Showing 144001 words to 147000 words out of 182919 words

Chapter 49 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

384

ma zan zo yanzu daga office din bata koma office din mr ata ba ta fito zuwa haraban ma’aikata kai tsaye inda tai parking din motarta ta nufa ta shiga ta d’auki hanya zuwa gidan mami .”




Sannu ahankali madam some take murza kan stearing tana adduar allah yasa ba hotunansu maryama da mr ata aka tura ma mami ba yasa take son ganinta cikin kankanin lokacin ta isa gidan a natse ta tsaya a bakin kofar shiga bayan an kira an sheidawa mami zuwanta ta bata umarnin shigowa cike dari dari ta shigo makeken had’ad’den parlour’n inda ta iske mami tsaye sanye cikin shiga ta alfarma cike da girmamawa madam some ta gaisheta ,inda mami ta amsa mata cikin sakin fuska tana nuna mata wajen zauna “ki zauna !”ta fad’a tare da shigewa parlour’nta na biyu .”madam some tayi matukar mamaki ganin yanayi mami wanda yake nuna alamun babu wata matsala ,cike da sanyin jiki ta zauna tana zance zuci to ko mai yasa mahaifiyar mr ata ta tace zo ?gabadaya kwakwalu warta ta toshe tare da jin wata irin mummunar fad’uwar gaba mami ta fito kunneta manne da waya “a’a babu wani abu kawai dai ‘yan tambayoyi zan mata kafin mu san irin macen da zata shigo family dinmu .” macen da zata shigo family kuma?madam some ta yiwa kanta tambaya tana cigaba da duban mami daga can bangaren aunty khadija tace “yanzu ke mami qoqrin kike yayi wani auren bayan ga maryam har yanzu bamu san matsayinta a wajen sa ba bare matsayin cikin jikinta?”ai kuma bazai yuwu khadija ace ya zauna haka babu mata ba, addua kawai zamuyi Allah yasa wannan auren ya zama silar samun kwanciyar hankalinsa da namu gabadaya.“Ameen !”amman mami shi yace miki yana sonta ne ?”



“Khadija ko bai ce min yana sonta ba ,nasan abinda adamcy yake so ni naga hakan acikin kwayar idanunshi wanda ke nuna min tabbas yana son yarinyar .”mami karkiyi haka tukun kinfa san halinsa tunda har bai ce miki yana sónta ba ki barshi kawai har sanda zai bud’e baki yayi miki maganarta karki sake yanke masa hukun cin a karo na biyu ki bar magna yarinya nan kawai “naji duk maganarki, yanzu ma gaskiyar da yake boyewa nake son nasani “.mami ta gama wayar tare da zama opposite din madam some alokacin da masu aiki suka cika gabanta da abinci kala kala “kici wani abu tukun kafin muyi maganar da tasa na kiraki .”madam some ta girgiza mata kai tana cewa “momy kiyi maganarki kawai dan right now akoshe nake “okay daman akan yarinyar nan ce maryama “.nan take gaban madam some ya bada ras tayi saurin gyara zamanta “nasan kusan kece mai kula da duk wani bangaren adamcy ,nasan zaki fi kowa sanin meke tfy abangarensa.”



“haka ne mumy “! yauwa some ina son ki fad’a min meke tsakaninsa da wannan yarinyar?“madam some tai shiru tana dubanta cike da matsanancin mamaki kenan abida suke zargi tsakaninsu itama mahaifi yarsa tana tunanin haka atsakaninsu “some karki boye min komai ki fad’a min abinda kika sani nayi miki alqawarin bazan bari ya sani ba ,shiyasa ma kikaji nace karki bari yasan zakizo madam some ta tsura mata ido tana kallonta da nazarinta kafin ahankali ta numfasa kana ta soma magana “a zahirin gaskiya mumy bansan akwai wani abu a tsakaninsu ba yadda kika min tambayar nan haka na tsare maryama nayi mata sai dai maganganun da suka fito daga bakinta ba masu dadi bane ,domin maganganu ne masu zafi sannan da nuna alamun babu wani abu a tsakaninsu wanda ya wuce aiki sai dai ko ta bangaren sir ko shi yana son yarinyar bamu sani ba ko da yake shi din ma gaskiya bazamu iya tabbatar da hakan ba ,dan wani lokaci kinsan halinsa birkice mata yake yayita wasu abubuwa ta yadda mutun bai isa ya fahimci komai akanshi ba .”



