Showing 93001 words to 96000 words out of 182919 words
kanta mutunci da daraja,shekaru sama da ashiri kenan amman har zuwa wannan lokacin rashin mutuncin dangin mahaifinta ba bar mahaifi yarta ta huta ba ,basu barta ba haka zalika suma ya’yanta basu tsallake rashin mutuncinsu ba .”
“amman duk wa janyowa kanshi ?ta tambayi wankakkiyar kwakwaluwarta tana sake share hawayenta ,inda ta samu waje ta zauna tare da rafka tagumi tana tunanin rayuwa “yanzu aunty haka zaki qarar da rayuwarki batare da kin koma ga ahlinki ba ?”why aunty?!me yasa bazaki koma garesu ba ?”
”me yasa kike jin tsoro ?“mikewa tayi tsaye ta had’e hannuwanta waje d’aya“lokaci yayi aunty ,lokaci yayi da zaki koma ga iyayenki dan dole nasan abun yi.”
A natse hjy zulai ta tura kofar d’akinsa ta shiga yana kwance flat akan gado har zuwa wannan lokacin babu abinda ya cire ajikinsa zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda take a hankali ta soma magana cikin zafin rai "kayi kuskuren Adam kuma dole na fad'a maka haka, wannan cin fuska ne qarara kayi , aikin nan kowa yasani baa yinsa a boye shiyasa kaga naki amincewa amman ka nace ai kaga abinda ka janyo ko ? ya bude idanunshi kadan wad’an da suka dan canza kala ya tsura mata yana sake jin zafi acikin zuciyarsa ,magana yake son yi amman yasan koya bude bakinsa maganar bazata fito ba saboda ‘bacin rai sosai ta dinga masa fad'a kafin daga baya ta koma nasiha "bazan gaji da fad’a maka ba baba qarami matsayin ubanka ne ba makiyinka ba yana son yaga cigabanku ne gabadaya kaga yanayin abinda yake amman na rasa me yasa baka fahimta,me yasa baza ka fahimcesa kuma kaji maganarsa ba?” bai dace ba abinda kake yi masa yana fad'a kana fad'a kuma a gaban d’ansa bana jin dadi sai naga kamar nagaza wurin baka tarbiya ne “
“Wallahi bana jin dadi adamcy ka daina zubar min da mutunci, ka daina yin abinda zaa dinga kallon ban baka tarbiya ba ,tunda tasoma fad’anta bai ce mata uhm ba bare uhm uhm har ta gama ta fita."
*****
Washegari
Knowking akayi har sau uku ajire Aunty hasana dake zaune akan daya daga cikin dining tabke ta mike tsaye tana cewa"waye Ke buga mana kofa haka da bazaiyi a hankali ba yanzu wannan yarinyar ce aka sake buga kofar ,kai jamaa gani nan zuwa ta qarasa ta bude tsaye taga umma sai dai kallo daya tai mata ta fahimci bata cikin haiyacinta "Aunty kece da yamman nan amman ya baki fad'a min dazu da safe cewar kina Kan hanya ba ?” sannnu da zuwa nasan agajiye Kike ?umma ta shigo tare da baba gali a bayanta wanda shima duk ilahirin jikinsa a sanyaye yake " bari naje na kawo miki ruwa ta fad’a tare da juyawa da sauri ta nufi fridge yayinda umma ta samu guri ta zauna .”aunty hasaana ta dawo hannunta rike da cup din ruwa ta mika "Kinsan abinda maryama tayi jiya kuwa ?umma dai ta kar’bi cup din ruwa amman bata kai bakinta ba “yarinyar Ingaya miki bata dawo gidan nan ba sai wajen shabiyun na dare .”
umma ta kalleta tare da yin shiru sai dai kana kallonta kasan ranta a bace yake “ ba wani abu nake nufi ba kawai dai bai dace ace kamarta yarinyar mace tana kaiwa dare a waje ba “ zaka iya sheidawar wanda kake tare dashi kema kuma kinsani maryama bazata ta'ba aikata wani abu da zai zubarwa ahlinta mutunci ba dan haka ki fadi alkhairi ko Kiyi shiru domin kema uwa ce kuma duk uwa ta gari fatan alkhairi take wa yayanta dama wadan da ba nata ba .”umma ta kawo qarshen zance .”
