Showing 276001 words to 279000 words out of 288345 words

Chapter 93 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

755

hannu.
Sakin su Amir yayi ya rumgumosu yana Fadin"Yauwa ya'yan Umma da Baaba.."
Harda su Farhan daya bayan Daya ya dinga dagasu yana kuma kiran sunayen su mamaki ya cika su Musty yace"Kai ya sunan ka tunda mu kasan sunan mu.?
Yana dariya yace"Ni sunana Baaba baka ji su Amir sun kirani da Baaba ba..?
Musty ya kallesa ya kara kallonsa kafin yace"Baaba..?
Cikin alamun tambaya ni ya kallah alamun hakane..?
Ina shirin nayi mgana sai kawai muka hada ido da Yaya Ishaq ya kureni da ido sai na kasa mgana na maida kaina kasa.
Ahmad ne ya yi karaf yace"Sunan ka da mamanka ta saka maka"
Engr ya kwashe da dariya,irin Dariyan da yake yi in yana jin Nishadi. kafin yaja kumatun Ahmad yace"Sunana da mamana ta sakamin Abdulbasit ne."
Zai kara mgana Anum tayi saurin cewa"Ahmad shima Baban mu ne kamar Daada.."
Sai ya washe baki yana Fadin"Baaba..Sai su Farhan suka Dauka shi kuma yana ta amswa da Fara'a ina ganin Fara'ar take fuskarsa ta kaunan yara acikin idanuwansa.
Zainab ta ce mu karisa ciki muna Tsaye sanda ya mike Dauke da Farhan da Fadil lokaci daya yana rike da Hannun Ahmad,Su Anum suka bi bayansa kallona yake yi da alamun nagode Fa'iza kin ga ma bani komai. Tunda kika saka na zama Uban ya'yanki nima.
Sai da muka kariso falon naga Mama ita tafara gaisheni sai na sauko daga kan kujera na duka ina gaisheta har Gaban Abada Mama uwa ce agareni bazan taba kin darajata ba ta amsa cikin Fara'a da nauyi.
Engr ma yadda nayi haka yayi sai naga Mama na kauda kai tana sharan kwallah fadi take yi'"Allah ya baku zaman lafiya Allah ya kad'e Fitina"
Ba kunya Engr ya rika amsawa da Ameen Ameen.
Sai alokacin na iya dagowa na gaida Yaya Ishaq ya amsa fusakarsa cikin yanayin da ban gane ba.
Zainab Shema'u ta saka ta kawo mana ruwa da lemu,yaran kuma suna tare da Engr duk tambayan da suka yi masa sai ya basu amsa shi fa yadda yake iya zama da manya haka yake iya zama da yara kafin wani Lokaci su Ahmad sun saki jiki da shi. Ishaq na gefe kamar mutum mutumi sai dai mirmishi kad'ai yake yi.
Allah kadai yasan Halin da zuciyarsa take ciki alokacin,Wlh tallahi bai taba sanin haka yake tsananin son Fa'iza ba sai da ta auri waninsa. A yadda yayi fama da zuciyarsa akan soyayyar Fa'iza ya tabbata ko Zainab da take zabinsa bai sota haka ba.
Ya shiga jarabawar rayuwa da baya Fatan wani ya shiga irinsa Son matar da ba Muharaminsa ba,tunda Zainab ta fad'amasa zuwan Fa'iza da Engr ya rasa natsuwarsa sai yaji abunda ya Binne na soyayyar Fa'iza na neman taso masa, ganinta da yadda ta sauya sai ya kara Saranda ya tabbatar ma kansa Fa'iza ta samu wanda ya fisa komai da komai sannan ganin irin kaunar dake idanuwan Engr ya tabbatar masa da cewa in ba ta Allah ce ta kasance ba Har gaban Abada Fa'iza tayi masa nisa nisan da ko shekara Dari ya yi yana Gudu bazai iya cimmata ba.
Ganin Fa'iza da yayi yau da irin sauyawar da tayi sai Shed'an ke kawata masa ita zaune yake ammh Kamar baya cikin hayyacinsa yak'e kawai yake yi Mama ta fad'a masa ya cigaba kawai da addu'a ammh fa Jarabawa ce da alhakin Fa'iza ke Bibiyansa shi yasa Allah ya Dora masa kaunarta alokacin da ta riga tayi masa Nisa mai tarin yawa.
