Showing 72001 words to 75000 words out of 182919 words
da idanu suka bita da kallo ."
Har qarfe biyu da wasu mintuna maryama bata dawo office ba, yayinda mr ata ya shiga office din yafi sau babu adadi amman bai ganta ba ya yi mamakin inda ta shige har zuwa wannna lokacin dan ya lura tun shabiyu bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba kuma shi bai ga fitarta ba dan hk ya kira layinta bai shiga ba ,hankalinsa ya dan tashi ya kira madam some zuwa office dinsa bayan ta shigo ya kalleta atsanake yace "ko maryama tana ina ne ?na ganta dazu da safe ,”yanzu nake magana "eh gsky bansan inda taje ba amman yau din dai kamar bata da lafiya dan naga yanayinta wani iri kamar ma tayi kuka amman naga su surayya suna ta rarrashinta nafi tunanin ko akwai matsala daga gidansu ne sir "numfashi da ajiyar zuciya ya sauke atare yana cewa "you can go "!ta juya a natse ta fita .”
Ya mike ahankali ya nufi d’akin da camerar cctv suke masu kula da bangaren wajen suna ganinsa suka mike cike da girmamawa domin dai duk lokacin da zasu ganshi da kansa abu ne mai mahimanci ya kawosa ,mr ata ya zauna a mazauninsa na musam man wanda an tanadi wajen ne dan shi kad’ai camera mai kula da bangaren office dinsu maryama zuwa first flow ya bukaci gani tukun, da sauri suka fara tariyo masa wanda zuwa wannnan lokacin ya hade hannunwansa duka waje d’aya ya tokare habarsa yana duban screen din tv ahankali ya fara kallon d’aukar yau inda mutane da suke shiga da fita har yazo kan shi da maryama yayi shiru yana kallon shi daita sosai yaga yanayinta cikin tsananin damuwa d’aukar tayi gaba zuwa inda su surayya da yusura ke tsaye akanta da sanda sultana tayi mgnrta ta juya ta bar office din kuma at the same time alokaci maryama ta mike tana goge hawaye ta fice daga ma’aikatar gabad’aya .
"me yarinyar nan take nufi dashi ?"yasan duk akan abinda ya faru ne da safe ta kama hanya ta wuce gida abunta ahlin lokacin tashi bai yi ba yayi kwafa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ."bayan ya gama ganin komai ya mike ya fito daga office din cike da jin kai ya koma office dinsa ransa a matukar bace dan ganinsa maryama tayi mugun mugun rainashi babu wani maaikaci ko maaikaciyar da zata masa haka ya d’auka itama dan matsayinta ne yake d’aga mata kafa yaja tsaki yana rike kugunsa da hannu d’aya,bangaren maryama kam kai tsaye gidansu ta wuce abunta, ta zarce zuwa bangaren aunty tayi kwanciyarta akan doguwar kujera tare da kashe wayarta nan da nan bacci ya dauketa sakamakon daman daren jiya bata runtsa ba ."
******
Qarfe takwas na dare da mintuna ashirin mr ata ya tako cikin parlour'n Mami wanda babu motsin kowa sai na na'urori da kuma hasken qwayaye, samanshi ya nufa kai tsaye yana furzar da hucin iska daga bakinsa yana tuno gamuwarsa da maryama d'azu da safe sannan zuciyarsa na tafasa akan barin office da tai batare da neman izininsa ba gamuwarsu a gobe kawai yake jira dan lamarinta na matukar 'bata ranshi ya tabbatar da cewa ta tafi ne dan musguna masa ta nuna masa iyakar shi wanda hakan ya sake tabbatar masa da bai isa daita ba kamar yadda ya isa da duk wanda ke qarqashinsa ,shima kuma yana nan akan nashi qudurin da raayi bai ga abinda zai sanya shi daga mata qafa ba koda kuwa suma zai dingayi akanta ko mutuwa zai yi sai ya juyata ya tankwasata ya laddatar daita, qarfin soyayyarta bazai sa ya juri iskanci ba haka zai aureta ya kasa zama tsayayyen nmj acikin gidansa "never maryama dolenki ki bini sannan ki zauna lfiya."