"Allah ya kyauta to ya kika bari yanuwa acan ijesha fatan kin barosu lafiya ?Kafin ta bata amsa baba gali yace "Aunty ki fahimceni dan Allah ?fahimtar me zan maka gali tun yaushe ma abubuwa suka dawo haka bansani ba, yanzu banda naje kamfanin da kenan bazan san halin da kamfani yake ciki ba ?”
”wannan karon fa bazan fahimci komai ba kuma zan iya daukar duk matakin daya dace wai ma duk me haka yake nufi ?wannan ai cin amana ne qarara kuma komai yazo karshe domin kuwa zan tsaida duk wani zalinci da aka dade ana yi "
"aunty !
Aunty hasana ta kira sunanta tana duban baba gali dake tsaye cikin matukar tashin hankali "yaya meke faruwa ne ?”me naji aunty tana fad'a ?"kar dai kai ne duk ka aikata hakan ?muryarsa na rawa ya soma mgn "dan girman allah aunty ki yafe min nasan nayi kuskure amman dan allah ki yafe min ,me ma yasa nayi mata haka ?”ya fad'a yana juya bayansa tare da dafe goshinsa ,"duk qoqarin da take akanmu me yasa zan mata haka ? wallahi ba wai na dauki lokaci ina yin haka bane ,wannan shine karo na farko kuma in sha allahu nayi miki alkwarin bazan sake aikata makamancin haka ba, dan allah ki yafe min aunty ina neman yafi.." "zan yafe maka ne kawai idan na tsaida kai daga abinda kakeyi wanda shi zai sa ka fahimci abinda ka dade kana yi ,ka kuwa san nawa aka nema aka rasa akamfani?"gabdaya kana neman ka karyar mana da busines koma nace ka gama lalata komai ,wallahi ina mamaki ace wai kaine da kanka ka aikata haka wannna abun kunya da ne yayi kama ."?
Aunty hasana ta kallesa a matukar rude "da gaske duk abinda Aunty ta fad'a yaya ka aikata hakan?ya gyada mata mai alamun eh "to gsky koni bana bayan abinda ka aikata ka cutar da Aunty gskiya" ta fda tana kukan karya " duk abinda take mana itace komai namu fa tana kokarin kula damu amman me yasa zakayi haka? me yasa ka cutar daita ? Aunty Aunty!! ta fad'a cikin rawar murya"kar ma ki bata bakinki dan bazan janye kudirina akan ba".
" dan allah aunty ki bashi wata damar bazai sake ba nayi imani bazai sake ba yanzu idan kika tsaidashi aiki dame zai dinga kula da iyalinsa dan allah ki duba yanuwantaka ki yafe ma.."bafa zan cigaba da yafe masa yana cigaba da cin amanata ba hasana kawai dan ya kasance danuwa sai ya dinga abinda bai dace ba ,"wannan shine karo na karshe da zan sake kuskuren maidashi matsayinsa "tana gama fadar haka ta mike ta shige dakinta ."
shiru sukai gabadaya cikin tsananin tashin hankali kafin ahankali aunty hasana ta kalli bayanta"kayi hauka ne yaya ?”me yasa ka bari ta fahimci wani abu ?”yanzu me kake tunanin zai faru ?”Kiyi shiru ki barni naji da abinda nake ji na rigada nayi kuskure bani da kuma abinda zanyi kowa nayi kuskure ko ba haka ba ?yanzu yadda zan samu ta sauko kawai zanyi dan bazan ta'ba yarda da hukuncinta ba idan ba haka ba sai dai afito araba gadon sadam kowa ya kama gabansa karshenta ma na mallaki kamfani tunda ni nmj ne cike da tsoro Aunty hsssna take kallonsa har sanda ya juya ya fita daga parlour'n ."