Yana nuna kamar ba ni yake kallo ba, ammh ni kaina na takura saboda duk sanda na dago ido shi nake ganin idanuwansa a kaina,Na dauka Engr bai gani ba ashe karyan so na ma yake yi. duk motsinsa yana gani sai dai ya barsa kamar bai gani ba.
Anum ce ta dawo kusa dani muna ta Hira kasa kasa Zainab kuma ta shiga Kitchen in ma abinci ne cikin mu ya cika ruwa kadai na sha Engr ne kadai ma yasha maltinan da aka kawo mana Tunda shi daman yana son maltina.
Mama na gefe bata sakamana baki nice ma na sako mata mganar Badariya,yasa ta dan saki jiki muna mgana da ita,har take fadamin kwanaki tazo ma tayi sati,araina nasan wani abu ya faru ammh tunda bata fad'amin ba sai ban nemi na sani ba.sai dai na fadamata zan je in sha Allahu in na koma Abuja.
Muna zaune Zainab ta kawo abinci ina ganin haka nace"Anya abincin nan..?mun koshi gidan Anty Fadila"
Zainab tace"Tab kun ma isa..?
Nan fa kamar Dole ne"
Dariya nayi ban kara mgana ba,Da gaske muke yi mun koshi saboda kada su ji ba dadi sai Engr yace zai ci shi da yaran shi ni kuma sai Mama tace Zainab ta sakamin mu shiga ciki zan fi sakewa.
Haka ko akayi har Dakinta ta kaimin Farar Taliya ce da miya ba wani Taste ma,ba kayan lambu,sai dai naman Rago da akayi miyar da shi,Dagani kila Shema'un ce tayi girkin domin gadai shi nan ne,Tsakura nayi kadan Saboda kada taji ba dadi ban ci ba na sha ruwa saboda bakin lemu ta kawomin ni kuma bai cika damuna ba na fi shan Madaran Hollandian ko Nutri ko Fresshyo.
Nan da nan Hira ta Bude a Tsakanina da Zainab tunda yaran Engr ya janje su ban damu sanin da ni da shi Duk Daya ne,Sai daga baya Anum ta shigo sai Zainab ta fita ta bamu wuri,Amir ma ya biyota sauran yaran ne ke falo wajen su Engr.
Na saki jiki muna Hira da su bansan Lokaci ya tafi ba sai da Zainab ta shigo tana fadin"Maman Amir daman ba nan zaku kwana ba..?
Ina rike baki nace"Kwana kuma..?haba masauki zamu koma"
Zainab tace"Ai yanzu yake fad'a nace sai dai shi ya tafi ya bar mana ke ki kwana zuwa da Safe don Allah"
Kuma yace shikenan in kina so sai ya barki din"
Har ga Allah nima zan so na kwana din tare da ya'yana ammh ban nuna hakan ba sai da na kintsa kaina muka fita falo muka iske har Engr yasa an shigo da Tsaraban yaran sun bude a falon suna ta murna.
Muna fitowa Engr ya mike yana fadin"Dare fa ya yi Faa'izaa.."
Kallonsa nayi kafin ma mayi mgana Zainab ta rigani da cewa"Ba nan zaka bar mana ita ba yallabai..?
Sai Engr ya kalleni cikin yanayin sa kafin yace"In tana so sai na barta.."
Yanayin mganarsa da kallon? da ya yi min yasa nasan mganar ba har zuci ba ne duk da ina so ammh bazan yi abunda zai bata ma mijina rai ba.
Da sauri nace"Zainab ki bar mganar kwana gobe fa zamu tafi kano .In sha Allahu in muka dawo zan kara zuwa yara kuma in sun samu Hutu ina Biko su zo min Hutu don Allah"
Zainab ta marairaice kafin tace"Kai mamam Amir naga megidan ya bari"
Sai kawai nayi mata yake,Engr dai bai yi shuru ba yace ma Ishaq yana neman alfarman su Amir suzo mana Hutu murya ba karkashi yace"In sha Allahu"
Har dakin Mama muka shiga yi mata sallama Engr ya bata kudi ban san ko mawa ba ne tana ta godiya,mun fito duka har yaran suka rakomu suna na ne dani suna rigiman sai sun bini Ahmad da su Farhan kenan ni kuma ina Lallashin su da cewa in suka yi Hutu za'a kawo su gidana su yi kwanakin Hutun su.
