Showing 174001 words to 177000 words out of 182919 words

Chapter 59 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

392

maganr kaje kayi aure yake maka , amaman mutanen dake tare daku sai suna masa kallon yana sonka ne kuma umma kinsan wani abu, shi dai wannan mutumin ya dawo daga baya yace a auresa batare daya furta kalmar so ba .”ta qarasa maganar tana kallon fuskar mr ata acikin kwayar idanunta”umma tayi shiru tana saurarenta.”ahankali maryama ta numfasa sannan ta cigaba da magana “umma Ina son ki fahimtar da wani abu a cikin maganata .”?


“eh to ni dai abinda na fahimta hakan zai iya yuwuwa ace so ne, saboda kowani d’an adam da yanayinsa da kuma yanayin yadda yake shigar da soyayya rsa,” su waye wadan nan mutane ?” “amm wasu mutane ne a office dinmu”maryama kodai kice da mr ata?umma tayi mata tambayar kai tsaye “ware idanuwanta tayi tare da cewa “kai no no haba umma ina ni ina shi wannan mutumin da bai da sakin fuska ,ai muddin ya zamo mijina to nasan kwanaki da allah ya bani a duniya bamasu yawa bane .”ta qarasa maganar tana dariya sun jima suna hira maryama tayiwa umma sallama ta shige dakinta ta kwanta zuciyarta fess babu wani alamun damuwa sai dai hakan nan zuciyarta ta dinga tunanin mr ata wanda ya zame mata jiki tana son raba zuciyarta da wannan tunanin amman abun ya citura most especially a yau din nan ahankali ta gyara kwanciyarta tana sake rungume pillow ajikinta tana jin kamar shi ta rungume .”


Bayan kwana biyu akayi ma maryama salary sannan ranar ta kasance babu wani aiki a Office dan duk wani aikin da’aka bata ta kammala dan haka tayi tunanin da zaman da take ta tashi taje tay masu siyayya abubuwan da basu dashi a gida ta mike ta fito rataye da jakarta ta fito ta sanarwa madam some sannan ta sauko zuwa qasa .”
tunda ta sauko taji gabanta yayi wani irin mummunar fad’uwa sai dai bata kawo komai ba ta biyo dogon titin da zai fito da mutun zuwa babban titi stil dai gabanta bai daina fad’uwa ba duk ilahirin jikinta yayi mata wani iri taji kamar ana mganrta a baya , ta tsaya tare da juyowa wasu mutane tagani sanye da suit suna magana wanda ke nuna alamun bama daita suke ba dan haka ta sake juyawa ahankali ta cigaba da tafiya har ta fito bakin titi kai tsaye mota ta shiga zuwa bank mafi kusa da inda take ta ciro kudi masu yawa ta shiga wani shago siyar da Kayan sakawa na mata dana maza ta siyawa aunty da umma kala biyu biyu ,habib ma haka da takalmin itama ta siyawa kanta dogayen riguna guda uku kowanne da kalar takalminsa da jaka ta biya kudin ta fito ta shiga wani super market domin siya masu kayan kwalama ,anan ne ta hadu da wani alhaji mansoor wanda ya nuna qaunarsa agareta baro baro .”


ba wani dogon turanci maryama ta aminta dashi saboda daman irin wannan damar take nema wanda zai aureta ido rufe tunda bata da wani tsayayye maganar mr ata kam shirme ta daukesa duk da tana tsananin jinsa aranta .”nan sukai musanyar number da Alahji mansoor dan zuciyarta ta natsu dashi haka zalika bugun da zuciyarta take ta kau har tai tunanin watakilla haduwarsu dashi ne yasa taji wannan yanayin ajikinta , taiwa kanta fatan Allah yasa haduwarsu ta zame mata alkhairi arayuwarta alhji mansoor ne ya biya maku kudin shopping din da tai ya kuma kawota gida bayan ta shigar da siyayyar datai ciki ta dawo inda alhaji mansoor yace mata shi fa da gaske aurenta yake so yi kuma cikin kankanin lokaci sai dai yana da mata biyu da yara takwas kai tsaye maryama tace ta amince sai dai ta fad’a masa tana zuwa aiki .”



