Showing 1 words to 3000 words out of 182919 words
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 14385094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 091368331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 1
Wani irin abu ya dinga jin yana bin jijiyoyin jikinsa ,zuciyarsa kuwa banda bugawa da matsanancin karfin babu abinda take tmkr zata fasa qirjinsa ta fito waje haka ya dinga ji ,"tabbas wannan fuskar fuskar yarinyar mafarkinsa ce tsaye a gabansa ."suna cikin wannan halin some ta turo kofar office din ta shigo cikin tsananin tashin hankali, muryarta na rawa ta soma magana cike da tsoro "me yasa kike da matsala? "maryama hussein mai ya shigo dake cikin office din nan bayan na fad'a miki mai gida baya da bukatar ganinki?" "sir please kayi hakuri ban san lokacin data shigo ba "ya d'ago idanunshi wad'an da suka rikid'e zuwa ja ya saukesu akan some dake rawar murya da jiki "kayi hakuri sir yarinyar ce tana da taurin kai na fad'a mata baka da bukatar ganinta am very sorry sir." "malama ki gyara kalamanki dan suna sani jin wani iri acikin kwakwaluwata ,na shigo ko aka shigo dani ?" Idanunshi dake kan some ya dauke ya maidasu kan maryama caraf sukayi 4 eyes da ata ido cikin ido suke kallon juna wani irin zirrrr ya soma ji a gbdy sansar jikinsa ,wani irin kallo mai tafiyar da ruhi ya dinga mata , a zuciyarta tace" ko me yasa yake min irin wannan kallon kamar zai cinyeni ?saurin cire kwayar idanunta cikin nashi sakamakon bugawar da zuciyarta ta fara yi ."
Sosai ya sakankace a kallonta har sai da some ta soma zargin wani abu akan mai gidan nata dan bata ta'ba ganin macen da yayiwa irin kallon da yake mata ba hasalima shi mutun ne da bai fiyye son kallon mata ba , ta juya ta kalli salim dake tsaye shima ata yake kallo fuskarsa d'auke da tarin damuwa,sautin muryarta ce ta dawo dasu natsuwarsu ," kisani ko nace kusani gabd'aynku maryama tafi karfin wulakanci sannan tafi karfin tayi aiki akarkashin mutane irinku marasa mutunci da tausayi ."gaban ATA yayi wani irin mummunar fad'uwar da bai ta'ba jin irinsa ba sai a yau din nan ."yay mugun tsura mata kwayar idanunshi yana kallonta nan take yaji maganarta tayi balain d'aga masa hankali 'yayi taku biyu zuwa inda take tsaye jikinta na kyarma sai dai ya kasa cewa komai dan koma yace zai yi magana a halin da yake ciki bakinsa bazai iya furta komai ba "an fi karfina ne yasa kuka sake ganin qafafuwana acikin kamfaniku dan wlh a karon kaina bazan ta'ba turo maku sakon neman aiki ba tunda nasan halinku bare har na tako domin yin aiki ".tana gama fad'ar haka kan ATA yayi wani irin tsarawa tare da sauke wani zazzafan numfashi ya kai tattausan tafin hannunsa daidai saitin zuciyarsa da ke mugun bugawa da sauri sauri dan tun data soma magana qirjinsa yake bugawa fiyye da kaida "kisani ko nace kusani maryama tafi karfin wulakanci sannan tafi karfin tayi aiki akarkashin mutane irinku marasa mutunci da tausayi shine maganar da yake ta yiwa ata yawo acikin kwakwaluwarsa ."
