Showing 189001 words to 192000 words out of 288345 words

Chapter 64 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

776

ma gansu ba sai ya rarrafa cikin Fitan hayyaci ya na kokarin rikoni nayi maza nayi baya da jajayen idanuwana ina fad'in"Kar ka kara tabani. Kar ka kara in ba haka ba wlh zan sharara maka mari"
Na fad'a ina nuna sa da yatsa cikin bacin rai da bai taba ganina aciki ba
Sai ya kasa karisowa gabana,cikin rawan baki da na murya yace"Fa'iza ba kin ce kin yafemin ba..?
Me ya sa..?
Kai Tsaye nace"Eh da gaske na yafe maka,.ammh ba shi zai goge tabon da kayi ma rayuwata ba.
Dalilinka aure ya fita kaina na Tsani duka maza sannan nake Tausaya mata ire ire na da Tunanin wata irin Rayuwa su kuma suke fuskanta a gidan nasu auran..?ka taba Tunanin ko sau d'aya kayi min adalci?
Nace ka taba wannan tunanin.?
Sai kawai na kara fashewa da kuka ina fadin"A? gabana ka kori yar'uwata uwa d'aya uba d'aya,Har kana ikirarin in ka kara ganinta a gidanka zaka had'a ta da Hukuma?ashe ko bata ci darajan aurena da kake yi ba, bazata ci Darajan zumunci ba Ishaq..?
Mahaifiyata ta rasu bata san Dadina ba. Har ta koma ga Allah ban taba zama da ita na yini d'aya ba.
Ranar da zata rasu ma baku barni na kwana da ita ba,ta rasu ban sani ba.
Na rasa uwata ammh ko gaisuwa baka zo min ba, kana wajen wacce ta fini muhimmanci a wajenka.Sai da ka dawo baka iya ce min Fa'iza ya hakuri ba sai Duba na kayi kana ce min ashe wai kuma babarku ta rasu..? Wai ne ma baka Tabbatar ba.?shine kake so na manta..?ko kuwa yadda ka ware ni daga cikin sauran mata a dalilin auranka yasa nayi shekaru ina fama da Gulit din mata masu kyau da gata ne suka chanchanci ado da kwalliya,a gidan ka na fuskanci mata ire irena basu dace da samun soyayyar miji irin Ishaq kabir karofi ba. Shiyasa na yanke shawaran karshen zama na dakai yazo daga yau.Na rantse da Allah bazan bika ko'ina ba. Daganan karofi zan koma daman ranar da Baba yace zai had'a aurena dakai Mama ta koreni sannan tayi alkawarin bazan koma mata gida ba,Karofi na koma wajen Goggo kuma chan aka daukoni nan duniya bani da gatan da ya fi gaban Goggo gabanta zan koma na zauna Domin Fuskarta Sabuwar rayuwata"
Na karishe Fad'a ina share hawayena lokaci Daya na mike da Sauri ina fadin"Zainab zata iya kula da kai. Yara kuma Amir da Anum sun yi girman da zasu iya kula da kansu. Ahmad da mutsy ba su da matsala zasu kula da su.
Ba lalle ba ne don na faro rayuwata dasu na karishe ta da su ba..Haka Allah ya kaddara Labarin ya kare daga wannan Lokacin"
Na fad'a Lokaci daya ina Daukan karamar jakata,Mama na gefe sai sharan kwallah take Anty Hure ta sha gabana tana fadin"Haba Fa'iza ku ba yara bane. yi hakuri mu tafi in mun je chan sai a zauna a fahimci juna'
Kallonta nayi kafin nayi mirmishin takaici na tuna har da ita a masu biye ma Mama suna cin zarafina,sai kawai na kad'a kai ina fadin"Bakin alkalami ya riga ya bushe Anty Hure.."
Na kad'a kai na zan fita waje,Ishaq ya yi kukan kuran shan gabana yana rike Hijabina na balla masa harara ina fadin"Cikani kafin raina ya baci"
Yaki ko sakina fad'i yake yi"Fa'iza ina zaki.?Fa'iza kada ki yi min haka..?me zan ce ma yaran chan..?
