Showing 129001 words to 132000 words out of 288345 words

Chapter 44 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

787

tana da Hakki a kansa kamar yadda nake dashi daman kuma kin kirata tazo ta kula dashi tunda kin ce ni ba takansa nake bi ba,Ki kirata tana ciki ta fito ta karb'i kayansa ta wanke shima ai yana daga cikin Hakkokin da kika mgana"
Ina gama fad'in haka na kama Hanyar Dakina Mama ta rakani da kallo cikin mamaki tace"Fa'iza yanzu ni kike fadama wannan mganar..?
Kafin nayi mgana ya katseta da fadin"Don Allah kyaleta Mama tun jiya na roketa ta rantse bazatayi ba"
Sai mama ta shiga tafa Hannu tana salallami ni ko nayi shigewata Dakina na kwanta a gado na,ban san ya suka kare ba sai wajen sha d'aya na Safe na tashi na iske Hafsah ta gama Had'a zobon tana jiran ya huce ni ita ke bani Labarin yadda suka kare Zainab din ta fito tana wani yamutsa fuska tace a kwashe kayan aka kai wanki da guga zata bada kudin wai har tana fadin"Honey sai da nace kayi zaman ka achan ka ki inda kana chan wani kuma wanki ne sai kayi da kanka..?
Dariya ma abun ya bani Hafsah tace"Yaya fa'iza wlh kin burgeni gwara da kika fara nuna ma Mama abunda take yi bata kyautawa"
Mirmishi kawai nayi ban ce komai ba,ni ba mgana na maida mata ba Abunda ta bukata nayi mata daman na rantse bazan kara yi masa komai ba indai matarsa na nan,ba ni sun raina nawa ba? to yar masu da shi tazo tayi musu su gani.
Ashe mgana bata mutu ba mama ta rika yawo dani wai Ishaq bai da lafiya bani da Tausayi da Imani na barsa zai wanke kayansa da kansa, da Mama tamin mgana nayi mata rashin kunya da Yammah sai ga Anty Binta tare da Anty Mahma har Dakina Anty Binta ta biyoni tana gayamin duk mganar da tazo bakinta cin mutumci sai wanda ta manta,Kamar na sani nace Hafsah ta tafi da Anum da Amir gidan nik'an Aya Ahmad da Musty ne kuma suna Dakin Mama wajen Fadil.
Ko daga kaina ban yi na kalleta ba,sai da naga ta Dage wai in nace zan cigaba da yi ma Mama rashin kunya zamana ne zai kare a inda aka rufamin asiri sai alokacin na Dago ina kallonta kafin nace"To ko a yanzu din ma me ya rage..? Adai yi sha'ani an cuci na kauye"
Bata Fahimci mganata ba ta cigaba da fadin mganarta ta dauka irin da ne har tana kokarin kamamin kunni nako mike nayi baya ina kallonta cikin Hargowa tace"Zaki dake ni ne Tattaciya..?bar ganin kin fara wannan sana'ar ta biyar goma dama bamu san asalin balbela ba ne sai ta gaya ma da ga kasar masar ta fito.."
Na lura suna adawa da samun Cigaba na, a raina ko nace sai dai ku mutu sana'a yanzu na fara shi wlh.
Ganin ta fara isata da mgana ga Musty ya shigo ya tsaya yana kallon mu yasa nace"kiyi hakuri Anty Binta ni fa ba rashin kunya nayi ma mama ba. Cewa tayi ta kira zainab ne saboda tazo ta kula da shi,Tunda ni ba na kula dashi. nayi laifi domin na sakar mata komai tunda gata tazo.? ai acikin kula dashi har da yi masa wankin kayansa.."
Kawai sai ta kalleni bataji kunya ba tace"Lalle kin cika mara kunya Zainab din sa'arki ce ko Matsayin ku da'ya da zaki rika had'a kanki da ita..?
Sai na dago ina mirmishi kafin nace'Tabbas ba matsayin mu d'aya ba, nasan wannan tun kafin ya aurota ya raba mana matsayi kuma kuka rabamananwannan matsayin. sannan ni nasan ba sa'ata bace saboda ni marainiya ce ban aje ba sannan ban ba wani ajiya ba, sannan ni ba yar gata bace kuma ba yar boko irinta ba, ni yar gargajiya ce da wahala da komai na ke rayuwata kin ga ni kaina nasan tazaran dake tsakani da ita kamar tazaran sama da kasa ne ku yi hakuri na manta ne ammh daga yau zan kiyaye zan kuma tsaya a iya matsayina"
Sai ta kad'a kai tana fadin"Da kin ma kanki kiyamullaili"
Ta juya ta fita Musty ya rugo da gudu ya rikeni yana fadin"Umma zagin ki take yi..?.
