Showing 162001 words to 165000 words out of 182919 words

Chapter 55 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

378

sake kallon fuskarta da kyau sai ma yaga kamar yasan fuskar ko kuma yace ya ta’ba ganin mai yanayin irin fuskar .”




Shiru yayi yana nazarin fuskar sosai amamn ganin ba abinda ya kawo shi kenan ba yayi qoqarin qawar da hakan acikin ransa ,sai dai aransa yana mamaki yadda yatsunta hannu dana qafa yayi kama dana sweetheart iska ya feasar yace “ kawai halittar yatsunsu ne ya zama iri d’aya bayan sun gaisa daita umma ta bukaci mb ya sake yin magana agaban aunty bai yi mutsu ba yabi umarnin umma yana dasa aya mr ata ya soma magana kanshi a kasa cike da nadama “ kuyi hakuri da abinda ya faru idan zaku d’aura laifin ku daura laifin akaina domin ni ne mai laifi if nayi shishigi acikin rayuwarta da duk hakan bata faru ba .”yana gama fadar haka yayi shiru yana jiran yaji abinda zasu ce.”numfashi umma ta sauke sannan ta gyara zamanta tace “duk na fahimceku sannna kai ma baka da laifi haka Allah ya qaddaro bawa kuma bai isa ya canza qaddararsa ba Allah yasa mu dace duniya da lahira “haka ne sai batu na gaba naji mryam tace ta daina aiki damu ?
“kwarai kuwa haka tace ammn bisa tsarinta ne ban sani ba ko dan mahaifiyarta tace ta fito da mijin aure nan da two month ne yasa ta yankewa kanta wannan hukunci bansani ba, amman kuma aganina hakan da tayi shine daidai agaremu gbdy domin tsare mutuncinta da kuma namu,duk da ina da yarda da kuma yakinin maryama ba mutuniyar banza bace a gabana aka haifeta in fact ma nice nayi mata tarbiya nasanta ciki da bai macece data san ciwon kanta duk dai ba’a sheidar d’an yau amamn maryama she’s the best kuma ina mata kyakkwan zato .”umma fad’a haka tana tsaresa da ido domin son gano wani abu atattare dashi ita dai tun bata ganshi azahiri ba take ma maryama shaawar aurensa bare yanzu data ganshi Allah yasa hasashenta ya zamo gaskiya mutumin son maryama yake kuma da aure .”



shiru adamcy yayi yana kallon umma da aunty wacce aka kira da mahaifiyar maryama yana tunain yadda gabad’aya take son rayuwar diyarta ta lalace idan ba haka ba mai zai sa dan mutun yayi kuskure kankani ace ya fito da mijin aure nan da wata biyu ba’a jin tsoron abinda zai biyo bayan auren ,” nasan kuna da gaskiya akan hukuncinku a matsayinku na iyayenta sai dai ina jin kmar ni ne na aikata laifin ita kuma ta dauki hukuncin mai tsanani .”ya fad’a yana furzar da numfashi sanan ya cigaba da magana cike da natsuwa da kamala “nasan ko ni ne naga diyata a wannan yanayin zan yi iyakacin bakin qoqarina na kare diyata amman bata hanyar tillasta mata ta fito da mijin aure acikin tsukukun lokaci nan ba saboda yadda rayuwar nan ta zama yanzu .”
shiru sukai gabad’aya suna sauraronsa da kunnen baseera “nasan abinda ya faru ba daidai bane amman kuma wannan hukuncin da kuka yanke mata yayi mata tsauri dayawa a matsayinta na diya mace mai qaranci shekaru nasan babu wanda yake son yaga rayuwar iyalinsa ta tagayyara tunda nake d’aukar masu aiki ban ta’ba d’aukar mai aiki irinta mai tattare da basera da kamaun kai ba, wallahi na yarda kuma na amince kunyi qoqri sosai akan tarbiyarta .”