Alokacin ne Ishaq ya nemi gafaran Engr shi kuma yace bakomai Bai taba rikesa aransa ba.
Har Mama sai da ta rakomu wajen mota sai da na fara shiga sannan Engr. Zainab na d'agamin hannu ita da yaran Ishaq ya leko ta barayina yana Fadin"Ki yi hakuri Faa'iza da abunda ya faru a baya"
Ina mirmishi nace"Bakomai.."
Yayi min mirmishi na maida masa nima,suna d'agamana hannu har Motarmu ta tashi,sai da na share hawaye Engr ya jani jikinsa yana Fadin"Kiyi hakuri kin yi kukan nan fa har kin gaji.."
Sai na kasa tsaida kukana jina acikin jikinsa shi kuma bai gaji ba yana aikin Lallashina yana fadin"Naga kin so ki kwana ki yi hakuri zuciyata bata iya barin ki,ki kwana gida daya da Ishaq ba. Bazan iya ba Faa'izaa ki yi hakuri.."
Ban ji Haushinsa ba na dago kaina ina Fadin"Nima kayi hakuri"
Mirmishin ya yi min kafin yace"Nayi miki afuwa tun kafin ki rokeni"
Ki yi hakuri na roki Ishaq d'in in sun samu Hutu lokacin mun zo Abuja zasu zo mana in sha Allahu"
Da irin kalamansa ya gama lallashina har muka isa masauki ya bama mai Taxi Atm ya cire kudadensa masu yawa.
Ranar min jima bamu barci ba,muna Hiran yaran Engr na yaba ma Zainab da Ishaaq tunda yaran mun gansu Tsab ba cikin wahala ba ni kuma na fad'a masa zainab ko a baya batayi zaman kishi dani ba.
Ta so ni ta kuma kaunace ni nima shiyasa nake kaunarta.
Shima kai tsaye yace tunda tana so na shima yaji yana kaunarta, domin shi duk wani mai sona to yana son shi shima.
Washegari karfe 12biyun rana jirgin mu ya tashi zuwa kano,Da muka sauka Direban gidan Hajiya Tafeesu yazo ya Daukemu chan muka fara sauka yar Tsohuwa mai kirki da karamci gida cike ko da Dangin Maa,da ya'yan yan'uwa su karbeni cikin karramawa da Soyayya kamar su lasheni,nan muka kwana.
A shashe na musamman ni da Engr,Hajiya Tafeesu ta sakamana albarka da Fatan zuru'a Dayyiba kamar bakinta zai cire. sai da Safe bayan mun yi wanka muka shiga gidan su Ammi na gaishesu ,bamu jima ba Daganan muka je gidan Yaya Asiya Engr ya kaini da kansa cikin Daya daga cikin motocin gidan ya kuma barni chan na kwana wajenta itama tana ta zuzuta kyan da nayi.
Mun kwana muna Hirar rayuwa ashe Zuwan da Mama tace Badariya tayi gajiya tayi da wahalan uwar Yusuf da matansa har takai basa bata abinci maman na kulle Store shine tayi yaji taje Lagos sai da Yusuf yaje ya Daukota da kansa,to gwara ma Badariya Labarin Halisa ba Dad'in ji Yaya Asiya ta fad'amin miji duk ya saida kayan dakin Halisa tunda Dila me na yan kwaya yana sha kuma yana Saida ita.
An taba ma kamasa dakyar aka sake shi Fad'a kuma ya kacame tsakanin Anty Binta da ya'yan Hajiyan Dala akan tace ai susan halinsa suka yi shuru ya auri yarta,Fada har da Gore gore,A raina nace Dara taci gida.
Kafin Engr yazo ya Daukeni sai da Yaya Asiya ta rakani gidan Halisa ya ma saida wannan gidan sun koma gidan Haya,wajen su goma agidan daki Ciki daya Halisa har sai nayi mata kwallah Rayuwa kenan,da zamu tafi Dubu biyar na bata ta amsa tana ta min godiya muka fita muna Tausayamata.
Ranar yawo muka sha agari mune har Shoprite ba inda bai kaini ba sai Dare muka dawo,washegari muka tafi Dutse gidan Nana Fatima,mun ko ga Tarba Nana Fatima tayi zencen sauyawata har sai da nagaji har addu'a ta rika yi Allah yasa ciki gareni. ni kuma in mata Dariya Engr ma ya hade da mijinta suna ta shan Hira abun su agidan muka kwana Barayin megidan suka barmana mu da zamu yi kwana daya sai gamu mun yi biyu. Ranar yawo muka fita cin abinci mu da su da yaran sai dare muka Dawo sai washegari muka koma kano a ranar muka bi Jirgin Dare zuwa kaduna.