Tsab tsab ya iske dakinsa koina neat sai kamshi turare yake wannan kuma yasan aikin sweetheart dinsa ne ita ke tsayawa akan masu gyara masa daki
A natse ya qarasa bakin gado ya soma fidda kayan jikinsa byn ya gama cirewa bandaki ya shige yana niyyar hada ruwan wanka,yaga an had'a masa tsayawa yayi cike da shakku yana tunani ta ina aka samu haka? , cikin kokwanto ya sanya hannunshi cikin ruwan, anya ba jinnu ke neman yi masa wasa da hankali ba,dan tun da yake sweetheart bata ta'ba sawa an masa haka ba ,share mamakinsa yayi yayi wankan ya fito ya saka kayan shan iska farare sol ya fito yana taka step da kyar turus yayi sakamakon ganin maryam da sweetheart tare da aunty shahida zaune suna magana ganinsa yasa duk sukai shiru ya qaraso ya gaishe da mami da aunty shahida duk suka amsa masa ".maryam tayi karfin halin gaishesa duk da tasan bazai amsa mata ba "ina yini yaya ?"shareta yayi kamar yadda ya saba “ adamcy maryam na gaisheka ".
“lafiya!” ya fad'a atakaice sannan ya zauna mr ya daura kafarsa daya akan daya ya dauki remut ya kunna tv ya Kure volum alokacin da aunty shahida da maryam suka mike "to mami mu mun wuce sai an kwana biyu kuma "Allah ya kaiku lafiya zan lekoku in sha allahu maryam ki kula da kanki ki dinga shan maganinki akan lokaci Allah ya sauke min ke lafiya bai ji abinda suke tautaunawa ba shi dai yaga sun fice ko cikakken minti goma basuyi ba sai ga baba qaramin ya shigo kamar wanda aka jehosa kai tsaye kan mr ata yayi yana nunasa da dan yatsa yana cewa "duk tsarinka ne bana wacce sabuwar maaikaciyar bace maryama akace sunanta ko me ,to kasani na samu labari komai kuma bamu yarda ba bamu amince ba ayi wani aiki a boye sai dai a bari lokacin da kowa ya hada nashi sai ayi atare" .
Baba qarami ya kalli inda mami take zaune yana sauke numfashi “ki gaya ma danki dan nasan yana da matukar taurin ka idan kuma yayi Kuskuren yin yadda nace zai hadu da mummunar bacin raina da bai ta'ba gani ba ."wai meke faruwa ne baba qarami kai da danka kullum sai a jiku "karki qara cewa dana dan ba dana bane nasan ya'yana shima yasan ubansa numfashi mami ta sauke kana tace "shikenan Allah ya kyauta karka damu baba qarami zai ji maganata in sha allahu company AGC din ma zan sa ya bar maku tunda shi allah ya rufa masa asiri yafi qarfinsa " okay haka ma zaki ce ?to me kake son nace wannan yaron danka né halak malak kace a'a ."adamcy danka ne banga amfanin idan zakayi mgn dashi ba ka dinga daukar zafi ,idan kabi shi a hankali zai yi abinda kake só ta juya inda mr ata yake zaune wanda yayi kamar tunda akayi duniya bai san da wani halitta baba qarami ba bare ma yasan me yake cewa .”