Fa'iza..Fa'iza"
Sharr sai kuka abunda ban taba gani ba,kai na kauda abubuwan suna dawomin kamar yanzu komai ke faruwa,kwace hijabina nayi ina fadin"Na fada maka kuma zan kara fad'a maka na gama zaman aure da kai. Na tsani aure na tsani kowani zamantakewa,Ka sauwak'e min Ko kuma ka k'ara Turgud'e shi daman jinginanne ne"
Na turesa zan wuce sai ya makale kafafuwana yana fad'in"Kada ki yi min haka Fa'iza,Kada ki yi min haka"
Kasa kwace jikina nayi sai kawai na juya ga Mama tana kuka nima ina Hawaye nace"Mama ki fad'a masa ya cikani don Allah"
Sai Mama ta sunkuyar dakai shi ko,sai alokacin yaga su Maman sai ya sakeni ya Rumtuma wajenta ni kuma sai na kwashi Sauri na fita Daga Falon ina Fitowa sai nayi Turus ganin yaran duk Tsaye suna jin abunda ke faruwa ga Anty Binta itama.
Cikin mamaki tace"Fa'iza meke faruwa ne har kofar gida ana jin Hayaniyar ku..?
Ban bata amsa ba Ishaq ya fito rike da Hannun Mama ya kawota gabana yana fadin"Mama ki gaya mata wlh nayi nadama.bKi gayamata abunda Baba ya sha fada'min,Yace in na rabu dake zan lalace Fa'iza ko so kike kada nayi albarka..?
Komai ban ce ba kaina na kallon kasa ina Digar kwallah,Mama ma sai sharan hawaye take yi Anty Binta ta kalli Anty Hure tana fadin"Anty meke faruwa ne..?
Anty Hure cikin Damuwa tace"Fa'iza ce tace bazata bisa lagos ba. Tana neman saki ne da wasu mganganun da ban gane ba.."
Sai ta waro ido kamar yadda yaran suka yi cikin wani yanayi tace"Fa'iza yanzu kuma?kika ma zauna dashi a bai da shi sai kuma yanzu da Dadi yazo sai kice haka.?aa ku bari muje chan sai mu zauna mu tattauna kin ji ko..?tafad'a gabanta na fadi domin bata san ya wannan al'amarim zai kare ba.
Jallonata nayi ina tuna Yadda tayi Tsawon shekaru tana Tozartani har da ita masu saka bakin na zauna sai kawai na share hawayena ina fadin"lokacin da bai da aiki wannan yanayin da mata ire iren Fa'iza ya Dace shiyasa ban tafi ba tun a wanchan Lokacin,sai yanzu kuma da komai nasa ya dawo sai nayi Tunanin Lokacina ya kare daman kema kin sha Fad'a jin dadi bai dace da mata ire irena b???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a,wahala ce da bauta ta Dace dani kamar yadda Mama ta sha fada. Shiyasa zan tafi zainab itace ta Chanchanci zama da shi Tunda ita ta tako kashin arziki sannan bata yi kama da matan bauta ko wahala ba.."
Dukkansu Tsaye suka yi an kasa mai mgana ina gani Anty Binta na zaran ido sai kawai nayi Dariyan takaici kafin nace"Na kwashe fin shekara goma ina bautar aure kuna ganin komai ammh baku taba zaunar da shi kin fad'amasa bai kyauta ba..?sai ni yau don a shekaru goma sha Biyar da auran mu na yunkuro sai ku nemi Danne ni.?wannan karon ba wanda ya isa ya hana Fa'iza tafiya.
Zan tafi kuma tafiya ta har abada"
Ina gama fad'in haka na ratsa Mama zan wuce sai ta riko Hijabina tana kallona,yanayinta zai sakani rauni sai na daga kaina sama cikin wata murya tace"kiyi hakuri Fa'iza.
