Showing 126001 words to 129000 words out of 182919 words

Chapter 43 - Mar'adams Book 3 Hausa Novel Complete

Unknown   

23 Dec 2024

613

ba,haka zalika kin so mutumin da ba kece asalin true love dinsa ba, amman kika zauna kina yaudarar kanki kina cutar da kanki a banza har kika kasa cigaba da rayuwa mai dadi adalilinsa ."



tunda ya soma magana kukanta ya qaru hankalinta ya sake tashi zuciyarta ke qoqarin son amincewa da maganganunsa amman tayi saurin kawar da hakan dan amincewa da hakan ma ganganci né da butulci . "kuka take sosai har da sheshekan tamkar ranta zai fita "wayyo allah ni mryama !"wayyo allah rayuwata ni kuwa wace irin maseefa ce take yawo acikin rayuwata ?"kullum rayuwata cikin jarabawa da tashin hankali take, ahankali ya matso kusa daita tare da kiran sunanta cike da tausayawa ."
"maryama .!"
still dai bata d'ago ba "bazan hanaki kuka ba saboda ya cancaci kiyi kuka fiyye da wanda kikeyi a yanzu so continue crying okay "dan yana da kyau kiyi kukan yarda da amanar da kika bashi na tsawon lokaci so kiyi kuka iya kuka sannan ki dawo ki canza rayuwarki zuwa reality ."sai lokacin ta d'ago shayayyun idanunta da suke cike da ruwan hawaye ta tsura masa tana kallon yadda ya tsareta da nashi idanun yana kallonta cikin tsananin damuwa ahnkl ta motsa lip's dinta dake rawa rawa tace "na.."na kasa fahimtar komai sir bare na fahimci abinda kake nufi dani  a yanzu amman dai ina jin kamar yaya sadam dina yana raye kuma zai dawo gareni sai dai nasan bazai dawo ba ."ta qarasa maganar idanunta na zubar da ruwan hawaye masu rad'adi ".



"shikenan ni da umma da kowa mun rasashi mun yarda mun rasashi sai dai ba zamu ta'ba mantashi arayuwarmu ba most especially ni saboda shi da mahaifiyarsa sun min komai arayuwa tun daga tasowarta har zuwa girmana I never thought I will loose yaya sadam, sai dai mun nemesa sakamakon yarda da zuciyata tayi na cewar yana raye acikin duniyar nan bai mutu ba wanda shine ma dalilin da yasa rayuwata take tsaye a waje d'aya na kasa cigaba da rayuwa kamar kowa a kullum ina ganin kamar zai dawo ne .""maryama ki cire duk wannan tunanin arayuwarki da zuciyarki domin kuwa imagenation ne kawai kikeyi wannan mutumin ba zai dawo ba kina 'bata lokacinki da rayuwar ki ne kawai a banza akan mutumin da bai d'aukeki da matsayin komai ba ".wai mai yasa bazaka fahimci me nake ji araina ba ?"mai yasa kake masa kallon mayaudari agareni "? mai yasa kake ganin kamar cewar baya sona ?"
"wallahi da fari ne ya nuna min alamun rashin so amman daga baya ya soni fiyye da tunaninka .wayyo allah yaya sadam shikenan bazai dawo gareni ba ?"shikenan shima na rasashi ?"he wil never come back to me that's why I will never forget him in my heart ,ban sani ba "ban sani ba ko zuwa nan gaba ko zan iya ciresa araina amman for now I don't think sir bana tunanin zan iya raba zuciyata da tunaninsa dan bazan iya rayuwa babu shi ba idan kuma na rayu to tabbas rayuwata zata qare ne akan tunanin yadda na rasashi "ta qarasa maganar tana kai tafukan hannuwanta zuwa fuskarta ."




