Showing 177001 words to 180000 words out of 182919 words
zabgawa maryama mari kenan ya rike hannunta ya wanke ta da mari gudu biyu masu kyau “in your life don’t ever I said don’t ever see me with a girl and act like a fool banza sha sha this girl you seeing here tafi min dubu akanki kina jina mara kamun kai maryama kam baki bud’e take kallonsa ya dawo ya gaban maryama yace “sorry my princess kiyi hakuri I caused all this let just take a way muje nayi feeding dinki a mota plse I’m sorry.”
Haka sukai take a way yana bata hakuri a zuciyarta kam sam bata ji dadin yadda ya mari mace haka ba, kuma menene tsakaninsu “? ya bud’e mata ta shiga mota ya mika mata farar ledar hannunsa ya zagaya ya shiga mota ya zauna yana cewa “sorry my princess ko zamu shiga quest house din can ne saboda kici abinci muyi hira before I drop you tace “no tana girgiza masa Kai “wai da Ina son ki samu natsuwa ne kafin kije gida “wacece wannan yarinya “.karki wani damun kanki akanta “khairat sunanta tana masifar sona haka zalika duk sanda ta ganni da wata haukacewa take kuma fa wallahi ni bana sonta”.yayi maganar yana Shafa sumar kanshi “da fari dai mata ababen girmamawa ne bare mutumin da yake sonka gsky ni dai banji dadin abinda kayi ba .”
“Kenan kina nufin na bari ta tozarta min ke kamr yadda ta saba no no impossible I can take it hakan da nayi shine daidai kema yanzu kika nunawa wani darajata ni me yasa zan bar wata banza mara kanmu kai ta ta’ba min wannan kyakkwar fuskar taki da nake kallo tmkr lu’u lu’u never ai sai inda qarfina ya qare haba sonka fa take “to ni wallahi bana sonta ke kad’ai nake so kece madubina kuma zabina nifa da ke na fara haduwa bazan auri matana ba domin kece irin type dina “ni dai gsky banji dadi ba kuma hakan bai burgeni ba marin mace yaruwata akaina wallahi naji zafin marin ina jin kamar ni akawa “okay am sorry my princess da wannan hirar suka qaraso unguwarsu alokacin da qarfe shida saura ta buga ya sauketa ya kama gabansa .”
Jiki a sanyaye maryama ta d’auki hanyar gidansu inda zuciyarta ke wani irin bugawa kai tsaye bangaren umma ta nufa sai dai taga kofar a rufe ta duba inda take ajiye key ta d’auka ta bud’e ta shiga ta ajiye ledar hannunta a fridge ta fito tare da maida kofar ta rufe ta ajiye key a inda ta d’auka ,kanta na mata wani irin mugun sarà ta shiga bangaren aunty bata ganta a parlour’n ba akan kujera ta zauna jagwba tana rufe shayayyun idanunta tana tunani abinda alhj mansoor ya aikata mutumin da takewa kyakkwan zato da kuma halin data baro mr ata zame wa tayi kwanciyarta akan doguwar kujera tana sake zurfafa tunani yadda zatayi da mr ata gobe dan tasan dole yayi fushi sosai daita wasu hawaye ne masu azabar zafi suka taru a kwarnin idanunta alokcin tai nasarar fashe wa da kuka sai datai mai isarta sannan ta tashi ta shige d’akin aunty bayan wasu mintuna ta fito ta nufi bangaren umma har lokacin bata dawo ba tai shiru tana tunanin inda taje .”