Da sauri nace"A"a hira muke yi Musty"
Yaro da Fahimtar abu sai yace"Umma naga fa fada take miki"
Nasan sa da surutu su Amir na Dawowa zai gaya musu sai nace"Waya fad'a maka..?
Hira muke yi baka gani ba.?
Sai yayi shuru ya kasa mgana ni kuma sai na daga sa sama ina juyi da shi sai ya fara bangalan dariya.
Har Anty Mahma sai da suka kitso mata zencen ta shigo Dakina tana fadin"Gaskiya Fa'iza baki kyauta ba,ban san ki da haka ba,Bai kamata bai da lafiya ki barsa da wanki ba. kuma ina ruwanki da Zainab ita da ba mazauniya ba, dubiya tazo yi zata koma inda ta fito ke dai kiyi aikin ladanki kada ki manta duk abunda kika yi na lada agidan mijinki za'a ninka miki ne kin karanta na kuma san kin san haka"
Gani nayi in na tsaya mata bayani ma bata Lokaci sai kawai nace"In sha Allahu baza'a kara ba"
Sai taji dadi ta dafani tana fadin"Yauwa ko ke fa Fa'iza in anjuma ki shiga ki bama Mama Hakuri shima ki basa Hakuri"
Sai na gyad'a mata kai araina ina jinjina al'amarin wannan rayuwar.
Sai ta gyara zama tana fadin"Hajiya Fa'iza mai zobo da kunin aya naga fa alaman kin fara samun kasa da wannan sana'ar kin zama big madam"
Sai ta bani dariya na dara ina fadin"Kai Anty mahma da zoyala"
Agabanta Hafsah ta had'a kunin Ayan da zasu tafi na bata harda zobo ta karba tana fadin"Kada mu zama karya Jali fa..?.
Sai nace"Kada ki damu bazaku karya ba"
Sai tamin godiya ta fice zuwa Dakin Mama ina jin tafiyar su ita da Anty Binta Gogan daman dakin Mama ya yini shiyasa Tun safe bamu hadu da Zainab ba sai da Daddare muna falo ina ma yara karatun Hadisi suka shigo ita da shi,Yaran sun riga sun sani in suna karatu ba na barinsu su tashi sai ba su tashi ba Ahmad ne ya mike da gudu ya nufesa sai ya Dagasa sama yana fadin"Kai ma fa ka fara zama Lukuti irin musty"
Saukesa yayi ko sauraran gaurancin da Ahmad ke masa bai yi ba Zainab kuwa kala batace min ba,gani nayi kamar ranta yana bace ne sai nima na kame kaina haka suka shige ko sannu Daga shi har ita ba wanda yace min. nima ban damu ba na cigaba da yi ma yara karatu bayan mun gama nayi musu Tarihi sannan nace su je su kwanta.
Ni da Anum da Hafsah muke kwana adakina Hatta Ahmad na maida shi tare da su Amir da Safiyar asabar suna da Tahfezz karfe Takwas na tafi kaisu da kaina Saboda Amir ya shiga ajin yan Hadda akwai littafan da zai siya sannan ina son naji karin bayani,na jima a makarantan suna ta gayamin kokarin yarana musamman Anum da Amir malamin Qur'anin su Anum yake min godiya lokaci d'aya yana Fadin"Saudatu ta fadamin Ummansu ke musu karatu agida sosai na yaba miki kin yi kokari kuma hakan da kike yi ya kara taimakon yara wajen hazaka da maida Hankali da ace iyaye mata da maza zasu san amfanin koyar da yaro kad'an daga abunda ka sani agida da yara da yawa sun zarce Tunanin iyayansu"
Na jinjina kai ina yarda da mganarsa Saboda ban zauna ba ko na bangaran Bokon da ban iya ba ina sawa su koyama junansu na addinin kuma da na kwarewa ban ta gajiyawa ba domin shi kadai gareni da zan basu su godemin watarana.
