Showing 126001 words to 129000 words out of 288345 words

Chapter 43 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

709

ban ce ba na ba ma Amir dubu biyu suka tafi a ka mishi allurai da mganguna ashe maleria ce ta kamasa,ni iya dakina da dakin yara nake siyan ma mganin Sauro na kunna sai Dakin Mama ban yi tunanin yana jin cizon sauro ba ma.
Abu kamar wasa daga zazzabi sai zawo cikin dare haka ya kwana zagayawa,da safe har da Amai duk? karfinsa ya kare,washegari daga zuwa bayi sai dai na je na daukosa duk ya bata jikinsa da amai da zawo duk yadda nake kauce ma wata mu'amalan ganin sirin juna tsakanina da shi sai da na yaye wannan Hijabin ranar,Tun kafin auran sa da Zainab ko Hannuna sai da kuskure yake gegata ballatana ganin juna a yanayin da bai dace ba,Sai ranar ni nayi masa wanka Maman dai bata yi masa rana ba,Ina yi ina kauce kauce shi kuma jiki yayi lakwas duk yayi laushi sai abun yayi min wani barambaram kwai namiji da suna Hajara.
Bayan na yi masa wankan na koma na wanke bayin da kuma kayan shi da ya bata, sannan na fita baya damu kad'an inda Chemist yake na kira mai zaman wajen yazo ya gansa ya dora masa karin ruwa da allurai abu kamar wasa nan take sai da ya chajeni dubu Hudu,kada mutum ya raina ciwo komai kankantarsa,Yara sai dai suka Dawo makaranta suka iske sa rashe rashe ana masa karin ruwa,sai duk jikinsu yayi sanyi sai da nayi ta lallashin su sannan suka saki jiki yasha wahala rana zuwa dare duk ya fada abinci ma,ya kasa ci sai da Anty Binta tazo mai da Ferfesun kayan ciki ya samu ya ci kad'an yace bakinsa D'aci ga zazzabi ga amai da gudaawa.
Anty Binta bata neman zaman lafiya sai da tayi korafin wai meyasa ba'a kaisa asibiti ba? Mama tace mugunta ta ta ce ta tashi kuma ina da kudin naki kaisa asibitin,ni bana biye musu sai na nuna ma ban jisu ba Mama fa sai ciwon d'anta ta taba shiga bangarena ita kuma Anty Binta in asibitin banza ne meyasa bata Dauke sa ta kai sa ba..?
Wlh na yarda da maganan Hausawa da sukace in kana da abun yi,ba komai ke damunka ba. a baya ne in Mama ko Anty Binta sun min wani abu yake damuna nayi ta kuka yanzu na manta rabo na da kuka akan su,To ayyukan gabana ma sun isheni inaga naga Lokacin sauraransu ko suna yi baya Damuna, kamar irin na riga na zama Jan wuya a lamarin ballatana yanzu da nake yawan samun masu son Turaruka ta bangaran Hajiya sai ayyukana suka yi min yawa.
Ashe sun raina kulawar da nake basa balle da suka ga kurajen baki sun fito mai yaba yaba na alamun wucewa Mura, sai Mama ta saka Anty Binta ta kira Zainab na ta fad'amata wai tunda bazan iya kula dashi ba,yana da wata matar zata zo ta kula da shi,Sanda akayi ma bana gidan naje kasuwa da na Dawo Hafsah take fadamin sai nayi mirmishi ban ce komai ba.
Ashe ko sun kirata sun zuzuta abun Hankali tashe ta d'au alfarma a wajen aiki ta taso,ita da Fadil Farhan saboda makaranta ina tsaka da Hidiman Zobo na ta shigo,Direba na binta da kayanta A karamar a kwatinta kwata kwata ban yi mamakin ganinta ba, na tsallake komai na tarbeta sai dai Mama bata bari ba,ta janyeta zuwa Dakinta chan ta sauka a fili nace a gayyas.
Na koma dakina na cigaba da aikin da nake yi,Chan ba jimawa sai gasu sun shigo ita da Mama,Zainab na rike da Fadil sai alokacin muka gaisa kallo na take yi tana kare ma falon kallo Mama tayi mata Jagora har dakin Yaya Ishaq ni dai ban bisu ba saboda ba wanda ya gayyaceni sun dan jima aciki sannan suka fito sai ta kalleni tana fadin"Maman Amir zobo kike saidawa yanzu?
Ina yar dariya nace mata'"Eh wlh muna tabawa ya hanya..?ina Kika baro mana Farhan..?
Kai tsaye tace"Yana wajen mommy saboda makaranta"
