matukar mamakin ganinta amman dake bai san zuciyar mr ata bace kawai ya sakar mata murmushi yana murnar ganinta wunin ranar tana tare da ema inda mr ata bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba amman dai ance masa tazo kuma har an bata aiki sai dai bai nemeta ba duk da kwayar idanunshi ita suke son gani amman ya danne saboda kar ya bada kofar da wasu zasu fahimci halin da yake ciki ."
karfe shida daidai maryama ta hawo sama ta ajiye aikinta a gaban madam some dake zaune tayi mata sallama tace zata wuce gida tana gama fadar hk ta juya bayanta ya hango daga inda take zaune tana rausaya kmr ba daga wacan jagwal gwalaliyar unguwar take fitowa ba komai mata tsab tsab kuma a natse . ya hard'e qafafuwansa waje d'aya yana cigaba da kallon yadda take juya sansar jikinta anya kuwa bazata koma saka asalin kamilalliyar suturarta ba ? dan irin wannan tafiyar ai sai wani yayi masa ganganci ,haka ma the next day a kasa tayi aikinta tare da ema duk yadda mr ata yaso ya ganta taki yarda su had'u aranta tace "aiki take masa ba jikinta ta kawo masa ya dinga ta'bawa ba yana yin yadda yaga dama ita ba ."
Tsawon kwanaki biyu kenan bai sanyata acikin idanunshi ba sai dai ya hangeta daga nesa ta shigo ko ta sauka hankalinta ma gabad'aya baya Kanshi tsabgar gabanta kawai take, yana zaune akan kujera sanye da riga da wondo blue sai yar cikinta light blue yayinda nick tied dinsa ya kasance brown colou hannunsa rike da wani nicktie din brown yana nadewa ahankali har ya gama ya soka cikin aljihun gaban rigarsa yana kallonta ta shigo office din some . gata ga office dinsa amman ko d'aga ido tayi ta kalli office dinsa batayi ba haka yana kallonta ta juya yaga ta nufi qasa wani zazzafan numfashi ya sauke sannan ya yunkura ya mike ya fito ya biyo bayanta tana zaune tare da ema da wasu ma'aikatan takalmansa ya shigo office din ,kamshin sanyayyen turarensa daya ziyarci hancinta da kuma bugun da zuciyata yayi ne ya tabbatar mata da shine ya shigo "good morning sir "!!! duk ma'aikatan dake cikin office din sai daya gaishesa illa ita qoqarin juyowa take ta gaishesa taji sautin muryarsa a zafafe "ke me kike yi anan ? cikin tsananin firgita, da tsinkewar zuciya da tsoro, tare da kyarman jiki, ta qarasa juyowa ta fuskanci inda yake tsaye sanye da suit yayi matukar kyau kamar wani matashi dan shekara talatin” just one second na baki ki tattara ki koma inda aka ajiyeki. tamkar gilmawar walkiya yaga ta zabura ta mike ta rungume jakarta da kayan aikinta gam-gam cikin tsuma da karkarwa ta bace .
wani irin masifeffen dariya ne ya taso masa tun daga kasan zuciyarshi har zuwa kan lips dinshi amman dole ya taune lip din shi na kasa kana ya gimtse ya murtuke fuska cikin tsare gida yace.ema "! yes sir ya fad’a cike da girmamawa “da alamun kagaji da aiki damu ko ?"no sir wallahi babu ruwana sir bance .."
“enough! ya d’aga masa hannu “to be your last warning. iya abinda ya fad’a kenan ya juya ya koma office dinsa sai lokacin hankalinsa ya dawo gangar jikinsa duk lalacewa ko wani abu bazai had'asu ba gara tana sama yana kallon duk abinda take ."ranar kusan tare ma sukai aiki akan presentation dinsu dake motsawa ,yadda bata sakar masa fuska ba haka shima wanda daman shi kusan fuskarsa a daure take .”aiko ta gane bata da wayo dan ya lafta mata aiki kamar me dan haka a matukar gajiya ta qarasa gida tayi wanka tayi magriba da isha’i saboda tsananin gajiya ma bata ci abinci ba ta kwanta.”