Yace ai wannan ba matsala bane bazai hanata zuwa aikinta ba ,wannan ne abinda ya qara sa zuciyar maryama ta sakankance dashi har ma tayi tunanin zuwa satin da zasu shiga zata gabatar dashi ga iyayenta ,tun daga wannan lokacin alhji monsoor ya fara zuwa zance gidansu maryama wanda hakan yasa gabad’aya maryama ta cire tunanin wani adam aranta ta soma saka tunanin alhji mansoor aranta duk lokacin daya so ganinta yana ganinta ranar da suka cika sati biyu da haduwa ne yazo wajen aikinta suna tsaye dashi ajikin motarsa kwatsam sai ga mr ata ya fito daga masallaci tun daga nesa ya hangota tsaye tare da alhji mansoor ,gabansa ne yayi wani irin mummunar fad’uwa ganinta tare da wani Wanda bashi ba ,nan take zufa ta shiga karyo masa .”ahankali ya cigaba da d’aga qafafuwansa ya zagayo ta bayansu ya tsaya ta yadda bazasu gansa ba sai dai qirjinsa ne ke wani irin bugu da matsanacin qarfin gaske “cike da tashin hankali ya zuba duka hannunwansa cikin aljihunsa .”


Tunani yake anya kuwa ba mafarki yake ba ?”maryamarsa ce tare da wani kato tsaye tana washe masa baki ?to ya bazaka ganta da wani ba tunda Kai ka kasa furta mata kana sonta ai dole ka ganta tare da wani “to kuma ai duk alamunta sun nuna tana sonka “okay kenan jira kake tace kana sonta ?”yayiwa kanshi tbayar yana sake shiga rudani da tashin hankali “adam kaga irin abinda zaka janyowa kanka ko?“ka bud’e baki kace mata kana sonta ne matsala to ai gashi nan wani zai maka shigar sauri ?”yayiwa kanshi magana yana datse harshensa da qarfin .”ahankali ahankali yake jiyo duk hirarsu da suke sai dai zance auren da yaji suke har da tsare tsare yadda komai zai guduna shine yafi komai daga masa hankali “aure kuma maryama “?



Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.



Page 49


jijiyar kansa ne ya amsa har zuwa kan babban d’an yatsansa, ahankali ya zura hannunwansa duka cikin aljihun windonsa ya shiga d’aga qafafuwansa da kyar, qirjinsa na wani irin bugawa da matsanancin qarfi ya zagayo gabansu ya tsaya nisa kad’an da inda suke tsaye tare da tsura mata kwayar idanunshi dake cike da tashin hankali .”cikin sa’a shayayyun idanun maryama suka sauka akanshi gabanta ne yayi mummunar fad’uwa yayinda gbad’aya annurin dake kwance akan fuskarta ya d’auke cak ta daina murmushi da jin maganar da alhaji mansoor yake mata .”
nan take jikinta ya kama kyarma komai na duniya ya tsaya mata ,ba wanda yace ma d’anuwansa komai daga maryama har mr ata da alhaji mansoor wanda ya dawo tamkar mutun mutumi tsaye yana kallon yadda one time yanayin maryama ya sauya sakamakon ganin mutumin dake tsaye a gabansu .”



zufar data tsatsafo a saman goshinta ta share tana cigaba da kallon mr ata dake tsaye tamkar mashi kafin ahankali tayi kasa da kanta tare da kamo yatsun hannunta tana wasa dasu dan bazata jura irin kallon da yake mata ba mai d’auke da ma’anoni iri iri ,tasan waye mr ata kuma tasan halinsa tamkar yunwar cikinta wannan kallon da yake mata bana banza bane“.
sosai take jin wani iri a gbdy ilahirin sansar jikinta “ai dole duk wanda mr ata ya tsurawa wad’an nan tsumammun idanunwan nashi masu firgitarwa dole sai yaji wani iri ajikinsa bare ita da zuciyarta take jin wani abu akanshi .”har ga Allah da tasan zai zo ya samesu a wajen data shiga cikin motar alhj mansoor dan kwata kwata bataji dadin ganinsa ba koda bai furta mata kalmar so ba ai ya furta mata kalmar aure kenan gansu yanzu haka ya zama cin fuska ne .”



