Showing 141001 words to 144000 words out of 288345 words

Chapter 48 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

773

yara a karatu ne"
Ban dire ba ya tareni da fadin"Ko kina menene in na kira ki na sakaki aiki zaki ijiye kizo ballatana gyaran Shimfidar miji. Kin ga jiya kin kwana mala'iku na fushi da ke"
Mamaki ya bani na kallesa sai yace"Eh mana ai kin fini sanin haka tunda Lokacin kina gaban Mama a kwai ki da son zuwa islamiyan nan ta la'asar"
Araina sai nace ashe ya sani ganin ya nace da mganar ne yasa nace"To kayi hakuri"
Nan da nan yaji dad'i ya washe baki yana fadin"Yauwa ko kefa yar albarkata. Ina fatan in nakara kiran gyaran Shimfid'a baza'ayi min gaddama ba ko?.sai na gyada mai kai saboda ya kyaleni aiko bai barni ba. sai ya rika jana da Hira yana shigemin ni ko ina baya baya labarai har da wad'anda basu Shafeni ba abun mamaki har yana tambayata yaushe zamu je karofi mu gaida su Goggo..?
Sai kawai nace ranar da ya shirya sai yace sai weekend saboda yara.
Ban ko tsaya mamakin sa ba domin yanzu ya daina bani mamaki in dan yayi wata mganar ko ya yi wani abun.
Jamal ya yi shirin komawa makaranta acikin kayan abincin mu na dibar mai Taliya da shinkafa da man girki sai na bashi Dubu goma, biyar yayi pocket money, biyar yayi na mota nace in na samu zan bama yayansa ya Tura masa ya karba yana ta godiya har yana fadin"Allah ya kawo babban Shago Matar bro.'
Ina yar dariya na amsa mai da Ameen haka ya tattara ya tafi to yayan bai da ko sisi yana nema nema. itama kanta Maman bata da shi kawayenta duk sun gajeta ba wacce tafi bani mamaki sai Hajiya Barira bata zo ba tun bayan da Yaya Ishaq ya fito Sannan Mama ta shirya taje gidanta bata sameta ba,Kuma bata biyo sahu ba kuma bata Hakura da binsu ba shine da yagaji ya yi mata mgana fadi yake yi"Mama yanzu rayuwar nan ba irin da ba ne. In kana da shi ayi dakai daga Lokacin daka rasa bamai son rabarka ka zame masa wahala Mama.ni kaina alokacin da nake dashi abokai har da na banza kuma ai mun taimaka musu ammh yanzu ko kare bana gani ballatana kira an san bani da shi kowa Tsoron haduwa dani yake yi kada na gayamasa matsalata"
Ko nace ya taimakeni"
Mama ta gyada kai tana fadin"Uhm nagani,ammh na Dauka ko kowa zai gujeni ban Dauka harda Hajiya barira ba, ta bani mamaki kamar mafa blooking dina tayi fa"Dariya yayi yana fadin"Shi yafi komai sauki Mama bazata yarda ku hadu ba, tasan baki da shi yanzu zaki yi Tunanin samun wani abu daga barayinta, a baya kina da shi kuna nima ina dashi kinga dole ta rab'eki ki kama kanki da kowa kawai ki Rumgumi kaddaranki Mama kina gani ko a yan'uwa sai wanda yaga Allah ne yake tunawa dakai in ka shiga Halin babu, sai kuma wanda ma kake tsammanin zai tsaya maka ranar da baka da shi, sai kiga shine ke baya baya dakai. wanda ka gujema Lokacin da kake da shi shine in ka shiga Halin Rayuwa zai taimake ka"
Mama na hawaye tace"Hakane wlh nagani Ishaq"
Tana tuna Hajiyar Dala ko wayarta bata son dauka yanzu. Ammh Goggo ko bata zo ba zata aiko da Sakonta tabbas Lokacin da suke da shi basu mu'amalance ta da kyakyawan mu'amala ba,ammh ita bata rike su ba ta Duba zumunci ta kuma bi Umarnin Ubangijinta..