******
Yau ne ya kama zaa gabatar da presentation zaune mr ata yake tare da client dinsa mutun uku a gidan mami tun daga sama yasa akayi decoration har zuwa kasa surayya ce ta fara fitowa sanye cikin riga da siket na suit tayi juyi kamar yadda yan fashions desings keyi sannan ta koma gefe ta tsaya sannan yusura ma ta fito tayi Kmr yadda surayya tayi mutun na uku some ce sai wasu maikata guda biyu sai maryama wacce ta sauko cikin doguwar riga ta rike gefen rigar kad'an tana rausaya tamkr wata fure wani murmushin ne mai daukar hankali kwance akan fuskarta wanda ya bayyana wushiriyarta da dimples dinta ,tayi matukar kyau sosai mr ata ya gyara zama yana kallonta tun daga samanta har qaraso saukowa kwayar idanunshi na kanta .”
Mutane da suka zo ganin new design dinsu suaki tafi yayinda mutun daya acikinsu yace "wooo gsky naji dadin ganin representation dinku yayi min kyau sosai thank you so much mr ATA "wannan desings din ya bambamta da sauran desing daka saba kazo da wani salo dabam daman kuma ina da yakinin AGC company ne kawai zatayi min abinda zai kwanta min arai akan kowani kamfani dan haka akan wannan suprisse din zanyi double din order kaya."
" that's great mr ATA ya fada tare da mikewa tsaye yace "just a second !yasa hannuwansa a aljihun wondon suit dinsa ya qarasa inda yammatan suke tsaye "sannuku da kokari aikinku yayi kyau "thank you sir suka hada baki gurin fadar haka" sir ko zamu iya zuwa mu canza ?yes of course" ya fad'a yana kallon cikin kwayar idanun maryama tayi kyau matuka itace ta fara yin hanyar sama yabi bayanta da wani shu'uminn kallo tare da yin taku a hankali yabi bayanta da kallo ,jikinta a sanyaye ta dan juyo dan kallon bayanta ai kuwa ta zame tayi baya luuuu zata fadi kan tayis aiko da wani irin sauri mr ata yasa hannuwansa duka ya tarota bayanta ta fado jikinsa ."
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 26
Cike da sanyin jiki mami tabi bayan mr ata da kallo kafin ahankali ta d'auke idanunta ta maida kan baba qarami dake tsaye zuciyarsa cunkushe da haushi da bakinciki abinda mr ata yayi masa "kinga kalar tarbiyar ki ko ?a gabanki d'anki yayi min zagi bayan ya wulakanta maganata "tukuna ma ina alqawarin da kika min na cewa bazai yi aikin nan ba "?numfashi mami ta sauke kawai wanda hakan yayi sanadiyar qara hassala baba qarami dan haka a tsawace yace" kin tsareni da idanuwa kin kasa cewa komai tunda kinsan da had'in bakinki yayi komai ."shikenan tunda ke da d'anki kunyi son ranku amman fa ki sani bashi kuka ci." mami ta sake kallon baba qarami dake surfa maseefa ta hade hannu wanta waje d'aya kasamcewar ta rasa me zata ce masa ya fahimce ta .kusan mintuna goma ta d'auka tana kallonsa batare da tayi yunkurin dakatar dashi ba ko ce masa wani abu ba har sai daya gama amayar da abinda ke ransa sannan ta gyara tsayuwarta muryarta cike da laushi ta soma magana "dan girman allah baba qarami kayi hakuri kai ma kasan halin adamcy da taurin kai "sai da ya ta'be bakinsa sannan yace "ai dole kince min nayi hakuri tunda ke da d'anki kun gama ci min mutunci mami bata damu da maganarsa ba dan tasan kad’an daga halina idan ranshi ya ‘baci kamar adamcy ne .”
