Showing 15001 words to 18000 words out of 182919 words
zama da kai ne boss dole a koyi kalar halinka tsaki ata yaja yana cewa allah ya isa “what ?har yanzu dana fad’a maka gsky allah ya isa kake min ?kai nima Allah ya isa marin daka min Ata ya zabga masa harara “allah ka bani hakuri na yafe maka “wani tsaki yaja ka mutu idan dai sai na baka hakuri ai nine na cancanci ka bawa hakuri ni da ka kusan kaiwa lahira ammar ya kwashe da dariya “gsky dole fa muyi celebrity din wannan farinciki ko me kace ?”numfashi ata ya sauke yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa “ammar bana bukatar kowa yasan da zaman maganar nan bayan ni da kai da salim sai mb da dole na fad’a masa itama yarinyar banason ka fad’a komai “.
“itama iskancin zaka mata ?no ba haka bane a yanzu bazan iya fuskarta ta ba tunda kaga abinda ya faru a tsakaninmu gara na fara da dawo daita karkashin ikona da sannu komai zai tafi daidai fatan nasara abokina amman dan girman allah ka tausaya maryama yarinya ce qarama shiru ata yayi yana jin wani irin sanyi na mussaman na mamaye sansar jikinsa “ammar ina son yarinyarta nan soyayyarta gareni mai tafiyar da ruhi ce wallahi ina jin idan na rasata zan iya rasa komai nawa kuma zan iya sadaukar da komai nawa akanta “maryama tayi saa arayuwarta allah yasa ta gyara min kai ta caza maka kwakwaluwa “murmushin gefe baki yayi “kana ganin bazata iya ba ?”kai yanzu kaga nayi maka kama da irin wadan nan mazan?karka cika min baki ata yanzu fa kace zaka iya komai akanta?”yes of course nace amamn bazan dauki raini ba “iskanci banza yarinyar ma da bakasani ba ko zata amince da soyayyarka .” karta amince da soyayya amman zata amince da aurena “sun jima tare suna hirar farinciki a tsakaninsu wanda yaushe rabon su kasance haka sai da suka ci abinci sannan ammar yayi masa sallama ya wuce gida zumar zasu had’u gobe AGC.”
Washegari
Maryama na zaune akan gadon mahaifiyarta rike da takardan zanenta wayarta ta dauka tana cewa hello daga can bangaren taji ance “some ce daga AGC compaing shiru maryama tayi ta kicewa komai sai dai tana saurararta ATA dake zaune ya sauke naunayen ajiyar zuciya sakamakon jin sautin muryarta ,nan take yayi wa some alama ta saka wayar a hands free take some tabi umarninsa “fatan kin fahimci me magana ?can bangaren maryam tace “Eh naso na dan fahimta fatan dai lafiya kuka kirani ?“eh ! lafiya da..daman muna bukatarki ne domin Ki cigaba da ai.. “ai kar ma ki qarasa wannan mgnr dan har abada bazan qara tako wadan nan kafafuwan nawa acikin wannan banzar kafanin naku ba.” ta katseta ta hanyar fadar haka .”ni yanzu ma na samu aiki mai kyau a wani kamfani dayafi naku komai yanzu haka jibi jibin nan zan fara aiki dasu dan haka ki nemi wata ta soma qoqarin katse kiran “ki tsaya kiji maryam karki yi sau..” na tsaya naji nayi miki me ?me ma kuka daukeni shasha wacce batasan ciwon kanta ba ?“kunsan zaku bukaceni me yasa kuka wulakantani?“Kiyi hakuri dan allah maryama some ta tsinci kanta da furta hakan .”
