Showing 198001 words to 201000 words out of 288345 words

Chapter 67 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

765

zan wuce lagos fa Maman Amir"
Cikin murnata nace"Allah sarki..Kin gama shirin naki kenan..?.
Da kai tamin mgana kafin tace"Eh nagama gobe jirgin yammah zan bi zuwa lagos shiyasa da wuri zan bar nan"
Da jinjina kai na bita kafin nace"ammh tare da yaran gabad'aya ko..?
Cikin muskutawa tace"Da Farhan kadai Daddy ya roki Honey ya bar masa Fadil ban san ko ya amince ba tukunnah"
Da kamar bazan yi mgana ba sai nace"Naso da Fadil su Amir zasu ji dadin in kannen su na tare da su"
Sai ta juya ta kalli Nana Fatima taga tana ta latsa wayarta cikin Sauke murya tace"Maman Amir wajen ki nazo..Ina so mu yi mgana ne"
Ta fad'a tana kallona ni kuma kai Tsaye na gyara zama ina fadin"To ina sauraranki"
Sai ta juya tana kallon Nana fatima Fahimtar da nayi na abunda take nufu yasa da sauri nace"Kada ki damu Nana Fatima yar'uwata ce ta jini zaki iya yin mganarki bata da matsala"
Jin abunda nace yasa ta gyara zama tana fadin"Maman Amir sai naji mgana a bakin Honey mara dad'i"
Cikin son basar da zencen nace"Mganar me..?
Bude ido tayi kafin tace"Kin ki binsa Lagos sannan kin ce ya sake ki.
Haba Maman Amir"
Zan yi mgana kenan Nana Fatima ta katseni da fadin"Baiwar Allah kinsan fa tana kan dokar Likita ne ba'a so ana mata mganar da zata tada mata Hankali.
duba da Condition dinta, da zaki yi hakuri da mganar nan sai next time da yafi"
Sai naga Zainab ta mata wani Kallo kafin ma tayi mgana itama sai na tareta da fadin"Nana kyaleta ai na samu sauki"
Cikin tsareni da ido tace"Dokar Abba fa..?Shi yace kada a kara miki mganar mijinki har sai lokacin da yace"
Idanuwana na Lumshe kafin na bude Lokaci daya ina fadin"Fatin mu kyaleta ai mgana ce kadai ko..?
Ganin nace haka yasa ta koma gefe tana cigaba da danna wayarta Zainab kuma sai tayi wani iri ta Lura dai yar'uwata bata yinta kwata kwata.
Kallonta nayi ina fadin"Uhm ina jinki maman fadil"
Da Sauri ta rike hannayena tana Fadin"Nazo ne tattakiya daga Abuja na baki Hakuri maman Amir wlh Honey duk ya susuce ya kasa ma natsuwa kan aikinsa yara kuma kinga sun ki zama tare da shi,Mama ita kadai ce a gida tunda Badariya na kano,Kuma kinsan sun saba dake bai kamata ki yanke hukunci cikin Fushi ba. A madadinsa ina baki Hakuri gobe ki shirya sai mu tafi tare bazan ji Dadin zama agidan nan baki ba Maman Amir"
Ta karishe fada cikin marairaicewa,Sai na yi mirmishin yske kafin nace"Ba ga ki ba maman Fadil. Bani da Haufi kan su Amir zasu samu kulawarki kamar yadda suke samun nawa,mganar kuma ya susuce akan in koma ba gaskiya ba ne. Ke kanki shaida ce farkon zamanki dani kinsan wasu abubuwan kin kuma san Mijinki baya sona kece zabinsa to ki barni nima na sauwake ma kaina mana,da zama fa inda ba'a sonka gwara ka zauna inda ake sonka sau dubu Zainab"
Taran Numfashina tayi tana fadin"Wlh Honey na sonki ni Shaida ce"
Kai tsayen nima nace mata"Aa ban yarda ba,so d'aya ne yana wajen ki. Ke yake so kuma ke ce ki ka yi daidai da Ra'yinsa da Burinsa ni kawai na Haifa masa ya'yavne sannan na zauna na Kula da su,ko a yanzu ya damu ne Saboda haka ba domin ni din yake son zama na da shi ba,duka al'amarin na alfarma ne Maman Fadil kema fa kinsani kina so ki take gaskiya ne ki bi bayan karya"
Na fad'a mata kai tsaye ina kallonta ganin na cije sai ta kara rike hannuwana tana fadin"Don Allah ki yi hakuri nasani abaya ammh a yanzu ai ya sauya ko..?
