Showing 54001 words to 57000 words out of 165545 words

Chapter 19 - Gudu Da Waiwaye Book 1 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

374

amma ya turama Mudanseer kuɗi sau biyu duk da basu da yawa kuwa.
Baba ya fara magana akan zuwansa gida, hakan ya saka Ahmad shiga damuwa, dan shidai alokacin baima fara fahimtar komaiba game da abinda ya fito nema balle kuma ace yaje gida, ko kuɗin mota kawai sun isa gayya.
A haka wata ɗaya ya kuma shigewa suka zama biyu, dukda takurawar baba yanata jansa da ban haƙuri shidai tare da wasu dabaru.
Wannan sabuwar rayuwarce ta fara saka zuciyar Ahmad mantawa da wata Samina, dan shi kansa yakan manta da kansa balle ita, ibadar ALLAH da sana'arsa ce kawai damuwarsa, sai ƴan uwasa da basa barin zuciyarsa a koda yaushe, Umm-Rumana ma takan faɗo masa arai lokaci-lokaci, musamman ranar dazai taho da taita kuka ta kasa barin ransa, sai kuma randa tai targaɗe a ƙafarta tayi masa kukan taɓara.
Yakanyi murmushi idan hakan yazo masa a rai kuwa.
A hakane kuma suka samu aikin gadi shi da abokinsa Nura, babu musu suka amsa, dan kuwa mai wajen da zasuma gadin yay musu alƙawarin biyansu kuɗi masu ɗan tazara, dan duk wata dubu talatin su biyu su raba.
Ahmad yay murna, dan tun zuwansu bai tara kamar waɗannan kuɗinba.
Da rana zasuyi yawon tallarsu, da dare kuma suzo su kwana yin gadi a wajen.


_________________________


Ɓangaren Samina kuwa yanzu abubuwa sunyi nisa tsakaninta da Ma'aruff, kamar yanda mama gaje take buƙata Ma'aruff na kashema Samina kuɗi tamkar baisan ciwonsu ba, amma kuma yana lalubeta kullu yaumin a mota, yanzuma abin yakai har gidan gonar nan yake kaita susha masha'arsu.
A sheɗanci kuwa shigartane kawai bai taɓa yiba, amma duk wani ƙazamin romance Ma'aruff yanayi da Samina, idan ta dawo gida kuwa ko ranar abubuwa sukai masa yawa bai zoba to ka'idane zata shiga bayi taita ɗauka masa hoton kanta tsirara tana tura masa, har video sakata yake yana faɗa mata abinda zatayi, koya kirata video call ahaka zasu gamsar da junansu😭.

Sanda taji Ahmad yayi tafiya tsakima tayi, acewarta sun rage ƴan saka idon anguwa masu zuwa lahira da ƙoƙwan dambu, waɗanda talauci ya zautar da kwakwalwarsu basa fahimtar komai sai saka ido ga abinda bai shafesuba.
Maimakon Mama gaje ta kwaɓeta saima ta kama dariya kamar wata zautacciya.
Kullum kuma cikin yima Ammin Rumana shaguɓe ake akan ɗawainiyar da Ma'aruff kema Samina.
Sam idon mama gaje ya rufe takasa fahimtar ƴarta na cikin wani hali, abinda kawai tasani ƴarta tana fitane zuwa makaranta, idan kuma Ma'aruff ya fita da ita to sunje ya mata sayayyane kawai.
Bata taɓa tunanin bincikar wayar Samina ba, musamman yanda Saminar bata barin kowa ya taɓa mata waya har ita mama gajen kuwa, ƙannenta ko dasun taɓa ne zata mammakesu ta amshe kayanta, maimakon mama gaje ta fara tunanin akwai abinda Saminar ke ɓoyewa a waya amma sai tayi biris da hakan.
Ita dai kawai da an kawo mata kuɗi da kayan makulashe da zannuwa masu tsada shikenan.
Iyayen Saminar maza da kakanninta kuwa taje ta dafko musu asirin daya rufe bakin kowa a gidan babu mai ma Samina faɗa akan komai, sai idanu da suka zuba mata duk da abinda take yana cin zukatansu kuwa.
Dan wataran baba yusha'u har kuka yi yakeyi akan halin da Samina ta jefa kanta sanadin son zuciya..