“sorry for what?, wallahi ko duk duniya zaa bani a wannan kamfanin babu ni babu wannan kafanin har abada ki tsaya ki saurareni “mr ATA da kanshi ya bada umarnin a kiraki “me naji kikace yanzu ?sectary ta sake maimaita abinda tace “oh yanzu na fahimceki wulakanci da mutumin nan yayi min na lura yayi miki dadi ko ba haka ba ?,” a’a karki ce haka wannan ma dai allah ne ya qaddara hakan zata faru da km laifinki “amamn dai baki da hankali ko ?a gabanki aka tozartani byn kun daukeni aiki idan ke aka yiwa abinda aka min zaki iya cigaba da aiki?” “kinga sakariya karki damu kanki akaina “ki tsaya ki girmama wanda yace a kiraki ata ya zabgawa some wata katuwar harara yana hura hanci wanda batasan dalilin hararar ba “waye shi wanda yace a kirani ?some tayi shiru tana dubansa kamar yadda yake kallonta “shi wannan mutumin a wajenki yake wani abu mai mahimanci a wurin maryama kuwa zero ne ku nemi wata please Kmr yadda na fad’a dan ni har abada bazan sake dawowa AGC company ba “. tana gama mgn ta katse kiran maryam !!hello kina kina shiru taji alamun ta kashe ganin haka yasa ta kalli mai gidanta .”
“Sir fatan kaji duk bayaninta wai zata fara aiki da wani kamfani bazatai aiki damu ba gabadaya bata bukatar tayi aiki damu yanzu me zamuyi sir ?nasan me zanyi wannan abu yayi min dadi ina son haka ya fad’a tare da yin shiru yana jin wani iri a gabdaya ilahirin jikinsa “zuciyata da wannan kafanin yana matukar bukatar maryam y fadi sunanta yana lumshe idanunshi ina bukatar gabadaya diters dinta tun daga Kan address dinta kai komai da komai har zuwa Kan kafanin data samu aiki kai gabadaya komai daya shafeta ai idan ba wannan kafanin ba babu wani kafani da zasu dauketa aiki ya fad’a “okay sir .”ta juya ta fita da sauri domin ta nemo james dan shine zai fita hanzarta gudanar da komai .”sai bayan da some ta fita yayi tunanin kiran ammar dan dole zai san komai nata wayarsa ya dauka ya soma neman layinsa kira daya ya dauka nan ya fad’a masa komai ai kuwa ammar yace me zai yi idan ba dariya ba yana cewa “kai gsky maryama ta burgeni haka ake son mace “kai banason isknaci na kiraka ne dan ka fad’a inda take kuma diyar waye ba wai ka tsaya min dariya ba “.dan girma allah ka barni nayi dariya daman nasan bazaka samu maryama cikin sauki batare da kasha wahala ba “inna lillahi wai kai dole sai kagani acikin matsala ne ?”no ba haka bane amman wallahi abun yayi min sikari bari Gobe zan zo na kaika gidansu da kaina daga nan ..””dif ammar yaki ya kashe wayar ya kwashe da dariya yana nemansa a layi sai dai kiran na shiga yaki dauka .”
Tsaki maryama tayita ja babu kaukautawa tana fitowa zuwa parlour’n “ta zauna akan kujera tana furta “iskanci banza da wofi shasha ma suka daukeni kamar wannan né kawai kamfanin mutane zasu rayu dashi ,ina bazan ta’ba daukar wannan wulakanci ba gashi ma Allan yayi min arziki da wani aikin daman kuma haka lamarin allah yake idan ya kulle maka wata kofar sai ya bude maka wata .”washegari babu abinda aka fara gabatar dashi gaban ATA sai batun maryama good morning sir ?mornig ! Kawai ya furta atakaice sir maryam hussein zata fara aiki da alico insurance shiru yayi yana cigaba da abinda yake tamkar babu wata damuwa atare dashi “sai me kuma ? ya tamabayeta “sai danginta ita din family din bagoro ce tana unguwar gwagulori dake cikin agege da zama.” da sauri ata ya dago ya bar abind yake ya tsura mata ido har ya bata tsoro” ya shiga uku yar geto area ? ganin irin kallon da take masa yasa ya dauke idanunshi yana cewa “uhm ina jinki .”
