Showing 138001 words to 141000 words out of 182919 words
mayafinta tana goge hawayen dake fita daga cikin kwarnin idanunta ganin hawaye take zubarwa hakan ya sake kunno wutar damuwarsa”oh my goodness god !”yanzu menene abun kuka kuma ?” ya furta a fili yana mai runtse tsumammun idanunshi tare da Jin wani irin tausayinta na ratsa tsantsar jikinsa “why zanji tausayinta bayan ni ne abun tausayi? ya furta yana jan tsaki sannan ya Kai hannunsa ya dafe saman goshinsa yana murzawa yana jin wani irin zafi da ciwo yayinda zuciyarsa ta dinga tuttukin bakinciki”why maryama!”? “mai yasa baza ki fahimci irin zunzu runtun qaunar da nake miki ba?”kusan minti shabiyar yana tsaye zuciyarsa na jin rad’adin azabar rashin son data furta masa yanzu, kafin ahankali ya bud’e idanunshi ya tsura mata daga inda yake har lokacin tana zaune tana janyo numfashi da kyar.”yayi shiru tare da tura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa yana taku acikin office din ,wani tunani yayi dan haka nan take ya soma taku ahankali ya qaraso zuwa bakin kofar office dinsu ya tsaya tare da rike kugunsa yayinda kwayar idanunshi ke yawo a sansar jikinta ”
“qamshin turarensa daya kawowa hancinta ziyara ne yasa ta sauke wani naunauyen ajiyar zuciya ,sai dai ta qara sunkuyar da kanta qasa tana kallonsa tsaye a bakin kofar shigowa shi bai shigo ciki ba shi bai juya ya wuce ba, wanda hakan yayi sanadiyyar da gaban ta ya dinga dokawa da qarfi gefe guda kuma ta dinga jin wani sabon tashin hankali from know where yana shigarta.” ahankali take hango tahowarsa zuwa inda take zaune gabanta ne ya cigaba da lugud’en bugu tana zaune har ya iso inda take ya tsaya kyam yana kallonta tamkar ranar ya fara ganinta .”
d’ago kanta tayi tana mai mikewa tsaye da sauri tare da goge hawayen idanunta ,bai ce mata uffan ba illa tsumammun idanunshi daya zuba mata tamkar zai cinyeta wanda yasa nan take numfashinta ya dinga sauka da sauri sauri ta tsarke yatsun hannunta cikin juna tana sake jin mummunar fad’uwar gaba mai tsanani, bata san dalili ba amman kwata kwata bata son ganin yanayinsa haka domin yanayi ne dake matukar d’aga mata hankali da tsorata zuciya da gangar jikinta.”
tsurawa juna ido sukai na second goma kafin ahankali ata ya janye kwayar idanunshi akanta yana mai shafa sumar kanshi ,wani abu yaji yana tsarga masa tun daga tsakiyar kanshi har zuwa yatsun qafafun sa,ganin har loakcin kuka take wanda shi aganinsa shi ya kamaci yayi mata kuka saka makon mahaukacin soyayyarta dake huda duk wani sansar na jikinsa .”cikin wani irin sauri zuciyarsa yake bugawa kamar zata fito daga cikin qirjinsa nan take tausayin kanshi ya kama shi bai san sanda ya buga mata wani razanannen tsawa tare da furta “enough maryama !” nan take kukan da take ya tsaya cak sai shesheka “bana son jin sautin sheshekar kukan !”nan take shima ta had’iye jikinta na wani irin rawa, yanayinsa ya qara mata jin tsorasa “. matsota yayi sosai sukai mugun daf da juna da sauri ta d’auke numfa shi ,da zai qara taku guda tak to lallai zasu had’e cikin juna “maryama !”ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya mai matuqar ratsa zuciya “kasa amsawa tayi ila ta kame jikinta waje d’aya tana mai sake sunkuyar da kanta had’e da tattaro jarumta ta sanyawa jikinta“I don’t want to see your tears .”da sauri ta d’ago kanta ,a natse ta zuba masa shayayyun idanunta still akwai ruwan hawaye acikinsu “ki goge hawayen nan ki kuma saki fuskarki .” ido cikin ido take kallonta ko kifta idanunta batayi,shima bangaresna kallonta yake yana faman busa mata hucin numfashinsa.”
