Showing 147001 words to 150000 words out of 182919 words

Chapter 50 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

653

wanke maka shine zai sa ciwo ya bushe numfashi kawai ya sauke dan sosai yake Jin zafin ruwan da yake sawa yana goge masa ciwon sake kama hannun doctor yayi yadda maryama taga ana wanke masa ciwo ya sake d’aga mata hankali hakan yasa ta fara kuka tana cewa doctor yayi masa ahankali kalmominta ne sukai nasarar d’auke masa ciwo “sorry sir da zafi ko ?kayi hakuri a wanke maka shine zai sa ciwo ya bushe
ya runtse idanunshi sosai ana wanke masa ciwo tana kuka har sanda doctor ya gama wanke ciwon tsab sannan ya nada masa bandage.”
Doctor ya kalli innocent face din maryama had’e da jin mamaki sannan ya saki murmushi “ya shi ake wankewa ciwo amman kece mai kuka?to ki bar kuka haka .amman banda kuka maryama babu abinda take kwayar idanunta sunyi ja sosai fuskarta kuwa duk tayi face face da ruwan hawayen wasu magunguna doctor ya bashi sannan yayi masa sallama shima mr ata ya mike ya shige ya barta tsaye taji kamar ta bishi sai dai tsananin tsoro ya hananta .”



Kamar d’azu haka ta fita da sanyi jiki tana goge hawayenta sai dai duk bayan second sai ta Kai kallonta zuwa office dinsa gbdy ta kasa aiwatar da komai tana zaune a office dinsu ya fito yana zare yar saman suit dinsa ya ajiye had’e da qarasa wa inda fridge yake ya d’auki goran ruwa ya kafa a bakinsa sauke goran qasa yayi had’e da fitar da numfashi itama numfashi ta sauke ta fito daga office dinsa ta wani office din dake kallon nasu domin ta kira masu tsaftace waje suzo su gyara masa office .mr ata ya fito yana magana akan waya har ya kai kofar fita adaidai lokacin da maryama ta kunno kai zuwa office dinsa sukai karo dashi tayi baya zata fad’i yayi saurin kai hannusawa duka ya tallafo bayanta yayinda ita kuma a gigice ta kai hannunta d’aya saman rigarsa daidai saitin zuciyarsa dake luguden bugu ta dafe cikin tsananin tashin hankali da jin tsoron abinda zai mata .”



ido cikin ido suke kallon juna kowannensu fuskrsa d’auke da tarin damuwa saurin zare jikinta tare da gyara tsayuwarta tayi still suna kallon juna batare da sun cewa juna qala ba muryarta cike da rauni tace “kayi hakuri please” ya gyada mata kai kawai batare da yace mata uffan ba “sir ko zamu koma ciki ina son nayi magana da kai .”bai mata mutsu ba ya juya ya koma ciki ta biyosa tana jin wani irin fad’uwar gaba, ta karaso inda yake tsaye ta sunkuyar da kanta kasa “ka zauna !” kiyi maganrki “amm daman hakuri zan baka akan maganaguna sam banji dadin abinda ka fad’a min ba haka zalika nima banji dadin reaction dina ba amamn kayi hakuri da abinda na farfad’a maka”.tai maganar tana fashewa da kuka kayi hakuri bansan dalilina ba ,ban ta’ba tsammanin zan iya fad’a maka haka ba am very sorry sir .”



yay gyran murya yana cewa “is okay “!.yanzu ya kake Jin hannunka ta fad’a hawaye na sake wanke mata fuska tsaki yaja batare daya amsa mata ba “.shi kam wannan zubar hawayen na matukar yi masa ciwo ace mutun baya gajiya da kuka kalli yadda kwayar idanunta suka canza “kuka na menene haka ?”ya jefo mata tambaya d’ago kanta tayi ta zuba masa sosai adaidai lokacin da wani guntun hawayen dake makale acikin idanunta ya samu damar gamgarowa a fakaice ya kalleta “Ina ganin zaki iya wucewa gida dan ni yanzu gida zani ya fad’a cikin halin ko in kula yana mai latsa wayarsa dake rike a hannunsa.”hawaye ne suka shiga gangarowa daga idanunta kamar an bud’e famfo muryarta a raunane tace “ka taimakeni ka fad’a min zaka d’auki mataki akan issues dinmu ?”shiru yayi “dan Allah ka taimakeni kar ‘yan gidanmu suga hotunan mu most especially aunty hasana da aunty salma idan suka ga hotunan nan na shiga uku babu abinda zan fad’a su yarda dani bazan sake d’an d’ano wani abu wai shi farin ciki ba ka taimakeni banason mutuncina ya zube tuni wasu hawaye suka wanke mata fuska ..”



