Showing 219001 words to 222000 words out of 288345 words

Chapter 74 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

737

da cewa ba zencen kai kotu duk abunda kayi shi zaka girba walau khairan walau sharri kamar yadda ta hana Fa'iza zaman lafiya itama kwatankwacin haka za'a hana yarta ai sai tayi shuru tasan gaskiya"
Tagumi nayi har araina ban ji dadi ba nace"Allah ya kyauta"
Badariya tace"Amin ga miji dan iska manenim mata chan naji Suwaiban Hajiyar Dala na gulmar, suna ta zagin Halisa araina nace Allah ya kara"
Ajiyar rai na sauke nace"Allah ya kawo mata mafita"
Ta amsa da amin kafin tace"Har da ita amasu yawo dani ban yi aure ba ido cikin ido na fada'mata da aure irin nata gwara babban mace agida muka yi kaca kaca da ita naso Anty Binta tamin mganar. har ita ban so na kyale ba sai kuma batamin ba"
Nasan Badariya da Fad'a sai na Shiga bata hakuri ina fadin"Sai hakuri badar..Ki rika banza da irin su. aure Lokaci ne kuma in sha Allahu Lokacin ya kusa"
Tana mirmishin yake tace"Allah yasa"hira muka cigaba da yi a bakinta ma nake jin wasu labaran,mun gangara Hirar Raliya tace min tana da ciki taje ma kwanaki ta mata kwana Biyu tana fadin alherin Raliya gareta da basu had'a komai ba ina bata Hakuri,nasan irin zafin datake ji acikin ranta,muna tare da ita har Bayan La'asar sannan tayi shirin Tafiya,tace min gobe da asuba zasu dau hanya har ta siya ticket din motar,su Anty binta suna chan basu dawo ba,Na nuna mata kayan duka da na kowa da kowa tace ta gani ina da wata atamfa da Anty Nasara ta bani ban ko Dinkata ba,sai na hada mata da kayan kwalliya da Hajiya ta kawomin wanda na ijiye ma su Hafsat basu zo ba na bada kudi 5k nace tayi Hakuri zan yi mata sako tana ta Godiya.
Da zata tafi Goggo ta hadamata su zogale kubewa,kuka tace ta kai ma Mama,har zaure na rakata kamar kar mu rabu bayan tafiyanta abun ya Dameni har na fadama Goggo Abunda Badariya tace itama tayi shuru kafin tace"Allah ya kyauta ammh ai fadar Allah ne ya hana kansa zalunci kuma muna bayinsa ya hanemu da shi"
Daga haka bata kara mgana ba,a raina n??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a kuduri zan kara Dagewa da addu'an Allah ya kawo ma Badariya miji na gari na nuna sa'a.
Bata kirani ba sai da aka kwana tunda kwana suka yi tafiya ta hadani da yaran suna ta murna,sannan itama Zainab din ta kirani tamin godiya daga karshe tace"Naga sako Little tace bata Hakura ba,sai Takwaranta tazo ta ganta"
Dariya kawai nayi ban yi mgana Domin na saba jin korafin Zainab kan rashin zuwana.
Wannan kayan da Ishaq ya gani suka zaburar da shi yana son zuwa kuma yana Tsoro,ammh yana ta kamun kafa wajen Abba ko da yaushe yana kiransa shi ko Abba in ya kirasa sai ya bige da masa Hiran aiki da Duniya in kuma Ishaq yaso sako wata mgana sai Abba ya shanshantar da mganar,shi kuma nauyi da kunya yasa ya kasa neman ma kansa mafita ammh yasan Yana Bukatar fa'iza.
Mama kuma ya yi mata magiyan ta shiga Lamarin kai tsaye tace"Ishaq ba ruwana bazan kara saka baki a zalunci Fa'iza dani ba.
kaje ka sameta kafin ta gama Iddanta ka kara bata Hakiri in ta Hakura zata dawo don kantaina murna in kuma bazata Dawo ba Ishaq bazan saka baki ba sai kayi Hakuri ka rumgumi zainab din tunda ita ka zaba"
Tunda ta fadi haka yasan bazata kara mgana ba,Anty Binta ma haka tace yaje ya samu Fa'iza tunda baban nata baya tare da ita ya Lallasheta Anty Mahma dai bata ce komai ba amnh a ranta tana Fatam Fa'iza kada ta amince.
Ga su ga Zainab din nan ko su basu ci albarkacin ta zauna da su ba,Mama ce take yi da suka zo ne suka karbeta,Ammh tana jin sauki ta koma aiki wai basu bata hutu ba,sannan tareda Shema'u take tafiya saboda Renon Little,Allah yasa yaran na gida an yi Hutu da Mama ta shiga uku.
Jamal kuma an kira su yana Gombe ya tafi Camp abunsa.
Da shawarwarin su ya yanke shawaran tahowa karofi ya sameni bayan ya gama shirya yadda zai yi amfani da kalaman bakinsa ya shawo kaina.