bayan kamar second goma alhj mansoor ya kira sunanta a tsanake yana jin wani irin mummunar tsoro a zuciyarsa “my princess lafiya ko akwai damuwa ne naga duk yanayinki ya canza daga farin ciki zuwa damuwa ?”ba tace masa komai illa ta d’ago kwayar idanunta ahankali still dai tsumammun idanun mr ata suna kanta ya sake tsareta da idanunshi masu sata shiga taitayin ta ,kuma duk sanda zai d’aura mata su,wani irin sinadari ne ke fitowa daga cikinsu suna shiga cikin kwayar idanunta tare caccakar duk wani sashi na jikinta most especially idan suna cikin damuwa dole ne ka dabarbarce sai kayi da gaske ka samu ka dawo da natsuwarka,”



so take ta maida kanta kasa amman ta kasa dan wani irin mummunar fad’uwa gaba take ji ahankali ta lumshe idanunta dan kallon da yake mata ya saukar mata da jin kasala hakan tasa ta sake tsura masa ido tana tunanin mafuta dan bata san yadda zata bullo masa ba shi kuma banda kallonta babu abinda yake “my princess !”ta jiyo sautin muryar alhji mansoor ya sake kiran sunanta a karo na biyu ,still dai shiru tayi masa tana cigaba da kallon mr ata up and down wanda zuwa wannan lokacin ya kai hannunsa daidai saitin zuciyarsa yana shafawa ahankali dan baa maganar irin zugi da kuncin data shiga alokacin “Ina ganin ya kamata ki shiga mota na saukeki a gida nima na qarasa gida ko.”ahankali maryama ta sauke naunauyen ajiyar zuciya tana duba agogon dake d’aure da tsintsiyar hannunta tare da gyad’a masa kai alamun taji duk dai lokacin tashi bai yi ba amman itama a ganinta gara ta wuce gida zai fiyye mata kwanciyar hankali muryarta a sanyaye tace “habibi bani minti biyar bari naje na d’auko jakata na dawo “murmushi ya sakar mata tare da cewa “an baki ranki shi dade.”



Mr ata yana kallonta ta soma taku batare data kalli inda yake tsaye ba dan yi tayi ma tamkar bata san da tsayuwarsa a wajen ba tana daf da shiga lifter wasu abokan aikinta suka qaraso suka gaishesa cike da girmamawa sannan suka qarasa gareta suna mata magana atare suka shiga lift gabad’aya hankalin mr ata baya kansu yana kan maryama ne dan har lokacin ya kasa daina mamakin ta.” yana nan tsaye ta dawo ta wucesa tana latsa wayarta still tayi tamkar bata san da tsayuwarsa ba tun kafin ta qaraso wajen motar alhj mansoor ya bud’e mata gidan gaba yana sakar mata murmushi, ahankali ta d’an rage tafiyarta tana qoqarin shiga motar taji an fixge wayar hannunta ta baya a firgice ta juyo,nan take kwayar idanunta ya sauka akan mr ata yana huci tamkar wanda yayi gudun tsare ahankali ta rausayar da kwayar idanunta cikin nashi wanda hakan ya haddasawa zuciyarsa tsalle da shiga rud’ani “lafiya sir !” ya zaka amshe min wayata !?
”tayi masa tambayar ajere tana hura masa hanci wani mummunar kallo ya d’auketa dashi mai had’e da harara “lallai ma yarinyar nan ta mugun rainashi sai da tayi qasa da muryarta sannan tace “dan Allah sir ka bani wayata gida zani !”tayi maganar cikin salon jan hankali.”