Tunda ta fara magana bai d’ago ya kalleta ba sannan kuma bai daina abinda yake ba sai a yanzu ne da sheshekar kukanta ya cika masa kunne ya d’ago kansa daga latsa wayar da yake “wace irin yarinya ce ke mai son kanki dayawa magana d’aya taki ci taki cinyewa ke mutuncinki kad’ai ne abun dubawa?”ni rayuwata acikin duhu take shi yasa kaga na damu da mutunci…. tun kafin ta Kai ga qarasa maganarta ya juya ya nufi kofar fita biyosa tai da gudu tana kiransa “sir !”bai tsaya ba har ya isa kofar shiga lifter ya shige koda ta qaraso ya kusan kai wa kasa ta danna G wato number da zata kaita qasa ta shiga tana gama qarasowa ta ganshi yana qoqarin shiga bayan mota da sauri ta qarasa bangaren daya shiga ta bud’e murfin kofar ta durkushe qasa gabansa jikinta na wani irin rawa” idan ka tafi ka barni cikin wannan halin akwai matsala dan bansan ya zanyi da rayuwata ba “ta fad’a tana mai share hawayen dake kan fuskarta idanunshi ya zuba mata gabadaya idanunta sunyi jajur dasu kafin ahankali ya motsa lip’s dinsa “wai meye damuwarki ne maryama ?”



“Wad’an nan hotunan sune damuwata kai idan family’s dinka suka ga hotunanmu bazasu damu ba wallahi ni nawa family’s din zasu damu dan Allah ka taimakeni ka taimaki rayuwata kayi wani abu akai “tsaki yaja yana cewa “bansan dalilinki ba dole sai kin raba matsalarki dani ko ni nace a d’aukenu hoton?nace ki kwanta jikina ?iya kuka kawai nace Kiyi nace ki rungumeni bare har na samu damar rungumeki ajikina?” tai saurin girgiza masa kai alamun “a’a !kafin ahankali tace “amman ai daman ka saba rungumeni ba wannan lokacin ne karo na farko ba “naji na saba amman a wancan ranar nayi qoqarin rungumeki ?shiru tai wasu sabbin hawaye nabin kuncinta “ni dai taimakon ka nake nema kayi duk abinda zakayi a goge wad’an nan hotunan dan nasan zaka iya sawa .”



numfashi ya sauke da qarfi sannan yace “tashi ki shigo muje da sauri ta mike ta zagayo ta bud’e d’ayan bangaren ta shiga ta zauna tana qoqarin rufo murfin motar ko me ta tuna ta shiga girgiza kanta da sauri ta fito daga cikin motar tana cewa
” kawai kayi tafiyarka bazan bika ba dan bansan me zai sake faruwa ba idan na binka .”“kallonta yayi a tsanake ya fahimceta sosai ahankali ya motsa lips dinsa “ki shigo muje! “ina bazan sake gangancin shiga motarka ba idan mutane suka ganmu tare hakan zai sake tabbatar masu da abinda suke zargi akanmu tun kafin ta qarasa maganarta kawai taga mutun tsaye a gabanta yana haci tmkr wani zaki da sauri taja baya “.
Yayi taku biyu ya matsota sosai yana cewa “ anya bayan wannan matsalar baki da wata damuwa ?”
”sorry sorry!! sir bani da wata damuwa kai kasan yadda al’adarmu take wad’an nan hotunan zasu iya janyo mana wani sabon zargi ne” “nace muje na saukeki a gidanku had’e hannuwanta waje d’aya tayi tana cewa “ka fahimceni wallahi mutane zasu..”ke gidanku kawai zan kaiki nayi masu bayanin komai kafin hotunan su isa garesu “what ?! ta fad’a tana zaro idanu “dan girman allah ka rufa min asiri da wani ido zan kalli aunty da umma ya Allah ka saka min akan wanda yayi min wannan cin zarafin ,mai yasa na damu sai na had’u da nadiya ? nasan if na damu da bazaka d’aukeni ka kaini wanan wajen ba” myma muje !” nifa babu inda zan..”on expecting taji ya fixgota qirjinsa da hannunsa mara ciwo ya had’eta tsam da jikinsa yana sauke numfashi wanda hakan yayi sanadiyar katseta .