"adamcy tashi kaje dakinka zan kawo maka abincinka "zazzafan numfashi ya sauke sannan ya yunkura ya tashi ya wuce cikin zafin zuciya saka makon bai samu damar fadawa baba qarami mgn ba kuma daman mami tayi haka ne saboda gudun abinda zai biyo baya ."da kyar mami ta sauko da baba qarami akan lallai adamcy zai janye akan komai suyi duk yadda suke so jin haka ya hakura sai dai tafiya yayi yana bambame yayinda mr ata ya shiga zariya a parlour'nsa goye da hannuwansa duka abayansa tunanin wanda ya fad'a ma baba qarami shirin maryama yake." tabbas ko waye yasan bai wuce sultana ba saboda da ita aka shirya komai . tafiya ya fara yi acikin parlour'n lallai tayi haka ne dan ta janyowa maryama mummunar tsana daga garesa amman shi hakan ba damuwarsa bace dan zai iya karawa da kowa most especially akace za'a ta'bo masa zuciyarsa , abarshi shi a karon kanshi yayi mata duk abinda yaga dama amman wani yayi mata he can't take it sai inda qarfinsa ya qare,da fari bai yi suppoting din plan din maryama ba amman a yanzu zuciyarsa ta yarda kuma ta amince bazai karyar mata da gwiwa ba zai yi supporting dinta da dukkanin karfinsa da rayuwarsa.”
Mmn Sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 21
Mr ata na zagaya parlour’nsa mami ta turo kofar parlour’n ahankali ta shigo tare da mai aikinta tabawa wacce ke d’auke da madaidaicin tray mai d’auke da kular abinci da flak’s sai qaramin cup da spoon nacin abinci dana shan tea, ahankali ta ajiye tray din akan qaramin stood, cak mr ata ya tsaya daga zagaya parlour’n da yake sakamakon shigo warsu,ya tsura ma mami tsumammun idanunshi yayinda ta’bawa ta juya ta bud’e kofa ahankali ta fita, idanunshi na kan mami har sanda tayi taku uku ta qaraso inda yake tsaye zuciyarsa cunkushe da haushin baba qarami “tsayuwar me kake yi ?tayi maganar cike da tausasawa bai ce mata uhm ba bare uhm “kamata yayi ka zauna.“sweetheart bazan iya zama ba saboda wani irin zafi da suya zuciyata ke yi min “shiyasa nace ka zauna domin ba’a son mutun yana tsaye tattare da fushi dan komai zai iya faruwa dashi “madadin ya zauna kamar yadda mami ta ce masa sai ya cigaba da magana cikin zafin zuciya “sweetheart baba qarami yana son yaga kalar nawa rashin mutunci ,so yake na murje idanuna nayi masa rashin kunya fiyye da nashi “ban yarda ba kuma ban amince maka ba kada naji kuma kada na gani ina mai umartarka daka kiyaye harshenka akanshi .”
“Sai data numfasa kana ta cigaba da magana atsanake “bazan daina fad’a maka ba, baba qarami uba ne agareka, indai zaka iya masa rashin mutunci tabbas zaka iyawa tariq mahaifinka da yana raye “.da sauri ya shiga girgiza mata kai yana mai runtse idanunshi gam dan jin zafi da ciwon abinda ta fad’a ya d’auki mintuna goma idanunshi na runtse sannan ahankali ya bud’e tsumammun idanunshi ya tsurawa mami dake tsaye a gabansa tana faman fad’a masa mahimanci baba qarami agaresa “sweetheart nasan mahaifina “ mahaifina bazai ta’ba aibantani ba .”bazai ta’ba min irin abinda baba qarami yake min ba “ya qarasa maganar kwayar idanunshi na canza kala tamkar wanda aka watsa garwashin wuta acikinsu .”Shiru mami tayi tana dubansa a tsanake domin dai gaskiya ya fad’a amman kuma duk da hakan baba qarami yana da qarfi iko da mahimanci arayuwarsa
Numfasawa tayi irin nasu na manya sannan ta riko tafin hannunsa cikin nata tayi taku biyu tace “zauna ka samu natsuwa “!cike da zafin zuciya ya zauna yana dafe goshinsa da hannunsa d’aya “adamcy !”Mami ta kira sunansa “yana jinta amman bai amsa ba dan ko yace zai yi magana a halin da yake ciki maganar ba fitowa zatayi ba .”
