Showing 138001 words to 141000 words out of 165545 words
iya furtawaba, Gaddafi da matarsa Jiddah da ƴarsu data haifa mai suna Subayya sunata masa dariyar zumudin da yake famar yi, bai kulasu ba, idonsa akan ƙofar jirgi da mutane ke fitowa
Can kuwa saiga taurarinsa guda uku na fitowa, Umm-Ruman ɗauke da Haysam a hannu tana cikin jallabiya ruwan siminti datai mata masifar ƙyau, ta naɗa gyale ruwan ƙasa da yay dai-dai da adon duwatsun da akai kwalliyar rigar mai zubin bubu dasu, sai Zainab dake sanye da wando da riga itama ta ɗora baƙar afterdress a sama, ta sake zama budurwa abinta, dan yanzu tana a shekara ta goma sha uku ne, Haysam kuwa yana sanye da wandon jeans da t-shirt mai ƙyau, shima ya ƙara girma sosai a idonsa yaron, ga kamaninsu da suka sake bayyana tattare da yaron musamman ma shi.
Ahmad ya sauke wani sassanyar ajiyar zuciya yana lumshe idanu, duk yanda yaso yin haƙuri su ƙaraso kasawa yay, ya shiga takawa zuwa garesu.
Inda itama Umm-Ruman idonta ya sauka a kanshi lokacin da Zainab ke faɗin, “Lah aunty Rumana kinga Yaya�?
Da ƙyar Rumana ta iya haɗiye yawu da zuƙar numfashi saboda canjawar da Yayan nata kuma mijinta ya sakeyi, ya sake girma da ƙiba tare da wani ƙyawu mai ban mamaki saboda canjin wajen zama daya samu, sai kace baima taɓa aureba balle tunanin ajiye ɗa kamar Haysam.....
Jitai kawai an rungumeta ita da Haysam ɗin, hawaye suka silalo mata akan kumatu saboda buɗe ido datai ta sauke akan Ahmad dake rungume dasu su duka har zainab ɗin da itama ta ƙanƙamesa cike da farin cikin ganinsa.
Dukansu shida Rumanan sun kasa magana, sai ɗagowa yay suka zubama juna idanu tamkar baƙin ganin juna, ya ɗage mata gira yana cizar leɓensa na ƙasa, murmushi tayi tana duƙar da kanta ƙasa saboda kunya.
Shima ya murmusa yana maida idonsa ga Haysam daketa kallonsa, shi dai ya manta da Abban nasa, amma koda ya miƙa masa hannu bai musaba yaje garesa, ya shafa kan Zainab itama yana mamakin canjawar da duk sukai masa.
Gaddafi da Jiddah da suka matso ne suka katsesu, suka shiga yima su Umm-Ruman barka da zuwa.
Ansan juna a waya, dan suna gaisawa da junansu, hakan yasa babu tambaya Rumana ta ganesu, amsar Subayya dake hannun Jiddah, tayi tana mai yaba kƴawu da girman da yarinyar tayi a watanni bakwai da haihuwarta.
Gaddafi ma ya miƙa hannu domin amsar Haysam a hannun Ahmad, amma sai yaƙi, dariya suka sanya, Gaddafi yace, “Wato shi Abbu duk da ka daɗe baka gansaba ka gane abunka? Niko da baka saniba shine zakamin ƙiwa?�?.
Dariya Ahmad yay yana kallon Haysam dake wasa da ƙasumbarsa, yace, “Sadaukina Uncle nefa, wanda ya baka mata tunkan kazo gata nan�?.
Amamakinsu sai sukaga Haysam na dariya kamar ya fahimci abinda ake nufi, hakanne suma ya sakasu darawa baki ɗaya.
Motar Gaddafi suka shiga gaba ɗayansu domin tafiya gida...........✍�?