maryama ta sauke idanunta da suke a rine tsabar tashin hankalin da take ciki akan ATA dake tsaye wanda ya tsareta da tsumammun idanunshi masu firgitarwa hakan yasa ta kawar da fuskarta gefe sannan ta fara fad'ar abinda take son fad'a "karo na biyu kenan kana ci min mutunci laifin me nayi maka ?" ta tambayesa tare da d'ago fuskarta ta zuba masa tana mai danne kwalla dake qoqarin zubo mata "baka son ganina arayuwarka ko "?ta fad'a tana sheshekar kuka " wallahi ban san me yasa na yarda na kawo kaina inda zaa tozartani ba ."subhallah !ata ya furta a kasan ransa yana jin kamar ya qara taku biyu din da yayi saura a tsakaninsu ya fixgota yayi mata kyakkyawan riko tare da mata masauki a faffad'an qirjinsa "what the hell is going on?me yasa kike fad'awa mai gida haka instead ki bada hakuri ko zai taimaka ya d'aukeki aiki sannan ki gyara kuskurenki shine zaki zauna kina fad'awa mutane magana I can't tolerate that "saboda me zan bada hakuri ?"laifin me nayi da zan bada hakuri ?Ko kuma kuskuren me zan gyara idan kina wasa ne to ki daina dan babu hakurin da zan bayar dan kawai nayi aiki daku "cike da tashin hankali ata ya fixgar da numfashi sannan ya motsa labbansa a hankali ya soma magana "some !"
jikin some na kyamar ta amsa da "yes sir! leave.."!
"Okay sir am sorry !ta juya da sauri ta nufi kofar fita hakan da maryama taji yasa ta biyo ta bayansa ta ra'ba ta gefensa zata fita har tana zozon jikinsa wani abu yaji mai kama da wutar lantarji ya ziyarci gabad'aya ilahirin jikinsa ,fuskarsa dake a murtuke ya tsaida akanta yayinda da sauri salim ya biyota ya sha gabanta yana cewa "dan Allah maryama ki tsaya ki natsu ki kwantar da hankali duk abinda kike bukata acikin kamfanin nan a shirye muke zaa miki shi amman ki dan bamu dama zamuyi magana mai mahimanci dake ."nan da nan 'bacin ran maryama ya sake nunnukuwa zuciyarta ta dinga tafarfasa bata ce masa komai ba sai dai ta balain had'e fuskarta sannan a natse ta ra'ba gefensa ya sake shan gabanta "a gaskiya raina ya fara 'baci da abinda kake min sannan zuciyata ta fara tafarfasa ,ni mace ce mai tsnanin hakuri karka bari nayi maka abinda ban ta'ba yi wa wani mahaluki a duniyar nan ba ".
"me zaka fad'a min ko kuma nace me zaku me bayan wulakanci da tozarcin da kuka min ?nasani shima ATA daya aikata haka bai san ko ke.."enough please bana son jin komai matsa kawai ka bani hanya na wuce bana bukatar taimakonku."ta fad'a tana mai sake ra'bawa gefensa ya sake shan gabanta ai kuwa zuciya ta rufeta bata san sanda ta d'aga hannunta ba ji kake tas ..! ta sauke masa wani lafiyayyen mari akan Kuncinsa a gigice ya dafe kuncinsa yana kallonta cike da tsananin tashin hankali. ta juya a matukar fusace tana kallon ATA dake tsaye tamkar wanda aka dasashi a wajen tsabar tashin hankali "ka fad'a masa ya fita rayuwata ya bani hanya na kama gabana". yadda ta tsura masa ido tana kallonsa cikin 'bacin rai haka shima ATA kallonta yake baya ko kifta idanunshi ga wani kalar tashin hankali dake shigarsa yana bin ilahirin jinin jikinsa ."bai ta'ba jin yayi laifi yayi nadama ba sai a yau ."