“Adamcy ka qara hakuri da yan’uwan mahaifinka “ka cigaba da ganin girmansu sannan kayi masu biyayya albarkasu albarka mahaifinka ce .”sai lokacin ya samu damar sarrafa harshensa “sweet heart ki daina fad’ar haka ki daina bani umarnin most especially akan baba qarami dan bazan iya ba kuma ko yanzu darajanki yaci .“ya qarasa fad’ar haka yana cire hannunsa daga goshinsa ya cigaba da magana “aiki kuma da yake magana a kanshi wallahi wallahi sweetheart sai anyi aikin nan kuma kafin time din presentatoin day in yaso yayi duk abinda zai yi bazan bi umarninsa ba dan ba ubana bane kamar yadda ya fad’a nasan mahaifina shima yasan ya’yansa.” shiru mami tayi kawai tana kallonsa har sanda ya dasa aya sannan tace “da farko dai na gode daya ci darajata kuma naji dadin yadda kayi masa daman kullum mutun yana girma yana qara hankalina ne a duk sanda zai zo maka da fad’ansa na umarceka da kayi qoqari ka danne zuciyarka wata sai labari Allah kuma yayi maka albarka .”
“Sai magana ta biyu zan so ka hakura da aikin nan kai idan ma da hali ka bar masu kamfanin gbdy.” “a’a sweetheart karkiyi min haka dan girman allah ki cire bakinki acikin lamarin nan ki barni dashi tunda abayan ya’yansa yake mutane sai son zuciya kullum basa duba cigabanmu sai abinda zasu samu “.ya fad’a yana jan tsaki tare da fesar da iska mai zafi .”
“Nasani adamcy nasani baba qarami baya maka adalci akan ra’ayinsa dana ya’yansa amman duk da haka hakurin shi yafi ka bar masu ba dan komai ba sai dan a zauna lafiya ”hankalinsa amatukar tashe ya zamo jikinsa ya durkushe a gaban mami ya risinar da kanshi sosai yana cewa “sweetheart kiyi hakuri kiyi min fatan alkhairi in sha allahu wannan aikin shine aikin da zanyi na qarshe a AGC na tattara na bar masu kamfanin gabad’aya tunda haka kike so kike buqata ,daman wahalar abbana nake duba ba akan kamfanin nan ya sha matuqar wahala akanshi kuma mutanen dake amfana da kamfanin nan suna dayawa idan nã barshi baba qarami da ya’yansa zasuyi hamdame komai tare da yin babakeri amman tunda kince na hakura nayi amman dan allah ki barni nayi wannan aikin kawai nayi miki alqawarin zan bar masu “.
shiru mami tayi tana nazarinsa gabad’aya baya cikin natsuwarsa bare a yanzu da take qoqarin hanashi yin abinda yake so ,zata iya barinsa amman ita bata son abinda zai zama damuwa da tashin hankali a tsakaninsu “sweetheart ki amince nayi aikin nan na miki alqawarin wallahi zan bar masu kamfanin jin haka yasa jikin mami a sanyaye tace“to shikenan na barka Allah yasa albarka allah kuma yayiwa rayuwarka albarka “Ameen sweetheart na gode .”ya fad’a tare da yunkurawa ya mike ya zauna akan kujera yana sauke wani sanyayyen numfashi yasan tunda mami ta amince ta kuma sa masa albarka to fa kamar yayi nasara ne akan wannan aiki sai dai idan mutuwa zasuyi su mutu amamn sai yayi nasara mami ta mike tsaye tana cewa “zan koma qasa kaci abinci idan kuma akwai abinda kake bukata ka kirani “okay !”ya amsa tare da mata sallama .”ya runtse idanunshi “layin maryama ya soma nema domin ya fad’a mata tazo da new designs din da sukai gobe sai dai abu daya computer take fad’a masa “swcthoff “!me kuma ya samu layinta da har yanzu akashe yake .”bai san me yasa take kashe phone dinta ba yaja tsaki .”