Cikin jinjina kai nace"Ba kamar yadda kike Tunani ba,ke kad'ai yake so to meyaasa zai zama laifi don na bashi Dama ya zauna da abunda yake so ita kad'ai"
Ajiyar rai ta sauke kafin tace"Naji ni yake so..kema ai yana sonki da bai sonki bazai zauna dake shekarun nan ha har ku yayyafa ba Maman Amir"
Tunamin da yadda aka samu rabon ya'yana yasa Hawaye sun cikamim kwarmin idanuwa na, kai tsaye nace"Bai gayamiki duka rabon su ne ya rantse ba?
Sai ta kasa mgana ni kuma sai Hawaye suka samu Damar gangaromin na kwace hannunawana cikin nata ina fadin"Kinsan akwai ya'yan da ba'a so haifarsu ba,rabo ne kawai in Allah ya rantse yasa suke Fitowa duniya.
Ki yi hakuri Maman Fadil bazan iya komawa ba,ina rokin ki da kiyi hakuri,amanar duka yarana yana Hannunki ne"
Na fada ina share hawayena,Cikin jimani tace"Nima ba zama zan yi ba Maman Amir Daddy na kokarin nema min aiki in na samu aiki zan rika fita wazai zauna da yaran sannan wazai kula da mama..?
Aikin ki ne fa..Kema kinsan bazan iya duka wannan ba"
Ba ni kadai na kalleta da mamaki ba. har da Nana Fatima daman ranta nata baci da mganganun Zainab din,Kalamanta na karshe sun fassara inda ta dosa wato Fa'iza ce yar wahala ana so ta koma ne saboda kula da yara da megidan ita yar boko aiki zata rika fita,ni ko mamakina kad'an ne daman nasan aikina ne kuma don shi ake min bikon na dawo.
Sai kawai nayi wata karamar Dariya kafin nace"Hakanan zaki koya,ammh ni kam ba inda zani"
Itama kai tsaye tace"To in hakane nima na fasa komawar shikenan"
Tafad'a tana bata rai sai na maida abun dariya ina yar dariya nace"Kada ma ki fara. Dolen ki ki bisa chan In kika komawa wazai kula da shi da yaran mu da na baki Amana..?
Sai ta kasa mgana ganin haka yasa na Dafa kafadarta ina fadin"Kiyi hakuri Maman Fadil..Ban zan iya miki wannan alfarman ba,da zan iya da tuni na yi miki.."
Ki bi mijinki a duk inda yake hakki ne akanki ni kuma kada ki damu dani daman a Dofane nake tuntuni"
Duk sai na kashe mata jiki ta kasa mgana cikin wani yanayi tace"Kin dai ki jin mganata Maman Amir a yadda na sanki mai hakuri..?
Sai kawai nayi dariya ban yi mgana ba,Haka ta cigaba da kawo min mganganu ina kauce mata,Sai da aka kira sallar isha'i muka saki mganar muka mike mukayi sallah Nana fatima ficewa tayi ta barni da ita na Lura takaici ya isheta tayi tayi na rantse mata bazan koma ba.
Sai ta kyaleni ammh jikinta yayi sanyi sai fadi take yi daman haka kike Maman Amir ni dai sai dai nayi mata Mirmishi.
Da daddare tea kadai Zainab ta sha tace ya isheta,Nana Fatima bata ci komai ba sai ruwa tace batacin abinci da Daddare,Dakin da nake ciki muka bar ma Zainab sai muka koma Dakin da Hafsah ke zaune a baya da katifa a kasan Dakin a kanta nayi mana Shimfida,Sai da muka yi shirin kwanciya sannan Nana Fatima ta kalleni tana fadin"Ba dai kishiya zaki bar mijinki ba Fa'i?