Nan ya fice yana fadin"to haka halin mutanen duniya yake Mama Lokacin da kake da shi ayi da kai, in kuma baka dashi ayi da wanin ka"



*Janafty*



*KNKB2009*

*Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488*


Haka muka cigaba da lallab'a Rayuwarmu yau fari gobe Tsumma. abunda aka samu aci agode ma Allah ba domin ina samun,masu son Turaruka ba,da tuni jarin Zobo da kunin aya sun Dargane da Hidiman gida na yau da kullum,To riban da nake samu na turarukan,sun fi
na su auki. da shi nake had'awa muna rufa ma juna asiri sannan Allah ya sanya ma kasuwancina Nasibi komai na yi sa sai ya kare kuma ana nema,Shi kan shi Yace min ya gaji da zaman gida ba abunda yake yi ranar har ce min ya yi ko zan fara doramai zobon da kunin Aya ne yana zuwa tasha ya zauna min..?
Sai da naji kwallar Tausayinsa na kallesa yana bakin kofa zaune duk ya rame ya lallace ba wannan farin ba kyau ba fafa ba,kwanbo rayuwa kenaan.
A lokacin ban ce mai komai ba sai da ya karamin mgana sannan nace mai"Ko fita da shi baka ga inayi ba, a gida ake siye shi. Kai ma da wata mgana ka ke"
Cikin bayyana yanayin dayake ciki yace"Bazaki gane ba ne Fa'iza wlh na gaji ne ko Dako zan je na fara ne..?
Na kallesa ina maimaita"Dako..?
Sai ya gyad'amin kai yana fadin"Shima sana'a ne kuma akallah zan rika samun wani abun da zan rika taimaka miki da shi"
Da sauri nace"Aa ka bari dai mu yi Tunanin wata sana'ar tukunnah"
Da haka ya bar mganar tunda muka yi wannan mganar sai ta Dameni sai naga yana da gaskiya shi magidanci ne,zama agida kad'ai ya isa yasa bawa Damuwa na yi ta tunanin sana'ar da zai fara ban samu mafita ba, yanzu fa ko wata sana'a ta kudi ce sai kana da shi,ni kuma d'an jarin nawa kad'an ne Riba kuma agida muke cinye su don ma yan'uwa suna ta tallafawa.
Babban sallah tazo tana matsowa bani da matsala tuni na wanke ma yara kayan su na goge ga kuma na wajen Zainab, daman basu saka ba,ni daman bani da matsala in dai ya'yana zasu saka su fita cikin tsara Allah ya gama min komai Mama bata nan ta tafi Yamai da Hure zata koma sai ta bita,tafi wata achan ina jin Yaya Ishaq na fadi'n kila chan zatayi sallah Sai kuma naji gidan ba Dadi ba Mama ko yaya mutum yake? Rahma ne haka ma yaran su yi ta fadin"Daada yaushe Mama zata dawo..?sai yace"Zata dawo in sha Allahu"
Ga Hafsah ma sun yi Hutu ta koma korafi tayi ma su Goggo Hutu, Badar kuma tana gidan Anty Binta suna ma Jarabawar Fita ne bayan sallah zasu gama makarantar gabada'ya ita da Raliya tun nesa da kofa tazo ta sameni tace min"Anty Fa'iza zamu gama makaranta akwai kudin riga da zamu yi na graduation din mu, wajen dubu ashirin ake so kowannen mu ya bada kinsan ba ni da shi Mama bata da shi ko da ta na nan Yaya ne kuma kina gani kece komai nasa yanzu,Anty Binta kuma bata ta kaina da na fara mata mganar kudi zata fara masifan itama bata da shi ke kad'ai gareni Anty Fa'iza don Allah ko rabi kika ragemin bakomai nagode".Sai ta bani Tausayi wane ni na manta da Badariya da Sanadinta na samu Rufin asiri, batare da sanin kowa ba na bata Dubu goma nace zan cika mata in na samu shima Dubun goma Sa'adatu ce chan inda muka taso ta samo min wata mata mai son Turare Humra,to da yake ina da Sauran kayan amfani sai nayi mata amfani da shi na samu ba laifi,Sai na koma ina Fafutukar yadda zan sama mata cikon sauran ga shi kuma salla ya matso,Allah ya taimakeni na samu aikin zobo da kunin aya na masu son da yawa da sallah dakyar na had'a mata dubu biyar na kara mata godiya har da kuka ta Rumgumeni tana fadin"Nagode miki Anty Fa'iza yadda kike jin kanmu Allah ya baki wanda zai ji kank'i watarana Allah ya Dauwamar da farinciki da arziki da wadata acikin rayuwarki gabad'aya"
Na amsa mata cikin fara'a ina Fadin"ke meye na kuka share hawayen ki ko sai na kira miki Ya'yan ki ne..?jin haka yasa ta goge Hawayenta,ni na hanata nace ko yayanta kada ta fad'amawa ana saura kwana Hudu sallah tazo da murna tana Fad'amin Hajiyar su Raliya ta biya mata kudin sannan ta bata dubu goma tayi dinkuna sai tace zata maidamin da kudina na riga nayi niyya sai na karbi biyar din da na bata Daga baya na barta mata goman nace tana da bukatu tayi amfani da shi,Badariya ta yi murna tayi murna kamar bakinta zai yage addu'a kam na shata ni ko tana da Muhimmancin da bazan manta da alherinta gareni ba.