Sai wajen Tara na Dawo gidan na iske Rigima acikin gidan Tsakanin Zainab da Yaya Ishaq,Allah ya taimaka Hafsah bata nan na aiketa kasuwa ammh Badariya na gidan,Suna Dakinsa ne ammh fad'an nasu yayi kamarin da gabadayansu suke daga muryoyin su,da na dawo na kasa karisawa Dakina kamar zan shiga na gani wata zuciyar ta kwabeni tana fadin"Ke fa'iza ina ruwanki.?
Aiko sai na kama kaina na kama Sabgan gabana dakin yaran na fara gyarawa na fito falo kenan Sai ga shi ya fito har yana Tureni bai sani ba nayi Saurin yin gefe kamar kububuwa haka ya shige Dakin Mama itama sai gashi ta fito tabi bayansa tana fadin"Wlh baka isa ba Ishaq"
Itama tabi bayansa Fuu kamar zata tashi sama,sai gani rike da baki ina binsu da kallo ina nanata sunan Ishaq din da naji ta ambata, tunda nake ban taba jin ta kira sunansa gatsal ba sai dai Honey, ashe su Honey an jiki yau din nan.
Domin duk rashin karfin jina haka na rika jiyo tashin muryoyin su Mama nayi suna yi kamar ta kasa tsawarta musu ne sai ga Badariya ta shigo da Fadil tana Lallashinsa yana ta kuka na ijiye tsintsiyan Hannuna na karbesa ina fadin"Me ya same shi?
Badariya sai ta koma ta zauna tana fadin"Rudewa yayi da hayaniyar iyayan.Ni kaina barci nake yi sai da na tashi a firgice"
Kamar zan tambayeta sai kuma na fasa,Daman nasan zata koramin yadda akayi Kitchen na shiga na Dauko Purewater nazo na zauna ina basa yana karba da sauri alamun kishi yake ji cikin alamun Tausayi nace"Allah sarki bawan Allah kishi yake ji"
Badariya tace"Komai ma zai ji tun safe an fara fada,Daman ni nasan sai haka ya faru yadda Yaya Ishaq ya gina auransa ba kan turba mai kyau ba ne Anty Fa'iza"
Sai na kalleta ina fadin"Hala me ya ke faruwa..?.
Sai ta gyara zama tana fadin"Nima ban san kan mganan ba ina dai jin Kan tafiyar Anty zeey ne.Babanta ya Turo mata Mota tuni Direban ma ya iso zata koma Abuja to ina ga shine Yaya yace wlh bazata tafi ba sai dai in ta tafin ta fara shirin dawowa nan gabadaya ku zauna tare. shi bazai rika binta ba tunda baya aiki achan yanzu ita kuma ta Daka Tsalle tace bai isa ba sai ta tafi kuma????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? bai isa ta ijiye aikinta ta Sauya rayuwarta Saboda shi ba,in bazai Bita ba sai dai ya bar shi"
Sai na jinjina kai jikina duk yayi sanyi Badariya tace"Ta wani fanni fa tana da gaskiya abunda ya zaba mata ne Tun farko rana tsaka ba shi da Hujjan da zai ce a'a duk wanda ya siya rariya yasan zata zubda ruwa"
Kafin nayi mgana Zainab ta shigo Dakin tana kiran Badariya ta kawo mata Fadil na mike na mika mata shi ta fita dashi nima sai na bita Daidai Zainab din ta fito da karamar akwatinta ta kalli Badariya tana fadin"muje mota da shi"
Taci gayunta ta yafa mayafinta abun nasa ya shafeni ko sallama batamin ba ta juya ta fara tafiya kenan Ya fito Daga Daki cikin Daga murya yace"Wlh Zainab in kika saka kafa kika fita daga gidan nan batare da izinina ba kin tafi kenan"
Dam!naji mganar nasa na d'ago ina kallonsa ita ma sai ta tsaya cak kafin ta juyo tana kallonsa Mama ta fito daga Daki hannunta a saman kai tana fadin"Na shiga uku ni Saudatu me zan ji haka..?Don Uban ka ka janye kalaman ka ko ranka ya baci"
Idanuwansa sun sauya launi yace"Bazan janye ba Mama haka nace.Wlh bazan zama jani talau ba..Ni ke auranta ko ita ke aurena..?