Kai tsaye nace mata"Eh mana in mijin ya fi son zama da kishiyar ba laifi bane, ne in na bar mata shi"
daman nata ne ita Kad'ai"
Sai ta saki baki tana kallona,ni kuma sai na basar da mganar,itama bata karamin min ba ammh ta tabbatar ma da kanta akwai mtsala a mganganuna ta Fahimci cewa da akwai lauje cikin nadi,da muka tashi da Safe sai kawai tace min"Gaskiya zan gayama Abba. Bazaki bar ma kishiya mijinki ba"
Kai tsaye nace"Tuni na bar mata ma, kune baku sani ba.."
"Bamu sani ba..?
Ta maimaita kai tsaye nace"Eh mana baku sani ba,ammh lokaci zai fada ma kowa komai"
Daganan ban kara mgana ba itama sai ta kauce ma mganar,Zainab ta fara wucewa Tunda Direbanta nan ya kwana,Kafin tafiyarta har Goggo ta tuntuba goggo tace mgana na Hannuna da Hannun Abba sai an zauna,ganin ba sa'a yasa ta tafi da magiyan don Allah na dawo mu zauna tare sai kawai nace mata insha Allahu daga haka muka rabu lafiya bayan na kara jadadda mata amanar su Amir a hannunta.
Tafiyan ta ba jimawa Direban Nana Fatima yazo daukanta itama mun rabu cikin kewa karfe sha biyu da wani abu ta mika Hanya suka barni ni kadai ina Tunanin makomar rayuwata..
Mun yi waya da Nana Fatima da yammah ta isa gida lafiya,Zainab dai sai washegari muka yi mgana ta tabbatar min ta sauka a lagos,sai tamin korafin gida shuru ba yara,dariya kawai nayi ban ce komai ba sai tace in Honey ya dawo zasu je su Daukosu nace Allah yasa,daganan muka yi sallama,hankalina sai naji ya kwanta tunda Zainab ta koma ina mata kyakyawan zato zata kula da su Amir dai dai kulawan ta.
Su Zainab sun tafi da kwana hudu sai ga Anty Binta da Anty mahma tunda nagansu nazata gaisheni suka zo yi sai da Anty Binta tace tana son mgana dani muka kebe. shine take bani Hakuri da bakinta da bakin Mama kan nayi hakuri na janye kudurina na koma Dariya ma ta bani sai dai ban yi mata rashin kunya ba, na bita da toh zan koma,Har da Anty Mahma a bani Hakuri mganar su kuma duk na koma Saboda yara ne a raina nace nima ai bai Darajani Saboda yaran ba.
Bayan Anty Binta ma Badariya ta sauka a Karofi daga kano itama haka ta tasani tana fadin"Haba Anty Fa'iza tun a baya baki nuna haka ba sai yanzu..?ai yanzu kin wuce wannan wajen da naji labari hankalina ya tashi bansan ya zan koma Lagos a gidan nan naga baki nan ba"
Ni dai ban ce mata komai ba sai dai na bita da toh zan yi tunani zan koma kwana Daya tayi ta koma kano tace zata bi mota zuwa Lagos tunda bata da kudin jirgi,ammh sai taje ma Jamal graduation dinsa tukunna.
Bayan sati daya sai tayo min Taron Dangi ta Dauko min harda Jamal suka sake zubewa gabana suna magiya,daman ranar a raunane nake mun yi mgana da Zainab sun dauko su Amir ammh Ahmad da Musty sun ki sakin jiki suna ta rigima su dai Umman su,har kukan nasu ta karamin ta waya naji sai hankalina ya tashi tace Ishaq ma basa yarda da shi ballatana ita har gwara su Amir suna yarda da su,makaranta ma an saka su wacce ya'yan Anty Fadila ke yi ammh Ahmah da Musty ranar da kuka aka kaisu, su dai wajen Ummansu zasu hankalina duk ya tashi ga magiyan su jamal wanda fadi yake yi"Matar yaya ki yi hakuri. Ki godema Allah kin zama giwar mata Mama da kanta tace nazo na baki hakuri ki dawo su Ahmad sun ki zama suna ta rigima"
Sai naji zuciyata ta karye,har suka tafi ban basu amsa ba,da asuba ranar ishaq ya kirani sanda naga kiransa sai da Gabana ya yanke ya fadi kamar bazan dauka ba har ta katse ganin ya sake kira yasa na Dauka ina Dauka naji sa cikin wani yanayi yana fadin"Fa'iza kin kyauta taurin kan ki zai yi silar kashe mana Ahmad gamu nan a asibiti, tun jiya yaron nan ke kakkafewa yana suma saboda ke"
Sai na Rud'e hankalina ya tashi na Fashe da kuka cikin kukan nake fadin"Innalillahi wa'inna ilaihirraju"un"
Salati na ya shigo da Goggo tana tambayan Lafiya sai na gayamata jikina na rawa na mike ina had'a kayana Lokaci daya ina fadin"Goggo Lagos zan tafi..kada Ahmad ya mutu Goggo.."