Mama sai jiranta take yi daga waje ganin muna ta mgana yasa ta Dago labule tana fadin"Zainab muje ki yi wanka ki yi sallah sai ki ci abinci"
Sai ta amsa mata kafin ta fitan sai da tace min"Ashe Honey haka yayi ta rashin lafiya..?
Sai na gyada mata kai ina fadin"Ai yama ji sauki yanzu'
Cikin jimami tace"Ayya Allah ya basa lafiya"
Na amsa mata da Ameem sannan ta fice zuwa Dakin Mama ni ko sai da na gama zuba zobo na sannan na shirya ma zainab abinci daman da rana Shinkafa da miya nayi mana da Salat har dare saboda na gaJi bazan iya wani girki ba,har dakin Mama na bita da shi har da zobon na zuba mata
Bata a falo kila tana ciki Mama sai Hararata take yi ban bi ta kanta ba na sauke abincin hannuna na fice abuna.
Sai da na had'a kayan wanke wanke bayan yara sun dawo makaranta ni nace su shiga Dakin Mama su gaida Antynsu suka shiga gabadayansu suka gaisheta daganan bayan sun ci abinci suka shige Dakin babansu Fadil na Hannunsa suna ta wasa Amir ne kadai ke falo yana duba Littafansa na makaranta.
Da kaina na shiga zan dauko kololina da wanda na kai ma Mama nata,na iske zainab na zaune tayi wanka ta sauya kaya waya a hannunta tana ta Dannawa sannu da gida tamin na duka ina kwashe kwanukan da suka yi amfani da shi Mama na gefe nasan hira suke yi da na shigo ne Maman ta Dauke mganar ammh saboda salon cin Mutumci sai ta gyara zama tana fadin"Zainab nace ba.."
Sai ta Dago tana fadin"Na'am Mama"
Mama tace"Daman so nake naji ko zaki d'an kwana biyu kafin ki koma..?
Zainab ta yamutsa fuska kafin tace"Anya? hutun kwana biyu suka bani a wajen aiki"
Mama ta kalleni ta gefen ido tana fadin"Gaskiya gwara ki tsaya ki kula da shi.ita wannan baya gabanta ta sana'arta take yi tunda ta fara wannan sana'ar nata bata kallon kowa da Daraja kema matarsa ce shiyasa nace Binta ta kiraki kizo ke kila kya kula da shi yadda ya kamata"
Sai tayi Dariya batace komai ba ni kuma ina cigaba da Tattara kwanukana ina jinta daman tayi mganar ne saboda naji.
Ganin Zainab batayi mgana ba yasa Mama ta cigaba da fadin"Ni dama in kin tashi tafiya zaki tafi dashi chan Abujan,zan fi samun kwanciyar Hankali zamansa anan bai da wani amfani"
Na mike kenan Zainab tace"Mama naga Maman Amir fa na kula da shi"sai Mama ta wani yarfa Hannu tana fadin"Wlh bata kula da shi, wannan da kika gani ai muguwa ce ta sosai"
Tafad'a Lokaci daya tana nuna ni da baki kamar zan fita na barsu sai na fad'a kamar an min wahayin mganar na Tsaya ina kallon Mama kafin nace"Aiko baki ce ta tsaya ta kula da shi ba tunda tazo, na sakar mata komai Tunda itama matarsa ce, kamar yadda yake da Hakki a kaina itama yana da Hakkin akanta"
Daga haka na juya nayi ficewata Mama ta rakani da fadin"babu abunda ta iya yanzu sai rashin kunya har shi ta raina"
ni dai bansan ya suka kare ba ina wanke wanke abun na dawomin ni kaina ina mamakin yadda bakina ya bude wani Lokacin na yarda ba shawara ko nuniya ke saka mace tayi baki a gidan mijinta ba Wuya ce mutanen duniya ke chanzata,batare da tama sani ba kamar yadda yake faruwa dani domin ban taba kawowa ma kaina zan iya maida ma Yaya Ishaq mgana ba ko shi ko Anty Binta ba sai ga shi shakkar da nake ji da yanzu wlh bana gani,wani abun ma ina raga musu ne saboda wasu Dalilai.
Tunda Mama ta raina kokarina ni ko a raina nace sai na bata mamaki na tsame hannuna a kula da shi ai daman ba hakki na ba ne, ita da bai jingine auranta ba,yafi zama Dolenta ta kula da shi nifa daman taimako ne da Darajan ya'ya sai ta wani Fanni in na Duba zumumci.
Sai ana mangariba na gama wanke wanken nan sai lokacin Hafsah da Badariya suka dawo,Amir da su musty sun bi babansu zuwa masallaci daya fara rarrafa d'azu,sannu da gida suka yi min kowacce ta shige inda tafi wayau.