wani bakinciki ne ya tokare masa kahon zuciya wanda yasa ya soma ganin dishi dishi yayinda zuciyarsa ta soma tafasa yana jin duk laifinsa ne daya biyewa girman kan zuciyarsa da bata mahimmanci akan komai gbdy qasa magana mr ata yayi sakamakon ‘bacin ran daya tsinci kanshi ciki dan shi a ganinsa ta fahimcesa ta kuma tasan yana sonta so kawai take taga qarshensa so take sai ya furta mata mouth to mouth sannan zata fahimcesa .”ganin bashi da niyyar bata wayarta yasa ta juya a natse ta kalli alhj mansoor dake tsaye yana dubansu zuciyarsa cike da jin haushi da tsananin kishi tace “habibi shiga mota muje “what !?mr ata ya furta a tsawace alhj mansoor dake qoqarin yin magana cikin farinciki wanke masa zuciya da tai bakinsa ya rufe jin mr ata yana cewa “karka sake kayi wata magana anan salin alin ka shigar motarka kai kad’ai ka wuce ka kama gabanka ,and you ki koma ciki”. ya juya kanta kamar wani nmjin zaki duk wani matsayinsa da miskilancinsa da jin kanshi ya nema ya rasa saboda tsananin kishin dake dawainiya dashi .”



da mabambamnta idanu maryama da alhj mansoor suka bishi dashi .” alhj mansoor ya tsaida hankalinsa da natsuwarsa sosai akan maryama yana lashe lip’s dinsa wanda ya zame masa miji kafin ahankali cikin tsananin fushi yace mata “waye shi !?”tace please kayi hakuri me gidana ne “mai gidanki !”?ya sake furta wa idanunshi na kan mr ata wanda cikin Kankani lokaci ya fahimcesa baya raba dayan biyu kishi ne ke dawainiya dashi abun tambaya anan shima mai gidanta na sonta yake kenan ?”
“Mintu biyu!” minti biyu kawai na baki maryama ki fad’a masa kin fasa aurensa“ idan ba haka ba zan shayar dake mamaki.” nan take rauni ya lullubeta ganin yadda yake shirin tujarata agaban alhj mansoor mutumin da yake shirin zama miji gareta “wai mai yasa mr ata yake son wulaqanta ta a bayanan nasi ?


katse mata tunanita yayi ta hanyar sakin wata tsawar yana mai cewa “wai ba dake nake magana ba kin tsaya kina kallon wannan banzar mutumin “maza maza ki fad’a masa kin fasa aurensa kuma a yanzu .”turo masa qaramin bakinta tayi tana cewa “haba yallabai wai me yasa ..”stop !” yayi saurin katseta ta hanyar fad’ar haka “I don’t want to hear anything from you maryama just tell him and let him leave this company right now “
“Wai a yanzu kake nufi na fad’a masa na fasa aurensa “?matsota yayi yana kallonta yana Jin yadda zuciyarsa ke kutememiyar bugawa fiyye da Kaida “tambayata ma kika tsaya yi kenan bazakiyi abinda na sakaki ba ?”ya tambayeta a hassale “naji shikenan zan dai fad’a masa ya wuce shima tare zamu wuce tunda ma’akatan takace amman gasky bazan iya fasa aurensa ba tunda Ina son shi washe baki alhj mansoor yayi yana Shafa kanshi,shi kam ata tsoro da matsanancin firgici ne ya bayyana a fuskarsa yyinda zuciyarsa ta dinga bugu numfashinsa ya soma baraza nar daukewa cikin zafin zuciya yace “malam ka d’auke wannan akwalar motartaka ka bar nan yanzu tun kafin nasa ayi maka abinda zai fi komai muni gareka.”ya qarasa mgnr ahankali tmkr ba acikin fushi yake ba .”