Shiru baba qarami yayi zaune a parlour'nsa sanye da jallabiya fari sol yana tunanin abinda ya faru jiya gabadaya maganganun ATA yana sake zurfafa tunaninsa har sanda matarsa ta qaraso rike da cup din tea ta zauna kusa dashi "ba dai kana nan har yanzu kana tunanin abinda ya faru jiya ba ?ya juyo ya kalleta bazaki fahimci irin zafin da nake ji acikin zuciyata ba “wai dan damuwa na yana son ya zama tamkar ma Kiyi a wurina wannan abu na min ciwo matuka shi sam bazaa fad'a masa magana yayi aiki dashi ba ban san ina zulai ta samo wannan yaron ba idan ance ga abinda zaiyi shi kuma yace ga abinda yake so shi sam baa isa dashi ba . yaro kamar wanj sheidan gashi uwarsa bata ganin laifinsa "karka fadi haka ta mika masa cup din tea data shigo masa dashi "tabbas Adam bai kyauta ba kuma yana da taurin kai amman kuma zulai na kokari akan taga ya sauka akan wannan tsarin nasa wallahi ko jiya ba qaramin bude masa wuta tayi ba kuma bata goyi bayansa ba akan abinda yayi amman kasan wannann yaron yasan Kan business sosai “nasan haka “.
“Kasan haka amman me yasa kake jin haushinsa akan komai ?”to shi me bazai tsaya akan tsarinmu ba? abinda yake yi ba daidai bane cin amana ne "duk fa abinda kake tunani akansa ba haka bane kuna son cigaba kamfani Adam ma haka koma nace yafi ku kuma nasan komai yayi yayi dan cigaba kamfani ne matsalar dai ta sultan ce ya kamata ka fahimci haka dan ni bana bayan karya ,Eh na yarda da haka amman shi wannan business din baya bukatar mutun yayisa shi kadai tunda ba haka aka fara ba tun mahaifinsa na raye komai tare akeyi kuma yasan da haka me yasa zai dawo daga baya yayi haka dole nasan yayi haka ne da wata manufa sanin manufar ya rage mana kada yayi abinda yayanmu zasu shiga damuwa ".ya kamata kasan wani abu Adam bazai ta'ba barin wani mummunar abu ya same kamfani ba “Ke yanzu kina ganin abinda yayi daidai ne ?”
“Aa ni bance haka ba san nasan kuskure ne yayi business din cikin sirri batare da sanin kowa ba hakan ya sabawa dokar kmafani amman kai kuma kayi over react jiya sai mahaifiyarsa ta dauka saboda danka kayi haka, amman fa kasani Adam ya sadaukar da komai nashi dan yaga kamfaninan ya tsaya da kafafunsa kuma kai kasani nasani dan saboda muni ne gbdy yake yin haka ,da dan ta sauran ne da yanzu babu wannan kamfanin kawai dai ni nasan bazai yi komai ba kuma bashi da wata manufa akan haka kamata yayi ka zaunar dashi kayi masa bayani yadda kake son ya dinga tafiyar da komai ,yau ko dan daka haifa sai kabi shi a hankali bare dan da ba naka ba, amman kai duk kuskuren da yayi sai kace acikin mutane zaka masa mgn to me yasa shima bazai dinga maka kallon makiyinsa ba ?"
“Ina son ka yarda wannan kamfanin ya samu cigaba ne saboda shi idan ma baka yarda a fili ba ka yarda da hakan acikin zuciyarka kuma kowa yasan hakan yau da zai cire hannunsa ya tattara hankalinsa akan nashi kamfanin komai zai iya faruwa dan acikin yaran nan babu wanda zai iya da kamfani ka yarda ko karka yarda yana cire hannunsa kowa sai yasha wahala acikin kamfanina nan "yanzu ni me zanyi kenan yaron nan fa ya rigada ya gama rainani ?