Ina komawa Daki daman na Dafa ruwan zafi nayi wanka,Hafsah kuma nace in tayi sallah taci abinci taje makotan mu ta Dauko min ninkan Ayan da dazu yaron gidan ya shigo Siyan zobo na bashi sai ta amsamun na shige Dakina nayi wanka nayi sallah na zauna ina azkar,ina ga sai da sukayi sallar isha'i suka dawo shi Uban Gayyar Dakin Mama ya shige yaran kuma suka dawo Daki Hafsah da ta dawo dauko nikan na saka ta raba sauran abinci nace ta diba ta kai Dakin Mama da yawa Saboda Zainab sauran su ci su da yara.
Akace Namiji ya iya munafunci nidai tunda na shiga ban fito ba Hafsah na bari da hada kunin Aya,Ashe da ya gama zamansa Dakin Mama tare da Zainab suka dawo Dakinsa sai suka bar Fadil wajen Mama bakinta washe,Adakin nasa ta kwana ni ban sani ba ko da na tashi da asuba ban lekasa ba ina ma yara shirin tafiya makaranta,muna falo da ni da yaran suna cin abinci sai gata ta fito tana mika sanye da rigar barci Riga da wando masu taushi gashinta kanta ya bazu wata hula ce ta saka ana ganin kanta,sau daya na kalleta ban kara ba ita ta fara gaisheni na amsa ta cikin Sakin Fuska har ga Allah ban ji Haushi ba, to me zai dameni ai ba yau aka fara ba an dade ana haka.
Abun karin ma na aika Dakin Mama basu ci ba Zainab ta basu kudi suka siyi kayan tea Badariya tazo kitchen dina ta soya musu kwai, ni ina Dakina Hafsah ke fadamin nace saji da shi dai.
Sai da chan rana na shiga na Duba sa yana kwance sun yi kaca kaca da Dakin,daga nesa na tsaya na gaishe shi da jiki ya amsa sai naga yana karemin kallo sai na Tsargu da Sauri na kalli kaina Riga da sikat ne a jikina Atamfar ni na siyeta da kudina na Dinkata sai dai dinkin yayi min Cif a jikina ganin yadda ya kuramin ido ne yasa kawai na juya zan fice da Sauri ya yunkura ya mike yana kiran sunana na Juyo ammh ban karisa gabansa sai yace"Fa'iza kariso mana bana jin dadin yadda kike maida Dakina kamar bakon ki"
Sai kalamansa suka bani mamaki kai tsaye nace"ai bakon ne a wajena.."
Bai damu ba sai ya dan kalli D'akin yana fadin''Haba Fa'ita kwana biyu ba'a zo an gyaramin Dakin ba. sannan kuma ga kayana duk sun yi Datti wlh ko na sawa bani da shi"
Na kura masa ido ina Dariyan sunan da ya kirani wai Fa'i ta abunda ban taba ji ba ko acikin mafarki har da wani lankwasa wuya yake yi na yaudara sai kawai nayi Dariya kafin nace"Ai wannan ba Hurumina ba ne Hurumin Matarka ce ka kirata ta gyara dakin sannan ta kwashe kayan naka ta wanke"
Kai tsaye yace"Saboda me sai zeey.?ai ke kika saba yi Fa'iza kada ki bata ladan ki don Allah"
Karfin Halinsa ke bani mamaki cikin gajiya da mganar na juya ina fadin"Ba bata lada ba ne, Itama Hakkin ka na kanta ta kula dakai tunda tazo ta amsheni daman ni taimako nayi ba Hurumina ba ne"
Har zan fice ya kwalamin kira "Fa'iza..'
Sai na juyo ina fadin"Wlh bazan yi ba ka kire Zeey din taka mana, inace ita ma Matarka ce"
Sai kawai ya koma ya zauna yana fadin"Fa'iza yaushe na fara mgana kina min gaddama sannan yaushe na fara mgana kina sa'in sa da ni..?
Kai na tsaye nace"Tun ranar da ka furtamin da kanka ka zabi wata matarka fiye da ni nima tun ranar na zabi rayuwata da ya'yana sama da kai.Komai kaga ina yi maka don Allah da taimakon zumunci ne"
Daga haka na fice na barsa da sanyin jiki Hidmar hada zobo na fara satin nan Hafsah karatun Safe suke yi,Allah yasa tamin shara da Safe wanke wanke kadai nayi sai na share tsakar gidan na wanke ina wajen Zainab ta shige bata fito ba, ni ko dakin ban koma ba Fadil ne ya dinga kuka a Hannun Mama ta kasa lallashinsa sai na shiga na karbesa sai na Fahimci yunwa yake ji ina da Sauran garin kuni nan da nan na dora ruwan zafi daya tafasa na Damamai na Duramai tas ya shanye sai barci,naja zani na goyesa ram a bayana na cigaba da ayyukan gabana Mama daman tagaji da renon ta shige Daki tayi kwanciyarta Tunda baiwarta ta Dauke komai.