a matukar rud’e ta soma magana cikin rawar murya “meye haka kake qoqarin yi ? ta fad’a tana waige waige “I don’t know and keep quite ya fad’a yana d’aura yatsan hannusa akan lips dinta “dan ..“dan Allah sir ka sakar min jiki jin yaki sakar mata jiki tace “bana ciki da iskanci kada wani yazo ya ganmu haka ka sake janyo min matsala “ni zaki cewa baki ciki da iskanci?”eh mana dan wallahi iskanci ne dan Allah ka sakar min jiki kar azo aganmu haka “karki damu ai nafi son aganmu haka ba taqamarki rashin kunya ba ?” zanyi maganinki dan na fiki iya rashin mutunci “dan Allah ka sakar min jiki “tayi maganr cikin mawuyacin hali tana haki “dan allah kayi hakuri ka sakar min jiki zan shiga da kaina .”jin haka yasa ahankali ya soma zareta jikinsa yana dubanta duk ta fita haiyacinta kwayar idanunta gabad’aya sun sake canza kala daga fari zuwa kore tsabar kuka “shiga muje wannan shine mafutar da zai kawo miki qarshen matsalarki duk wanda kike ganin zai kawo miki matsala ki had’ani dashi .”Juyin duniya yayi daita ta shiga taki “nace ki shiga zanyi wani abu akan matsalar” ta girgiza masa kai alamun a’a suna cikin haka sai ga motar madam some ta shigo haraban kallo d’aya yayi mata ya d’auke kanshi .”



bayan tayi parking ta qaraso garesu ta tsaya da girmamawa tana kallonsu wanda sai lokaci yace “daga ina kike baza ta iya masa karya ba dan muddin gasky ta fito bazai sake yarda daita ba ,dan haka tace “daga gidanku nake mumy ce ta kira tana son ganina” what?!” akan me kena?” inna ilaihi wa inna ilaihi rajiun shikenan abinda nake gudu ne yake shirin faruwa inji cewar maryama wani kallo ya d’auketa dashi mai had’e da gargadi “me tace mki da kikaje ?”ta tambayeni akan meke tsakaninka da maryama kuna soyayya ne ko kuwa ni narasa me ta gani daya sa tai ta nemi na fad’a mata abinda ke tsakaninku sir “shiru yayi kawai kafin daga bisani yace “some ki sauke min ita a gida ki tabbatar kin kaita har unguwarsu ya fad’a tare da zagawaya ya shiga gidan baya ya zauna yayinda direbansa ya shiga mazaunin direba maryama kam cikin tsananin tashin hankali ta saki baki da ido tana kallonsa hannu ya kai fuskarsa yana shafawa motar escout dinsa ne suka fara yin gaba sannan motar da yake ciki har sanda driver yaja motar idanunta na kanshi sai dai jikinta ne yake wani irin kyarma.”