*****

Bani da masaniyar zuwansa ko abunda ya shirya a ransa,Ranar asabar da nake da kwana hamsin da shidda cikin idda ne ranar na tashi da jini na Biyu,Da aranar Abba da Ammi za su Karofi sai suka fasa An kira su Abba taro a Parthercourt sai ya tafi ajiyan. har Goggo ta saka su Yaya mariya sun je sun gyara gidan an saka Turare sai kuma zuwan nasu bai yuyu ba.
Da Safe bayan na tashi nayi wanka nayi mana abun karyawa jummala bata zo ba sai karfe goma,sai na gyara Falon Goggo na zauna ina karyawa ita taje kaima Mallam nashi ta dawo ta zauna kusa dani tana shan koko da kosai shi nayi mana lokaci d'aya kuma muna taba Hira sama sama acikin Hiran ne nace"Goggo bayan na gama Iddata na ina so na dawo da girke girke na tunda kuna da Fili a nan"
Goggo tace"Sosai ko Tunkuya goma ce za'a dorata a gidan nan kuwa. Sai ki Dauki ma'aikata su rika tayaki ayyukan"
Ina tusa kosai bakina nace"Haka nake Tunani da na bari sai Abba yazo ne sai nayi masa mganar"
Goggo tace"Eh ki yi mganar da shi hakan yana da kyau sana'a nada Dadi zaman haka bazai dameki ba"
Mun dan saurara da Hirar sai chan nace"Goggo yaushe za'a je katsina a kwasomin kayana..?ina so a kwasomin wasu ina so nayi amfani da su. wasu kuma sai na kyautar da su kada su lalace" Goggo tayi shuru kafin tace"Kin ga mun Sha'afa da wannan mganar to yanzu ya za'ayi?Dole sai an kira Ishaq din tunda kila key din gidan na Hannunsa"
Kai tsaye nace"Nima ina da shi Goggo"
Domin kamar na sani na cire na kofar gida guda daya da na Dakina.
Goggo tace"To shikenan zan saka mallam ya kira Baban naku a gayamasa abunda yace shikenan"
Da haka muka Rufe Hirar Goggo tace min zata shiga ciki ta kwanta kanta na saramata nace toh.
Kafin jummala tazo na hada wuta na Daura zobon da tazo karisawa ne kawai muna yi da yawa sosai kafin yammah ya kare,tunda duk barayin ni kadai ke yi har barayin su Yaya Mariya ma,kuma ina samun alheri in ina da Hadin Turaren wuta shima Tana tayani mun saba ita kan je kasuwa tamin siyayya har katsina nasha aikenta.
Bayan mun gama hada zobon mun dura a gorina muka zuba cikin Frerzer akwai wuta ba'a tada in ji ba,Sai ita kuma jummala ta wanke Aya ta hada shi ta fita kai nika
Sai na koma Daki na cire kaya zan shiga wanka Nana Fatima ta kirani a waya na zauna gefen dago muna ta shan Hira da ita fiye da Minti talatin sannan muka yi sallama.
Kwata kwata ban san da Mutum a bakin kofar dakin da nake ciki ba,Na ijiye wayar kenan saman gado na mike sai naji kaina ya daki kirjin mutum,A tsorace nayi baya ido na rufe garin yin baya na ci Tuntunbe da Matashi sai na kusa tintsirawa sai ji nayi an rikoni har da karfin Halin Rumgumeni bai yi mgana ba ammh kamshin Turarensa da Yanayin rikonsa yasa na gane ko waye ba kowa ba ne sai ISHAQ KABIR KAROFI.!
Har yana d'ora kansa a saman kaina Lokaci daya yana sauke ajiyar zuciya,Haushi ya kamani sai na Daddage na saka hannuwana na Turesa baya har zanina na kwancewa nayi Saurin taresa da hannuna.
Kai tsaye na ke kallonsa kamar yadda yake kallona sanye yake da Kaftani Riga da wando kalan Sararin Samaniya har da Hula ya rame ammh ya sake Fari da hutun jin dadi