Da rana Danwake nayi da salat,aiki duk ya Chudemin Zainab kam da uban gayyar sun shige daki ba mai jin motsin su, Fadil na Dakina yayi barci da ya tashi nayi mai wanka nima nayi ban san fitan ta ba ta koma Dakin Mama tayi wanka ba,sai da ya tashi ya fara rigima na lekata sai na ganta na mika mata shi ina fadin"Ya tashi yana rigima"
Ta karbe tana fadin"Daman tunda naji sa shuru nace yana Hannun ki"
Mirmishi nayi mata na fice,ina komawa Daki na ci karo da shi ya fito Daga kitchen da ya gani sai yayi Turus ni kuma sai nayi kamar bangansa ba zan wuce dakina yace"Dama..dama kuna da ruwan zafi ne..?garin ai ko sanyi zazzabi bai sakeni ba kada na Dawo da shi da wanka da ruwan sanyi"
Da nayi niyyar na yi wucewa ta ne sai wata zuciyar tace ashe ya Dameki..?sai na juya ina"Ka kira Zainab ta saka maka mana"
Sai ya bude ido yana kallona,na ganin na juya yasa yasha gabana yana fadin"Don Allah Fa'iza don Allah nace.Zeey bata shiga kitchen achan komai ma'aaikata ke yi mata"
Rashin kunya ba Halina ba ne yasa na juya na koma kitchen na kunna gas na Doramai ruwan zafin na fice na barsa nan falon inaga da yayi zafi ne ya kashe gas din ya juye,yau alhamis ne da la'asar yara suka dawo makaranta Amir ya taimakeni ya tayani Dura zobon a gorina Anum na shirya mana nayi na Safe har ya kare wannan na yammah ne,Addu'a nake yi Allah ya dawo da Hafsah ta dora girki sai biyar da wani abu ta shigo tana shigowa Amir yace'"Umma ga Antyn Hafsan ta dawo"
Daga ganinta ta gaji ta sauke jaka tana fadin"Da Antyn Hafsah tayi me..?
Ina Dariya nace'Yaji ina ta cigiyarki ne aiki yayi min yawa ban dora girki ba"
Sai ta ce"Bari naci abinci na dawo hayyacina"Da sauri nace"Yauwa yar albarka mu in mun gama sai mu had'a kwanuka mu yi wanke wanke"
Da Sauri Anum tace"Umma ni zan yi"
Ina dariya nace"Ko baki ce ba tare zamu yi kafin nan gaba ki iya na sakar miki,ammh kafin sai kin share inda muka bata"
Musty yace"Ummi ni zan share"
Nace"To ya'yan Umma yan albarka"
Ahmad na gefe yace"Umma zan wanke miki robobi"
Amir yace"Kadai samu na wasa"
Gabadayanmu muka saka Dariya gabadaya bani da damuwa indai ina ganin Dariyan ya'yana su nafi damuwa da su bangaran su Mama tunda zainab tazo ta bud'e musu bakin aljihu suna cin dadin su yau nama gobe kaza ni dai ya'yana suna daki basu gani ba,ballatana su saka rai ammh fa Fadil na wajena ni nake mai komai har wanka uwar tana nanike wajen miji ana shan soyayyah.
Washegari da Safe bayan yara sun tafi makaranta na fada ma Hafsah yau zobo Sau daya zamu yi,sai kunin Aya shiyasa da Safen bayan yara sun tafi makaranata na samu kujera na kwanta sai barci Hafsah ke dafa zobon awaje basu da shiga makaranta yau,ai naji dadin zaman Hafsah a wajena tana bala'in taimakamin kan sha'anin gida da sana'ata wani lokacin ba domin ita ba,bansan ya zan rika yi da wasu ayyukan ba.
Na fara barci sama sama na rika jin Hayaniya na gyara kwanciyata saboda ban ji hayaniyar ko ta macece ba,Sai da Mama ta shigo har Falona ina kwance kawai naji ta Dakamin duka na Bude idanuwana da suka yi ja Saboda barci sai naga Mama a saman kaina
Tsakani ga Allah ina gajiya saboda aikin Hannu nake yi komai sai na sarrafashi da kaina.
Ina kokarin tashi zaune kawai ta hau ni da fad'a nama kasa gane in ta dosa sai da nace"Lafiya Mama..?
Cikin wani kallo tace min"Bansani ba.Kya ce lafiya mana kina kwance kina barci,shi kuma ga shi chan bai da lafiya shi kika bari da wankin kayansa"
Sai taga na mike kawai zan shige cikin D'akina kai tsaye ta saka hannu ta fizgoni na dawo gabanta tana zare min ido tace"Don ubanki ina mgana kina wucewa,ni sa'arki ce.?