Shiru maryama tayi zaune rungume da pillow akan kujera a parlour’n umma tare da zabga tagumi cikin
zullumi da rashin sanin madafa, tunaninta abu 'daya tasani yau ma ta tafka babban laifin wanda babu mai kwatarta a wajen mr ata sai allah daya haliccesa shiyasa ma zuciyarta take mata gargadin barin aiki akarkashinsa amman kuma tana tsananin qaunar aikinta a yadda aiki ke wahalar samu a kasar nan tace zata bar aikin nan ai ta cuci kanta kuma tayiwa rayuwarta mugunta kuma daman malam bahaushe yace “idan har baka yiwa kanka mugunta ba hakika baka cika mugu ba “amman Kinsan da haka kike wasa da aikinki bayan kinsani mai wannna kamafanin yafi mahaukaci iya hauka idan abunsa ya motsa ,gasky maryama bakya kyautawa kanki ba ya dai kamata kisan mahimanci aikinki kiyi abinda yake so ki bar wanda bai so shikenan sai ki zauna lafiya dashi ahankali zuciyarta ta dinga mata fad’a akan abinda tayi “me ma yasa kika baro office batare da wani dalili ba ?” baki bar office da mr ata ba sai dan wata sultana din banza “.
shiru tayi yayyinda ta koma ta kwanata akan doguwar kujerar numfashi take saukewa kamar wacce tayi gudun tsare kanta ya shiga ya mutsawa kafin ahankali ta soma sakin murmushi alokacin da take tunanin mr ata wanda ta rasa dalilin haka dan kusan yanzu yana yawon shigowa cikin tunaninta babu abinda zatayi da bazai shigo ba wani lokacin halinsa dariya yake naunayen ajiyar zuciya ta sauke alokacin da taji sautin muryar umma kusa daita tana kiran sunanta .”
“Maryama bacci kikeyi ne ?”a’a umma idanuna biyu ta fad’a tare da yunkurawa ta zauna tana kallon umma ,umma ta zauna kusa daita tana jin wata irin qaunarta kamar itace ta haifeta musamman a yanxu da take hango tarin soyayyarta mai tsanani a idanuwan maryama dinta”yau kin dawo aiki da wuri fatan dai lafiya “?maryama tayi murmushi har wushiyarta ta bayyana kana tace “babu komai umma “amman kuma sai naga kamar akwai abinda ke damunki dan duk jikinki ya sake maryama tayi shiru “karki boye min kinji yar ummanta “.
“uhm !ta furta akasan makoshinta sannna tace “gsky umma kamar koda yaushe dana saba fuskatar matslaa da mai kamfanin AGC yau ma hakan ce ta kasance “wallahi umma na fara gajiya da takurawar sa ,wani irin bahagon mutun ne da bai da fahimta ga shegen taurin kan tsiya gashi ya tsaneni kamar ni kad’ai ke aiki a qarqashinsa ,duk sanda nayi aiki sai ya kushe min ko yace bai masa ba,ko kiga yana disgani kuma fa umma acikin mutane nan dai ta dinga korowa ummah halin da take da mr ata har da abinda sultana tayi mata a yau din nan sai dai ta kasa fad’awa umma cewar d’an sigari ne haka nan taji maganar tayi mata nauyin da bazata iya fad’a mata ba .”umma tayi murmushi irin nasu na manya sannan tace” anya duk wannan tarin qiyayya da tsana tare da tsamgwamar mai tsanani da yake miki bazata juye qaunar ba kuwa ?.”
Maryama ta zaro idanu waje da sauri tana dafe qirjinta da hannuwanta duka “umma rufa min asiri da yardar Allah ma bazata kasance ba koda zata kasance ma zan rusheta tazama babbar kiyayya dariya umma ta kwashe dashi tana