Ahankali ta shiga d’akinta ta cire kayan jikinta ta d’aura towel ta shiga bayi tayi wanka tare dauro alwala dan alokacin sallah yayi ta fito tana goge jikinta da gefen towel bayan ta gama ta saka wasu Kayan marasa nauyi adaidai lokacin aka Kira sallah ta qarasa inda daddumar sallah take ta Kai hannu ta d’auki hijab dinta dake ajiye a gefe ta zira ta tada sallah .”bayan ta idar bata mike ba ta cigaba da zama tana zikirin la ila a illa anta subuhanaka inni kuntu minal zalim tana zaune haka nan ta dinga Jin fad’uwar gaba jifa jifa km tana jiyo sanayayyin kamashi turaren mr ata ta lumshe idanunta kawai tana tunanin gezo qamshinsa yake mata tmkr yadda kammaninsa yake mata gizo acikin kwayar idanunta tana zaune har aka Kira ishai ta mike ta gabatar bayan ta idar ta cire hijab dinta ta daura hulla akanta ta fito zuwa parlour’n tana gama fitowa idanunta ya sauka akan mr ata zaune akan kujera mai zaman mutun d’aya gabanta ne bada wani irin ras rass !! har bata san lokacin data Kai hannu ta dafe qirjinta ba .kallo d’aya tayi masa ta fahimci ranshi a matukar bace yake sai furzar da iska mai zafi yake daga bakinsa sosai tayi mamaki da ganinsa dan bata ta’ba tunanin zai biyota ba tamkar mai shirin yin kuka ta qarasa bakin kofar umma tare da ta’ba kofar ta zuge labulen kad’an ta hangota zaune akan dadduama hannunta a sama tana addua.”
Ahankali ta saki labulen tare da janyo kofar kamar yadda take ta dawo kusa dashi tace “lafiya sir ?”me kazo yi km ?”yayi mata banza tamkar bada shi take ba ya cigaba da furzar da iska yana girgiza qafarsa d’aya babu alamun zai mata magana qara matsowa tayi tace “I’m talking to you sir “?what the fuck do you want “?ya fad’a a hassale“ganin yanayinsa da kum yadda yyi mgana yasa tayi kasa da muryarta tace “dan Allah sir kayi magana ahankali kar umma ta fito koma nace ka tashi ka wuce karta fito ta iskeka anan tayi shiru tana dubansa kamar yadda yake dubanta “ban san me zance mata ba idan ta fito and bansan me yasa kake damun kanka akaina ba alhalin ba sona kake ba ..”
“Zaki iya kasheni ?”tai shiru kawai tana dubansa gabad’aya yanayinsa ya sake canzawa “kill me maryama I no you have already hate me so it’s normal if you can kill me. ya qarasa maganar yana sake tsura mata tsumammun idanunshi sauke numfashi tayi tana kallonsa ranta a dan bace tace “be serious sir please ka tashi ka wuce yanzu da da ba d’aya bane a yanzu Ina daf da zama mallakin wani” tai maganar tana Jin fad’uwar gaba mai tsanani tsaki yayi sannan yace “ni me na kashe miki da zaki auri wani ki barni ?”ajiyar zuciya maryama ta sauke “wannan shine kuskuren da zanyi arayuwarta na amincewa aurenka batare danasan matsa…”saurin dakatar daita yayi a fusace yace “look maryama if you’re here to joke or talk about some useless issues just stop “ya qarasa maganar yana zaro mata ido kallonsa ta cigaba da yi da mamaki “leave this useless man and marry me” ya fad’a a zafafe .”
Hawaye ne ya gangaro daga idanunta yayinda bakinta ya kasa furta komai sai kallonsa data cigaba da yi “ taya zan fasa aurensa byn mun gama tsara komai “wannan kuma ya rage naki amman lallai komai ya rushe zuwa gobe ki kirani a shirye nake da aurenki yana gama fad’ar haka ya mike ya nufi kofar fita da sauri ta biyo bayansa alokacin har ya fito haraban gidansu ta riko hannunsa “ka tsaya muyi mgn .”a fusace a juyo “me kuma zaki ce min ?”bana bukatar Jin komai baya ga kin fasa aurensa dan ko kin auresa sai dai kiyi aure akan aure .”inna lillahi wa inna ilaihi rajiun “bansan me zan fadawa iyayena ba “dont be stupid maryama yadda kika fad’a masu zaki aurin wancan usuless din haka zaki koma ki fad’a masu kin fasa ni zaki aura “.