“sannan yayan mahaifinta yana da qaramin kafanin bired wanda yanzu ya zama mallakin matarsa sakamakon mutuwar da yayi wannan kafanin yayi karfin da yake supply din biredi ga ciki da wajen agege a halin yanzu kanin mahaifinta mlm gali ne Ke kula da komai na gidansu da kuma gidan biredi “ya zaayi a samu numbresa ?ai gabadaya mukayi komai gashi ta ajiye masa cike da girmamawa “yanzu kuma sai me sir ?zaki iya wucewa “amman sir kayi wani abu da sauri dan gobe ne zata fara aiki da alico insurance,karki damu kota fara aiki dasu zasu koreta ta juya ta fice ta barshi tana jin dadi da kuma jinjinawa karfin ikonsa gbdy mutun ne shi da baya wasa da kasuwancinsa da kuma karfin ikonsa.”
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 65
Numfashi ya sauke ya koma ya samu guri ya zauna a kan kujera yana jujjuya jikinsa gabansa na wani irin bugawa da karfin gaske haka nan yake jin zuciyarsa na matukar jin tsoron abinda zai faru yayinda a hankali maganganunta na jiya da sukai waya da some ya dinga dawo masa daki daki " na tsaya naji nayi miki me ?me ma kuka d'aukeni shasha wacce bata san ciwon kanta ba ?"kunsan zaku bukaceni me yasa kuka wulakan tani?"ya runtse idanunshi gam yana jin matsamanancin tashin hankali "wannan yarinyar fa da gani rigimammeya ce ."ya furta a fili qirjinsa na lugud'en bugu alokacin da maganarta ta sake yi masa kuwa acikin kunnuwansa da zuciyarsa ".sorry for what?, wallahi ko duk duniya za'a bani a wannan kamfanin babu ni babu wannan kamfanin har abada "shi wannan mutumin a wajenki yake da mahimanci amman a wurin maryama zero ne ,dan haka tun wuri ku nemi wata amman ni har abada bazan sake dawowa AGC company ba ".
Wani irin zufa ne ya shiga tsatsafo masa akan hancinsa da ilahirin jikinsa ,ahankali ya kai hannu ya lalubo wayarsa ya soma binciken unguwar da take domin dai yana bukatar yaga yanayin tsarin unguwarsu "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ya furta a fili yana mai sake tsurawa wayarsa do tagumi yayi da hannu d'aya yana tunani irin rayuwar da mutun zai yi a irin wannan bazar unguwar numfashi ya janyo da kyar ya sauke sannan ya soma neman layin mb yana d'agawa yace "kazo yanzu yanzu ina AGC yana gama fad'ar haka yayi discounting din kiran ya kira salim da ammar."yayi baya da kujerar da yake zaune yana ciza lip's dinsa da qarfi babu abinda yake gani acikin kwayar idanunshi sai kyakkyawar fuskarta mai mugun kyaun gaske da yanayin jikinta tana rayuwa acikin unguwarsu imagenation dinta kawai yake tun daga qarancin shekarunta har zuwa sanda ya fara daura kwayar idanunshi akanta ,yanayin tsayinta da dogon hancinta shine yafi komai fito da ainihin sahihin kyawunta da Allah yayi mata ya numfasa yana sake lumshe tsumammun idanunshi "hakika maryama iyayenki sun iya haihuwa tunda suka haifa muradin zuciyar Adam .”yana cikin wannan halin sai gasu ammar sun bayyana a gabansa ."