Sai ta saki baki tana kallona cikin mamaki tace"Lagos ke kad'ai Fa'iza?
Ban ko Saurareta ba na cigaba da Had'a kayana ina kuka ganin bana cikin Hayyacina, yasa ta fita zuwa Dakin mallam ta gayamai Halin da ake ciki kai tsaye ya fiddo wayarsa yana Fadin"Aa bazai yu yu mu barta ta fita cikin wannan Halin ita kad'ai ba, bari na kira baban nata na fad'amai"
Sai goggo ta aminta da mganarsa kai Tsaye ya kira Abba shima ganin kiran safe sai hankalinsa ya tashi.
Ya na jin jawabin abunda ke faruwa yace maza su Dakatar dani. bari ya fara kiran Ishaq din yaji abunda ke faruwa.








*Janafty*
[7/25, 8:30 PM] Hauwa Galadima: *KNKB3003*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWOWINRL ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY*


Lokacin da Mallam mijin Goggo ya kirasa yana shashen Inno ya shiga gaishe su da kwana ita da Baba Ati,shiyasa yana gama wayar Inno ta jefamai tambayar me ya faru..?ba shi da mafita illah na gyara zama ya fayyacemusu abunda ke faruwa.
Inno ta rike baki kafin tace"Ikon Allah. Shi aure fa daman rai garesa Usman duk yadda ka so ka san al'amarin sai kaga daga baya komai ya Sauya, ya kamata a zauna da ita da shi din domin yi musu sulhu, ba saboda komai ba sai domin yaranta"
Abba yace"Daman akwai niyyar haka Inno. rashin Lafiyar da tayi ne yasa na Dakatar da komai sannan ga Dokokin Likita a kanta"
Inno ta jinjina kai tana fadin"Allah Sarki wlh duk cikin ya'yan Hafsah tafi bani Tausayi sai ka ganta shuru shuru bata da Hayaniya Allah kad'ai yasan bakin cikin data Had'iya, sai dai bazamu yanke ma barayin mu Hukunci ba har sai shima yazo an zauna da shi, an ji Daga ina aka Haihu a Ragaya"
Baba Ati na gefe tayi karaf tace"Fad'i ki kara Inno yarinyar nan Fa'iza ta Had'iye Bakincikin wannan mijin nata da danginsa"
Daga Inno har Abba Hankalinsu suka maida kan Baba Ati na neman karin bayani sai ko ta gyara zama ta cigaba da Fadin"Mganar gaskiya sauran yan'uwanta sun fita sa'ar gidajen mazaje,Nasan wasu abubuwan tun Tamadina nada rai sannan ita Hajiyar Fatiman Goggo nasu na fad'amin wasu abubuwan"
Da Sauri Abba yace"Don Allah Baba ki fadamin abunda kika sani kan auran Fa'iza da Ishaq"
Ya fad'a Lokaci daya yana jin ransa na kuna,Baba Ati tayi shuru taki mgana Inno ta kalleta Lokaci daya tana Fadin"Atine ki fadamasa komai Uba yake gareta kuma domin a samu gyara in zai gyarun kenan fa"
Baba Ati tace"Da dai ban so nayi mgana ba. ammh Tunda takai suka Kure Hakurin yarinyar nan nasan komai ya zo karshe.