Ranshi a matukar’bace ya shigo gidan da mami ya soma cin karo kallo d’aya tai masa ta fahimci yana cikin damuwa ya zauna a wata kujera” adamcy lafiya ?lfya sweetheart amman mai yasa zaki kira some zuwa gidan nan kina tambayarta akan yarinyar nan ai sai ta rainani .”
”haba adamcy meye aciki dan na tambayeta na tunanina kana son yarinyar ne sai gashi ta fahimtar dani komai”.“ ta fahimtar dake komai kamar ya?”ya tamabyeta yana mai hura hanci “ce min tayi ba soyayya bace tsakninka da maryama amman ita da kai kuna son juna da..”what ?!ya fad’a yana zaro ido waje jikinsa na d’aukar rawa” ai kuwa some tayi min sosai gata da biyayya gata kyakkyawan kawai dai matslar crista ce amamn wannan duk ba wata matsala bace tunda tana sonka kana sonta babu damuwa zata muslimta dan Allah ka aureta kaji adamcy nah duk da nasan ta ta’ba aure kuma tana da yara biyu Amman duk wannan ba damuwa bane idan akwai love ta fad’a tana guntse dariyarta “haba haba sweetheart ni nasan ko giya some ta sha bazata soma fad’a miki haka ba .”



murmushi mami tayi tana riko hannunsa cikin nata ta zaunar dashi duk bata lura da ciwonsa ba “gsky sweetheart ki sani wannan fa kuskure ne kikayi ai yakamata ki kirani kafin kice some tazo wannan ma ai sai ta rainani me zanyi daita saboda Allah wani irin lalacewa nayi haka da zan rasa wacce zan so sai some ?” meye illarta adamcy ?”mami ta fad’a tana sake kunshe dariyar ta “haba sweetheart yanzu ke bakiga illarta ba ? sam sam bangani ba sai dacewarku dana gani “to ni nasan tana da illa kuma babu wani dacewar da mukayi daita “nasan kace rashin sallah yasa kake kame kame” dan girman allah sweetheart ki bar maganar nan sam some ba kalar type dina bace bare kuma babu komai a tsakaninmu zan had’u daita qarshen aikinta ne tare dani yazo “ya fad’a yana qoqarin mikewa tsaye mami ta riko hannusa da sauri tana kallonsa tana murmushi “idan ita baka sonta maryama fa ?”“ko itama ba kalar type dinka bace “?lumshe tsumammun idanunshi yayi alokaci da mami ta kira masa sunanta hakan nan ya tsinci kanshi cikin tsananin shaukinta yana tuno yanayin daya barota.”



💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.



Page 42



Mr ata ya kasa tashi daga zaunen da yake yana cigaba da tunanin maryama kukanta na d’aya daga cikin abinda yake matuqar d’aga masa hankali da tsuma zuciyarsa ,dauriya kawai yake, kasancewar soyayyar da yakewa maryama yafi wanda yakewa kanshi fatan shi Allah yasa ta so shi fiyye da komai.”sosai yayi zurfi cikin tunanin maryama yayinda mami take zaune tana kallon kyakkywan fuskar tilon d’an nata .”ahankali mr ata ya ajiye hannunsa mai ciwo a saman cinyarsa yana jijiga qafarsa d’aya wanda hakan ya bawa mami damar ganin bandage din dake hannunsa .”a matukar tsorace take kallonsa jikinta har rawa yake gurin kiran sunansa ”adamcy!” a natse ya bud’e idanunshi ya zuba mata yana dubanta a tsanake “me nake gani haka a hannunka?ko kuma nace me ya sameka a hannu?”tayi masa tambayar ajere cikin tsananin tashin hankali ahankali ya sake lumshe idanunshi yana tunanin abinda yayi sanadin jin ciwon nashi .”