Gidammu muka sauka bamu kira kowa ba,Saboda muna cikin gajiya sai da muka yini muka kwana sannan mukaje gida.
Sai dai su Abba suka ganmu kamar Daga sama,Ammi sai da ta Rumgumeni ita da su Hafsatu suna ta min Ihun wai na zama kamar black american.
Nan Engr ya barni sai Dare yazo ya Daukeni tunda sun ma fita tare da Abba ne,da zamu tafi Abba nata sakamin albarka ko bai Fada ba nasan yaji Dadin ganina ahaka.
Engr hutunsa ya kare zai koma bakin aikinsa sai yace zamu je Karofi mu gaida su Goggo,daganan Abuja zamu tafi chan zai barni ya koma Edo in ya Sake dawowa sai mu koma tare.
Haka ko akayi sati daya muka yi muna Hutawa a kaduna na sake Dibar wasu kaya tare da Hafsatu da Nana Khadija muka tafi sun gama jarabawa har sun samu hutu.
Arana daya mukaje karofi muka Dawo,Inno daman tana Karofi cham muka sameta,mun je har gidan Yaya Mariya sannan mun shiga Dutsemah gidan da Tamadina tayi aure Engr ya yi musu Kyauta,daganan mun shiga katsina har gidan Hajiya na kai mata Engr ta gansa tana ta Saka albarka,ban manta da makotana ba Sa'adatu da Habiba na kuma saka Engr yayi musu alheri suma suna ta Mgaanan na sauya na zama kamar bani ba.
A katsinan muka kwana Hotel ya kama mana washegari muka Dauki Hanyar Abuja a mota,daga ma'aikatansu na kaduna aka bamu mota da Direba,gidan su Papa muka Fara sauka sai Dare muka karisa gidanmu su Hafsah ganin su kafaya suka ce nan zasu kwana Maa tace a barsu muka rabu suna ta godiya da Tsaraba.
Engr yaji dadin zaman su gidan su Papa yace gwara su bar shi yayi kara'in bankwana aivko ya yi. kwana Biyun nan mun yi soyayya kamar bazamu kara had'uwa ba.
Ranar lahadi ya Hau jirgi zuwa Benin,ya barni cike da kewarsa ba domin Su Hafsah ba da na sha kewa ko da yake ga su Kafayatu.
Sai da gajiya ta sakeni na samu sararin kiran mutane muna gaisawa.





*Janafty*




[8/2, 7:21 PM] Hauwa Galadima: *KNKB3020*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*


*Prologue*
*Ina rubuta muku wannan shafin alhinin kewarku da zan yi*. Na gode wa Allah da ya haska mini wannan labarin*.
*Na kuma gode muku. Dan haka wannan shafin kacokan sadaukar wa me ga duk wacce ta saka ku'dinta ta siya. Na gode, Allah ya saka da alheri*.
*Sai mun sake haduwa a sabuwar tafiya nan ba da jimawa ba*.
*Janafty tana muku albishiri din bayan Faiza ta kau ce, Yabi zata bakunce ku nan ba da jimawa ba, cikin littafin BAK'AR TA'ADAH*.
*Son so fisabidillahi*


Tafiyar Engr Edo ta dauke sa kimanin Sati uku da wasu kwanaki ne sannan ya dawo. lokacin su Hafsatu sun gama min Hutun su.
Sati uku suka yi min sannan suka koma saboda an koma makaranta har ga Allah naji dadin Hutun su a wajena tun ballatana ga su Kafayatu da suka saba da su watarana duk gidana ma suke kwana, A taru ayi ta Hira ana dariya Su hafsa na son koyon yarbanci su kuma suna son iya Hausa sosai Diramansu ma abun dariya ne.
Engr kudi ya turomin masu yawa tun yana chan muka je nayi musu shooping kamar yadda yace haka ma Papa ya bada kudad'e yace aje kasuwa su dauki duk abunda suke so.
Maa ma ba'a barta a baya ba. dukkansu kowacce da akwatinta shake da Sabbin kaya da kayan amfani sai wanda ya gani.