Atamfa taje ta siyo da less sai mayafi da takalmi da jaka,Sai kayan shafa ina D'aga kayan ina fadin"Ehee! kaga yan mata."
Tana Dariya tace"To Anty Fa'iza mace sai da kwalliya mazan nan, kuma suma kyale kyalen suka fi so"
Na aminta da mganarta yasa nace"Hakane Allah ya kawo miji nagari"ta amsa tana rufe fuska ni kuma ina binta da Dariya sai da Yaya Ishaq yaga kayan ne ya tsareta sai ta fad'amai gaskiya kallo na yayi yana fadin"Lalle kina da d'aure ma karya gindi ke baki bukatar kayan kwalliyan sai ita..?
Ina dariya nace"Me Fa'iza zata yi da kayan kwalliya ai wannan sai irin su Badar mata masu kyau da nasaba"
Ita Badariya bata gane mganata ba sai ta karb'e da fadin"Kai Anty Fa'iza wlh kwalliya bata zaba bace.Mu mata kowa yasan yan ado ne da kwalliya"
Shi kuma da yasan kan mganata sai yayi gum ya koma yana kallona ni ko na basar da shi,Daga ni har shi bamu san Zainab da yara zasu zo mana sallah ba,Mun samu tallafi shinkafa da naman sallah Daga gidan Hajiya Daga Korofi kuma Goggo ta aiko mana da kaji da kayan miya mangyada su maggi da sauran Cefane,an yi idi lafiya an sauko ranar nayi mana? shinkafa da miya sai nayi mana cowslow,Sai zobo da kunin Aya Saboda Sallah Jamal ma ya dawo da da bai da kudin mota, yayan yace ya zauna chan yayi sallah nace hakan bai kamata ba na hada dubu hud????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? 'u aka turamai nace ya taho gida yayi sallah cikin yan'uwansa.
Ranar idi da yammah sai ga Direba ya kawo zainab da yara,Gida sai ya Rud'e da Murna su Anum nata tsalle da Murna ganin kannensu Farhan na ganina ya Nufeni bakinsa har kunne yana fadin"Umma.."
Na daukesa na daga sama yaro kamar balarabe wajen kyau yana bangalamin Dariya nace"Farhan d'an Umma"
Tazo da naman sa an soya tare da naman kaza anyi pepe dinsa ga su cake samosa da su sprill role, ta zo da kantan kantan na lemuka da biskit, ta ce min Saboda sallah ko kuma in mun yi baki,Nace mata"Angode. Sai dai gaskiya sai kunin aya da zobo ya kare tukunnah"
Tana dariya tace"Ga abun arziki wazai bi ta na kwalayen bature masu shegen zaki"
Ishaq basa gidan shi da jamal sai dai suka dawo suka ganta kuma daga alamu uban gayyar yaji dadin ganin matarsa, Dakin mijinta na Sauketa,Yaran kuma suna tare dani Direban daya kawo ta bai koma ba. tace zai tsaya sati d'aya zasu yi zai maida su sai aka sauke sa Dakin Jamal.