Kowa yasan zuwa yanzu idanun Samina sun ƙara buɗewa, ta fetsare sosai, dama karatun islamiyya kam ta ajiyesa gefe, na bokonma da take fakewa dashi yanzu bayi takeba, tunda da taje Ma'aruff ke zuwa ɗaukanta, wani lokacinma ko cikin makarantar bata shiga, kai tsaye gareshi take tafiya, abun yakai har Company dinsu Ma'aruff Samina zuwa take Office ɗinsa susha sha'aninsu.
Gaba ɗaya ta manta da wani halitta Ahmad balle rayuwarsu ta baya da ƙoƙarin gina rayuwarta da yayi, gaba ɗaya ita a dole yanzu ta zama babbar yarinya, budurwar babban yaro da ya fi mijin novels komai.
Abinda yasa Samina taƙi yarda ta bama Ma'aruff kanta 100% saboda tana tuna yanda marubuta kansa amarya tasha gata wajen minjinta a daren farko saboda budurcinta daya samu, amma yanda yasha kawo farmakin amsa da tuni ta bashi.
To tanason dai itama taga wannan gatan shiyyasa.



_________________________


Rayuwa a wannan gida a yanzu babu abinda zance kam, dan bazance ina a ƙuntace ba bazance kuma inajin daɗiba.
Sauƙina ɗaya yanzu tunda safe damunyi kari muka gyara ko ina makaranta muke nufa, bayan na saka Uniform nakan saka hijjan dina har ƙasa da niƙaf, ba ruwana da malamanmu, harma wani girma suke bani, hakan kansa ƴan ajinmu suyitamin shaƙiyanci, iyakata dariya kawai, sai ko su Salima dakan taremin.
Idan aka tashi daga can gida su Fa'iza suke wucewa, nikuma na wuto gida nima, nakan tadda su maman Ama a ɗaki ɗaya zaune suna hira, ko a tsakar gidan wadda na tabbatar bata wuce gulma ba, dama ni tunda na sanar musu zan koma makaranta suka dasa yi dani, nakanji har dariya suke wai tundafa miji ya rainani ai dole ya maidani cikin ƴammata, tunda bani da maraba dasu.
Da farko bana fahimtar zancen, amma a hankali saina gane manufarsu, sam ban damuba dan kuwa ni abinda suke nufin ba shine damuwataba, koda zamu shekara goma Yah Ahmad bai nema komai daga gareniba bazan taɓa ɗaukarsa komaiba.
Dan laulayin ciki da kausar ta farane ya kan kawo a zauna anamin shaguɓe a kansa, tunma bana fahimta harsu Fa'iza suka ankarar dani, banji komaiba a raina, sai ma mamakin rashin ya kamata irin nasu maman Ama nake gani, su miye damuwarsu dan yaya Ahmad bai taɓa mu'amulantata a shimfiɗaba to?.
Zanyi ƙokarin mana girki nasa a kula, la'asar nayi zan shirya na wuce islamiyya, daga can muke haɗuwa mu dawo gida da su Salima idan an tashi.
Ko mun dawo kuwa muna ɗaki abunmu, idan kinga mun fito kuwa ban ɗaki zamuje ko yin abu mai muhimmanci, hakan ya saka su Kausar sake maidani naman cinsu, duk da a hakan kuma suma basubar junansu ba.
Yanzuma likafa ta cigaba har gidan maƙwafta suke zuwa suma suna zuwa nan.
Babu ruwana da kowacce mace bayan gaisuwa.

Lamarin Yah Ahmad kuwa bai cika damuna ba, duk da bawata waya mukeyi da shiba, tundama ya tafi baifi sau uku na taɓa waya da shiba a wayar Yah Mudanseer.
Duk abinda na buƙata Yah Mudan na ƙoƙarin kare mani mutunci ya saya mani, idan kuma yafi karfinsa zai sayo dai-dai ƙarfinsa.
Nima bamma faɗar wanda yafi ƙarfin nasa sam.
Zuwan Ayyah gidan biyu dan taga yanda muke, hakama Yaya Maryam da yaya Sakina da Raheenatu, suma duk sunzo mani harma da yaya bintu yayar Samina.
Suma duka zuwansu ya sakani farin ciki, duk wanda ya ganni kuma zai shaida hakan a fuskata.
Kullum dai nakanbi mijina da addu'ar fatan alkairi da kariyar UBANGIJI aduk inda ya tsinci kansa, ALLAH kuma ya azurtashi da halalinsa komai kankantarsa, ya tsaresa daga haramun komai yawanta da ribar da zaici a cikinta.
A farkon tafiyarsa naji kewarsa, amma zuwa yanzu sam babu hakan a raina.............✍�?



_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_

_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_

_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_

_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_

_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_

_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_

_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_

_GUDA DAYA DARI BIYU_

_GUDA BIYU DARI UKU_

_GUDA UKU DARI HUDU_

_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_


_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*


2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*


_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_


Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻 *ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*

07067124863

*Ko kuma*

09032345899


*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽

https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo


*_GDW_*



*(19)*



..............Tun su baba na saka ran dawowar Ahmad a kusa har abin ya fara basu tsoro, dan kuwa gashi ya shiga wata na huɗu da tafiya.