Nima cikin wani yanayi yake karemin kallo,ganin haka yasa na juya na Rarumi Hijabina na zura jikina na rawa nace"Mallam lafiya?
Sai naga yayi mirmishi kafin yace"Lafiyar kenan. wajen matata Fa'iza nazo"
? Idanuwana kamar zasu fad'o na hararesa kafin nace"Baka da wata mata mai suna Fa'iza in Zainab kake nufi tana inda ka barota"
Na fada ina matsawa baya ganin yana Tunkaroni,tsoro ya kamani kada Ya min akuyanci.
Ai ko naga rashin ta ido sai da ya matseni a jikin bango sannan ya Takore bamgon da Hannayensa yana bina da wani kallo kafin yace"In gama gudun..?ina bakin tsiwar..?
Na bude baki nayi mgana ya Hade bakin mu waje d'aya yana sumbatata yana Hadawa da taba jikina da iya karfina nake turesa ammh ko gizau,abun ka ga Namiji,gajiya nayi na koma ina Tsiyayan hawaye sai da ya gaji don kansa ya saki bakina yana maida numfashi Cikin sanyin murya yace"Fa"iza ki yi min afuwa ki kuma yafe min kura kuraina ki Dawo rayuwata mu daidaita kanmu, in muka Daidaita kan mu ba wanda zai ce kada ki koma Don Allah Fa'iza"
Ya fada yana kallo na a narke ni kuma ina kallonsa ina tsiyayan hawayen takaici yadda Ishaq ya raina ni.
Hannayena ya sake Rikewa ya jani gefen gado muka zauna yana wasa da yatsuna yake fadin"Fa'iza yaran mu. Sun saba da ganin mu tare basa jin Dadi in suka wayi gari baki a gidan nan. Komai ya daina min Dadi wlh tallahi na Fahimci ke ce gata na ni da ya'yana ki taimakemu ki dawo garemu Fa'iza I so much Love u.."
Ya fad'a Lokaci d'aya yana sa ke hannuna bakin sa ya yi kissing,na kasa wani motsi kukan takaici yaki Tsayamin ina jinsa yana ta mganganunsa cikin taushin murya ganin ban daina kuka ba yasa sunkuyo ya fito da harshensa yana Lashe hawayena har ya gama yaga ban yi wani motsi sai ya tallafi Fuskata yana Fadin"Kin amimce Fa'iza..?
Kaikayi ne ya tasomin a idona sai na Kifta kamar kiftawan ido ya Rumgumeni Lokaci daya yana Fadin"Nagode Fa'iza nayi miki alkawarin bazaki kara kuka saboda ni ba,zamu reni ya'yan mu ni da ke,saboda Farincikin su"
Hawaye sharr suka zobomin na wani Turiri a kasan raina,a kaf kalamansa da Nadamansa bai taba cemin zamu inganta sabuwar rayuwar,bai taba ce min Fa'iza zan baki farincikin da ban baki a baya ba,Shi dai tunaninsa ya'yan mu ya'yan mu kawai.
Saboda rainin da ya yi min sai kawai ya shiga Budurinsa a jikina ni ko kamar an Saremin kuzarin jikina ina ji ina gani ya rabani da Hijabi na, ya kwantar dani kan gado yana kokarin janyemin zanin jikina sai a lokacin na Dawo Hayyacina sanda na Fahimci zai yi wasa da Hankalina da na iyayena.
Da karfi na turesa bayan ya saki jiki,sai da ya fadi kasa na mike a gigice kamar zakanya na gyara Daurin zanina yana Dagowa ni kuma na juya na Dauki Hijabi na,ya sake riko hannuna yana Fadin"Fa'izaaa!
Tas..! Na daukesa da mari Lokaci d'aya ina juyowa idanuwana jajir na nunasa da yatsa ina huci kafin nace"kada ka kuskura"
Kada ka kuskura ka fara wannan tunanin Ishaq"
Na fad&a lokaci daya ina kara kankance idanuwana ga huci ina Fitarwa kamar wata zakanya.