tunda madam some ta fara magana mami ta zuba mata ido tana kallonta tana jin fad’uwar gaba har sanda madam some ta dasa aya kana ta numfasa tace “yanzu dai kina nufi babu komai tsakaninsu?” gaskiya mumy ni dai a iya sanina babu komai atsakaninsu sai muamula ta aiki “numfashi mami ta sauke tace” to shikenan na gode sosai”! babu komai mumy ta mike tsaye tana cewa” ni zan koma office saboda sir yana jirana,” okay sai anjima “.
madam some ta d’an rusuna tanawa mami sallama inda mami tabi bayanta da kallo dan taso taji kyakkwan labari daga bakinta “kenan dai gaskiya adamcy ya fad’a mata babu komai a tsakaninsu da yarinyar ta d’auki lokaci zaune tana zurfafa tunaninta dan ta rasa dalilin da yasa zuciyarta ta kasa amincewa da adamcy ba son yarinyar yake ba.”



Cikin tsananin tashin hankali kukan da take ,ya shiga kai kawo acikin office din hannunsa d’aya rike da kugunsa cikin haka daya daga cikin wayoyinsa ya d’auki sauti amman bai bi ta kan kiran ba ,ya sake komawa inda take wanda zuwa lokacin ta durkushe kasa tana kuka yana son hukuntata akan cika masa kunne da tai dan duk abinda zai faru akan hototunan dole zai ta’ba kima da mutuncin sa amman ya kasa sai ma ya bige da durkushewa a gabanta tare da kira sunanta cikin wata irin murya mai sanyi da kashe sansar jiki “maryama ! wanda yasa tsigar jikinta mikewa yrrr”kiyi hakuri ki yafe min nasan duk ni ne na janyo faruwar komai “.jin sautin sanyayyiyar muryarsa yasa ahankali ta d’ago shayyyun idanunta ta zuba masa batare da tace komai ba sai dai a kallon da take masa bugun zuciyarta ke qaruwa “yayinda har lokacin kira na kan shigowa wayarsa.”



ya mike ahankali ya isa inda wayar take ya d’auka yana dubawa sai daya lumshe idanunshi na second biyu sannan ya bud’e ya d’aga wayar yana cewa” hello !”kwayar idanunshi yana kanta yana kallonta yana jin kamar ya furta mata abinda ke cin zuciyarsa ko ya huta da azabar da yake sha akanta ,waya yake amman sam natsuwarsa da hanakalinsa basa kan wayar suna kanta ya kai hannu ya d’auki iPod dinsa yayi connecting dinsa da wayarsa ya manna a kunnesa wanda hakan ya bashi damar ajiye wayar akan table ya qaraso zuwa inda take durkushe “har kullum yana son ta zama jarumar mace mara rauni ,mace me qarfin zuciya Sam baya so ta zama raguwar mace domin idan ta zama mallakinsa zata fuskanci abubuwa ,idan ta cigaba da zama raguwa za’ayi galaba akanta, tsoronta zai zama rauninta hakan zai sa ayita cutar masa daita hawaye ya cika masa ido ahankali ya kauda kanshi daga kallonta .”