Wata ranar alhamis Ahmad ɗin ya shiga wani shago na masu sai da yari, saboda kiran da mai shagon yay masa zai wanke masa takalmi, dan yanzu ya gama sanin gari ba tare suke yawo da Nura ba, kowa yana fita neman nasane, da yamma su haɗu a inda suke zama, zuwa dare su wuce wajen gadinsu.
Tunda Ahmad ya zauna wanke takalmi mai shago ke binsa da kallon ƙurilla, tun Ahmad bai fahimta ba harya fahimci kallon da mai shagon ke binsa dashi.
Ɗan ɓata fyska yay, hakan yasa mai shagon yin murmushi, yace, “Na dameka da kallo ko? kayi haƙuri, mamaki nike kamarka fine Boy da wannan sana'ar�?.
Ahmad dai baice komai sai murmushin yake da yay, harya kammala ya tattare kayansa zai wuce mai shago ya mika masa ɗari biyu yana faɗin, “Inda zaka yarda dana koya maka wannan sana'ar tamu ta yari?�?.
Shiru Ahmad yay yana kallonsa cikin nazari,
Mai shago ya sake cewa, “Karka zurfafa tunani ƙanina, haka kawai haɗuwar jini ta sakani maka wannan maganar duk da kuwa yauce rana ta farko dana fara ganinka, amma dai kamin kamanni da bakatsinen barume hakanne ya sakamin ƙaunarka ta musamman, idan har ka aminta zakayi na baka dama ka samo jarinka kazo insha ALLAHU zan taimakeka�?.
Kai kawai Ahmad ya jinjina ya fita bayan ya amshi kuɗinsa.
Koda ya koma ya sanarma Nura sai yay murna, yakuma bashi ƙwarin gwiwar karɓar tayin Alhajin, dan acewarsa wata damace dasu basu samuba tazo masa dukda bai jima da zuwa garinba kuwa. Amma maganar jari ya jira wanda sukema gadi ya biyasu sai yayi amfani da kuɗin.
Ahmad yaji daɗin shawarar Nura, dan haka ya aminta sosai, washe gari yaje ya sanarma Alhajinnan komai, Alhaji ya amsa da babu komai shidai yana jiransa.
Kwanaki goma dayin haka suka jira a basu albashi shiru, har haƙurinsu ya ƙare sukaima mai wajen magana, amma ƙiri da muzu ya hanasu yama yi musu korar kare.
Wannan abu ya saka su Ahmad a takaici, harya hanasu talla a wannan ranar sukai yinin baƙin ciki.
Da abokansu suka dawo daga tasu sabgarsu suma sai suka sanar musu, suma ransu ya ɓaci, nanne wani ke basu shawarr idan zasu iya aikin sauke kaya suzo suje, shi mutumin kullun yake biya adadin kuɗin aikin da kayi.
Da farko Ahmad ya musa, amma da Nura ya lallashesa saiya yarda washe gari sukaje.
Wajene kamar kamfani, ana kawo kaya sukuma za suke jigilar saukewa daga motar zuwa store. A sati ana sauke kayan sau biyar ne.
Duk da wahalar dake cikin aikin haka Ahmad ya dage, bayan sun kammala na ranar kuwa aka biyasu haƙinsu, sunsha ciwon jiki saboda rashin sabo, dan daƙyar sukai barci ranar, amma daɗin kudin da aka biyasu ya saka washe gari suka sake komawa.
A hankali sai gasu sun zama ƴan gida, dan kuwa harma sun saba komai anayi dasu na harkar dako a ma'aikatar.
Duk kuɗin da suka samu Ahmad kan kai nashine wajen Alhajin nan yana tara masa, a randa suka cika sati na huɗune kuma sai kawai ogan wajen ya basu sanarwar duk wanda yazo gobe yaga sunansa an kafe to karya sake zuwa aiki, an koresa kenan
Hantar cikin su Ahmad ta ɗuri ruwa, dan kuwa suna samun alkairi a wajen babu laifi.
Washe gari duk a cikin damuwa sukazo, sai yazam gaba ɗaya waɗanda aka cire hausawan ne, kukane kawai Ahmad baiyiba, suna shirin tafiyane kuma matar mai gidan ta dakatar da Ahmad, acewarta wanan ƙyaƙyƙyawan babu inda zaije, dole ogan ya maida sunan Ahmad kuwa.
Duk da yaji dadi ya nuna damuwarsa na rashin Nura, haka ya cigaba da aikin har tsawon sati huɗu sannan ya bari saboda yaga dai Alhmdllh yaɗan tara wani abu da zai ishesa jari.
Lokacin da zai wucene sai matar ogan ta nuna rashin jin daɗinta, hakan yasa tai masa tayin gadi a gidansu, zasu kuma bashi ɗakin mai gadi ya zauna.
Nanma bai bata amsaba sai da yazo ya shawarci Nura, Nura kuwa ya bashi kwarin gwiwa akan hakan.
Ahmad bai amsa zaiyiba sai da ya koma wajen Alhaji aka fasa asusun kudinsa na dako da ya tara Alhaji ya haɗa masa kwabar ƴan kunne ta hannu, aka zuba kaya dai-dai kuɗinsa sannan, ya bashi tare da sanar masa dabaru akan sana'ar.
Daganan kuma ya koma ga ogansa ya sanarma matar zaiyi gadin, amma zaike zuwa sana'arsa da rana.
Babu musu suka amince, a cewarsu aiba zaman gidanma sukeba da ranar.
Tundaga wannan ranar rayuwa ta sake sauyama Ahmad, dan kuwa a cikin watannan gaba ɗaya saiya cinyesa a yawon tallar ƴan kunne da gadi, koda ƙarshen wata yay yaga yaɗan farfado sai ya fara tunanin zuwa gida, lokacin yanada wata shida cif a garin porthercout.
Babama har yayi fushi da rashin zuwansa ya haƙura yabar masa magaba.
Tun daga randa yay aniyar zuwa gida yaɗan fara sayen tsaraba yana ajiyewa wadda zai fuskanci gida da ita, haka kawai kuma sai yakejin ɗokin ganin Umm-Rumanan sa.