"Ka fad'a masa ya bani hanya na wuce na kama gabana."tayi maganar muryarta cike da rauni a hankali ya furzar da wani iskan mai zafi daga bakinsa cikin wani irin salon magana tmkr bashi da laka yace "salim barta ta wuce !"yana gama fad'ar haka ya juya masu baya jin haka yasa salim ya matsa gefe ya bata hanya batare da ya sake cewa komai ba ,batare da 'bata lokaci ba maryama ta gyara zaman jakarta ta fice daga office din tana jan tsaki ,jiki a sanyaye maryama take taku tamkar bata son taka qasa."tasa hannu ta goge hawayen dake tsiyaya daga cikin kwarnin idanunta ta fita daga haraban ma'aikatan inda zuciyarta ke wani irin bugawa da karfin gaske ."tana tsaye a gefen get din ma'aikatan jiran abun hawa sai ga motar ammar kallo d'aya yayi mata ya fahimci tana cikin damuwa nan take shima yaji damuwa ta shigesa umarni tsayuwa ya bawa direbansa tun kafin ya shigar da kan motar ciki ." direba bai gama daidaita tsayuwarsa ba amar ya fito ya tako ya sameta har inda take tsaye tana goge hawayen dake tsiyaya "maryama !ya kira sunanta ta d'ago da sauri ta tsura masa ido "lafiya kike tsaye a bakin titi kina kuka ?yayi mata tambayar cikin tsananin damuwa "ba wannan mara mutuncin mai kamfanin ATA creation din bane .."sai hawaye sharr suka zubo mata dan haka ta kasa cigaba da magana "zo mu shiga daga ciki Kiyi min bayani abinda ya faru ".ta girgiza masa kai "har abada oga amar qafafuwana bazasu sake shiga cikin wannan ma'aikatar ba "tana gama fadar haka ta juya ta soma tafiya tana bin gefen titi da sauri ya biyota ya sha gabanta "fad'a min wanda ya 'bata miki rai ? yayi mata tmbyr ne domin ya tabbatar da abinda yake son sani "mai kamfanin da kanshi sai wani da bansan ko waye ba sun taru sun wulakantani sun tozartani "mai kamfanin ATA creation da kanshi ?ya sake tmbyrta cike da mamaki ta gyda masa kai alamun "eh! yana kallonta ta ra'ba gefensa ta wuce ta cigaba da tafiya da kallo ya bita dashi kafin ya juya da sauri ya nufi cikin ma'aikatan."
Cike da matsanancin tashin hankali ata ya zagaya ya koma mazauninsa yana sauke wani zazzafan numafshi sai dai ya kasa zama ya d'auki wani file da kwayar idanunshi ya kai garesa ya soma dubawa cikin tsananin tashin hankali yake amman dake shi din nmjin duniya ne bazaka ta'ba iya gane hakan attare dashi ba sai dai acikin zuciyarsa kuka yake yi irin kukan da bashi da mafuta "me yasa rayuwarsa take shiga rud'ani?"me yasa abubuwa suke faruwa dashi ne ?"wannan wani irin tashin hankali ne mai sarkakkiya?yarinyar nan itace yarinyar da kasa aka kora a sakonni da suka gabata "I know? ATA ya fad'a atakaice ya na mai ajiye file din hannunsa ya sake zagayowa ya tsaya cak a tsakiyar office din ya zira hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa yana jin wani irin tashin hankali mara misaltuwa na kusanto rayuwarsa ga ciwon da kansa yake yaki dainawa sai ma cigaba da sarawa yake ." salim ya tsaya sororo yana kallonsa tamkar mai shirin yin kuka "kace ka sani ?"yes of course na sani amman a yanzu kenan bayan nasa an koreta naga kana magana hankalinka kwance yarinyar mafarkinka ce fa ?"I know! salim ya girgiza kai yana kallonsa ."