“Cikin tsananin tashin hankali mami ta mike tsaye ta soma taku tana dubansa da ciwon nashi har ta qaraso inda yake zaune ta zauna kusa dashi tana kallon bandage din dake nad’e ahannunsa kafin ahankali tace “adamcy garin yaya kaji ciwo a hannunka?”shiru yayi mata tare da kamo lip’s dinsa na kasa ya soma cizawa yana tunanin abd zai fad’a mata “kamin magana mana ?”numfashi ya sauke yana bud’e idanunshi sai daya d’an fito da harshensa kad’an ya lashi lip’s dinsa sannan ya fara magana a kasalance “wani abu ne ya faru yau a office kin san halin naki shine fa bansan yadda akayi ba kawai naji na samu wannan ciwon “kai da wa?”yaji tai masa tambayr ta qasan idanunshi ya d’auki kallonta “nace kai dawa kukayi rigima? ta tambayesa tana mai tsaresa da kwayar idanunta hakan nan ya tsinci kansa da cewa “.maryama .”!
“Maryama .” mami ta furta sunan sai da mami ta furta sunan sannan ya fahimci yayi kuskuren ambatar sunanta dan haka ya kai hannunsa ya shafa sumar kanshi yana cewa “wani suna na kira yanzu ?”maryama kace !”numfashi yaja da qarfi ya sauke yana kawar da kanshi gefe “.wni irin yanayi mami ta tsinci kanta ciki na tsananin damuwa “amman me faru tsakaninka daita haka ?”.
ba wani abu bane sweetheart kawai dai ….“sai dai yayi shiru ya kasa qarasa maganarsa “ban gane ba wani abu bane kawai dai ?”yarinya tayi maka illa haka amman kace ba wani abu bane ?”mami tayi maganar cikin tsananin ‘bacin rai “wallahi adamcy kasan abinda kakeyi na fahimci kana boye min abubu wa akan yarinyar nan abinda baka saba min ba aman yanzu duk shi kake min kuma duk akanta ne .yanzu data kasheka fa ?”d’an zaro idanunshi yayi “eh !”mana ai na d’auka tana da hankali she dai bata dashi idan ba haka ba komai zaka mata yanzu ya dace ta ji maka ciwo?”
”yanzu daya zamo silar mutu warka fa “no sweatheart karki yi wannan tunanin kawai dai tsautsayi ne amman kwata kwata bata da laifi idan akwai mai laifi to ni ne domin ni jiwa kaina ciwo .”yana gama fad’ar haka ya mike ya nufi hanyar step mami tabi shi da kallo tana jin zafi aranta dan kwatakwata
Bata qaunar abinda zai ta’ba lafiyar yaranta most especially shi .”




Bangaren maryama tsayuwa ta cigaba yi cikin matsanancin tashin hankali “maryama shiga mota muje ko.”! “madam some tace daita tana qoqarin bud’e mata gidan gaba dan ita kam ta gaji da tsayuwa madadin maryama ta shiga sai ma ta juya ahankali ta soma tafiya tana cewa “bari naje na d’auko jakata.” madam some tabi bayanta da kallo batare da tace mata koma ba sai dai zuciyarta cike take fal da jin tausayinta .
maryama bata wani jima ba ta dawo makale da jakarta ta shiga gaban mota ta zauna tare da takure jikinta waje d’aya tana goge hawaye idanunta inda tuni madam some ta shge mazaunin direba.”hankali suke tafiya hawaye kawai maryama take gogewa yayinda madam some take faman sauke ajiyar zuciya akaro na barkatai had’e da sake rike stearing mota tana kallon agogon dake d’aure da tsintsiyar hannunta.”a fakaice madam some ta kalleta ta gefen ido sannan ta maida hankalinta akan tuki “Ina ganin ya dace ki bar kukan nan haka idan ba haka ba mutanen gidanku zasu fahimci akwai damuwa atattare dake .“kamar kar madam some ta fad’a haka hawaye suka shiga turereniyar zubowa daga cikin idanunta “shine babban tashin hankalina ma.” “bana son yan gidanmu su san halin da nake ciki “ai kuwa babu abinda zai hana basu fahimta ba da wannan kukan da kike “nasan kina wannan kukan ne dan kar su ga hotunanku da mr ata to fa ba lallai su gani ba tunda ni a fahimtata iyamu kawai ake son mu gani “dan Allah ma ki taimakeni kar hotunan nan su fita idan suka fita bansan ya zanyi da rayuwata ba, tun farko na fara rayuwata ne acikin qunci ban san wani abu wai shi farinciki ba sai daga bayan nan ne na d’an samu sausaucin rayuwata ki taimakeni banason na koma baya “is okay maryama ki bar kuka ki bar komai a hannun sir da sannu zai gano komai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login