_________________________________

Zuwa wannan lokacin maganar Ma'aruff ta shiga gidansu Samina, yayinda alakarsu ta sake ƙazanta sosai, dan tunda aka tsaida bikinsu wata biyu kacal sai yazam babu abinda Ma'aruff ke burin samu daga gareta sai jikinta.
Har takai dai yau yaci galabar rabata da budurcinta a gidan gonarsa, tasha kuka iyakar iyawa, shiko ya katsatstsareta da lallashi da daɗin baki akan ai babu komai tunda shine zai aureta, kuma bikin nasu duka saura wata ɗaya ne kacal ai.
Tun tana kuka da ƙarfin zuciya har ta aminta da daɗin bakinsa, ya tainaka mata ta gyara jikinta, tare da saka abokinsa ya kawo mata magunguna da allurar rage raɗaɗi, ya kuma kaita Shop rite yay mata shopping na hauka da bai taɓa mata irinsaba, ya maidota hargida tare da bata maƙudan kuɗi.
Mudanseer dake shago Shi da Abu yana kallon yanda Ma'aruff keta saukema Samina kaya niki-niƙi, baki kawai ya taɓe ya ɗauke kansa danshi yanzu babu abinda ya damesa da ita.
Maimakon lokacin da aka shiga da kayan Mama gaje ta fahimci halin da Samina take ciki sai idonta yafi karkata ga manyan ledojin.
Duk uwa mai hankali aka taɓa mata yarinya, kuma yarinyar ta dawo gareta a randa abin ya faru dolene ta fahimci akwai matsala, dan duk macen da aka raba da budurci komai tsahon shekarun da take dashi babu aure wlhy sai taji daban, idan ko babu aurene fargabar fara yinta bata hanyar daya daceba koda itace takai kanta saikin sameta tattare da ita, iyaye kalubale ne agareku, dan yanzu har sai ƙaton banza ya gama lalata miki ƴa a waje ta ɗau ciki ta zubar bama ki saniba saboda sakaci da sakarci kosan duniya irin namu.
Da wannan damar rashin kulawar tamu samari keta lalata yara ta yanar gizo da zahiri ba tareda kun fargaba, damuwarki kawai ki gyarama mijinki kanki dacin kwalliyar tafiya biki domin ki birge mata ƴan uwanki, idan kishiyace dake hankalinki na kanta, saikiga ƙanin uban yarinya ko ƙaninki ko wani na kusa daku ya gama warware tufkar tarbiyyar da kukayi kina nan shatata da baki, sai rashin mutunci ya saka saurayi sakin videon baɗalar da yay da ƴarki a yanar gizo ki haukace har takaiki da faɗawa wani hali ki kamu da ciwon hawan jini kona zuciya, bayan kuma kinbar gini tun ran tubani.
A tunanina duk uwa datasan ƴarta budurwa nada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login