_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_
_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_
_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_
_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_
_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_
_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_
_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_
_GUDA DAYA DARI BIYU_
_GUDA BIYU DARI UKU_
_GUDA UKU DARI HUDU_
_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_
_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_
*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*
2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_
saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*
*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇
*09032345899*
_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻
.............A gidan Gaddafi suka yada zango, dan Hafsat tace itace mai tarban.
Sun iske abinci kuwa mai rai da lafiya na musamman da aka shirya domin su, yanda Rumana ta sake da Hafsat sosai ya faranta ran Ahmad, dan ya kula Babie R ɗinsa ta sake wayewa sosai fiye da sanin da yay mata kafin tahowarsa.
Sai kuwa satar kallon juna suke ita da shi suna sakarma juna murmushi.
Bayan sunci sunsha kowa yay nak sukai shirin tafiya gidansu suma.
Gaddafi dake miƙewa yace, “Ai sai dai ku tafi ku biyu, amma ni nan a barmin ƙanwata Zainab da yarona kuma surukina Haysam sumin kwana biyu kafin su biyo bayanku ko Zainabu?�? ya ƙare maganar da kallon Zainab.
Babu musu Zainab dake riƙe da Subayya ta amsa cikin ɗoki, dan batason a rabata da ƴar ƙyaƙyƙyawar yarinyar dama.
Murmushi Ahmad yayi, dan sarai ya fahimci abokin nasa kuma ɗan uwansa a wannan ƙasa dama ya basu suje su more kewarsu shi da Gwal ɗinsa.
Da alama kuma shirin harda Hafsat a ciki, dan ɗaki ta janye Rumana ta bata wasu abubuwa akan suna zuwa gida yanzu kartai sanya tai amfani dasu.
Murmushi Rumana tai tayi tanama Hafsat godiya, dan Hafsat zata iya girme mata, saboda ita tayi karatu har matakin masters ma kafin ALLAH yay aurenta da Gaddafi, amma da yake tanada ƙaramin jiki bazaka taɓa kawo cewa ta girmi Rumanan ba, kasancewar ana cikin yanayin jin daɗi kuma Hafsat akwai gaye da tsafta.
Wayo akaima Haysam suka gudu, to saima akai sa'a shi bai farga da fitar tasu ba, hankalinsa na kan Baby Subayya gaba ɗaya.
★★★★�?
Ahmad dake tuƙa motar Gaddafi da suka taho a ciki sai faman murmushi suke suna shaƙar ƙamshin juna shi da Gwal ɗinsa.
Amma abin mamaki bakunansu sun gaza furta komai, yakan juyo dai ya kalleta lokaci-lokaci, itama dai satar kallonsa taketayi ta gefen ido.
A cikin wannan yanayin dai ALLAH ya kaisu gida lafiya, sosai gidan yayma Rumana ƙyau, duk da kasancewar madaidaici kuma basu kaɗai bane, amma sashen kowa daban dan ɓangare ukune a gidan, kuma duk haya suke a ciki.
Bayan Ahmad yay fakin ya zagaya ya buɗema Rumana itama.
Wannan girmamawa ta ƙayatar da ita sosai, tai murmushi tana miƙa masa hannu kamar yanda ya miƙa mata nasa shima.
Babu wanda baiji wani sabon yanayiba tsakanin a jikinsa ba shi da ita lokacin da suke rumtse hannayen cikin juna, amma sai ko wanne ya fuske abinsa saboda tsaro ba tsoro ba😎🥺.
Sai da ya ɗauki wasu kayan sannan ya nuna mata hanya alamar suje, tai guntun murmushi itama tana ɗaukar akwatin Zainab daya rage dan basu wani kwaso kayaba kamar yanda yace mata, akwatinta babba ita da Haysam, sai na Zainab ɗan madaidaici, sai Handbag ɗinta da wata jikka itama dai madaidaiciya.
Kansa ya girgiza mata alamar ta ajiye zai ɗauka, amma sai ta noƙe kafaɗa tare da girgiza masa kai itama.