Sosai wannan sallar tayi mana Dadi,babu abunda yafi kwanciyar Hankali Dadi ni nake hidiman abinci na gida da na yara, Zainab sai da tana tayani da Hiran duniya,Farko da na sauke Zainab a dakinsa samu na yayi yana min mgana wai meyasa sai Dakinsa na sauketa,dakina fa..?
Na kallesa ina fadin"Saboda mene?sai mu gamutsu da ni da ita da Anum kamar ba bu wani da'kin..?
Kuma nan din ta saba sauka in tazo a Dakin naka shi yasa na sauketa anan"
Sai kawai ya juya yana fadin"Ki bude dakin Mama ki sauketa anan mana"
Mamaki ya bani Namiji sai a barsa da gulma ya gama wannan borin kunyan, sai ga shi suna kulewa a daki bamai jin su ammh yazo zai min dad'in bakin su na maza.
A gida muka cinye sallar mu sai ranar washegarin sallah da kwana uku Zainab ta matsa sai na shirya mun fita. da zamu tafi,na saka atamfata da Hajiyar su Raliya ta dinka min,Zainab tace ban isa ba ta dinka mana Less mai kyau iri d'aya,har dinki daga Abuja aka dinko ta matsamin sai na saka Saboda kada tace ko ban karb'i kyautar nata ba ne,yasa na saka Doguwar riga A shape dinkin ya fita haka ya fitar min da Shape dina in kika ganni a lokacin bazaki taba yarda na haifi Yaro dan shekara sha biyu kamar Amir ba.
Ina nan da kuruciyata sai dai kowa yasan Fa'iza yar gargajiya ce,ammh zainab bata barni haka ba,Hijabi na saka tace ban isa ba Dole na Dauko mayafin data aikomin da shi da Takalmi da jakata na saka,sai gani na fito ras dani na yarda da Hausawa da sukace kowa ya gyara ya sani ni kaina sai nake ganin kamar bani ba.
Zainab ta kalleni sama da kasa kafin tace"Komai yaji ban da abu d'aya"
Ina dariya nace"Ban yi kyau ba ko..?
Sai tace"Aa fa.Lalli ne yayi miki cikas"
Sai kawai na wuceta ina fadin"Lalle ai naku ne na fararan mata yan gayu"
Domin tayi nata Hannu da kafa, abun ka ga farar fatar kamar don ita aka fito da zanen jan kunshi tana bi na a baya muka fito daga daki Lokaci daya tana fadin"Wlh ko ke kika yi ba karamin kyau zai yi miki ba Maman Amir"
Ina jinta ban ce mata komai ba, ina jan abu zai fito a wannan bakar fatar tawa ina fitowa yaran na Falo suka dago suna kallon mu sai kawai Anum da Amir suka hada baki wajen fadin"Laa! Umma kin yi kyau wlh.."
Musty da Ahmad ma suka karb'a Farhan na jin haka shima yace"Umma jin yi kyau"
Fadil na gauranci yace"Chauu.."
Gabadaya muka saka Dariya,Ni na sabe Fadil na rike yaran duk sun ci yan kanti mazan kaf iri d'aya Zainab tayi musu Anum kuma an cakare da Doguwar riga da takalmin yan gayu Badariya ta kaita akayi mata jan kunshi da kitso da yake bata dauko suma na ba,tana da gashi an yi kitson gaba yaji bit sai yanga take da farko ma kin saka Hijabi tayi sai da nayi mata jan ido,Zainab ta hana sai ta Dauko mata wani karamin mayafi ta nad'a mata, muka fita daman ta fad'ama megidan zamu fita gari gidan Anty Binta mu gaisheta yace to.
Ban kulle dakin ba tunda suna waje da Jamal jakata na Hannun Amir na Zainab na hannun Anum ta kama ta rike in ka ganmu bazaka taba cewa muna cikin wani hali ba,ko mijin mu bai da aiki ba kila in an fad'a maka ma bazaka yarda ba.
Suna tsaye suna mgana da Jamal yaran suka fara fitowa ganin su shar da su yasa yafara washe baki Jamal ne yace su? jere a dauki Hoton Tarihi ko da muka fito har Baban duk suna ta Hotuna Zainab ce a gaba sai ni a baya ina rike da Fadil zainab nata min Tsiyan na nad'a mayafi a kaina,nace mata ban iya saka shi a saman kafad'a ba ne.