Ta dinga jin kamar ta barshi ta kama gabanta amman kuma Tana tsananin jin tsoron abinda zai biyo baya dan a kallon da take masa zai iya aikata komai “smile !” ta jiyo fitowar sautin daga bakinsa.a d’an rikice take kallonsa batare da tayi abinda ya bukata ba “nace kiyi dariya”! Dan banason ganin wannan yanayin akan fuskarki “gaba daya maryama ta rud’e ta gigice tana kallonsa da sabon mamaki akan fuskarta “nace kiyi dariya !”wannan karon a fusace yayi maganar batasan sanda ta soma murmushin yake ba wanda ya bayyana d’an murmushin a saman lebbansa yayinda idanunshi ke kanta .”
Ganin irin kallon da yake mata yasa ta janye jikinta tana cigaba da murmushin data saka masa sunah “gashi karka kasheni a natse tabi gefensa ta wuce tana taku a natse ,ya tsura ma bayanta ido yana kallonta tana taku ahankali ,wani naunauyen ajiyar zuciya ya sauke kai tsaye office dinsa ta nufa ta duka ta d’auki jakarta ta fito ta nufi hanyar fita, tafiya kad’an tayi ya juyo taga ita yake kallo ido cikin ido suke kallon juna sannan ta
Sake juyawa” mai yasa nasa tayi dariya ?”nasa tayi dariya dan na daina jin damuwa acikin raina amman har yanzu ban daina jin abinda nake ji ba mai kuma zanyi na samu natsuwar zuciya? Ina son naji farinciki amman kuma na rasa samun wannan farinciki what do I want?”ya furta a fili yana Jan tsaki Allah yasa kar yarinyar ta kasheni !ta kasheka ko dai ka kashe kanka da kanka,haka kawai ka zauna kana cutar da kanka a banza numfashi ya sauke da qarfi ya samu waje ya akan kujera ya zauna yana kallon hanyar data bi.”
Ahankali aunty hassana ta fito daga cikin d’akin umma hannunta rike da takardar gidan biredi,adaidai lokacin umma ta shigo dan dama ba fita tayi ba d’akin yaya sadam ta shiga da sauri aunty hasana ta zauna akan kujera tana tura takarda qarqashinta tasa hannunta ta dafe goshinta ,umma ta tsaya tana kallonta kafin ahankali ta qaraso tana cewa“lafiya hasana meke damunki ?wallahi kaina ke min wani irin ciwo shigowa nayi ko zan samu magani a wajenki “okay bari na duba miki ko zaa samu magani wayyo allah kaina kamar zai cire ,umma ta nufi d’akinta da d’an saurinta cikin kankanin lokaci umma ta fito ta tsaya gabanta tana cewa”kar’bi ki sha .” aunty hassana tasa hannun ta amsa tana sauke numfashi da kyar tace “na gode aunty tana qoqarin kai magani bakinta taji umma tace “ki sha maganin idan kin gama sha ki tashi na d’auki takardar da kika saka qarqashinnki.” a matukar tsorace aunty hasana ta tsurawa Umma ido tana kallonta gabanta na faduwa “ki sha maganin ba kanki ke ciwo ba ?
Aunty hassana tai shiru cikin tsananin tashin hankali “idan bazaki sha ba ki mike na d’auki takardar” jikinta a sanyaye ta mike tsaye sai ga takardun gidan biredinsu ,umma tasa hannu ta d’auka “yanzu dake za’a had’a baki a cuceni na yarda na amince dake amman da irin abinda zaki saka min kenan ? kije ke da allah amman karki sake shigowa zuwa inda nake na rantse da ..”da sauri aunty hasaana ta zube kasa tana kuka tun kafin umma ta ida maganarta “dan girman Allah aunty Kiyi hakuri wallahi ba halina bane yaya gali ne ya turo ne ,ki yafe min wallahi bazan sake ba ,ai baki ta’ba kamani da irin wannan halin ba ko tunda muke dake kin ta’ba neman wani abu naki kin rasa?”wannan ma sausauyi ne ,ki yafe min idan kika sake kamani da laifi makamancinsa na yarda ki dauki duk matakin da kika ga dama numfashi umma ta sauke batare da tace komai inda aunty hassana tayita mata kuka tana mata magiya da kyar dai ta samu umma tace ta tashi taje zatai tunani jiki a sanyayye aunty hassana ta mike tsaye ta nufi kofar fita zuciyarta cike da nadamar abinda ta aikata.”