SALIM ,AMMAR ,M.B duk suka zuba masa idanu suna kallonsa fuskarsa a sukwane kuma d'aure take kamar ko wani lokaci sai dai kallo d'aya sukai masa suka fahimci akwai abinda ke damunsa duk suka samu gurin suka zauna sukai shiru suna jiran suji abinda zai fad'a masu."ahankali ATA ya lumshe tsumammun idanunshi tare da sanya hannunsa d'aya adaidai saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take beating very fast bayan kamar second goma ya ware tsumammun idanunshi sosai akansu yana kokawa da lamarin princess dinsa saka makon matsayinta daya fahimta domin duk a tunaninsa bai d'auka zata fito daga irin area daaka fad'a masa ba ,ya d'auka zai ganta acikin royal family ne ko wani babban attajirin ne mahaifinta sai a yanzu ne ma ya fahimci bayan mugun abinda take rufe fuskarta dashi har da ma unguwar da take rayuwa aciki ya janyo rashin had'uwarsu .wani abu ya had'iye mai d'aci daya tsaya masa a mak'oshinsa kafin ahankali ya mike tsaye ya tsaya ajikin bangon office din tare da tura hannuwansa duka cikin ajihun wondonsa ya tokare qafarsa d'aya da bango yana cigaba da dubansu kamar zai yi kuka cikin kasa da murya ammar yace "Adam ya'akayi ne ?ka taso mu daga kan ayyuka masu mahimanci meke faruwa ?meye dalilin taramu dakayi ?ammar yayi masa tamvayoyin a jere duk da jikinsa ya bashi akan maryama ne dan idan akan kasuwancinsu ne bai zai nemi har da mb ba dan meye had'in soja da kasuwanci ."
"kasani ammar! "ata ya fad'a yana kokawa acikin ranshi "kasan dalili kiranku ammar amman kafin nan nasa some ta kira yarinyar nan jiya amman gabad'aya kalamanta sun nuna bazatayi aiki dani ba, amman ni ba wannan bane damwta ." meye damuwarka ata ?"mb ya tambayesa cike da kulawa "sai da ata ya sauke wani naunayen ajiyar zuciya sannan ya motsa lip's dinsa "wai princess dinace tayi rayuwa a irin wannan banzar unguwar ."yayi maganar cike da tsananin fushi yana zare hannuwansa daga cikin aljihunsa yayi taku d'aya biyu sannan ya tsaya cak atsakiyar office din tare da juya masu baya "gyaran murya salim yayi kana ya fara magana cike da sanyin murya "to meye aciki Adam kowani bawa ai da irin tasa kalar qaddarar "a ina take zaune ne ammar ?"inji cewar mb yayi tmbyr yana duban fuskar ammar ". "tana zaune ne a unguwar gwagulori "ina ne haka kuma ?""wata geto area ce acikin agege local government "cewar ammar "kunji abinda naji kuwa acikin zuciyata kamar ni Adam tariq Abdallah ace matar da nake haukar so ce tayi rayuwa a irin wannan banzar unguwa wani irin rayuwa ma tayi ?"gidansu ne ko haya suke yi ? Ata yayi masa tamvayar yana dungule hannunsa ya kaiwa bango naushi .da mamaki gabad'ayansu suka mike tsaye cikin tsananin tashin hankali suka qaraso inda yake suka rikesa suna kiran sunansa "what's wrong with you Adam ?" gabad'aya suka had'a baki wajen fad'ar haka."ka natsu mana ."
Shiru yayi kawai yana fesar da numfashi da iska mai zafi daga bakinsa gbdy yanayinsa ya canza zuwa na tsananin damuwa, fixge hannunsa yayi yana shafa daidai qashin hannunsa daya bugu yana watsa ma ammar wani mugun kallo .da sauri ammar ya d'auke idonsa saboda mugun tsoro daya kamasa ya koma ya zauna ."mb ya kallesa cike da tausayawa domin dai ya fahimci tausayi ne mai tattare da tsananin son da yake mata yasa shi shiga damuwa janyosa yayi ya zaunar dashi yana cewa "ka kwantar da hankalinka Adam haka rayuwa take kai a tunaninka zata zamanto diyar wani kamar yadda ka kasance to shi Allah ba haka yake son ganinta ba sannan ba hk tsarinsa yake ba ,ganin damarsa ne ya hada masoya masu wadata waje d'aya haka ganin damarsa ne ya hada talaka da mai arziki ." nasan kasan dukkanin rayuwa rubutaccen lamari ne daga rabbi yadda yaso haka zai yi ,saboda haka kasan duk wannan mai sauki ne a wajen Allah fatan mu yarinyar ta amince da soyayyarka tun da ka rigada ka gano Inda take .”