alhj mansoor ya kalli maryama ya juya ya kalli mr ata yana jiran taji mai uwar gayya zata ce maryama kam kallonsa kawai take batai mamaki ba dan tasan zai iya aikata fiyye da haka mr ata ya sake tsare gira “muje ciki !”cikin sanyi jiki tace “please sir bana son irin abinda kake min domin kuwa barazana ne ga rayuwata idan ma wasa kake ka daina dan gsky sai da kayi hakuri dan ban zan koma ciki ba zan bi zabina kuma mijin da zan aura habibi muje ko .”kamar jira alhj mansoor yake ya sauke ajiyar zuciya ya zagaya ya bud’e murfin mota ya shiga ya zauna mr ata kuwa ya sake d’aure fuska ya fara mgna cikin fad’a da jin haushi “look at me maryama kinga alamun wasa atattare dani ?”babu wasa acikin maganata yaushe kika hadu dashi da har kika amincewa aurensa “?ba gara ni ki aureni ba at least kin sanni kinsan halina, maryama ta girgiza masa Kai cike da tsoro sai dai bata bari tsoron yayi tasiri ba ta shige motar alhj mansoor ta zauna ta rufe murfin kofar da qarfi yayinda shigarta keda wuya alhaji mansoor yaja motar ya fice daga ma’akatan inda mr ata yabi bayan motar da kallo mai cike da tashin hankali.”



Ahankali motar alhj mansoor take guda akan titi sai dai zuciyar maryama bata cikin natsuwa gabad’aya ta rasa meke damunta “tabbass tasan ta baro wani bangare na rayuwata a AGC sannan tasan tsananin kishinta mr ata yake amman mai yasa bazai fito da abinda ke cikin zuciyarsa ba?” shin darajarta ce bata kai haka ba ko kuwa kasancewarta daga tsatson talakawa ne yasa haka ?”wannna abu yasa zuciyarta ke tsananin bugawa da matsanancin qarfin gaske “my princess da alamun shima wannna mai gidan naki sonki yake yi “kunnuwanta suka jiyo mata maganar alhji mansoor kai tsaye tace “ba so bane haka yanayinsa yake ,shi mutun ne mai tsananin son wulaqanta duk wanda yake qarqashinsa “no my princess wannan mutumin akwai so atattare dashi sai dai idan bai furta miki ba amman tabbas akwai so idan ba haka ba ,ba rami me ya kawo zance rami “.yayi mgnr yana qoqarin riko hannunta wanda taji tmkr garwashin wuta yake barazanar konata da sauri ta zame hannunta tana cewa “ka yarda dani habibi babu wani abu makamancin haka atare dashi ,shi dai haka rayuwarsa take bama akaina ba akan kowa ne.”



Gyad’a kai yayi kafin ya cigaba da magana”na fara wani tunanin !ta waigo a natse ta kallesa sannan tace wani tunani kenan ?“bana Jin zaki cigaba da aiki a qarqashin wannan mutumin zan nemar miki aiki a wani guri dan kwata kwata zuciyata ta kasa samun natsuwa da mutumin kar yaje yayi min illa, numfashi ta sauke tace “shikenan idan har hakan zai samar maka da natsuwa da kwanciyar hankali fine anything for you habibi khairan in sha allahu” na gode sosai shiyasa nake qara sonki akwaiki da biyayya a natse yake janta har suka qaraso ikeja sun kusan jara mall yace”my princess let me order diner for us ko kuma muci anan tace “okay ba dan ranta ya so ba dan ba dabiarta bace cin abinci a waje yanzu ganin girmansa da kuma ganin shi zata aura yasa ta amince .”




Suna isa jara mall sai ga wata budurwasa khairat wacce take mutuwar son shi sun dade tare suna bin juna dashi har da alqawarin aure a tsakaninsu sai dai shi har ga Allah baya sonta kawai jikinta yake so tazo ta wuce taganshi tare da maryama ,haba nan zuciya ya debeta ta d’aga hannu zata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login