Ahankali ta cigaba da jiyo maganarsa cikin rauni “ki tashi ki samu waje ki zauna kafin nasan abun yi ,ta yunkura da kyar ta mike tana wani irin taku ta samu waje ta zauna dafe da kanta cikin sanyi jiki ya isa gaban fridge ya bud’e ya d’auko goran ruwan mai sanyi ya juyo zuwa inda take “have some water!” ya mika mata goran ruwa bata kar’ba ba haka zalika bata d’auke kwayar idanunta akanshi ba shima kuma bai janye hannunsa akanta ba idanunshi yana kanta har sanda ya gama wayar wani kiran ya shigo wanda ya kasance na mami ne” the way yadda yake amsa wayar yana kiran sunan sweetheart ta fahimci daita yake wayar duk da batasan abinda yake fad’a mata ba amamn hankalinta yayi mugu magun tashi yana gama wayar ya sake cewa” maryama take some water ki sha ruwa ko kad’an ne “dawa kayi waya yanzu ?”tayi magana cike da raunin zuciya” my mother ya bata amsa atakaice yana kallonta “shikenan nasan itama an tura mata hotunan ai nasan za’ayi haka nasan za’a turawa yan’uwanka da mahaifiyarka.”“ ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru” ni kawai ka fad’a min wani mataki zaka d’auka dan ni naga kamar ma baka damu da halin da nake ciki ba ,a kallon da nake maka ma gani nayi kamar dadin faruwar haka kayi.”



A d’an rikice yace “bangane nufiki ba ?” Ai dole kace baka gane nufina ba gashi har an turawa ma mahaifiyarka aman babu wata alamun damuwa atattare da kai. yayi shiru kawai yana kallon yadda take motsa qaramin bakinta “ka fad’a min gasky an tura mata hotunanmu ko “? still dai shiru yayi kawai yana cigaba da kallonta “ an tura mata hotuna ko ba’a tura mata ba ?”wannna ba matsalrki bace ko an tura mata ko ba’a tura mata ba “to yanzu ka fad’a min matakin da zaka d’auka kafin zuciyata ta buga “what I will do is my own business it my decisions how I wil manage my hanger, duk yadda nake qoqarin kwantar da zuciyata akanki baki gani ,duk yadda nake faman rarrashinki baki gani har kina iya cewa naji dadin faruwar abinda ya faru idan naji dadi menene ribata bayan dole wad’an nan hotunan zasu ta’ba mutuncina ?”tunda nã had’u dake kullum nida kamfanina cikin damuwa muke dan haka idan kinga dama ki fad’a abinda yafi naji dadin faruwar abinda faruwa ba damuwata bace .”



nan take gabanta ya wani irin bugawa da qarfi , ta mike da sauri tana cewa “tunda ka had’u dani kullum kamfaninka da kai kuke samun matsala as how ?”me kake nufi dani sir dan bangane nufinka ba ?“idan akwai wani abu acikin ranka akaina say it directly ba wai ka dinga kwana kwana ba “what !” ya furta da qarfi yana jin kamar ya d’auketa da mari sai dai baya Jin zai iya aikata hakan akanta lip’s dinsa ya kamo na kasa yana taunawa da qarfi kafin ahankali yaja tsaki yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa “kamar yadda kake tunani haka akaina nima haka nake wannna tunanin akanka,tunda na hadu da kai kullum cikin damuwa da shiga matsala nake a yau nayi dansani ,a yau nayi nadamar kasancewata acikin AGC company “matsala ba daga kamfanin bane matsala daga ke ce “what? me kace ? yana jinta ya shareta “ina bukatar na sake jin abinda ka fad’a yanzu tayi maganar tana takowa zuwa inda yake tsaye “ ke banson iskanci tunda abun naki ma wulaqanci ne na ma fasa d’aukar mataki akan abinda ya faruwa, bazanyi bincike komai akai ba kije kiyi duk abinda zaki yi idan anga dama a yad’a hotunan zuwa social media is not my own business.”cikin tsananin tashin hankali ta had’e hannuwanta waje d’aya tana jin wani irin fad’uwar gaba from no where yana shigarta “muryarta na rawa ta soma mgn “yanzu abinda zaka fad’a kenan ?I can’t say more than that ,dan haka kiyi min shiru anan ki barni .”