Mama ki duba fa wannan mgana taya za'a kafa min sharadin zuwa Abuja ina naga ko kudin mota.?zirga zirgan kansa ina naga kudin yinsa..?in a baya ina da aikin yi na dauki wannan Dawainiyar yanzu ta sani bani da shi To meyasa bazata zo ta zauna da ni a inda nake da shi ba in dai har da gaske tana so na?
Yafad'a cikin bayyana bacin ransa,Mama kuwa ta kasa mgana Ni kaina ban ce komai ba ni da Badariya muna tsaye cirko cirko,kamar wasu zakaru,ita ko Zainab sai batayi mgana ba ta jawo akwatinta ta shige Falona ta fito da waya tayi kira sai ta sauya Harshe turanci da Fillanci.
Shi kuma Mama ta shigar da shi Daki bansan me take fadamai ba,chan kuma sai ga Anty Binta suka sake kulewa Daki itako Zainab tana falo na kafa d'aya kan daya tana girgizawa karamar akwatinta na gefe sai hura Hanci take yi bini bini ana kiranta a waya tana mgana yadda batamin mgana ba nima sai na kama kaina na fito ina harkan gabana.
Zuwa azahar ina waje ina Dafa zobo na sai ga Mahaifin Zainab ya fad'o gidan kamar daga sama ashe jirgi ya shigo ya iso kano,Direban da yazo daukan Zainab yaje ya Daukosa Kai tsaye ya shigo cikin Hanzari ina gaishesa ko amsani bai yi ba cikin Kaushi da Dagawar murya yace"Ina Ishaq din..?
Muryansa ya fito da Zainab Daga dakina tana ganinsa ta nufesa da Sauri ta fada jikinsa ta fashe da kuka tana Fadin"Daddy wai ni Ishaq zai ce in na fita a bakin aure na..?ni Daddy Ishaq fa..?
Sai ta kara saka kuka,Cikin Kakkausan murya yace"Shi..Am here bai isa ya fad'a miki wannan mganar ba,Who is he.?
Mganarsa da kukan Zainab ya fito da Ishaq da Mama da Anty Binta suna ganinsa suka fara kame kame Mama ke fadin"Alhaji sai da ta taso ka?
Kallonta kawai yake yi bai yi mgana ba Ishaq ne ya nufesa yana fadin"Daddy k.."
Hannu ya d'agamin cikin tsawa kafin yace"Kayi min shuru Butulu kawai."
Sai ya tsaya ya kasa gaba ballatana baya Su Mama sai ido yayi kasa,Hannun Zainab ya kama kafin yace"Ina son mgana da kai domin ba zama nazo yi ba"
Da Sauri Mama tace"Mu shiga daga ciki Mana Alhaji"
Wani kallo ya watsa mata Lokaci d'aya yana fadin"Ba ni da wannan lokacin.Nazo ne Ishaq ya maimaita abunda zeey tace ya gayamata.."
Yafada yana bin su da wani kallo ni dai ina gefe ina kallon ikon Allah.
Ishaq ya sausauta murya yana fadin"Daddy da ka shigo ciki don Allah"
Cikin Tsawa yace"Ina da Lokacin shiga ciki ne ballatana naji shirmenka?nace ka maimaita abunda ka fad'amata so nake naji da kunnena"
Ishaq sai ya gyara Tsayuwa yana fadin"Daddy gaskiya na fada mata nace baan iya juran binta Abuja ba sai dai ta dawo nan mu zauna tare"
A wulakance yake kallonsa kafin ya nuna gidan cikin Yatsina yace" A wannan kejin gidan zata zo ku gamutsu da iyayanka da matarka..?
Yafad'a yana masa wani kallo lokaci daya yana kare ma gidan kallo a wulakance,Gabadaya su Mama sun daskare sun kasa mgana Yaya ishaq kuma sai ya sunkuyar dakai ya kasa mgana cikin kakkausan murya ya cigaba da fadin"Na ce a wannan a kurkin gidan kake tunanin y'ata ta bar komai nata ta dawo ta zauna dakai saboda kai ne autan maza ko?
Yaya Ishaq ya dago yana fadin"ammah Daddy.."
"Dakata min shashasha butulu a irin wannan gidan ka ganta ka aureta..?
Nace a irin wannan gidan ka ganta ka aureta da zakace hakkun Dole sai tazo ta zauna da kai a haka..?
Ya fada bayan ya katsesa,cikin Fusata da Bacin rai.