Sannan Direba ya kai su har gida sannan ya juyo Abba da Ammi sun kira suna ta fad'an Hidima tayi yawa nace ba ruwana Aikin Engr ne tunda nace haka sai na kashe bakin su.
Sanda ya dawo na fad'amai abunda su Abba suka ce dariya kawai ya yi kafin yace"kyaleni da Rigimammen baban nan naki. ya kirani zai fara mganarsa nace ni sisters d'ina nayi ma alheri ko Haramin ne..?
Ai daganan bai kara mgana ba nasan mganinsa"
Tsungulinsa nayi ina fadin"Uban nawa..?sai da ya yi wata dariya kafin yace"Nima ai Ubana ne. Tunda ya bani ke ammh wani lokacin ki kauda idanuwan ki bayan Uba shi abokin aikina ne"
Dariya kawai nayi ban ce masa komai ba tunda nasan gaskiya ya fada tare na gansu kuma ban isa nasan Tsakanin su ba.
Sati Daya ya yi min ya koma,yaso ma mu koma tare zuwan Hajiya Kudirat Abuja yasa ya barni. bamu tafi tare ba yace sai in dan ya dawo.
Shiyasa gudun zaman shuru na kan je gidan su Papa na yini watarana har kwana ma ina yi Hajiya Kudirat ne ta tsawatarmin akan na rika zama agidan mijina yau da gobe sai naga na Saba,jin haka yasa sai Papa yace su Kafayatu su bini in Oluwatosin ya dawo sai su dawo gida hakan sai ya ragemin zaman kadaici tunda muna tare da su basa dai yini a gida ne suna makaranta sai weekend wani Lokacin ma Ranar Lahadi ne kadai suke gida. ammh tunda muna kwana tare a kallah dai nasan akwai mutane a kusa dani,kuma a baya nasan na yi zaman kadaici ammh lokacin akwai yara suna Debemin kewa yanzu ko bayan kewar mijina har da ta yara ina yi kuma ko da yaushe cikin Tambayar Zainab nake yi yaushe zasu samu hutu Saboda ina so suzo su yi min Hutun su awajena.
A na cikin haka sai ga wayar Badariya daman na jima bana samunta a way??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a tun sanda muka dawo in na kirata wayarta a kashe nayi ta Damuwa har sai da na fad'ama Engr sai yace mu mata mun cika raggon azanci meyasan bantaba karban lambar mijinta ba..?Da sai na kirasa naji ko lafiya sai da ya fad'a naga gaskiyansa kuma ban taba wannan tunanin ba shiyasa akace mu mata karkatattu ne duk ta inda aka gyaro mu sai mun sake karkacewa.
Lokacin da naga kiranta da Zumudi'na na amsa kiran sai dai yanayin da na jita ya fad'armin da gaba cikin damuwa bata budemin komai ba kawai tambayata tayi ina ina..?Nace mata ina Abuja sai ta nemi da in turo mata address din ta manta Dakyar ta iya kawo kanta.
Ban rike anguwan da kwatancen ba Sharifatu na bama ta rubuta mata duk sai jikina ya yi sanyi da na kara tambayan ta meke faruwa muryanta a matukar Shake tace min"Zamu yi mgana Anty Fa'iza in da na zo"
Sai na kyaleta har tazo din,har ga Allah na zata ba ta saka ranar Tafiyar ba,ban dauka da wuri haka ba sai dai a daran da misalin Tara na Dare sai ga Badariya cikin wani yanayi mara Dadin ji da gani tazo a galabaice saboda Tafiyar mota tana ta faman amai ga jikinta da zazzabi.
Na rude sosai da ganin yanayinta Fadi nake yi"Badariya lafiya..?
Ko wani abu ne ya samu Yusuf din..?
Duk bata bani amsa ba tana cikin wani yanayi,tsabar na rude ma na rasa taimakon da zan bata sai su kafaya ne sukace bari su kira Family Doctor din su yazo ya dubata jin haka yasa na samu Tunanin kaita Dakina na taimaka mata tayi wanka,sai rawan Sanyi take yi hakoranta na Haduwa waje daya ga shi ta rame ammh naga ta kara fari kumatunta sun cika sosai.
Suna ko kiransa ba jimawa sai ga shi yazo ya dubata sai ya Dibi jininta yace da safe zai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login