Ya lumshe ido yana kaɗa mata kai alamar suje to.
Gaba yay tana binsa biye har ciki. Sosai gidan ya kuma ƙayatar da Rumana, dan ya haɗu babu ƙarya masha ALLAH.
Rayuwa kenan, duk mai rai baya yanke ƙauna da rahmar ALLAH, ko a mafarkinsu basu taɓa tunanin zuwa wannan matsayinba a rayuwarsu........
Rungumetan da taji anyine da zare a kwatin hannunta ya sata kawo numfashi mai ƙarfi tana dawowa duniyar mutane, kallonsa tai, shima idanunsa a kanta.
Ya zare handbag ɗin hannunta yana kuma mannata da jikinsa, su duka sauke numfashi suke a gurguje saboda tsigar jikinsu dake mimmiƙewa.
Umm-Ruman ta ƙanƙame Ahmad itama tana sake masa wani kuka mai tsuma zuciya da ruhin masoyin ƙwarai daya fahimci na shagwaɓane kawai.
Murmushi Ahmad yayi yana ɗagota jikinsa, idanu kawai ya zuba mata ganin yanda take hawaye harda shashsheka, ya sake murmusawa yana haɗiye abinda ya tokare maƙoshinsa maiɗan ɗaci tare da jinginata da bangon da suke gab dashi.
Hannunsa yasa ya ɗago haɓarta tare da ɗora bakinsa kan nata......😚🤫
Komai cak ya tsayama musu, ji da ganinsu gaba ɗaya baya tare da duniyar mutane, takai har ƙafafunsu na neman gaza ɗaukarsu, ganin suna neman zubewa a wajen Umm-Ruman ta janye da ƙyar tana faɗawa ƙirjinsa ta ƙanƙamesa.
Bashi da zaɓin da ya wuce shima ya ƙanƙametan, suka durƙushe ƙasa a tare suna sauke huttai tamkar waɗanda sukai gudu a sahara.
Sunja kusan mintuna biyar a wajen basu iya tashiba, babu abinda suke faɗama juna sai irin kewar da sukayi da nisan da ya jawo hakan.
Ahmad dake kallon bakin Umm-Ruman tana zubo masa bayani ɗunbin kewarsa da tayi ya shafa fuskarta yana haɗiye ƙwallar data taru masa a idanu na tausayin kansu.
“Gwal ɗina ke ta dabance a duniyata, bakina yayi kaɗan wajen furta miki kalaman godiya ko kewa da ƙishirwar jinki a kusa dani dana tsinci kaina a wattani goma sha ɗayannan, kinriga da kin zama Ahmad, Ahmad ya zama ke tuni, kece zuciyata, kece jinin jikina, kece farin cikina da komaina matata, ashe kema haka kike sona?�?.
Sake ƙanƙamesa Rumana tayi tana dariya yanzu, shima dariyar yake mata, da ƙyar suka miƙe a wajen manne da juna.
________________________________
Bayan sunyi wanka Ahmad ya fita gabatar da sallar magrib da Isha'i, yabar Rumana itama zatayi anan.
Kafin ya dawo duk abinda Hafsat tace tayi sai da tai abunta, dama gashi kafin su tahi Ayyah da Iya sun mata tsumawa ta musamman, Yaya Maryam ma da tata gudunmawar, banda wanda itama taima kanta a bayan fage.
Kasancewar cikinsu taf yake basa tare da yunwa Ahmad ya shigo musu hannu rabbana, dan jiya duk wani sayayya data dace ya yita a gidan na kayan abinci, to sai yazam harda fruits duk ya ajiye gwargwadon ƙarfinsa.
Koda ya dawo ɗin zaman gaisawa sukayi da tambayar ƴan uwa da abokan arziki.
Daki-daki kuma take sanar masa da saƙon gaisuwar kowa yake masa.