“this is complete no mr ata I can’t betray him bai jira me za tace ba ya juya ya cigaba da tafiya sake tare hanyarsa tayi tace “why mr ata why you al ways huts me ?”amman kasani komai zai faru bazan fasa auren alhji mansoor ba “ba shawara nake baki ba umani ne ki gaugauta fasawa batasan sanda hawayenta ya yanke zuwa murmushin takaici ba tace “wallahi bazan fasa aurensa ba in sha allahu sai na zama mallakinsa domin kuwa shine daidai ni kuma Ina tsananin son shi da dukkanin ra…”hannunsa ya shake mata wuya yace “be serious maryama idan har kina son ki cigaba da rayuwar farinciki ya zama dole kibi umarnina ya qarasa maganar yana zare hannunsa a wuyanta sannan ya cigaba da taku a fusace .”
Hannuwanta duka ta Kai wuyanta tana shafawa kafin daga bisani ta zube a qasa ta fashe da kuka tana cewa “why mr ata ?” ahankali kana son dawo min da abinda nayita qoqarin binnewa mai yasa kake son ruguza min lissafi ?yadda teke jin radadi haka mr ata tafiya kawai yake yana Jin wani irin zugi acikin ranshi fiyye da nata i love’s you so much that I can die just to fight for my love “.shine abinda yake fad’a.”ahankali taji an dafa kafadanta wanda yasa da sauri ta d’ago kanta tana goge hawayen dake idonta hakan bai hana habib gane cewar maryama kuka take ba ta yunkura ta mike tsaye da kyar tare da sunkuyar da kanta tsayawa yayi gabanta jikinsa a sanyaye yace “heartbeat .”d’ago kanta tai batare da wani energy ba ta kallesa hannunsa yasa ya goge hawayen dake zuba a idanunta cikin mamaki yace “heartbeat kukan me kike yi ?”shiru tayi batace masa komai ba sai ma sake yin kasa datai da kanta tana cigaba da kukan da take d’ago kanta yayi yace “what’s wrong with you?”.
muryarta na rawa tace “mr ata ?”
“Mr ata ?”ya fad’a ,a zafafe cikin kuka tace he won’t marry me” tsura mata ido yayi cikin tsananin tashin hankali “no no wannan karya ne kawai so yake yasa kiyi two zero me yasa tun farko bai ce yana sonki ba sai da wani yazo ?”muryata a can qasan makoshi tace “ya fad’a min since ?”what ?!”ya furta da qarfi .”Amman me yasa baki amince ba ?”ba sona yake ba he didn’t begging me for marry ,he ordering me for marry after dad abinda bazai yuwu bane “ta fad’a tana kallonsa tana Jin fad’uwar gaba “he ordering as how “?umarni yake bani akan auresa shi kuma aure baayinsa bisa umarni yayinda ni nafi son ya furta cewar yana sona “
Murmushi habib yayi sannan yace I’m sorry to say to ke kina son shi ne da kike son ya furta miki ?”“tai saurin girgiza masa Kai “no no me yasa zanyi haka? kawai dai Ina ganin karfa karfan da yake min ba daidai bane ,”wannan ba karfa karfa bane shima yana sonki shiyasa yace ki auresa “ cikin tsoro ta kallesa “lallai after dad bakasan waye mr ata ba duk da Ina Jin cewar akwai wani abu a zuciyarsa amamn zuciyata tafi yarda da baya sona baya dai son na bar qarqashinsa ne yasa yace na auresa yanzu ma dai lokaci ya kure.”it’s not too late heartbeat idan kin san kina son shi ki fasa auren alhj mansoor ki auresa domin in har mutun kamarsa zai ce yana son ki auresa lallai yana sonki ke yanzu fa kauyanci ne wani furtawa mace so “.yana gama fad’ar haka ya Kama hanyar bangaren aunty ya barta tsaye tana kallonsa a matuqar rud’e kafin ahankali ta soma d’aga qafafuwanta ta shiga parlour’n ummah zaune ta isketa tana cin tuwo semoviter da miyar kuka wacce taji d’anyen kifi “.