“abinda zakayi yanzu idan yayi maka laifi ka zaunar dashi Kmr danka ka fahimtar dashi kagani idan bazai maka biyayya ba, kayi kuma tunanin abinda na fad'a, kawai ka kasa tsayawa ne ka fahimcesa saboda abinda ya faru .”ka cire son rai idirs adam yaron kirki ne dan da zaayi alfahari dashi ne fiyye da kowa acikin family .”
“kuma nagartarsa yasa kake son had’a aurensa da hindu .”da lokacin da yace bai sonta ka hakura da yanzu komai yana tafiya daidai daka tsira da mutuncinka ,sannan diyarmu tana tare damu amman ka dinga biye mata kana karfafa mata gwiwa har tayi yunkurin kashe maryama wanda hakan yasa aka samu damar daura mata laifin da ba nata ba yanzu wa gari ya waya ?”wallahi mu dinga cire son zuciya muna fadawa kanmu gasky ka duba lamarin nuzla da mahaifinta ya biye mata da yanzu an ta’ba daya goma bata gyaru ba amamn kai ka dinga biyewa hindu so hauka ne da zatai yunkurin kashe yar mutane ?”ai duk sharrin daaka bita dashi daidai ne ni na wuce amamn ka zauan kayi nazarin maganata da kyau wannna tashin hankalin babu abinda zai haifar sai qarin kiyayya wallahi sam bakayi wa mahaifin adam adalci ba dan nasa kwaya daya zaka maidashi makiyinka abinda shi bazai ta’ba yi maka ba kenan .”tana gama fadar hk ta juya ta kama gabanta baba qarami yabi bayanta da kallo ” daman ita haka zuciyarta take sam bata goyon bayan karya koda kuwa akan kanta ne kuma tabbas yasan gsky ta fad'a masa sai dai me zai yi yanzu ?” ya cigaba da zama a wajen yana tunani maganganunta."
Mmn Sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 27
Gabad'ayansu a tsaye suke acikin office dinsu fuskarsu d'auke da murnar samun nasarar da sukai
a jiya inda madam some ta zagayo ta tsaya kusa da maryama tare da dafa kafad'anta tace "duk wannan cigaba mun samu ne saboda ke . maryama ta saki kyakkyawan murmushi wanda yayi matuqar bayana kyawunta sannan tace " karki ce saboda ni ,nasarar gabadayanmu ce, kuma kowa acikinmu tayi kokari .
"kowance daga cikinmu ta cancacin yabo na mussa man tunda tare mukayi, wannan cigabanmu ne gbdy. ". sukai murmushin jin dadi suna sake yaba mata "amman fa duk da haka kin cancanci a miki ban girma ,kuma kinsan wani abu ?maryama ta girgiza mata kai tana cizan lip's dinta na qasa . "yanzu gbdy a kamfaninmu kece sama da kowa kuma kece wacce tafi kowa iya tsara zane mai d'aukar hankali you're the best maryama ."
"maryama ta sake yin murmushi batare da tace uffan ba ."sultana dake zaune tunda suka soma maganar bata ce komai ba sakamakon jin haushin babu ita ciki presentation din , sai dai aranta tace "in sha allahu wannan dariyar da kike yi sai tazame miki damuwa arayuwarki .
Ahankali yusura tayi taku ta nufo inda maryama take tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tace "ai sani ne bakuyi ba wannan nasarar ba komai bace a wajen maryama ,ai nasara a koda yaushe tana biye daita ,duk abinda tasa gaba sai tayi nasara, ba akan aiki ba kawai , ko akan karatu haka take akwaita da kwakwaluwa ko lokacin da muke karatu first class take d'auka ita din yar baiwa ce "karki manta ni din marainiya ce ta gaskiya tun da na bud'e idanuna na ganni acikin maraicin kinsani mahaifina ya rasu tun ina yarinya kakata data rungumi maraicinmu da kyau take nuna mana qauna muraran sai dai itama bamuyi tsawon rayuwa daita ba ta rasu kinga babu yadda zanyi dole na jajirce nayi karatu "duk da haka maryama ke din yar baiwa ce ,"kunga mu bar mgnr haka muyi aikin dake gabanmu kafin mr ata ya shigo ya fara rikita mana lissafi ". inji cewar maryama ."gabad'ayansu sukai dariya tare koma mazauninsu kowacce ta soma aikin dake gabanta .”