Ba domin na isa ba..Ki yi hakuri ki Duba yara nan kada ki bar su yi maraicin uwa"
Ta fad'a tana nuna su Amir,Anum har ta fara kuka da su Ahmad zuciyata ta karye ammh ban damu ba Hawayena na Shatata saman fuskata nace"Ke kan ki shaida ce Fa'iza bata dace da D'anki ba.,yaran nan kuma rabo ne Allah ya sa na same su,maraici kuma baza su yi maraici ba Mama kina nan ga Zainab,sannan shi ma babansa zai kula da su tunda ya'yansa ne sune Dolensu bazan ce a zama da shi bai Tabamin wani abun alheri ba,yayi min Tunda dalilin sa yasa yau nake amsan sunan uwa,ammh mganar na Duba yaran nan bai taso ba. Nima a lokacin da yake tozartani ko sau d'aya bai tab'a Duba darajan ya'yana ba.."
Na fad'a ina kallon su, bana so na cigaba da mgana a gabansu kada su ji,kamar ma Amun da Amir tunda suna da wayan su.
Na tuna Lokacin da Anty Binta tazo ita da Mama suna min watsi da kaya akan sai na bar gidan,meyasa yau don nace zan tafi sai su damu..?
Wani tukuki ya taso min dayasa har jiri na fara gani cikin Duhun ido na juyo ina fadi'n"daman kuna so na tafi,Aurena ba alheri ba ne ko ba haka kuka fad'a ba..?meyasa don yau nace zan tafi kuke magiyan kada na tafi..?Wlh kaina tuni ya Dauki Dumi kuka na kara Fashewa dashi na juya ga ya'yana da suke kallona cikin rauni hatta Amir da ba kasafai ake ganin kukan ba yau har da majina,Ahmad kuwa da gudu ya nufeni ya rumgume ni yana fadin"Umma zan biki ni dai"
Musty ma ya kariso yana kuka ya rikemin Hijabi gam yana fadin"Nima Umma ke zan bi na fasa zuwa Lagos din"suna mgana kukana na karuwa Anum ma ta rugo ta makalemin jiki ta fashe da kuka tana fadin"Umma nima ke zan bi"
Ina Kuka suna kuka Amir na Tsaye shi bai zo ba na dago ina kallonsa cikin kuka nace"Amir ku yi hakuri ka zo ka taimaka min ka lallashi kannen ka"
Sai kawai shima ya rugo da gudu ya Rumgumeni yana fadin"Umma zaki tafi ki barmu?don Allah kada ki tafi Umma kada ki tafi ki barmu"
Sai kuka yadda suke kukan ne yasa naji gabbaina sun yi sanyi in na tafi na barsu yaya rayuwarsu zata kasance?sai na juya ina kallon Ishaq da idanuwansa suka kad'a jajir,sai kawai naji Duhu ya rufeni da Hanzari na yakice su a jikina na duka Bisa gwiyoyina dukkansu na rike hannayensu cikin nawa sannan na Dauki na Amir na rike ina fad'in"ba inda zan je ina karofi gidan Goggo zan koma,In ina bukatar ganin ku zan zo ko ku kuzo wajena,sannan zan rika kiran ku a wayar Anynku muna gaisawa kun ji ko?
Ahmad ya makale kafada yana Fadin"ni dai umma zan biki"
Musty ma yace haka Anum Sarkin kuka tace"Umma ki tafi damu chan gidan goggon mana"
Ina girgiza kai hawaye na zubomin nace"Bazai yuyu ba Anum. ku kuna da Baba sannan ga kakar ku nan bazai yuyu ku bini ba,ni kuma bani da uwa ba ni da uba,Goggo itace gata na shiyasa zan koma wajenta ku kuma Babanku na da mata Antynku ga kannen ku su Farhan,ku zauna lafiya da junan ku ku zama masu jin mgana Amir kai ne Babba ka rike kannen ka Amana ka ja su ajikinka a matsayinka na Babban Yaya,ku zama masu jin mgana da Tarbiya Anum ki kula da Ahmad kin ga shine karamin cikin ku kada ku takurama Antynku komai tace ku yi kuyi kun ji ko..?.sai suka kasa dagamin kai ina kokarin Dauriya na saki Hannayensu na rika bin su daya bayan d'aya ina share musu hawaye ina fad'in"kada ku ce zaku rika saka Anynku mgana,Amir karatu ka rika duba na kannenka,Karatun Qur'ani ku rika bita kada ku manta da azkar din safe da maraice,ban da abokan banza sabon waje ne bakusan kowa ba,kada ku manta da Tarbiyan da na baku Anum kece mace ki rika taimaka ma Antynku da ayyukan gida kuna ji ko..?