ata ya kallesa a d'age yace "sannu da shan mari na qoqarin tsaidaita ai da kasani ka barta ta wuce ."ya fad'a tare da samu guri ya zauna akan kujerar sofa dake office din ya daura qafarsa d'aya akan d'aya yana girgizawa tmkr baya tare da wata damuwa salim ya shafa kuncinsa daidai inda yasha mari yace" gasky na maru ,mari biyu kenan na sha a hannunta". ata ya kallesa da tsumammun idanunshi dake cike da tashin hankali "tayi min d'aya a waje kafin na shigo daita yanzu kuma tayi min d'aya a gabanka "wani irin kuncin ya sake mamaye zuciyar ata dan shi kad'ai yasan halin da yake ciki "dan allah ka tashi muje ka tsaidaita idan ta tafi bakasan inda zaka sake ganinta ba ."wa kenan zai tashi ?ya tsare salim da kwayar idanunshi masu firgitarwa "wai ni !?ya sake tambayesa yana nuna qirjinsa da yatsan hannunsa "ka sanni kasan halina hakazalika duk wanda yake tare dani yasan ina mutuwar son yarinyar nan , nayi hauka a bayanta amman bazan yi haukan soyayya a gabanta ba ."matsalata da kai kenan girman kai wallahi tun wuri ka dawo cikin hankalinka shekara da shekaru kana neman yarinya amman ka ganta har ka wani tsaya jin kai? " ka sani salim wannan ajinina yake" yana gama fad'ar haka ya mike tsaye "kasan wani abu na had'u daita kwanaki baya acikin ma'aikatan nan sai dai sanye da nikaf na ganta amamn naji ajikinta cewar itace sai dai wannan mugun abun da take amfani dashi ya karyar min da gwiwa har na tsaida zuciyata akan ba ita bace ina ganin wannan mugun abun da take rufe fuskarta dashi ne yasa nayita shan wahalar nemanta wata kila da bata sakawa da iwar haka munyi aure har ma ....."shiru yayi ya kasa qarasa maganarsa yana jan tsaki "
"har ma me ? salim ya tamabyesa a d'age ata yayi shiru ya kasa cewa komai yana mai cizan lip's dinsa da karfi "da har kayi mata ciki ba ?ata ya kallesa kawai batare da yace kala ba "nasan abinda kake qoqarin kace kenan "wannan kuma fad'arka ce ba tawa ba ." ya zarce da cewa "wancan zanen hotona da kake ta magana akansa itace ta zana shi ya nuna masa zanen da yatsan hannunsa "woooo gsky yarinyar ta had'u sosai yanzu ya zaayi musan gidan su ?bai bashi amsar tambayarsa ba ya shiga wata magana " kasan yarinyar nan muguwar yar rainin sense ce itace fa yarinyar da muka bukaci tayi aiki akarshin Z&A daman ni tun tuni jikina ya bani itace "congratulations! na me kenan ?na ganinta da kayi ga kyau ga ilimi ga baiwa wacce ba kowa yake daita ba ina tayaka murna domin kuwa lokacin farin cikinka ne yazo "ka daina murna salim dan kuwa matar aure ce .."yana gama fad'ar haka ya juya masa baya ."what?ya furta da karfi shi kuwa ata kasa juyowa yayi sai ma numfashi da yake janyowa da kyar tmkr mai cutar asthma duk abinda yake dauriya ce kawai irin tashi amman da zaa bud'e qirjinsa da an hadu da gimgima gimman tashin hankali."
Jikin salim na wani irin kyarma yace "matar aure kace fa ? shiru ata yayi masa yana kokuwa da numfashinsa dake qoqarin barin ganganr jikinsa "wani irin matar aure adam ?still shiru ata yayi "dan girman allah ka juyo kayi min bayani ta yadda zan fahimceka still shiru yayi tamkar ba magana yake masa ba "da gaske matar aure ce maryama ?"tabbas matar aure ce salim !suka jiyo murya daga bayansu wanda yasa suka juyo atare amar suka gani tsaye fuskarsa dauke da damuwa sanye cikin brown t shirt da blook trouser hannunwansa rike da wasu takardu da alamun saka hannun ata ne ya kawoshi ."
Ahankali ata ya kai hannunsa yana shafa goshinsa yana ciza lip's dinsa da karfi,da sauri salim ya qarasa ga ammar tare da dafa kafad'ansa yana dubansa "yaakayi kasan matar aure ce ?ammar ya zame kafadansa ya soma taku acikin office din ya isa kusa da ata "nasan komai akan maryama ,yadda kasan ata na bulayin nemanta haka nima nake tayasa nemanta batare da saninsa ba kwatsam na ganta Z&A amatsayin mai bautar kasa na yita qoqarin su had'u dashi saboda ina son nayi surprised dinsa amman taurin kai irin nasa ya hana "me yasa kayi masa haka ammar ?me yasa bazan masa haka ba?" shi me yasa bai bukaci ganinta ko sau d'aya bane ."ai shi kullum acikin matsla zai qare rayuwarsa ." ata ya kallesa idanunshi cike da tashin hankali gashi sun jazur tmkr garwashin wuta "yes kana min wani irin kallo bancin kana da matsla da tuni ka sameta arayuwarka ".