“me yasa zaka fad’a haka ?”wallahi ni dai abinda nasani ni ba matslar kamfanin nan bace kaine matsalar kamfaninka kuma ko kaso ko karka so ni ba matslar kamfaninka bace dan kasani kasancewata aciki cigaba ya kawowa kamfaninka aikin banza kawai Ina zaman zamana ka shigo rayuwata wanjen nuna son asaninka ka jawowa mutun shiga matsala .”“maryama how dare you talk to me like this ?me yasa kaima zaka ce nice matsalarka data kamfaninka”? sannan me yasa zakace ka fasa d’aukar mataki akan abinda ya faruwa?”me yasa bazaka yi bincike akan abinda ya faru ba “?me yasa zakace naje nayi duk abinda zanyi idan anga dama a yad’a hotunan zuwa social media is not your own business?”idan har kai ma zaka iya fad’a min haka nice bazan iya fad’a maka haka ba?wallahi kwata kwata zuciyarka bata da tausayi bare fellings kai ganinka babu wanda zai iya fad’a maka mgn ne ?”ta fad’a hawaye na zubo mata.”shiru yayi yana kallonta “wallahi da kana da fellings dole zaka zamo mai tausayin halin dana tsinci kaina a yau “duk lokacin da mutun yake cikin damuwa kai lokacin kake da damar qara ninkawa mutun damuwa akan wanda yake ciki idan ma mutun mutuwa zai yi ba ya mutu ba damuwarka bace ,”ta qarasa maganar tana kallonsa ido cikin ido .”



still dai shiru yayi kawai yana kallonta “ai bazaka ta’ba jin tausayin wani acikin ranka ba saboda zuciyar dutse gareka,” ka wani zuba min ido kana kallona baka da wani bambamci da dutse still kallonta kawai yake yana jin kamar ya kamota ya soma yaryarfa mata mari “da fatan kaji abinda na fad’a yanzu there’s no difference between you and stone” yadda dutse yake da qarfi haka zuciyarka take da qarfin da rashin Imani da rashin tausayi dan ..”enough maryama !”ya furta da qarfi yana dukan glas cup din dake kan table, nan take cup din ya fashe tare da ruwan ciki aiko nan take hannunsa ya yanke sai ga jini ya fara zuba wani irin qara ta saki mai sauti tare da yowa kanshi tana kiran “sir me yasa zaka yi haka ?kaga irinta ba ?kaga irin abinda zafin zuciyarka ya janyo ?” kalli yadda kajiwa kanka ciwo ?ta kai hannunta zata ta’ba shi yayi saurin katseta ta hanyar cewa “karki soma kai hannunki jikina stay a waya from me “dan Allah ka ..” nace banason go and do your work matsowa tayi kusa dashi sosai muryarta na rawa tace “a halin yanzu babu wani aiki da zan yi wanda ya wuce na duba hannunka “mar..”dakatar dashi tayi ta hnayar d’aga masa hannunta “ka barni nayi abinda ya dace” ta fad’a tana haki “maryama there’s no need for this kinsan zaki damu me yasa kika ‘bata min rai “sir babu ruwana da abinda ya bata maka rai ka zauna kawai “ ta fad’a tana zubar da hawaye yaki zama kamar yadda ta bukata .”gashi zafin zuciyar da yake cinsa yasa jinin ke qara zuba .”