Sai gabadayansu suka bare min baki Amir jikina ya fad'a yana fadin"Umma mu ba ma a son Antynmu ke muke so.."
Hawaye suka kwaranyomin na kamkamesa ina kuka Anum ta ruga wajen Babansu tana fadin"Daada kaje ka ce Umma kada ta tafi.."
Tana fada tana jan Hannunsa,sai ya biyota har gabana shima dukawar yayi,yana fadin"Don Allah Fa'iza ki duba yara nan"
Ban ko amsa mai ba na hada ya'yana na Rumgume gabad'ayanmu muka saka kuka,Mama na gefe sai ta juya kawai ta fice tana kuka Anty Binta ma duk jikinta yayi sanyi in Fa'iza ta tafi ya kuma abubuwa zasu tafi?Zainab wannan yar son jikin da bata iya komai ba, ta ina zata yi da Dawainiyar yara?akwai matsala babba kuwa.
Suna kuka ina kuka da na ga bazai Fissheni ba na rarrashi kaina na koma ina ba su hakura suka makaleni suna kukan sai sun bini Hon din masu mota ne ya ankarar damu suna jiranmu,Ishaq ya marairaice yana fadin"Na siya mana Ticket Fa'iza asaran kudina kike so nayi..?
Kai tsaye nace"Ai ban ce ka siya har dani ba. Tunda ban ce maka zan bika ba"
Cikin wani yanayi yace"To dukkanmu mun fasa bazamu tafi ba, mu tattara muje karofi a warware komai"
Cikin yak'e nace"Kada ka biyoni Karofi Ishaq ka lallaba ya'yanka ku tafi,kada ka manta aikin.?ka fara ba jimawa rashinka a office zai iya zame maka matsala sannan meyasa bayan ka kashe kudin jirgi zaka fasa?
Na fad'a ina kuramai ido gani yayi kamar na fara saukowa yasa da Sauri ya rikeni yana fadin"Fa'iza zuwan bashi da amfani idan baki kin sani ko?
Kai tsaye nace"Bazan bude baki nayi mgana ba.ka lallashi yaran nan ku tafi in kuma kace zaka bini karofi zaka Fallasa kanka da kanka. Daman na Fada maka da bakina bazan fad'i komai ba,sai dai in kai ka fad'a da kanka"
Shuru yayi yana ajiyar zuciya a Firgice kamar wanda yayi karya,Ban damu ba naja hannun su Ahmad da Musty,su Amir suka biyo bayana muna zuwa kofar gida masu motoci na jiran mu sawa nayi aka Fitomin da akwatina da jakunkuna na,nace a sakamin a karamar Golf din nan,Mama na gefe tana sharan kwallah,su Ahmad nata kuka har Lokacin sai na Daure saboda bazan bari su hanani Tafiya ba,key din gidan na isa gaban Ishaq na Damka masa ina Fadin"Key din gidan nan, ne Sauran kayana in ka sauwakemin zan zo na kwashe"
Makullin fad'i ya yi a kasa,ya kasa amsa ni kuma na juya ina goge kwallah na bude bayan mota na shige,Su Amir sun yinkuro zasu shiga na rufe kofar da karfi ina kuka ina ganinsu suna kuka suna dukan jikin mota ammh na kasa motsi,Direba ya shigo yana fadin"Hajiya yaran nan zasu hanamu tafiya fa"
Kai tsaye ina kuka nace"Glass.! d'agamin"