shiru ata yayi ya fad'a kogin tunani sosai hankalinsa ya bar duniyar da yake ya lula dashi can duniyar maryama inda zuciyarsa ta shiga hasko masa ita tare da wani tana rayuwar aure daahi . wani dogon tsaki yaja yana sake taune gefen bakinsa da qarfi saboda zafin kishin da yake ji hakika idan yace yaji dadin kasancewarta a bazawara yayi wa kanshi karya yaso ace shine mutun na farko da zai fara muamula ta aure daita bawani katon bazan can ba "Adam ka daina zurfafa tunani da yawa akanta tunda already kasan ta ta'ba aure ,tunda ta ta'ba aure kasan dole wani abu zai shiga tsakaninta da wanda ta aura ita kad'anta kake so kuma ko a wani hali take zaka kasance daita ." "jin an dafa kafad'ansa yasanyashi sauke kwayar idanunshi akansu "ba shiga damuwa ko dogon tunanin zaka tsaya ba abinda ya kamata kayi yanzu ka gaugauta aurenta domin ka inganta rayuwata kayi ma iyayenta duk abinda kasan ya dace ."inji cewar mb "Allah kad'ai yasan irin rayuwar datayi acikin wannan banzar unguwar mb ku duba map kuga yanayin tsarin unguwar datai rayuwa aciki inna ilaihi "ya sake furtawa yana yarfe hannu alamun abun na masa ciwo ".kai yanzu meye damuwarka da unguwarsu ? unguwarsu kake so ko ita ?"salim ya tambayesa wani kallo yayi masa yana fesar da huci yana sauke ajiyar zuciya da sauri da sauri." rabu dashi salim dan ma bai shiga lungun unguwarsu bane yasa yake fad'ar haka ."wani sabon zufa ne ya karyowa ata yayinda salim ya barke da wata irin dariya yana cewa "ai daidai kenan kamuwa da soyayyar yar talakawa zai sa wasu abubuwa su..."wani mugun kallo ata ya watsa masa wanda yasa salim yayi shiru yana kunshe sauran dariyarsa "ba hararar mutane ya kamata kayi ba kayi maza kayi abinda ya dace ku fahimci juna da yarinya ka aureta kafin wani yazo yayi maka shigar sauri "wannan duk ba matsala bane zan yi duk yadda zanyi ta dawo karkashin ikona . "fatan nasara abokina sun dan jima suna tautau nawa kafin daga baya kowannensu yayi masa sallama ya wuce suna fita yasa a kira masa baba gali "
*******
Cikin sauri sauri maryama ta fito daga bangarensu tana wa Aunty sallama kai tsaye part din umma ta shiga domin tayi mata sallama ta saka mata albarka tana rungumeta ajikinta "fatan alkhairi diyata "na gode umman ,maryama tai murmushi ta qarasa gurin hjy granny " Kiyi min addua kakata "allah ya tsareki maryama allah yasa zaki fara wannan aikin a saa sosai sukai mata addua ta soma kokarin barin parlour'n suna tsaye suna kallon bayanta suna rakata da addaua ."tana daf da kaiwa bakin kofa sai ga sallamar baba gali da aunty hassana tana ganinsu tai saurin durkusawa har kasa ta gaishesu"baba ina kwana aunty hassana ina kwana ? bata gama rufe bakinta ba sai ga mahaifiyarta itama ta shigo adaidai lokacin da yake amsa mata da "lafiya! Atakaice yana qare mata kallonta tare da cewa ina zuwa haka ?zani aiki ne ta bashi amsa jiki a sanyaye."what !? ya furta da karfi ai kuwa gara dana daka sammako ai wannna aikin baza kiyishi ba saboda ke na shigo bangaren nan .a matukar tsorace maryama tabishi da kallo kafin daga baya kalmar "inna ilaihi wa inna ilaihi rajiun