Sai ya Dafe kuncinsa cikin mamaki kafin yace"Yau ni kika mara Fa'iza..?
Sai da na juya na zura Hijabina kafin nace"Na mareka din. kuma ka bari hannunka ya sake taba jikina? kaga ni,marin makauniya zan yi maka ma.
Ka daina Tunanin ni Fa'izan zan koma ga auran ka. Har gaban Abada ni da kai Ishaq Karbi karofi ta kare, Fa'iza ba Turanci ba ajinka bace na barka da zabin ka meyasa bazaka kyaleni ba.?
Meyasa bazaka daina damuna ba..?
Na karishe cikin tsawa kamar mahaukciya sannan ina Fitar da Hawaye,Idanuwana jajir ya Tako zai iso gabana na Dakatar da shi da Hannu ina fadin"Wlh ka kara matsowa kusa dani zan maka ihun kwarto"
Jin kalamai na yasa ya Dakata kuka na Fashe da shi kafin na hada hannayena ina fadin"Don girman Allah ka kyaleni ka ce baka sona na barka ka zauna da wacce kake so,Na roki ka barni na samu salama Dalilinka aure ya fita kaina da dukkan wani namiji Ba domin ni ba domin Darajan Mama ka Rabu dani don Allah"
Sai kawai na saka fuskata a cikin Tafukan Hannayena ina kuka ban san yanayin da yake ciki ba ammh naji motsi da Tafiya sai da na Dago naga bashi a dakin kenan ya fice. wankan da ban yi ba kenan na kwanta nan ina ta Rusan kuka jummala ta shigo da Sauri tana Fadin"Maman Amir waye ta fita yanzu..?na hadu da shi a zaure kadan ya rage bai tureni ba"
Ina kukana ko sauraranta ban yi ba,Sai ta juya taje ta kira Goggo,Sai ga su sun dawo tare har Goggon tayi mganan duniyan nan ban ce komai ba sai kuka karshe ma na shige Bayi na kulle kaina.
Abun sai ya basu mamaki,Shigowar Mallam yasa sukan sa bakin zaren,Yace ya hadu da Ishaq din a gabansa mota ta sauke sa Goggo najin haka tace"Ko da naji Nasan shi kadai ke saka Fa'iza kuka haka"
Jummalla dai duk ta rude ranar kunin Ayan ne sai dai jummala tayi shi ita kadai ban kara fitowa ba.
Abba na kira domin nasan shi kadai zai iya takama Ishaq Burki ina ko gayamasa abunda ya faru ina kuka na Boye taba jikina da yayi ba, illah cema nayi yazo ya na ta min magiyan na koma.
Ran Abba a bace ya katse wayar ya kira Ishaq ya masa gargadi da kakkausan murya kada ya kara zuwa inda nake ya kashe wayarsa,Ishaq ranar yayi kuka kukan nadaman da bai Taba yi ba,Hotel ya kama ranar bai iya komawa Lagos ba. A katsina ya kwana sai washegari ya koma sannan ya kuma kara jin Tsoron Rasa Fa'iza har Abada.
Goggo ganin zuwan Ishaq ya sauya ni gabadaya yasa ta kira Abba tamai mganar kwaso min kayana yace su Yaya Mariya suje su kwasomin a Da'u tashar Mota zai biya kudin komai da komai,Haka ko akayi Yaya mariya da Anty Nasara sai Aminan Yaya isa suka je katsina da Katuwar mota mai Budadden baya.
Goggo ta min mgana na basu key din suka Bude gidan suka kwasomin duka kayana Mutanen anguwan su suka kira megidan suka Fadamai an shiga gidan shi kuma yazo da kansa ya zata ko barayi ne. Anty Nasara tamai bayani sun dawo suna bada Labarin sai da ya jinjina kafin yace"Lalle Ishaq ya tafka asaran Rabuwa da mace tagari in matarsa"
Yana gaya musu bai sanni ba ammh ya basu labarin irin yadda na rika rokonsa da yazo kan mganar kudin haya,Sai jimami yake har suka gama kwashe kayan yana wajen ya kuma bada sakon gaisuwa gareni.