Shiru mr ata yayi  cikin tsananin tashin hankalin abinda ya gani acikin akwayar idanunta tabbas son mutumin ya hango acikin kwayar idanunta "yaji duniya ta tsya masa cak , hatta numfashinsa dake kai kawo yaji ya tsaya ,yaji kmr kasa ta tsage ya shiga saboda muzantar da yayi ,ahalin yanzu yafi bukatar ta fiyye da komai a rayuwarsa  baya son tana yawon magana akan wannna mutumin gumi ne ya shiga tsaftsafo masa takoina ajikinsa, tsayuwa ne ya soma gagaransa, ahankali ya zura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa tare da juyawa ya fara kai kawo acikin office din yana kallonta da tsumammun idanunshi da sukai jajur suka canza kala tamkar yadda nata idanun sukai yayinda zuciyarsa ke tuttukin bakincikin maganganunta "yana son raba zuciyarta da tunaninsa ,yana son yaji ta furta kalmar tsana a garesa "yana son yaji tace daga yau ta daina son shi ."sai dai har yanzu data san duk abinda ya boye mata ta kasa ciresa a zuciyarta da rayuwarta har ma tana ikirarin bazata rayuwa babu shi ba."




ahankali ya zare hannunsa d'aya daga cikin aljihunsa ya daura akan hannun kujerar dake ajiye abayanta yana tunanin matsayin rayuwarsa idan rayuwarta ta cigaba a haka ,sosai ya zurfafa tunaninsa still dai kwayar idanunshi suna kanta suna aikin kallonta sannan at the same time yana tunanin matakin daya kamata ya d'auka akanta "shikenan shima na rasa shi ?"he wil never come back to me that's why I will never forget him in my heart ban sani ba "ban sani ba ko zuwa nan gaba ko zan iya ciresa araina amman a yanzu bana tunanin zan iya raba zuciyata da tunaninsa dan bazan iya rayuwa babu shi ba ,idan ma rayu rayuwata zata qare ne akan tunanin yadda na rasashi ."wad'an nan kalaman nata sunyi matukar kona masa zuciya."sai dai kallonta kawai ya cigaba da yi tana kuka akan wani bashi ba "ji yayi kamar ya fashe mata da kuka shima ko zuciyarsa zata rage jin rad'ad'in dake tattare daita."



"Hakika  yau din tana cikin ranakun datazo masa da abubuwa da yawa marasa dadi shi da ya d'auki tsawon shekaru yana dakon soyayyarta batayi kukan soyayya dan shi ba take yi dan wani banza can katon mayaudari, ahankali cikin takunsa na izza ya soma taku ya iso inda take zaune sai jin tsayuwar mutun tayi a gabanta sai dai bata d'ago ba dan tasan shine muryarsa cike da matsanancin tashin hankali yace "maryama come with me !" yana gama fad'ar haka ya juya ta d'ago kanta ahankali tabi bayansa da kallo "where are we going sir ?"don't ask me just come "ya fad'a a dan zafafe .bata mike ba sai dai bugun da zuciyarta ke yi ya qaru gabanta ya dinga dukan tara tara, jin alamun bata da niyyar mikewa ya sa ya dawo da baya da baya ya kai lallausan tafin hannunsa ya cafki tsintsinyar hannunta cikin nashi ya soma tafiya daita cikin zafin nama tace "sir ka tsaya ka saurareni ina kuma zaka tafi dani adaidai wannna lokacin ?"ta fad'a a matukar tsorace hawaye na gangaro mata ".



"ai kince bazaki iya rayuwa babu shi ba zan nuna miki hanyar da  zaki samawar zuciyarki salama né "yana gaba tana biye dashi tana sheshekar kuka tana kiran"sorry sir! am so sorry sir dan tun kafin tasan me zai mata taji matsanancin tsoronsa ya mamaye kowace gaba ta gangar jikinta bai tsaya daita a koina ba sai a wani wawakeken fili dake sama na qarshe wanda anan jet dinsa yake saukesa a duk sanda bukatar hakan ta taso yana gama qarasowa tsakiyar filin yayi filinging da hannunta dake rike cikin nasa yana yarfe hannunsa yana furzar da wani huci mai zafi tare da haki yayinda 'bacin ransa ke sake qaruwa "sir akan wani dalili zaka kawo ni ?"ta tambayesa tana sheshekan kuka "ki tsaya da kyau ki fahimceni kince bazaki iya rayuwa babu shi ba okay ?"ta tsura masa kwayar idanunta dake cike da ruwan hawaye "ba dai kina son kashe kanki akan mutumin da bai damu da rayuwar ki ba? ".sir why I are you saying that?"wa ya fad'a maka bai damu dani ba ?"tai masa tamabayr wasu hawaye na turereniyar zubowa ."