Yaji daɗi kuma yanata amsawa da godiya, daga ƙarshe dai hirar ta canja sabon salo zuwa......🤫.
😚to babu ruwana, su o'e an buɗe kunnuwa aji, salon aje wajen malam ace Bilyn Abdull ce ta hiɗi😌😏🤣⛹♀⛹♀⛹♀.
★★★★�?
Rumus Umm-Ruman ta tashi a wannan rana, dan da gaske dai Ahmad ya fanshe watanninsa na kewa.
Kallo guda zakai musu ka fuskanci ɗunbin farin cikin da suke ciki, ALLAH ya sosuma ranar tazo a ranar hutu bazaije makaranta ba, amma ya dace yaje wajen business dinsu da sukeyi da Gaddafi kamar yanda ya saba a duk randa baida karatu.
Sai dai ba zai iya hakanba, to tunma da safe Gaddafin ya kirasa akan ya hutashshesa basai ya fitoba.
Hakanne ya saka Ahmad sake bararrajewa sukai ramuwar barcinsu na dare da ya gagara.
Koda suka tashima tare suka shiga kitchen suka haɗa abincin rana dan ba'ace masa breakfast ba dai😹.
A wannan yini dai gaba ɗayansa a kogin soyewa da rushewa waɗannan ma'aurata sukayishi, suna manne da juna kowa na bama ɗan uwansa labarin abinda akai a watanni 11 da basa tare, sai kiran ƴan gida da Ahmad yayi suka gaisa.
Washe gari ma har rana Ahmad na gida, sai da ƙyar da yamma ya iya fita makaranta saboda yanada lecture ɗin yamma.
Kwannan su Umm-Ruman biyar da zuwa saudia sannan su Haysam suka dawo nan gidan, familyn Ahmad ya dunƙule waje guda kamar yanda ya daɗe yana kewa.
Dan danan shaƙuwa ta shiga tsakaninsa da Haysam sosai, dan yana jansu a jiki shi da Zainab dansu sami farin ciki daga tsamosu a dangi da yayi, soyayya kuwa shida Gwal ɗinsa ai ba'a cewa komai.
Suna da watanni biyu da zuwa saudia Ahmad ya nemawa Zainab makaranta, shima Haysam kuwa aka sakashi, duk da ma dai Gaddafi ne ya ɗauki nauyin saka Haysam makaranta dan yana ƙaunar yaron, haka zasuzo su ɗaukesa yaje can yay musu kwana biyu.
Wannan yasa Haysam yazama mai gida biyu, yau yana gidansu gobe yana gidan Gaddafi, idanma akai kwanaki ba'a kaisaba sai yayta kuka yana kiran sunan Ubaya, (Subayya kenan yake nufi😂).
Itama dai Umm-Ruman ɗin Ahmad yanada burin sakata makarantar, danshi dama can mai sha'awar son ganin iyalinsa sunyi zurfi a karatune, hakan yasa yaji bazaiyi ƙasa a gwiwa ba, dukda shi bamai ƙarfi bane zaiyi ƙoƙari da abinda ALLAH ya hore masa insha ALLAHU, tunda da dai karatune ya kawosa ƙasar ba kasuwanciba, amma duk da haka babu abinda zai cema UBANGIJI sai Alhmdllh.
A gefe kuma yanata zuba ido yaga gwal ɗinsa ta fara laulayi, dan Ahmad yay ƙwarin da ko ciki ta samu a yanzu basu da wata damuwa, ballema yaron yanada girman jiki, hakan yasa ta yayesa tun yanada shekara ɗaya da rabi, gashi yanzu har yanada skekara biyu da wata ɗaya.
Tom ALLAH dai bai kawo ɗinba, sai dai a cigaba da fata.
_______________________________
*_NAGERIA🇳🇬_*
_Ya kamata mu waiwayi Samina matar manya😉😌_⛹♀
Lamari ya sake caɓewa sosai a gidansu Samina ko nace gidan Ma'aruff, dan tunda Mufida ta haihu komai ya ƙara canja salon taku.