Tunda muka fito idonsa ke kaina kallo kamar zai fad'i,har yana wani bude ido sai ji nayi kawai ya kira sunana"FAA'IZAAA...!
na dago ina kallonsa Fadil dake ta mika masa hannu alamun ya Daukesa bai ma gansa ba ya saki baki da hanci yana kallona Ya nuna ni yana fadin"Fa'iza ke ce.?
Sai dariya ta kamani nace"Ba Fa'iza ba ce Wannan Uwar Fadil ce"
Sai nan ya gano abun da yayi sai ya fara sosa keya Jamal yayi dariya yana fadin"Matar bro ba bro ba,koni ban gane ki ba da farko".
Hararansa nayi ina fadin"Uhm ka manta ne"
Karaf ko Anum tace"Daada yaga Umma tayi kyau ya saki baki yana kallonta"Zainab ta kwashe da Dariya tana fadin"Yes my Daugther"
Sai kunya ta kamani na sadda kaina ya matso ya karbi fadil daga hannuna ammh sai da ya gogi jikina Lokaci daya yana fadin"kin yi kyau,Sannan kamshin yayi dad'i"
Sauran Humran da nake hadawa ce in ta ragu sai na ijiye ban ma cika shafawa ba yau ma Zainab ce ta matsamin sai da na shafa,da sauri nayi baya ina yake sai ya basar ganin Zainab kusa dani sai ya kalleta yana fadin"Matan Abuja sun yi kyau"
Hararan soyayya tayi masa tana fadin"Ai yanzu ta zama matar katsinawa"
Dariya mukayi gabad'aya Fadil ne ya fara kuka yana mika hannu muna juyawa muka ga yara har sun rigamu shigewa mota nayi dariya ina fadin"Dole fadil yayi kuka yaga za'ayi masa kan ta waye"
Mikamin shi yayi yana fadin"Sai kun dawo, kada kuyi dare jamal fita zai yi ni kad'ai ne agidan"
Zainab ta wuce tana fadin"Honey sai fa mun zaga gari ka ma yi hakuri kawai"
Ni dai ban ce komai ba muka shige mota wata bakar Jeep ce kaf ta Daukemu su Anum an kame agaba kamar motar gidan su dariya ma tabani,Gidan Anty Binta muka fara zuwa mun iske har su Anty Mahma,suna gida sun yi mamakin ganin mu dukkanmu a tare sannan cikin shiga mai kyau Anty Binta haka take ta kallona kamar idonta zai fad'o ina gaisheta ta amsa min cikin wani yanayi.Anty mahma ko ihu ta Buga tana fadin"ku zo ku sha kallo wajen Hajiyar Zobo da kunin Aya"
Badariya na gidan tace"Kin manta harda Turaran humra da kwallacha"
Dariya suka bani Zainab tace"Maman Amir yadda kika san bata haifi Amir ba"
Anty mahma tace"Fa'iza nada jiki mai kyau gaskiya"
Mun dade agidan kafin mu yi sallama Anty Binta dai sai kallo na take har muka tafi, sun yi mgana da zainab tace yaushe tazo tace shekaran jiya Daga gidanta Badariya ta biyomu muka taho tare da ita,jin nace har gidan hajiya zani mata yawan sallah.
Ba gidan Hajiya mukaje ba da muka fita ba,sai da muka fara zuwa anguwan da muka tashi. Allah sarki gidanmu an buge sa ya zama sai Filin gwamnati Sa'adatu da Habiba sun yi murnan ganin mu sosai,na kullo musu nama da lemu da Zainab ta zo mana da shi, duk wanda yayi maka mutumci kada ka manta da shi, gidan Hajiya sai yammah muka je bata gidan sai su Raliya da yayyinta da suka zo sallah, ammh sun kirata a waya nan muka yi sallar mangariba muka ci abinci sai gata ta Dawo tana shigowa su Anum suka nufeta suna oyoyo Hajiya ta tarbesu tana fadin"Oyoyo Ya'yan Hajiya"
Zama tayi muka gaisa Zainab ta gaisheta ta amsa sai na gabatar mata da ita sai ta kalleta tana fadin"Maraba


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login