To shi ya kira Ishaq ya fada masa an kwashe kayana ya kara da fadin"Kai ko bawan Allah me ya kai ka..?ka yi waauta ko nace kayi asara..!
Saboda Takaici bai bari ya karisa ji ba. ya Katse kiran kamar ya zagesa haka yaji Lalle ya yarda Fa'iza da gaske take malkulin gidan daman megidan suka mikamawa tunda ba wani abu kuma zan yi da shi ba, A dayan dakin dake tsakar gida aka jibge kayan na fito na gani kayan amfani kawai na kitchen na cire gadon da kujerun basu komai ba Yaya Mariya na baa,tare da Dirowowin yaran nace ta gyara,cafet ma duk ita na bamawa,Tv kuma nace Goggo ta Dauka,Kayan su Amir kuma daman har da su aka kwaso na ce Goggo ta kyautar nasan ba kara waiwayan su kuma za'ayi ba.
Goggo ta ga duka na kyautar da kayan har Jumnmala na bama kololi da Tukwane,Sai ko tamin mgana da cewa? ta ga na rabar da kaya nifa..?
Sai nace ba abunda zan yi da su.
Goggo tace"In kika tashi wani auran fa..?kai tsaye nace''Wa tab..Ni kasuwancna zan cigaba yi da karatuna"
Sai Goggo tamin shuru bata kara mgana ba,sanin Halina tunda na cije bamai sauke ni kan ra'ayina.
Tun faruwar abun da ya faru Ishaq bai kara min waya ko sako ba,sai na samu zaman lafiya cikin ikon Allah na gama iddata Abba sun zo garin sun yi Sati da kudin sa ya yi min Hidiman shiga Haddan al'hamis da jumma'a
Da karfe hudu zuwa bayan isha'i sai Islamiyan matan aure da Safe karfe 9am zuwa Goma da rabi na safe,Duka na hada na shiga zuwa Lokacin tuni yan gari sun san aurena ya Mutu,na samu salama yanzu da kwanciyar Hankali ina zuwa makaranta na maida Hankalina a karatuna ya'yana kuma ina mgana da su bani da wata damuwa.
Jummala ta samo min wata yarinya Laure ta na tayata aikin zobon da kunin aya in bana gida,ko kuma aikin su Tarare,na riga mun yi mgana da Abba zan fara kwangilar girke girken sha'ani a gida zai siyamin manyan Tukwane da murahu da Kololi,daman alokacin na kara siyan wata Frezeer guda d'aya ta daina isa ta tuni kuma mata su gane bangaran kayan kamshi da Gyaran jiki tunda ina tallata kasuwancina a makaranta.
Sai gidan Goggo ya zama wajen shiga da Fice gefe d'aya kuma ina kokari wajen karatuna ban yarda wani abu ya Daukemin Hankali ba.
Sauka nake so nayi na zama Mahaddaciyar Alqur'ani mai girma.





*Janafty*
[7/27, 7:24 PM] Hauwa Galadima: *KNKB3008*

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWOWINRL ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY*


*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

*BAYAN SHEKARA D'AYA DA WATTANI*

*KAROFI*


Ko daga tsakar gidan Goggo in ka shigo Dariyata zaka fara jiyowa. saboda yadda nake faman kyalkyata Dariyan ba kakkautawa har ina Dukawa rike ciki na jin ya fara kullewa.
Goggo ce ta dago labule ta Leko Dakin Lokaci daya tana Fadin"Ke kuma ke da wa kike ta Dariya haka har waje fa ana jiyoki"?
Ina Dariya ido na har ya tara kwallah na Dago ina fadin"Goggo ni da Badariya da Anum ne. ina Dariyan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login