“please sir site !”shiru yayi kawai yana sauke numfashi kafin ahankali ya samu waje ya zauna yana cizan lip’s dinsa ko zai rage masa azabar zafin da yake ji ,”muga hannun ta fad’a cike da tsananin damuwa kin bari yayi taga hannu, ta kai hannnuta ta riko hannun ta qarfin tsiya tana kallon ciwon da yaji shima kallonta yake tana hura masa iskar bakinta a ciwon wanda yayi sanadiyar da ya dinga jin wani sanyi na bin lungu da sako na sansar jikinsa lumshe tsumammun idanunshi yayi” tabbas maryama ta kamu da tsananin sonshi batare datasan tana yi ba,” ta d’ago kanta ahankali idanunsu ya tsarke cikin juna cike da zafin zuciyata tace” ka tsaitsata zuciyarka, dan zafin da zuciyarka take yayi over shi yasa jinin yaki tsayawa, mutun bashi da wani aiki sai zafin rai please ka tsaitsaita kanka “maryama banason damuwa please ki sakar min hannu ki kama gabanki.” numfashi ta shiga saukewa sama sama tana jin wani irin a gabdaya ilahirin jikinta” i saida leave my office now ya sake fad’a yana nuna mata kofa .”tai mugun zuba masa shayayyun idanunta tana kallonsa hawaye na gangaro mata batare datayi yunkurin mikewa tsaye ba .”







Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.



Page 41


Ahankali maryama ta d’auke kwayar idanunta akanshi zuwa hannunsa ganin yadda jini yake bin yatsun hannunsa ya mugun d’aga mata hankali .”hawaye ne sosai yake zuba daga idanunta tunanin inda zata samo abinda zata d’aure masa hannun take amman sam ta rasa .”tana cikin tunane tunane taga ya mike tsaye cikin sanyi jiki tayi saurin riko d’ayan hannunsa mara ciwo cike da zafin nama ya fixge hannunsa yana mata gargad’i da kwayar idanunshi “ki tashi ki bar min office idan kuma ni kike son na bar miki sai ki bari nasani.”ya fad’a yana mai kawar da fuskarsa daga kallonta .”d’ago idanunta tayi ta cigaba da kallonsa gani tayi yanayinsa ya sake sauyawa ya wani maida kanshi gefe yana huci tmkr wani zaki tana kallonsa ya d’auki d’aya daga cikin wayoyinsa ya nufi d’akin dake cikin office din ,da idanu ta rakashi har sai da taga shigarsa sannan ta iya sauke numfashi da ajiyar zuciya atare sai dai kamar yadda ya bukata haka tayi jiki a sanyaye ta mike ta fita daga office din tana daidaita natsuwarta dan kada ‘yan office dinsu su fahimci wani abu .”



tana fita ko cikakken minti biyar batai ba mr ata ya fito ya samu waje ya zauna yana sauke numfashi tare da tokare hannunsa mara ciwo a kugunsa yayinda hannunsa mai ciwo ya ajiye akan ciyarsa yana kallo irin raunin daya ji. yana zaune doctor dinsa ya nemi izinin shigowa da kyar ya bud’e baki ya bashi izinin shigowa ya shigo a natse ya gaishesa cike da girmamawa sannan ya ajiye jakar kayan aikinsa ya soma had’a kayan aikin da zai bukata yana cewa “ranka ya dade garin yaya ka samu irin wannan raunin haka .”?shiru mr ata yayi masa dan bai san me zai ce masa ba .”doctor ya janyo kujera zuwa gabansa ya zauna yana masa sannu cike da kulawa ,kanshi kawai ya gyada, a natse ya d’auki bandage ya had’a da d’an digon wani farin ruwa mai d’auke da sinadarin akai ,hannunsa ya kai ya riko hannun mr ata ahankali ya soma goge masa ciwo da auduga wani irin zafi ya ziyarci sansar jikinsa yayi saurin runtse idanunshi tare da cije labbansa da qarfi adaidai lokacin maryama ta kai idanunta office dinsa inda ta hango doctor zaune yana treatment din hannunsa naunauyen ajiyar zuciya ta sauke da qarfi sannan ta mike ta fito .”



Ahankali ta tura kofar ta shigo ta tsaya akanshi sake rike hannunsa doctor yayi cike da kulawa ya cigaba da goge masa yayinda mr ata ya sake cije lips dinsa yana qoqarin zame hannunsa muryarta a raunane tace “sorry sir da zafi ko ?kayi hakuri a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login