wani sanyayen numafshi aunty ta sauke tana jin natsuwa acikin zuciyarta karon farko data gansa sai dai taji natsuwa dashi ,”tsannain yadda na damu na tsanata bincike akan abinda ya faru ina son na gano wanda ya d’aukemu hoto kuma dole zan gano kuma dole zai amshi hukuncinsa dan ba dan maryama aka yi wanan tozarcin ba saboda ni ne ,ni ake son tozartawa ba ita ba .duk suka jinjina kai ya lashi lips dinsa ya dan kalli inda maryama take tsaye tana wasa da yatsun hannunta sannan ya d’auke idanunshi ,ya tsurawa umma da aunty ido kafin ahankali maganarsa ta fito “ina rokon alfaram ku bar maryama ta cigaba da aiki tare dani nayi maku alqawarin zan kare mata mutuncinta ,zan kula maku daita zan tsaya mata km zan iya zuwa kowani irin mataki akanta nasan zaku yi tunanin ina da son kaina dawa wallahi ba haka bane ita kanta bazata cigaba da rayuwa mai dadi ba kasancewar tana son aikinta.”



“haka ne sai dai wannna hukuncinta ne ba namu ba itace bata bukatar cigaba da aiki “inji cewar umma “umma ki bar maganarta fatana ku bani dama ni zan mata magana ta yadda zata dawo aiki .”
duk suka yi shiru suka kasa cewa komai umma ta kalli maryama taga tana girgiza mata kai alamun karsu yarda karaf idanun mr ata ya sauka akanta da sauri tayi kasa da kanta tana jin wani irin mummu nar fad’a uwar gaba .”Mb ma bai yi sanya ba ya fuskanci wacce akace itace mahaifiyar maryama yace “aunty kiyi hakuri munyi miki alqawarin babu abinda zai sameta da izinin Allah duk abinda ya sameta ki d’auki duk matakin da yayi miki dadi akan mu.” numfashi aunty ta sauke ta kalli ata dake zaune shiru ,ta waiga ta kalli umma sannan tace duk naji bayaninku sai dai ni bani da abinda zance sai abinda umma tace idan ta yarda ta amince shikenan idan kuma bata amince ba sai ku hakura ,sai batun aure wannan kam bazan janye maganata ba bawai na gaji da zamanta haka bane ,amamn ta fito da miji dan aure shine darajar duk wata diya mace “ku yarda dani bazan ta’ba cutar da maryama ba “shikenan .”inji cewar umma “mun gode sosai shima mijin nan kusa zata samu da iznin Allah koma nace ta samu “wani irin kallo ata yayi masa” mb ya hararesa yana fuskantar umma inda itama umman cewa tayi “ shikenan Allah ya shige mana gaba amamn kuyi magana daita idan ta yarda babu matsala allah yasa haka ne abinda yafi zama alkhairi agaremu.”Umma na gama fadar haka ta mike auny ma ta mike tai masu sallama ta fice haka ma umma ta shige d’akinta mb ma ya yunkura ya mike tsaye yace “bari naje na jiraka a mota “.


adamcy ya gyad’a masa Kai ya fice ya barsu parlour’n ya saura daga ata sai maryama dake tsaye shiru taki zama har kusan mintuna goma tana tsaye daga gefensa on expecting maryama taji ya fixgota zuwa gefen jikinsa saurin d’auke numfashi tayi sannna ta waigo a gigice tana kallonsa cike da matsanancin tsoro.” iskar bakinsa da hucin numafshin ya dinga sauka a gefen fuskarta tayi saurin lumshe ido ahankali ya dawo daita ta gabansa still tana kwnace ajikinsa yayi mata kyakkyawan rikon da bazata iya kwacewa ba ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma rad’a mata magana cikin sanyayyar murya shi mai tsananin kashe jiki da tsuma zuciyar wanda akayi dominsa “maryama ni zaki wa butulci ?” wani bugu qirjinta yayi yayinda jikinta ya d’auki rawa “ina kallonki kina girgizawa umma kai alamun karsu yarda ki sani bazaki ta’ba iya gujewa adam ba domin shi din mai nasara ne
Duk abinda yasa a gaba sai yaga qarashnsa kuma duk abinda yake bukata sai ya zama mallakinsa duk inda nake dole ki kasance anan bare a halin yanzu da zuciyata take cikin garari “inna lillahi! ta furta a kasan zuciyarta tsigar jikinta na mikewa “.