A matuqar gajiye maryama ta shigo bangaren umma bakinta d’auke da sallama sai dai falon shiru babu alamun kowa dan ta shiga d’akin umma bata ganta ba ,sai dai jin alamun saukar ruwa abayi ta fahimci tana ciki ta fito ta shige d’akinta tai wanka tare da yin sallah bayan ta idan ta d’auki wani littafi tana dubawa sai dai ta kasa fahimtar komai ,dan madadin ta fahimci abinda ke cikin littafi sai ma ta shiga nazarin maganar madam some da kuma mganar mr ata da yayi mata a shekanjiya da kuma abinda ya faru a wannin da suka gabata “uhm !ta sauke numfashi da karfi tana cewa “madam some kenan gsky tunaninki akaina sam bai yi ba ta ina zan fara kai kaina cikin halaka ,ni ko sona mr ata yake koni na kamu da sonshi ai sai nasa wuka na raba tsakaninmu bare babu dayan biyu ta fad’a tana sauke numfashi tana zaune ta jiyo sautin muryar umma tana kiran sunanta “maryama! na’am umma ta amsa tare da fitowa ta sameta zaune a natse ta gaishe da umma yayinda umma ta riko hannun maryama tana dubanta kafin ahankali ta mike tsaye tare daita suka shige dakin umma , maryama ta zauna a bakin gado tana duban fuskar umma yayinda umman ta dawo kusa daita tana kallonta tare da dafata tana cewa “ya mai gidanki “yana lafiya da matsalo linsa , umma ban fad’a miki bane ya bawa kowa kyautar mota amman ni ya hanani amman ni bai dameni ba ina neman taimkon Allah ne umma tai shiru tana sauraron maryma har sanda ta dasa aya sannan tace “ amman dai gsky bai kyauta ba ,uhm umma manta da wannan mutumin kullmu maganrsa I don’t like bad behavior in this company ga tarin wulakantani da yake “.
“kawai fa taimako yayi min nayi qoqarin yi masa godiya amamn umma kinga uban wulakancin da mutumin nan yayi min sai kin tausaya min umma tai murmu shi irin nasu na manya kana tace “ai tunda yana iya taimako ai yana da kirki kad’an maryama ta yatsina fuska “ shifa abinda na fahimta yana da miskilanci tare da tarin wulaqanci kuma baya bukatar yayi maka abu kayi masa godiya”banda abunsa to meye acikin kayi ma mutun abu yayi maka godiya .”ni dai abinda zan fad’a miki shine kibi komai ahankali karki zake daywa ,idan mutun yana da irin wannan dabiar kana sanin yadda zaka tafiyar dashi ne,ki kula sosai kiyi duk abinda yake so kinji maryamata” naji umma in sha allahu na gode sosai yauwa diyar albarka allah yayi miki albarka ta amsa da “Ameen.