*INGANTACCEN ZANCE*.

*Akwai da INGANTATUN SAIWOWI na gyaran mejego ko amare*.
*Haka uwargida ma ba'a barta a baya ba da irin nata tagomashin*
*Kaya ne masu kyua ba garabiti ba, takanas ake kawo su daga chadi.*
*Idan kina da kannen da za'a aurar, ki zo ki yi musu tanadi na mussaman*.
*SAIWOWIN itatuwane da basu da illah*
*Da sau'ki zaki same su, amma aikinsu yawa ne dasu.*
*Kawai ki tuntu'bi Surayya HALIN YAU a wannan lambar dan samun gamshasshen bayani*
*08032773332.*

'?.




*Janafty*



[7/12, 10:17 PM] +234 906 320 7298: *KNKB2006*

*Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 0552179550,ban da tsarin kati wannan karon, a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488*

Ba nufina in yi Mama rashin kunya ba ne, saboda a uwa na Dauketa sai na Sadda kaina kasa ina fadin"Naga fad'an bai shafeni ba ne Mama"
Sai ta saki baki tana kallona lokaci daya tana fadin"Wato bai shafe ki ba? ko ni ki keso na kwashe kayan nasa na wanke mai ishashiya Dangin Jaraba?
Sai na dago kai kamar zan yi mgana sai na fasa na kama Hanya na fita Tsaakar gida yana Zaune kan kujerata ta tsuggunon Tsakar gida, ga kaya a gabansa ya saka Hafsah ta taran masa ruwan famfo Har ga Allah Dariya sai da ta kusa kamani yadda yayi kamar mai ko wankin,Karisa fitowa nayi ina fadin"wanki da kanka ina Zainab din..?
Ko kallo na bai yi ba nima sai na juya ina kallon Mama da ta zata da na fito zan karbesa ne, sai taga akasin haka kafin tayi mgana na tare ta da fadin"Mama kada kiga laifina ba ga Zainab ba, ai itama matarsa ce. kince

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login