Duk cikin ya'yan Tamadina ita ta Dauko hakurinta da Zurfin cikinta Wlh ni nasan ko yan'uwanta ba kasafai take zuwa Inda suke ba,mijin ya hana sannan Karofin ma sai ta shekara bata zo ba sai wani babban sha'ani,ance Mahaifiyarsa da yan'uwansa basa Son Fa'izar ne ta sha wahalan su,Uwa uba kuma yazo yayi aure,Goggon su ke fad'amin sai yafi wata uku a chan inda yake aiki wajen Amarya bai waiwayi Fa'iza ba. sai itace ke mata sako akai akai Saboda yaranan,kuma nima na gani Rasuwar ta madina wlh sau d'aya Surukarta tazo ranar uku daganan bata dawo ba.? mijin nata kuma ni dai har muka watse wlh bai zo ba,kuma har Ciwo Fa'izar tayi Goggon su ta wuce da ita gidanta ta yi jiyya har ta warke ta koma bai zo ba, ammh mazajen su Asiya sun zo wlh da su aka Sallaci tamadina sannan da su aka zauna akayi karban zaman gaisuwa,wannan mijin na Fa'iza yanzu ne ya yi sanyi daga shi har uwarsa da Rayuwa ta koya musu Hankali Saboda d'an rashin da Shi Yaron yayi Fama da shi"
Baba Ati ta karishe fad'a tana gyada kai Inno ta kalli Abba shima ya kalleta Cikin takaici da wani bacin rai,Inno na son mgana sai ya rigata da Fadin"Tabbas biri ya yi kama da Mutum.."
Sai yama kasa mgana Saboda bacin rai,Inno ta jinjina kai Lokaci da'ya tana Fadin"Gaskiya Yarinyar akwai zurfin ciki ga sanyin Hali"
Baba Ati tace"Irin uwarta ce. Har tamadina ta bar duniya bata da abokin Fad'a haka Mijinta da abokan zamanta suke fadin Tarin alheranta Ita kan ta Dace wlh ta samu shedar Duniya Saura ta Lahira"
Inno tace"Allah ya jikanta ta. Lahirar ma muna mata Fatan Dacewa in sha Allahu"
Kamar Daga sama sukaji Abba na fadin"Shi Ishaq din baya son Fa'izan ne..?
Baba Ati tace"To ni kam ban sani ba ammh ai auran zumunci ne. mahaifinsa Alhaji Kabiru mutum mai son zumumci shi ya had'a auran,zai iya yuyuwa Saboda kaga ita Fa'izar na da Lalura,ammh dai kam ta yi zaman Hakuri da shi da kuma iyayensa"
Cikin kaushin Muryan Abba yace"Shi ne an san wannan ba'a raba auran ba.?ta yaya za'a bar yarinya tana kunsan bakin ciki haka..?oh na gane Hawan jinin da ta samu ma Dalilin sa ne da Danginsa kenan..?
Baba Ati tace"To wa suke da shi da zai tsaya musu?Goggon su ce kad'ai da ya'yanta,kuma kasan sha'anin aure yadda yake, sannan zurfin cikin yarinyar ba'a jin kamai a bakinta sai dai in an Fahimta fa,To ta ina zasu fara sai mutum ya shiga mganar kuma ita tazo taki mgana shiyasa aka saka mata ido ake binta da addu'a. baga shi yanzu da tagaji don kanta ta nema ma kanta Mafita ba Usmanu..?
Abba sai sakin Huci yake yi yana auna wasu abubuwa kowa zai bude baki sai yace Fa'iza sai a Hankali Ashe sa'ar Gidan miji ne batayi ba.
Ya na ji su Inno na mgana baya Sauraransu sai ma mikewa da yayi yana Fadin"Cikin Satin nan za'ayi ta kare In sha Allahu"
Inno tace"Gwara hakan dai gaskiya. Nima ina son zuwa na Dubata in zaka tafi sai na bika muje tare"
Da Sauri Baba Ati tace"Ni kuma sai ki bar ni ni kadai..?ai kafata kafarki"
Abba duk da bacin ran da yake ciki sai da ya Dara kafin yace"Shikenan duk sai muje Direba ya tukamu.
Gidan nan daman an gama komai Funitures,kadai suka rage ban samu zama ba ne,ammh zamu yi? mgana da Maman Nana,saboda mu samu wajen sauka in munje garin"
Inno da Baba Ati suka hada baki wajen Fadin Allah ya taimaka ganin yadda Abba ke yi ne yasa Inno ta kira sunansa ya amsa sai ta kallesa tana Fadin"Kada ka yanke hukunci cikin Fushi Usman, mu bi komai a


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login