"wallahi ya damu dani kuma yana sona dan bazan ta'ba samun mutunmin da yayi min abinda yaya sadam yayi min ba, ya soni alokacin da wasu suka kini "yayi min dukkanin wani hallacci a rayuwata wallahi bazan iya manta shi arayuwata ba i can't never forget him I can't I can't !!"correct I know you can't do without him ba ?" ta gyad'a masa kanta alamun "eh! okay ki sani akwai abinda ya kamata kiyi domin ki kawo ma rayuwarki sauki akanshi "yana gama fad'ar taji ya sureta yayi sama daita nan take ta saki qara mai sautin tare da rud'ewa muryar ta da qarfi ta fito wajen cewa  "Where will you take me to ? dan girman allah ka saukeni duk yadda ta gigice tana masa magiya hakan bai sa ya sauketa ba ,tafiya kad'an yayi daita ya direta da qarfi yana hura hancinsa sannan ya riko yatsun hannunta ya kai kanta daidai inda zata iya hango kasan ma'aikatan ."



sosai take kallon qasan maakatan zuciyarta na wani irin tsinkewa babu zato babu tsamanin taji yace "jump!"ya fad'a hankalinsa a tashe yana sake hura hanci, gabata ne yayi wani irin mugun bugawa da qarfin gaske ta d'ago kanta a matukar gigice tana kallonsa a matukar tsorace tare da cewa "what?"yes wannan shine best solution agareki shine kawai abinda zai kawo miki qarshen kuncin da kike ciki kuma shi zai kawo qarshen rayuwarki "me kake nufi da haka sir?"kin manta kince bazaki iya rayuwa babu shi ba tô shine nake son ki kawo qarshen rayuwarki yanzu tunda bazaki iya manta shi ba "kina zubar da hawayenki a banza bayan Kinsan mutumin nan ya mutu baya raye "wani irin tsoro da matsanancin firgice mr ata yaga ya bayyana akan fuskar maryama "oya jump !"ya sake maimaita mata yana nuna mata qatangar  da yatsun hannunsa "ka fahimceni sir akwai shakuwa ne a tsakanimu koda aure bai shiga tsakninmu ba ni dashi mun taso tare more than 20 yrs kafin batun aure ya shiga tskaninmu shine dalilin da yasa nake jin bazan iya rayuwa babu shi ba ".



"Ai nima shine dalilin da yasa kika ji nace kiyi tsalle ki fad'a qasa ki huta da damuwar dake damunki kowa ma ya huta ki bishi zuwa inda yaje." shiru tayi ta kasa cewa komai tana kallonsa da shayayyun idanunta tana sake jin wani sabon mamakinsa duk da tasan halinsa da saurin fushi da d'aukar abu da zafi amman bata d'auka zai iya kwatata mata yadda zata salwantar da rayuwata ba "why  are you still westing your time maryama jump" ya sake furtawa a karo na uku "ynzu tsakaninka da Allah kana son na hau na fado na kashe kaina "?tayi maganar cike da tashin hankali "kana son na kashe kaina ?"ta sake tamvayarsa cikin muryar kuka taku ya qara ya matso kusa daita tare da cewa "no !"banason ki kashe kanki kawai dai nace ki fad'o ne dan ina son ki cire wannan mutumin aranki ki cigaba da rayuwarki kamar kowa coz life goes on ."