Ya fesa mata iskan bakinsa “bama haka ba har cikin zuciyata bana son yin nesa dake zan kulawar ummanki da auntynki ke.” yayi maganar yana sake damke jikinta dake rawa kamar mazari saboda tsananin tsoro “zuciyata na tsananin jin tausayinki bazan bar wani abu ya sameki ba ,addu’at da fatana Allah ya bani ikon cika alaqawa rin dana d’aukar masu ,sosai ya sake janyota jikinsa ta shige masa wanda hakan yayi mugun mugun d’aga hankalinta yanzu fa ya gama magana zai kula daita”kenan irin wannan kula war zai mata ?”muddin irin tace gsky bazata ta’ba kasancewa dashi ba ,ya sake Kai bakinsa daidai kunneta “ance baza’a d’aga miki qafa ba lallai sai kin fitar da miji aure “?ta lumshe masa ido tana sauke numfashi dan wani iri take ji a gabad’aya ilahirin jikinta “.ya sake sauke mata numfashin bakinsa a kunnenta “kinsan na ta’ba miki mgn akan ya dace kiyi aure? “muryarta cike da in ina tace “eh zanyi qoqarin na fitar da miji kafin lokacin da aunty ta bani “kenan kina da Wanda kike so ?”bani dashi amman zan nemo “zaki nemo ki auri wanda bakya so ?”to zanyi dole zan bi umarnin mahaifiyata ta qarasa maganar hawaye na cika mata ido yayi shiru na second biyu sannan ya cigaba da magana “tunda nemo mijin zakiyi to ki aureni ”




Mmn Sudais💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


45


zaro idanuwa maryama tayi jin furucinsa”tunda nemo miji zaki yi to ki aureni”ta maimaitawa kanta furucinsa na qarshe mai cike da tsarkakki ya da shiga tashin hankali,kai tsaye mgnrsa ta ta’ba kwakwaluwarta sannan ta samu kyakkwan mazauni a zuciyarta ,sai dai maganar tayi mugun gigitata ahankali ta kai hannunta ta murza idanuwanta domin tabbatarwa kanta gskiya ne ko kuwa mafarki take,bata gasganta a zahiri taji ya fad’i kalmar ba sai data d’an ciza yatsanta taji wani irin rad’adi sannan ta tabbatarwa kanta da shi din ne yayi maganar“.a matukar gigice take kallonsa hannuwansa duka zagaye da kungunta ya mugun tsareta da tsumammun idanunshi tamkar bashi yayi furucin ba “.



“ban ta’ba expecting ko da wasa irin wannan mganar zata fito daga bakinka ba ,plese sir can you say what you said again Ina son na sake tabbatar da naji abinda ka fad’a da kyau kuskure ne, ko kuwa da gaske ka furta wanan kalmar agareni ”tayi maganar jikinta na sake d’aukar rawa tamkar mazari ahankali ya lumshe tsumamun idanunshi tare da motsa lip’s dinsa “nace muddin kinsan baki da wanda kike so wallahi ni a shirye nake zan aureki.”sake ware idanunwanta tayi tana mai fuskantarshi sosai tasan ba da wasa yayi maganar ba tunda gashi har ya rantse .”
”maryama !”
Ya kira sunanta wanda yasa tsigar jikinta suka mike yrrrrr “ki aureni .”ya sake share mata tantamar dake damunta, bata san lokacin da ta saki murmushin yake ba tare da girgiza masa kai.”jikinta na rawa ta fara qoqarin zare jikinta daga nashi ya sake riketa da kyau ta sake girgiza masa kai a sanyaye alamun ya sakar mata jiki “.