sake kwantar da murya mami tayi "ni dai hakuri nake baka kuma in sha allahu..."saurin d’aga mata hannu yayi dan baya da bukatar alqawari ta "dakata ya isheni haka karki cika min kunne naji amman wallahi wallahi kinji na rantse ki ga yawa wannan d'an iskan d'an naki ya kiyayyeni kar ya sake gigin sake aikata mana haka "shikenan hakan ma bazai sake faruwa ba zai kiyayye yayinda aranta tace “bama zai cigaba da kula da kamfanin ba ,ya bar maku har abada domin dai tasan halin d'anta idan yace yes yes ne haka zalika idan yace no tô no ne tunda yayi mata alqawarin bar masu kamfanin tasan bazai ta'ba dawowa ya canza magana ba."da rarrashi da komai uncle jay da yaya Ibrahim da mami suka samu ya hakura ya fice daga parlour'n tare da sultan ."
yayinda mr ata ke zaune akan kujera a bedroom dinsa yana zukar sigari ahankali yana magana a fili "wannan mutumin so yake sai muyiwa juna rashinmutunci tukun zai fita a tsabgata,ko ina ruwansa da yadda zanyi da rayuwata? zanyi aiki a duk lokacin da nake so kuma dole ku barni koda kuwa ranku bai so “saboda son zuciya irin nashi kawai ya zauna yana biyewa ya'yansa inda ni d'ansa ne zai min haka ?"ya tambayi kanshi yana jan dogon tsaki tare da shafa sumar kanshi da hannu d’aya sannan ya mike ya fad’a kan bed dinsa yana cigaba da zugar sigari ."
Direban daya d'aukosu maryama, yusura ya fara saukewa sannan maryama, karfe goma daidai na dare maryama ta shiga gidansu part din umma ta shiga inda ta iske Aunty hassna zaune a parlour'n tana kallon tv "sannu da gida aunty ."ta fad'a muryarta a sanyaye sannan ta ra'ba zata wuce ta gefenta" ina kika tsaya har goma na dare"? maryama tayi matukar mamakin jin tambayarta ita da babu ruwanta da rayuwarta yau kuma me janyo wannan tambayar “ta tambayi zuciyarta tana duba agaogon hannunta goma ma har ta fara wucewa" .
“ki duba tun lokaci da kika bar gidan nan sannan ki kalli lokacin da kika shigo maryama kina yin abinda kike so acikin gidan nan kawai dan an baki dama ko ba haka ba ?"ta fad'a tana dubanta a kaskance bama zaki kira kowa ki fad'a dalilin da ya tsaida Ke ba karki manta wannna gidan namu gidan mutunci ne karkiyi abinda zaki 'bata mana sunan gida kamar yadda uwarki ta 'bata sunan gidansu dan nasan har abada irin guje gujen datai bazai ta'ba gogewa a zukatansu ba .”
Wani abu maryama taji ya caki kahon zuciyarta ranta yayi matukar 'baci zuciyarta ta dinga tuttukin bakinciki ,idan tace bata ji ciwon maganar aunty hasana ba wallahi tayiwa kanta karya ,amman data tuna bazasu wani sake d'aukar lokaci mai tsawo a gidan ba zasu tattara su barsu gidan su canza rayuwa sai kawai ta rarrashi kanta ta danne abinda take ji a yanzu muryarta a sanyaye tace "aunty hasana daman akwai wani aikai dazaa gabatar a office dinmu ne yau tun kwana uku daya gabata ake shirnsa umma ma tasan da zamansa to sai yau aka gabatar dashi shine dalilin da yasa nayi dare a waje amman in sha allahu bazanyi abinda zai ‘bata sunan family dinmu ba ,da safe ma naso na tsaya na fad'a miki koda na shigo d'akinki kina bacci amman Kiyi hakuri dan allah "ta fad'a tana ra'bawa ta bayanta zata shige daki "tsaya ! ta jiyo sautin muryarta."maryama taja ta tsaya tana lumshe idanunta "me kake ce a office ko me ?"