Mami ce zaune tare da yaranta mata uku aunty shahida,khadija da kuma zabiba yayinda mryam da nana hauwa’u ke zaune a d’akin sun kulle kansu suna zantawa,ahankali aunty shahida tace “alkubus fa kikace mami bayan tsawon shekaru “wallahi shahida ,ni kaina abu yayi matukar bani mamaki tun bayan rasuwar mahaifinku bai sake cinsa ba wanda hakan ya zamo silar da kowa ya daina cinsa acikin gidan nan kawai jiya bayan ya shigo yace shi zai ci nayi matukar mamaki .”gaskiya ne mami dole kiyi mamaki shekarun da yawa fa mami ta numfasa irin nasu na manya tace “kunsan wani abu ?”duk suka tsura mata ido suna sauraronta “ba kuyi tunanin wani abu akansa ba ?”atare suka girgiza mata kai me kike tunani akansa mami ?”inji cewar aunty khadija mami ta bud’e baki da zumar cigaba da magana sai ga ATA ya shigo yana qoqarin wucesu mami tace “yauwa ga adamcy din ma ya shigo ,ahankali ya tsaya yana dubansu “adamcy ka qaraso mana “yau ma nayi maka alkubus kuma nasan zakaji dadinsa fiyye dana jiya dan na jiya anyi aikinsa cikin sauri yau kam a natse akayisa .”
shiru yayi yana kallon fuskar mami dake kwance da tsananin farinciki “adamcy mami ka qaraso ka zauna mana” inji cewar aunty shahida still dai shiru yayi yana sauke numfashi gabad’aya suka tsura masa ido suna jin tsananin qaunar d’an uwansu, jiki a sanyaye ya soma taku sai dai hankalinsa da natsuwarsa baya gurinsu yana ga maryamarsa ahankali har ya qaraso zuwa inda suke inda aunty shahida ta kamo hannunsa ta zaunar dashi a kusa daita “wai kaci alkubus jiya ?”ka tuna da poverty din dady kenan khadija ko kin tuna lokacin da dady yake raye mami kusan kullum sai tai masa alkubus har compotetion ake gurin ci “murmushi aunty khadija tayi tana dubansa inda shi kam hankalinsa baya garesu cigaba da zantawa sukai cikin tsananin farinciki shi kam kasa cigaba da zama yayi acikinsu ya soma qoqarin mikewa adaidai lokacin da aunty shahida tace “a zubo mana muci tare dashi da sauri mami ta shiga kiran masu aikinta yayinda ahankali ATA ya yunkura da kyar ya mike ya haye samansa da idanu suka bishi gbdy yanayinsa ya sake canzawa ba kamar yadda yake abaya ba .”
yana shiga parlour’nsa ya zauna zagwab akan kujerar tare da yin shiru yana zurfafa tunaninsa “ mai yasa zuciyata zata min haka?” bazan ta’ba yarda zuciyata ta kamu da wata soyayya ba. numfashi ya sauke da qarfi yana hura hanci ya rasa dalilin da yasa maganarta ta tsaya masa arai kuma take masa ciwo .ahankali ya kai hannunsa ya ciro flower data siyo masa yana kallon yana jin wani irin tuttukin bakinciki mai had’e da shaukin qaunarta “
yana cikin wannan halin mami ta shigo parlour’n tana kiran sunansa “adamcy nah !kiran sunansa da mami tayi ne ya dawo dashi cikin haiyacinsa yayi sauri ya maida flower ya boye yana dubanta a tsanake “muna cikin tsananin farinciki daka dawo mana da cimar mahaifinka cikin ahlinmu “shiru yayi kawai yana kallonta kafin ahankali mami ta kamo hannun sa cikin nata taso muje kaci acikin yanuwanka bai mata mutsu ba sai dai ya zare hannunsa ya cire yar saman suit dinsa da niktie ya biyota har zuwa parlour’n kasa inda yan’uwansa ke zaune “ta zaunar dashi a tsakiyarsu bai wani ci mai yawa ba ya sake mikewa mami ta kallesa a natse har kayi me “sweetheart kinsani bana son cin abinci mai nauyi jiya ma dai naci ne yana gama fad’ar haka ya haye sama .”