“ki natsu maryama ki bani amsa zaki aureni ?”
Wannan karon da sauri ta girgiza masa tana waigen bayanta.” Sosai tayi kasa da muryarta
“ dan Allah sir ka sakar min jiki kar ummah ta fito ta ganmu haka “kinsan Allah ki bud’e baki ki amsa min zaki aureni ko a’a if not anan zan kwana.” “what !”ta furta a rud’e hankalinta na sake tashi ya d’age girarsa d’aya alamun”eh!”tayi Imani zai iya aikata abinda ya fad’a din dan haka cike da karkarwa tace “Ka kwana anan akan me zaka kwana anan ?”dan Allah sir Ina rokanka tare da girmamawa ka tashi ka tafi gidanka gun matar ka,dan wallahi idan ka qara wasu mintuna anan zan iya had’iyar zuciya .”tayi maganar tana sake waiga bayanta .”



gyara zama yayi sosai kamar yana parlour’sa ko na mami tare da sake mata riko mai kyau wanda ko maza biyu sun qaru akanta bazata iya kwace wa a hannunsa ba “dan girman Allah sir ka tashi ka tafi gidanka ka rufa min asiri Ina ni ina aurenka zan dai samu takala daidaini na aura …”maryama ta fad’a cikin marai raicewar murya tamkar zata fashe masa da kuka .”ganin idan batayi wani abu ba umma zata iya fitowa ta gansu haka idan kuwa hakan ta faru ta shiga ukunta dan bata san da wani ido zata cigaba da kallon umma ba ,idan tace abinda ya faru a hoto kuskure ne wannan dake faruwa yanzu fa “?.
a wani matsaya za’a kirasa dashi ?”dan haka cike da tashin hankali ta fara masa alamun kuka domin tasan shine kawai mafutar da zata kubutar daita daga hannunsa .”



ahankali ta cigaba da rokonsa tare da mutsumutsun kwacewa daga jikinsa tana furta masa kalmar” ka rufa min asiri idan umma ta fito ban san da wani kalma zan kare kaina ba .”
ganin haka yasa ya zare hannunwansa ajikinta ta mike da sauri tana sauke numfashi tmkr wacce tayi gudun tsere .”ya gyara zamansa sosai tare da jingina jikinsa da kujerar da yake zaune yayinda tsamammun idanunshi wad’an da suka fara canza kala ne tsaye a kanta, ya mugun tsura mata ido sai dai fuskar nan tashi a had’e take kwata kwata babu wani alamun annuri “kina rikon na rufa miki asiri kmr wanda zai yi wani abu dake byn taimakonki zanyi .“cewa nayi kawai ki aureni ba cewa nayi zan kwanta a mararki ba .”yayi maganar tsumammun idanunshi kyar acikin kwayoyin idanuwanta ba kunya ba alkunya ko alamun yaji nauyin fitowar kalmar daga bakinsa bai yi ba .”



nan da nan maryama ta qara shiga tashin hankali sai dai ta had’e fuskarta dan kar ma ya sake samun damar sake furta mata wata maganar iskanci dan ta fahimci ba kunya garesa ba duk abinda yaga dama shi yake yi ,haka duk mgnr datai masa dadi yake fad’awa mutun “.ni zan wuce ki fara shirin zuwa aiki monday “da sauri tace “nifa na fad’a maka babu wani aiki da zan cigaba da zuwa na hakura da aiki nan zan cigaba da zama a gida har zuwa lokacin da Allah zai fito min da miji “ki bar wannan maganr dan bazaki samu wani miji kina kunshe a gida ba , ni kuma da nace zan taimaka miki kince baki sona dan haka ki shirye ki fara zuwa aiki dan zai fiye miki samun kwanciyar hankali …..”