"uhm gskiya yanzu kin kware a iya tsara karya amman kisani na samu number wayar office dinku a hannun kanwar yusura kuma na kira an fad'a min lokacin da kika bar office a ina kike adaidai lokacin?eh amm gabad'ayanmu muna gidan mr ATA ne " me kika ce ?ta fada tana dubanta da mugun kallo "me naji kin fad'a yanzu "?sake maimaita min naji kawai dan iskanci sai ki kama hanya kije har gidansa anya ma kuwa ba iskanci kike yi awaje ba yasa maza ke gudu su barki ba ?"shi kuma wannan da yayi shahada ya aureki kin kashesa "muryar maryama ta na rawa tace "haba aunty hassana me kike kokarin cewa ? Karyar me zanyi idan nayi karya meye ribata ?" me zata bani” yanzu ke aunty hassana har kina tunanin ina yin iskanci a waje ."?dan allah ki cire wannan zargin aranki kawai dai akwai wani aikin sirri da zamuyi shine yace muje gidansa kuma bani kadai bace ki bincika zaki .."
“Kiyi min shiru banason jin wannna karyar naki yanzu dai rashi aure yasa zaki fara d’auko mana magana Allah yasa ba abinda yasa aunty tace nazo na zauna ba kenan idan ba haka me zai same ki dan kin zauna ke kad’ai “.?"akan me zanyi karya to ?" maryama ta fad'a a zafafe cike da jin haushi ta cigaba da mgn "dan allah ki daina min irin wannan kallon."ni bance ni ta gari bace amman ni ba yar iska bace idan na dawo aiki da wuri fine idan ban dawo ba shima daidai ne dan …”dakata ba dani kike wannan maganar ba da waccan uwar taki kike sannan ki bude kunnenki da kyau bazan mu yarda da wannna iskancin ba sannan shi mr ATA din akan wani dalili zai kaiku gidansa idan ba da wata manufa ba?” ko da yake sai dan iska ya bada dama sannan zaa kawo masa batun iskanci "Aunty hassan kin dade kina kirana da wannna kalmar amman idan allah yaso bazai jarabeni daita da zama yar iska ba dan bana aikata abinda ya danganci hakan , sannn karki danganta mr ata da wannna kalmar domin kuwa ke uwa ce ,kawai dai yau aikinmu ne yazo da wannna tsarin dan haka kisani naje gidansa ne kawai dan aiwatar da aikina ba dan wani abu ba .”
"idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata dan babu mai ciyar dani zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ." tana gm fadar haka ta shige daki ta barta zaune tana Maimaita kalmar karshe data fda” idan ma kuma dan wani abu ne babu ruwan kowa da rayuwata zan iya yin duk yadda naso rayuwata ce ."cab din jan lallai yarinyar nan wuyanki ya isa yanka tunda an fara danna miki jijiya kinsan dadinta ai dole ki fad'a min haka amman kisani ba ni kika fad'awa magana ba wacan ganta lalliyar uwar taki da ta gama zubar da mutuncinta kafin aure kika fad'awa mgn ,ta fad'a tare da yin kwafa tana gyara zamanta tare da cigaba da mita “a lallai maryama anji dadin maza ina fad’a kina fad’a .duk maryama na jiyota amman ta daure ta cije dan kar tayi kuka amman sai da wasu hawaye masu zafi suka zubo mata tana sharewa wasu hawayen na zubowa daga idanunta a lokacin da take tuna asalin mahaifiyarta sannan ta tuna irin rayuwar kuncin da sukayi a baya, ynx ma gashi
irinta sukeyi. .”
“Duk runtsi duk wuya baza tayi irin kalar rayuwar mahaifiyarta ba ,bazata ta’ba zabar namiji ta bar ahlinta ba ,haka zalika bazata ta’ba yarda wani namiji yasanta diya mace ba muddin ba aure sukayi ba ,zata rike mutuncinta da darajarta ta diya mace duk mijin data kawo suka nuna basa so wallahi ta barshi kenan har abada bata da abinda zatai dashi koda kuwa da zinari akayisa ,ba dan komai ba sai dan siyawa