Irin shagalin da akai wajen wannan haihuwa da ɓarnar kuɗin da Ma'aruff yayi abin har ba'a cewa komai.
Dan mahaifiyar ma'aruff kanta lamarin ya girgizata, hakama ƴan uwansa tunda kowa yasan ba haƙƙinsa bane shi kaɗai kuɗin da yake ɓaragaza dasu, amma saboda son ƙuntatama Samina sai basu nunaba balle zance ya fito, kowa ya haɗiye abun a ransa, dan dai kam tabbas Mufida bawai tabar Ma'aruff hakanan bane duk da kuwa mahaifiyarsa ta tsaya tsayin daka akan sai ya auri mufidan.
Rabonda Ahmad ya shigo sashen Samina da ƙudirin sauke haƙƙinta harta manta watan, dukta fige, dan ko lokacin bikin su Fa'iza a wannan tashin hankalin tajesa, to bayanma bikinsu Fa'izar sai abubuwa suka kuma taɓarɓarewa.
Dan ganin Ahmad a wajen taron bukinnan ya dawo mata da sabuwar zazzafar ƙaunar da take masa, wanda kwaɗayi da son duniya ya danneta a wancan lokacin, kullum shine a mafarkinta, shine tunaninta, saboda shi duk dare saitayi kuka mai yawan gaske, ga tashin hankalin gidan miji, gadai ci da sha amma babu miji babu farinciki babu ƙauna daga ahalinsa, ya kuma hana kowa zuwa gidan a ƙawayenta, wannan yasa ta haɗu ta kuma lalacewa, ko gidansu batason zuwa, indai ta fita iyakarta gidan inna mari, acan suke haɗuwa da mama gaje, mutanen gida kuwa duk sun ɗauka ko laulayin ciki Samina keyi shiyyasa ta ɗaukema gidan ƙafa, amma kuma basuji wani labariba har tsawon watannin da zuciya zata iya ɗauka wannan hasashe.
Ta amshi Number Ahmad, daga baya kuma sai aka sanar mata ai bamaya ƙasar, dan ita batasan zai tafi saudia ba, mama gaje bata sanar mataba gudun kar ranta ya ɓaci😹.
Babu kalar ƙulle-ƙullen da basuyiba amma asirin nasu yabar tasiri a halin yanzu, sun rasa a ina matsalar takene?.
Basusan matsalarsu itace Mufida ba, dan itama sai da tai duk wani yunƙurin daƙilesu kafin ta kafa nata shaiɗancin tsubbun ga Ma'aruff da ahalinsa.
A yanzu babban tashin hankalinta shine Ma'aruff kullum cikin zarginta yake akan wai maza takebi, dan watannin daya ɗauka baiyi tarayya da itaba bazai yuwu ta iya haƙuriba tunda yasanta ita karyace.
Tamasa rantsuwa yafi shurin masaƙi amma yaki saurarenta, abinda kuma bai saniba komai yawan bukata na ɗan adam inhar yana cikin tashin hankali bayama tuna wata sha'awa, musasaman ma mu mata da muke da rauni, ƙaramin ɓacin rai kan gusar da sha'warmu muji bama bukatar namiji.
Wasa-wasa abu ya fara tsamari tsakaninta dashi akan wannan magana, to abune lamari na kwakwalwar ɗan giya da babu Mathematics sam aciki, balle ga sammu na ɗawainiya da rayuwarsa.
Yau da su Rumana ke cika wattanni biyu da tafiya rikici ya ɓalle tsakanin Samina da Ma'aruff akan saita faɗa masa da wa suke cin amanar aurensa, dan da daddare ya shigo gidan a make Mufida ta hanashi shiga sashenta shine ya nufo nan, ya iske Samina nata sambatu akan begen Ahmad.
To da yake