Ya nuna Zainab cikin Daga murya yana fadin"Lokacin da ka y'ta kace kana sonta acikin rayuwar hutu da jin Dadi ka ganta.cikin iliminta da tarin gata ka ganta kaji sha'awanta ka nemi auranta na aura maka ba domin ka chanchanta ba, sai domin nayi maka alfarma ina kallon ka kamar D'ana ashe baka da mutumci ban sani ba..?yar tawa kake so ka saka ka maidamin ita bazawara..?
Yaya Ishaq yace"ni ban ce zan saketa ba"Ya taresa da fadin"Ba ka ce ba kalaman ka me suke nuni..?kace in ta fita kada ta dawo..?so kake ta ijiye rayuwarta da Aikinta da komai nata tazo ta tare a wajen ka, to ka ba ta mene..?Kada kaa manta ko da ka ganta chan ta fara gudanar da rayuwarta bazata iya zama a ko'ina sai a inda ta saba.Bazan lamunci wannan rainin da iskancin ba,in ba ma kana Butulu ba an dauke maka nauyin ya'yanka na Dauke ma nauyin gida da zirga zirgan ai duk hakkin ka ne sannan na Dauke maka nauyi ita kanta Zainab din hakan ma baka gode ba kawai naka ka shiga mota ka rika zuwa kana dubasu ne zai zame maka matsala..?batulci zakamin ko kuwa zafin Talaucin ne yasa ka fara Nuna min akan ya'ta..?
Ya fad'a yana kallonsa cikin fusata,Sai wajen ya Dau shuru Mama bakinta yayi nauyi sai Anty Binta ta rika ma alama da tayi mgana itace tayi karfin Halin cewa"Alhaji ayi hakuri duk mganar bata kai haka ba a zauna a warwareta"
Ko kallo bata ishesa ba yace"Zan iya warware mganar ko wata iri ne ba sai na zauna ba,Kan ya'yana zan iya shari'a da ko waye na lura D'anku baisan? mutumci da Hallaci ba,duka abunda nayi mai bai gani ba in na barsa da Dawainiyar Zainab din zai iya Dauka ne..?to bai isa ba ku fadamasa bai isa ba.ba haka na aura masa yata ba kuma bai isa ya dawo min da ita haka ba, zan tafi da ya'ta kuma ya zama Wajibi ya janye kalamansa a kanta,Domin shima yasan hakan bazai taba yuyu ba ni ba sakaran Uba ba ne kan ya'yana sai nayi shari'a dakai wlh."
Abun mamaki Yaya Ishaq sai gashi ya kasa mgana Har da mama,Anty Binta ne ke bada Hakuri yace sai Ishaq ya janye kalamansa,Mama ta kallesa tana fadin"Kana ji ana mgana kana banza da mutane shashasha kawai"
Ransa bace yace"Na janye kalamai na"
Da sauri Mama tace"Ya janye Alhaji don Allah kayi hakuri Zainab kema ki yi hakuri don Allah"
Bai ko saurare su ba ya kalli yarsa yana fadin"Ina fadil.?
Sai ta juya tana neman Badariya ita ko daman tana dakin Mama tana ji ta fito da Sauri yako karbesa ko kunya yaja hannunsa yarsa ya dago yana kallon su Mama da suka yi Tsumu tsumu,Lokaci daya yana fadin"Zan tafi da y'ata zata kuma zauna ta jiraka.Hajiya ki gayamsaa duk bayan Sati biyu zai rika zuwa yana ganin matarsa da yarsa in kuma yaki jin mganata wlh tallahi zan saka Hukuma aciki saboda tun farko yasan Da Tsarin ya amince da haka sai yanzu zai sauya mganaa..?ina ruwan aikin Zainab da rashin aikinsa..?da zai wuce a kanta..?to zan kai kararsa bai isa ya tozartamin ya' ya zauna lafiya ba.in kuma bai ji mgana ba zan nuna masa waye lawal bako dan mutanen Adamawa"
Daga haka yaja hannun yarsa ita kuma ta dauki Jakarta suka fice Daga gidan,Sai aka rasa tsakanin Mama da Anty Binta ko Yaya Ishaq wanda zai motsa ni ko Allah ya kyauta nace araina na cigaba da duba dahuwar zobo na,Mama da ranta ya gama baci da Ishaq ta kallesa tana fadin"Ka kyauta ga abunda taurin kanka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login