Ta qaraso ta zauna a kusa daita tana cewa “wash Allah!?sannu da gajiyar aiki maryama kin dai kusan d’aukar hutu ki hutawa ranki “numfashi kawai ta sauke batare da tace komai ba “shiru sukai har kusan minti biyar sannan umma tace “ki tashi kije ki dafa indome tun dare bai yi ba!”
Ta fad’a haka ne dan tasan bazata ci tuwo ba tace “umma ba sai na dafa akwai abinci danazo dashi yanzi warm dinsa akwai ice cream bari naje na d’auko miki har ta yunkura umma tace “barshi tukun har zuwa anjima idan zaki sha sai mu sha tare ta koma ta zauna tana lumshe idanunta mr ata kawai take gani acikinsu “ko ka furta ma kana sona bazan ta’ba aurenka ba in aureka in yi yaya da wannan baudadden halin naka?”ai gara na auri alhj mansoor mutumin ne mai sanyi hali da saukin kai nasan bazai ta’ba d’aga min hankali ba .”jin sallamar da ake yasa ta bud’e idanunta kad’an wani yaron makwaf cinsu ne ya shigo ya gaishe da ummah yace wai ana kiran maryama a waje “.
Cike da mamaki tace waye “basu fad’a min sunansu ba sun dai ce na kiraki yana gama fad’ar haka ya juya da sauri maryama tai shiru tana tunanin su waye ?”ki tashi kije ki duba kigani ko alhj mansoor ne ?”shi ya kawoni gida kuma bai ce min zai dawo ba “kije ki duba ki gani batai mata mutsu ba ta mike ta fito tun daga nesa ta hangosu tsaye ahankali take tunkarar inda suke har ta karaso kusa dasu tana masu kallon rashin sani “cike da natsuwa tace “sannunku kune kuke neman maryama “? eh mune muke nemanki tayi mamakin yadda suka santa amman ita bata sansu ba “gani da fatan dai lafiya ?ta fad’a tana jin wani iri ajikinta dan gsky haka nan taji mutanen basu kwanta mata ba bugu da qari rashin sanin da batai masu ba mutun d’aya acikinsu yace “naga kin tsorata da ganinu ki kwantar da hankalinki mu din ba mugayen muaten bane bamu zo da niyyar cutar dake ba jikita a sanyaye tace “to amman kuyi sauri ki fad’a abinda ya kawo ku Ina son na koma ciki .”
tayi magnar tana juya bayanta sannan ta juyo domin ta fuskansu ai juyowarta keda wuya taji ta shaki wani abu , nan take taji tunanin kanta ya d’auke ya soma ganin jiri tana qoqarin yin kasa kallon dayan mutumin yayi yace “sa’bata aka fad’a muje nan take ya taro maryama ya sabata a kafa suka nufi bakin titi inda sukai parking din motar su da sauri dayan mutumin ya bud’e masa gidan baya ya kwantar daita tare da maida kofar suka rufe atare suka zagayo cikin sauri suka bud’e gaban mota suka fad’a suka bar unguwar .”