Cigaba da kallonsa take jikinta na wani irin karkarwa"anyway idan kina son ki daina jin radadin rashinsa aranki kina bukatar kiyi kuka  mai tarin yawa da sauti mai qarfi batare da wani ya baki hakuri ko rarrashi ba ."gabanta ne ya bada dammm da qarfin gaske "kiyi kuka  iya kuka maryama ki cire wannan damuwar dake damun rayuwarki "wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki mai wuyar misaltuwa"wai me kake nufi ne ?"babu irin kukan da banyi ba da kuka zai iya sawa na mantashi nayi kuka mai tarin yawa abaya amman bai sa naji zan iya manta shi ba ."maryama !"
ya kira sunanta a fusace jikinsa na wani irin rawa "ki kalleni da kyau ba wasa nake dake ba nace kiyi kuka mai sauti irin wanda baki ta'ba yin irinsa ba zaki ga abinda zai faru bayan kin gama "amman .." listing maryama banason jin komai daga bakinki just cry with sound ki cire ciwon dake damun zuciyarki."
kiyi kuka mai sound zaki rage jin nauyi a qirjin ki "bazan iya wani kuka mai qarfi ba  bayan wanda nake yi a yanzu ba "nace kiyi kuka mai sound  "gsky ni bazan iya wani kuka ba wanda yafi wannan ba ."ta fad'a tana juya wa da sauri zata bar gurin dan a matukar tsorace take dashi dan gani take zai iya d'aukar ya jehota ta sama ta mutu tunda ba imani garesa ba.



da sauri ya biyota tare da riko tsintsiyar hannunta da qarfi wani qara ta saki da qarfi "auch!" cike da zafin zuciya ya juyo daita suka fuskanci juna har suna iya jiyo bugun zukatansu da kuma saukar numfashinsu "ina zaki ?" taji saukar numfashinsa adaidai saitin wuyanta da fuskarta "tambayarki nake ina zaki ?" tayi shiru tana dubansa a tsorace "matsawar kina bukatar zaman  lafiyarki  dani lallai sai kinyi abinda na bukaceki kiyi idan ba haka ba na rantse sai dai mu tabbata anan amman babu inda zaki ,taya zaki kashe kanki a banza "baki san cewar wannan tunanin da wannan tashin hankali zai iya shafar kwakwaluwarki da rayuwarki ba ?"common maryama cry ."
"sir I can't ! ya sake yin  kurkusa daita har babu wani space daya saura  a tsakaninsu wanda hakan yasa numfashinsu  ya gauraye waje d'aya dan sosai suke shakar numfashin juna wani wahalallen numfashi ya sauke yace "kiyi zaki iya kiyi kuka da iyakacin qarfinki maryama wallahi muddin bakiyi ba bazaki samu kwanciyar hankali ba oya one ,two three .." ai yana gama fad'ar 3  ta kamkame jikinta waje d'aya ta soma kuka mai qarfi tun daga qasan zuciyarta kukan ke fitowa da sauti  jikinta na d'aukar rawa kuka take sosai jikinata na cigaba da rawa har qafafuwanta suka kasa d'aukarta bata san sanda ta zube jikinsa ta rungumesa tsam ajikinta sauran kad'an mr ata yayi qasa amman qarfin da yake tattare a jikinsa ya bashi kariya ya tsaya bisa qafafunsa sosai batare daya kai hannunsa jikinta ba."



wani irin sanyi mai tattare da jin dadin samun nasarar da yayi akanta ya shiga bin jini da jijiyo dake aiki a sansar jikinsa lokacin da yaji ta qara kamkame shi ajikinta hakan yasa yaji wani maganadisun soyayyarta na sake shigarsa, yayinda har lokacin tana rungume tsam dashi tana wani irin kuka mai ban tausayi tana qoqarin goge duk wani abinda tasan damuwa ne acikin momery dinta sai daya tabbatar da tayi irin kukan da yake bukata kafin ahankali yasa hannunwansa duka ya zagaye kugunta dashi ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma mata magana cikin wata irin kasalalaliyar murya mai cike da tausayawa "maryama duniya cike take da jarabawa kala kala amman idan kayi imani da Allah ,Allah yana tare da kai ,ki manta komai da duk abinda ya faru a tsakaninki da mutumin nan zaki iya samun madadinsa koma wanda ya fishi arayuwarki, kisani da  kice kika mutu da yanzu yana tare da wata ko nadiya sun cigaba da rayuwarsu daga inda suka tsaya"ki mantashi arayuwarki shi zai bawa wani damar mallakarki ko baki damar mallakar  wani ."