“nifa babu wani aiki da ..”wani mugun kallo ya d’auketa dashi wanda yasa da sauri ta datse harshenta zuciyarta na wani irin bugawa da sauri sauri .”anatse ya yunkura ya mike tsaye bisa qafafunsa yayi taku biyu ya tsaya a gabanta yana tura hannunwansa duka cikin aljihunsa .”amatukar firgice take kallonsa yayinda qamshin turarensa ya dinga Kai wa hancinta ziyara yana kashe masa sansar jiki lumshe idanunta tayi kamar mai jin bacci dan gabadaya yau din sai take ganin ya sake sauya mata daga mr ata din datasani zuwa wani mutun dabam “yaushe muka fara haka dake ?”tayi shir tare da sunkuyar da kanta tana Jin wata irin fad’uwar gaba mai qarfi from no where na shigarta wanda bata ta’ba jin irinsa ba a tun tsawon rayuwarta.”



“wato dan taji zai taimaka mata ya aureta shine har ta fara rainashi kenan ?”sosai tayi kasa da kanta dan bazata iya kallon fuskarsa ba ,sai dai jikinta wani irin kyarma yake tmkr mazari sakamakon idanunshi dake yawo a sansar jikinta .” lumshe idanunshi yayi na second biyu sannan ya bud’e su fes akanta ,sosai yaji zafin abinda tayi masa bai san dalili ba yaji ya d’aura maganartata acikin zuciyarsa daram sai dai bazai yarda tayi tasiri ba “muryarsa a kasalance ta fito
“ ki san Allah muddin banganki AGC ranar monday ba kullum sai kin gani a gidan nan kuma abinda kike gudun faruwarsa ne zai dinga faruwa dan bazan d’aga miki kafa ba .”ya qarasa mgnr batare da yasan ya fad’a haka ba kawai dai ya tsinci bakinsa ne da maganar “.



lumshe idanunta tayi tana mai sake shiga tashin hankali mai tsanani ,muryata can kasan makoshi tace “ai sai ka zo ka sani dole sai naje .”ya sake matsota yana shafa gefen fuskarta tayi saurin matsawa baya da sauri ya cafko tsintsi yar hannunta cikin nashi yana murzawa,kwayoyin idanunshi cikin nata yace “mryama speek loud !“.Ina son naji abinda kika fad’a yanzu “yayi mgnr yana sake murza tsintsiyar hannunta sai dai wannan karon da zafi yayi mata ,da sauri ta shiga girgiza masa kai tana waigen waige gab d’aya a rude take “okay zabi ya rage naki kizo ko karki zo abinda na sani ne bana magana biyu, kuma bazan fara akanki ba ,zabi ya rage naki kizo ko karki zo .”yana gama fad’ar haka ya sakar mata hannu ya juya ya fara tafiya ”


Ahankali tabi bayanshi da kallo yana taku a natse har ya fice daga parlour’n, da sauri ta dawo jikin widow parlour’n ta d’aga labule kad’an tana lekensa yana taku a natse cike da izza tamkar baya son taka kasa “ya salam !”ta fad’a tana dafe qirjinta da taji yayi mugun rike mata “.
maryama ta kasa matsawa daga jikin window tana tariyo abinda ya faru a tsakaninsu yanzu,.”duk maganganunsa babu wanda ta manta domin kuwa sun zauna mata daram kamar hadda acikin kwakwaluwarta sannan sunyi mugun tasiri a kwakwaluwarta har suna son suyi tasiri a gangar jikinta da zuciyarta .”ya rab meke shirin faruwa dani ne?mai yasa mr ata zai ce na auresa ?”me yasa nake Jin kamar ana zarar raina a duk sanda yake tare dani ?”shiru tayi tana sake nazarin maganarsa dan ta kasa bawa kanta amsa “anya mr ata ba sonta yake ba kuwa ?” wannan shine tambayar farko da zuciyar maryama ta fara yiwa kwakwaluwarta “kuma tambayar ta daki brain dinta sannan ta wuce har cikin zuciyarta “yes yes !! kamar fa alamunsa ya nuna haka!” zuciyarta ta bata amsa da hakan ta sake dafe qirjinta sosai .”


Ahankali taji tamkar ta kunno wa kanta wani emotion ne da take qoqarin dannewa acikin zuciyarta nan take taji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login