Alamun kira ne ya shigo wayar maryama adaidai lokacin da take qoqarin zama ta kai kallonta ga wayar tana duba number dake yawo a screen din wayar "number da ake yawon kiranta dashi ne wanda ta d'auka ko sultan ne sai dai daga baya ta fahimci bashi bane "dan ta nemi numbersa taga ba iri daya bace, ta d'aga kiran tare da yin shiru daga can bangaren ma shiru akayi ana sauke mata numfashi acikin kunnenta dan tana jin sautin saukarsu ahankali ta fara taku ta nufi kofar fita daga cikin office din yayinda sultana ta zuba ma bayanta ido ganin yadda take bada step tana rausaya abun burgewa yarinyar tana da shep na d'aukar hankali ,ba lallai kowani nmj ya ganta ya iya hadiye miyonsa akanta ba".maryama ta numfashi kana ta cire wayar a kunneta ta duba har lokacin mai shi yana kan layi sai dai babu alamun wannan saukar numfashi muryarta can kasan makoshi tace "hello !sai dai shiru taji babu amsa .
"hello wake magana? "ta sake yin mgn still dai shiru ne ya biyo baya kusan second biyar babu alamun zaayi magana dan haka tayi disconnecting din kiran ta nufo office tana tunanin kiranta daakayi mata kwanakin uku da suka wuce akace mata daga office ne wai tazo da wuri bayan tazo din kuma taji shiru bata ga kowa ba sai mr ata wanda tayi imani ba muryarsa bane ,to waye ya kirata ?"waye wannan da yake son dagula mata lissafi ?"ta furta a kasan ranta tare da samun guri ta zauna ta kasa aiwatar da komai tana sake zurfafa tunaninta lallai ya kamata ta nemi mai wannan number da yake kiranta taji dalilinsa na kira wayarta yana damun rayuwarta ."
Ahankali tai dealing number a qaramar wayarta ta shiga neman layin sai dai ba'a d'aga ba tana cikin wannan halin mr ATA ya shigo office din yayinda kwayar idanunshi ke kanta sai dai ganin hankalinta na kan wayarta yasa shi d'auke idanunshi akanta ya soma mgn a natse akan qokarin da sukai jiya "naji dadi sosai da qoqarinku na jiya na jinjiwa kokarinku "sir ai ina tunanin maryama ce ta cancanci haka,dan gsky ta cancanci jinjina har ma da especially thanks ".inji cewar madam some "ta fad'a tana murmushin farinciki .”
asukwane ya kalli inda take zaune inda tayi busy sosai wajen bincike layin daake damunta dashi a truecaller tana son taga da wani suna akayi registrater layin sai dai wani birkitaccen suna ta gani ."mr ata yayi shiru yana kallonta a tsanake yana nazarinta dan tunda ya shigo ya soma magana ya fahimci bata tare dashi,haka hankalinta yana wani guri dabam ya cigaba da kallonta kafin a hankali yayi taku biyu ya dawo kusa daita sosai yana kallon cikin wayar dake rike a hannunta still dai bata maida hankalinta garesa ba." abinda yafi tsana kenan daga gareta ta ganshi amman tayi kamar bata gansa ba aranshi yace ko number wa take kira hk "?amman a zahiri muryarsa a kausashe yace "some ke kinfi kowa sani ina bawa wad'an da kad'ai suka d'auki aikinsu da mahimanci ne lokacina,yayinda ita wannan macece da bata bawa aikinta mahimanci any way kizo kisame a