"me yasa ka kasa gaya min cewar yarinyar mafarkina ce ?"you could have told me ammar da yanzu bata zama mallakin wani ba ata ya fad'a jikinsa a sanyaye "kasan karin maganar nan daake cewa jifan tsuntsu biyu da dotse daya shi nayita maka naso ka had'u daita tun kafin ta zama mallakin wani amman taurin kai da nuna isa da girman kai yasa kaki yarda dani saboda taurin kanka yasa ka rasata a rayuwarka."
"wallahi nayi imani a lokacin da zaka furta kana son maryama zata kar'beka da hannu biyu amman a yanzu maryama tafi karfinka kai tafi kowa tsanarka yanzu wa gari ya waya ?shiru ata yayi yana zurfafa tunaninsa "tabbas ammar yayi iyakar qoqarinsa na ganin sun had'u daita amman yaki sai gashi a had'uwarsu akaron farko ya fad'i warwas "me yasa kayi min haka ammar ?me yasa baka kasheni kafin zuwan wannan ranar ba ,you could have kill me ammar ." ya qarasa maganar kamar zai yi kuka nunfashi ammar ya sauke you know I can't fause you,abinda kasani ne baa takuraka baayi maka dole akan komai sai abinda kaga dama ."
kallonsa yayi cikin tsananin bacin rai "okay babu damuwa na hakura daita a fusace ammar ya kallesa sannan ya cigaba da magana cikin zafin rai kamar shine mai son maryama din "karya kake kace ka hakura daita domin wannan yarinyar itace rayuwarka itace nasararka."itace natsuwarka idan babu ita acikin rayuwarka komai zai iya faruwa da kai " ta yaya zaka fad'a min haka bayan tun daaka haifeni nake tare da nasarata "da farko zuciyarka na tsananin sonta ,abu na biyu zuciyarka na bukatar tayi aiki daita ,abu na uku ka rasata kasancewar matar aure ce , abu na hud'u gashi ta tsaneka" wadan nan abubuwan zasu shafi lafiyarka da komai naka kaga ka rasa nasararka ,to yanzu sai ya kenan? "sai na mutu me kake nufi ?ammar yayi shiru yana masa duban tsanake kafin ahankali yace kana sonta ko kuwa jin matar wani ce ka hakura daita "yes I love her so much " to muddin kana sonta sai ka shirya yadda zaka dawo daita cikin rayuwarka ko karkashinka amatsayin maaikayarka idan ba haka ba zaka cigaba da azabtar da zuciyarka da rayuwarka ne kawai a banza da wofi ."karka damu da wannan karka damu da irin son da nake mata dan babu abinda zan iya yi kasancewarta matar wani ya ruguje komai da nake ji akanta kana nufin ka hakura daita kenan ?tabbas ina sonta sosai amman na hakura domin bazan yi muamula da matar wani ba ,yadda bazan yarda wani ya keta min haddin aurena ba haka zalika bazan yiwa wani ba "ka bata aiki akarkashinka "shima bazanyi ba ."to kuwa zaka shiga matsla dan kimar data rage maka a idanun mutane zata rushe domin kuwa yanzu ne zakayi haukan so dan ka dinga ganin damuwa kenan akan damuwa sai ma idan ka gano irin son da takewa mijinta " me kake son yayi ammar byn kasan matar wani ce ? salim ya tambayesa cikin tsananin tashin hankali "ina son ya nuna shi din cikakken nmj ne ya fuskanci mijinta gaba da gaba ya kwace soyayyarsa daga hannun sa". salim ya girgiza masa kai yana masa kallon mara hankali da lissafi "taya zai yi haka ammar