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 65
Numfashi ya sauke ya koma ya samu guri ya zauna a kan kujera yana jujjuya jikinsa gabansa na wani irin bugawa da karfin gaske haka nan yake jin zuciyarsa na matukar jin tsoron abinda zai faru yayinda a hankali maganganunta na jiya da sukai waya da some ya dinga dawo masa daki daki " na tsaya naji nayi miki me ?me ma kuka d'aukeni shasha wacce bata san ciwon kanta ba ?"kunsan zaku bukaceni me yasa kuka wulakan tani?"ya runtse idanunshi gam yana jin matsamanancin tashin hankali "wannan yarinyar fa da gani rigimammeya ce ."ya furta a fili qirjinsa na lugud'en bugu alokacin da maganarta ta sake yi masa kuwa acikin kunnuwansa da zuciyarsa ".sorry for what?, wallahi ko duk duniya za'a bani a wannan kamfanin babu ni babu wannan kamfanin har abada "shi wannan mutumin a wajenki yake da mahimanci amman a wurin maryama zero ne ,dan haka tun wuri ku nemi wata amman ni har abada bazan sake dawowa AGC company ba ".
Wani irin zufa ne ya shiga tsatsafo masa akan hancinsa da ilahirin jikinsa ,ahankali ya kai hannu ya lalubo wayarsa ya soma binciken unguwar da take domin dai yana bukatar yaga yanayin tsarin unguwarsu "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ya furta a fili yana mai sake tsurawa wayarsa do tagumi yayi da hannu d'aya yana tunani irin rayuwar da mutun zai yi a irin wannan bazar unguwar numfashi ya janyo da kyar ya sauke sannan ya soma neman layin mb yana d'agawa yace "kazo yanzu yanzu ina AGC yana gama fad'ar haka yayi discounting din kiran ya kira salim da ammar."yayi baya da kujerar da yake zaune yana ciza lip's dinsa da qarfi babu abinda yake gani acikin kwayar idanunshi sai kyakkyawar fuskarta mai mugun kyaun gaske da yanayin jikinta tana rayuwa acikin unguwarsu imagenation dinta kawai yake tun daga qarancin shekarunta har zuwa sanda ya fara daura kwayar idanunshi akanta ,yanayin tsayinta da dogon hancinta shine yafi komai fito da ainihin sahihin kyawunta da Allah yayi mata ya numfasa yana sake lumshe tsumammun idanunshi "hakika maryama iyayenki sun iya haihuwa tunda suka haifa muradin zuciyar Adam .”yana cikin wannan halin sai gasu ammar sun bayyana a gabansa ."
SALIM ,AMMAR ,M.B duk suka zuba masa idanu suna kallonsa fuskarsa a sukwane kuma d'aure take kamar ko wani lokaci sai dai kallo d'aya sukai masa suka fahimci akwai abinda ke damunsa duk suka samu gurin suka zauna sukai shiru suna jiran suji abinda zai fad'a masu."ahankali ATA ya lumshe tsumammun idanunshi tare da sanya hannunsa d'aya adaidai saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take beating very fast bayan kamar second goma ya ware tsumammun idanunshi sosai akansu yana kokawa da lamarin princess dinsa saka makon matsayinta daya fahimta domin duk a tunaninsa bai d'auka zata fito daga irin area daaka fad'a masa ba ,ya d'auka zai ganta acikin royal family ne ko wani babban attajirin ne mahaifinta sai a yanzu ne ma ya fahimci bayan mugun abinda take rufe fuskarta dashi har da ma unguwar da take rayuwa aciki ya janyo rashin had'uwarsu .wani abu ya had'iye mai d'aci daya tsaya masa a mak'oshinsa kafin ahankali ya mike tsaye ya tsaya ajikin bangon office din tare da tura hannuwansa duka cikin ajihun wondonsa ya tokare qafarsa d'aya da bango yana cigaba da dubansu kamar zai yi kuka cikin kasa da murya ammar yace "Adam ya'akayi ne ?ka taso mu daga kan ayyuka masu mahimanci meke faruwa ?meye dalilin taramu dakayi ?ammar yayi masa tamvayoyin a jere duk da jikinsa ya bashi akan maryama ne dan idan akan kasuwancinsu ne bai zai nemi