Da misalin qarfe tara na dare da mintuna ashirin a natse ata yake saukowa parlour’n mami wanda yake d’auke da motsin mami dake waya tun kafin ya qaraso ya fahimci yan’uwnasa sun kama gabansu “wannan shawarar taku bazan ce batayi ba ,amman sanin kanki ne zulfa’u kinsan halin d’an naki da ra’ayin kanshi shi din ba kamar kowa bane ,har yanzu ban gama da matslar maryam ba .”wallahi koni abinda yake cikin raina kenan dan zamansa haka ya fara damuna..”guri ya samu ya zauna ya kasa kunnuwansa yana sauraron mami cikin natsuwa wanda zamansa ita ta katse hirar ammi ,ta zuba masa idanun wanta gabad’aya wanda hakan ya tabbatar masa da maganar sa suke cike “sweetheart!”ta zuba masa ido kawai tana saurarensa “ina tunanin next two weeks in sha Allahu nake son na wuce zuwa uk akwai sababin desing da wasu companies ke so na sabuwar shekara akan qarafe manyan motoci daman kuma na baro aikin da dadewa amman ina ganin zani domin a qarasa komai “:Kai kawai mami ke gyada masa cike da alfahari da kuma farinciki irin gwazon da Allah ya bawa d’aya tilo da take dashi Masha Allah Allah yayi maka albarka Allah ya tai maka suna zaune suka jiyo sallamar sultana cike da jin kai .mami ta sauke numfashi tana dubanta cike da tsananin kulawa dan ita kowa nata ne tace “sultana kece a daren nan?”wallahi nice mami ,ta qaraso ta samu waje kusa da ata ta zauna sannan ta gaishe da mami .”
Mami ta amsa tana tamabyarta abida “tana lafiya ta ma ce na gaisheki ina amsawa ya aikin da fatan dai kina jin dadin aiki da yayanki ?”mami ta fad’a tana murmushi “to babu laifi ta fad’a tana dubansa wanda shi ko kallonta bai yi ba dan idanunshi ma na kan tv yana kallon labarai ganin irin kallon da take masa yasa mami ta mike tace “bari na shiga ciki dan da alamun wajen yayanki kikazo?”murmushi sultana tayi .”bayan mami ta shige ciki ta iske maryam tsaye “akwai abinda kike bukata ne ?”maryam ta Kai hannu tana shafa kitson kanta tare da yatsuna fuska “babu abinda take bukata tana dai son ta fita taga muradin zuciyarta ne ganinsa ya fiyye mata komai dake cikin duniyar nan “kinyi shiru maryam !mami ta sake mata magana da kulawa “wai Ina son na sha custard ne “okay bari na kira tabawa tayi miki barta kawai mami zanyi da kaina ta fad’a tana qoqarin ficewa numfashi kawai mami ta sauke .”
tun daga nesa maryam ta hango sultana durkushe a gaban adam dinta tana masa magana gabanta ne yayi wani irin fad’uwa har sai da yar cikinta ta motsa,da sauri ta matso daf dasu ta tsaya adaidai lokacin da sultana ta cigaba da magana “ya adam ina sonka kamar yadda ka sani bansan yadda zanyi da rayuwata ba dan idan ma nace zan hakura da kai tabbas nayiwa kaina karya “nan take maryam ta tsinci kanta da zubar da hawaye tana qoqarin maganin sabuwar maseefar data kunno Kai cikin rayuwarta ga wata maseefar da me zataji? ta furta a fili jikinta na rawa ,yayinda ata yayi shiru yana sauraron sultana shi har kullum yana mamaki matan dake da qarfin zuciyar fad’awa nmj suna son shi “ wallahi da dai na rasaka gara na rasa rayuwata dan zan iya kashe kaina .”Idanunshi ya zuba mata kafin ahankali ya fara magana cikin zafin rai “ ke wai ni sa’an wasanku ne”? yayi maganar cikin tsananin fushi”tunda bazaki iya rayuwa babu ni ba to kije ki kashe kanki dan ko matan duniya sun qare sanin kanki ne ni adam bazan ta’ba kasancewa miji gareki ba ki tashi ki wuce abinda yafi mutuwa ma kije kiyi wannan ba damuwata bace.”
wani sanyayyen numfashi Maryam ta sauke tana gyara tsuyuwarta sultana bata ce masa komai ba har ya gama magana ta sake tsura masa idanunta duk sun cika da kwalla” tasan tabbas abinda ya fad’a din har cikin zuciyarsa ne ahankali tace” kayi hakuri dan allah nasan maganata