ahankali ya dinga mata magana batare da yace ta daina kuka ba , sosai maryama ta narke ajikinsa ta manta ajikin wanda take kwance inda daddan qamshin turarensa mai sanyi ya dinga shiga hancinta yana kaiwa kwakwaluwarta wani sako na musamman tare da táttaro duk wata natsuwa da
kwanciyar hankali zuwa kwakwaluwa dama gangar jikinta ."sosai zuciyarsu tai nitso cikin wata duniya inda soyayyar maryama ta sake samun kyakkywan mazauni acikin zuciyar mr ata yayinda daga can nesa hasken camera sultana ce ke faman aikin d'aukarsu hoto "bazaki ta'ba samunsa ba maryama ,yadda ban samesa ba kema bazaki ta'ba samunsa ba bayan baki samesa ba kuma kin shigar da kanki cikin matseefar da bazaki iya kwatar kanki ba sai kinyi nadama da danasani arayuwarki, idan kuma kince zaki iya wannan fad'ar lallai zan koyar dake yadda ake dandana dacin mutuwa ."kwanciya maryama tayi lamo ajikin mr ata tana kuka tana shaqar qamshin turarensa , zuban hawayenta yake ji agaban rigarsa dan duk ta 'bata masa gaban rigarsa da ruwan hawaye "tabbas duk maganganunsa gaskiya ne ya kamata ta manta komai kamar yadda kowa yake fad'a mata domin ita din macece bata da wani dogon lokacin da zata bata , wani irin dogon numfashi mr ata ya sauke yana hura mata iskar bakinsa cikin kunnenta inda maryama ta sake shigewa jikinsa yayinda sultana ta zuba masu ido cikin zallar bacin rai ganin yadda yanayin ata ya canza one time acikin kankanin lokaci ."



ahankali mr ata ya soma qoqarin dagota daga yadda ta kwanta a qirjinsa maryama ta sunkuyar da kanta kanta qasa tana mai tsananin jin kunyarsa "am very sorry  sir maryama ta furta  had'e da  juyawa da sauri tana tafiya cike da kunya tamkar bata son taka qasa ya tsurawa bayanta ido most especially tsukakken west dinta wanda ya bawa bombom dinta damar nunawa kad'an"alhamdulillah ya rab ."ya furta a fili sannan ya tura hannunsa d'aya cikin aljihunsa ya biyota da sauri sultana tayi baya daga maboyarta ahankali mr ata ya kamo maryama kasamcewar bata da sauri suka jera kafad'a da kafad'a "bai ce mata komai ba dan ya fahimci kamar a yanzu take jin kunyar irin rungumar datai masa suna qarasa saukowa qasa direbansa da masu tsaronsa suka taso tare da zagayesu  .da kanshi ya bud'e mata murfin mota kamar yadda ya saba mata kuma duk akan idanun sultana kuma batayi sanya ba gurin saurin d'aukarsu a hoto  ,wadan nan hotunan sun isheni blackmailing dinsa ko ya amince da aurena cikin sauki ko kuma na yad'asu a social media duniya tasan halin da yake ciki a ma'aikatansa "nasani bazai ta'ba yarda mutuncinsa ya zube ba dan dole zai yi abinda na bukata."



Tun jami'an tsaronsa da direbansa  a ruwa suna mamakin yadda mr ata yake ma maryama har sun zo sun daina  mamaki domin dai zuwa yanzu sun gama fahimtar mai gidansu ya rufta cikin shaukin soyayyar yarinyar né ,sai dai suyi masa fatan alkhairi jiki a sanyaye maryama ta shiga motar ta zauna tare da lumshe idanunta inda zuciyarta ke bugawa da qarfin gaske ."ya d'an duka ta gefenta, hakika ran sultana baqaramin baci yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login