Ba musu ya d'agamin na Leko da kaina da sauri suka nufeni Ahmad sai fadi yake Umma nima zan biki shi da Musty,Amir na share ma Hawaye Na rike hannun Anum ina fadin"ba na ce ku lallashi kannen ku ba..? To in dai kuna kuka bazan dawo na Dauke ku ba"jin haka yasa suka daina kukan Amir yace"Umma to kizo mu tafi tare"kai tsaye nace"Aa ku fara yin gaba, ni zan zo daga baya..Ka kula da kannen ka kaji ko Amir"
Sai ya gyad'amin kai dukkansu na Shafa kansu ina fadin"Allah ya yi muku albarka"Sai kuka yaci karfina cikin kukan nace"Direba muje"
Lokaci daya na maida glass din na zuge,mun fara tafiya na juyo ina daga musu hannu Ahmad ya kwace yabi motarmu yana kiran sunana har yana Fad'i ina gani Baban yaje ya daukesa,Anum kuma Mutsy ta rike tana kuka Anty Binta ta rike Amir kasa Daurewa nayi na juya ina kuka kamar in ce Direba ya Tsaya sai kuma wata zuciyar tace"Fa'iza ki sani ko kin koma baki da wata daraja. Ishaq Zainab kadai yake so ke alfarma yake miki"
Ammh ya'yana fa..?basu saba da kowa ba sai ni wazai kula da su..?zasu fara sabuwar rayuwa a inda bani ya ya zasu tafiyar da rayuwar su.?Zainab bazata kulamin da yarana ba bazata iya ba,yar gatace bata saba da wahala ba ,yaranta ma yan aiki ke daukan mata su,Tarbiyan su da na dauk'i shekaru ina ginawa in ta rushe fa..?
Kuka nake yi da karfina har sai da Direba ya juyo yana fadin"Hajiya ki yi hakuri,In bazaki iya tafiya ba sai mu koma ko kuma ki taho da su naga yaran basu son tafiyarki hala rabuwa kuka yi da Baban nasu,duk da shima naga kamar bai so tafiyar ta ki ba..?
Irin dirobobin nan ne masu fad'i ba''a tambaye su ba.
murya shake nace"Karofi..Karofi zaka kai ni"
Na katse mganarsa lokaci d'aya ina cigaba da kuka zuciyata na Zafi kaina ya fara Dif Dif ga jirin danake ji. alama ce ta jinina ya haye sama.
Har mun yi nisa sai naji bazan iya wannan jarumtar ba ya'ya na,ya'yana kawai nake tunani.
Sai kawai na ce ma Direba"Tsaya mallam.."
Sai ya juyo yanaa fad'in"In tsaya..?
Sai kawai na gyad'a mai kai da sauri ina fad'in"Mu juya mu koma..! mai dani da sauri'
Ina haki na fad'a,Tunani na da zullumi na,kada kafin mu koma mun iske sun tafi.
Na fasa bazan iya nesa da yarana ba. tunda na iya kwashe tsawon shekaru goma sha, cikin tozarci na jure me zai hana yanzu bazan jure ba..?kuma yayi nadama zan karbi Tubansa zan bisa naje na zauna tare da yarana.
Muna tafe ina fadin"Kayi gudu don Allah ka yi sauri."
Yadda nake mganar zaka san bana cikin Hayyacina.





*K'arshen littafi na Biyu,Littafi na uku zai zo in na samu natsuwa insha Allahu,Ammh ba gabadaya zai zo ba,zai zo kamar yadda muka fara daga farko.*
*Nagode..Nagode da Soyayyarku Allah ya bar zumunci Ameen*




*Janafty*
*19/17/2023*




*KNKB3001*

*Madallah da ku,Nagode da soyayyarku gareni.*
*Nagani kuma na yaba,Ubangiji ya saka da alheri. Ina gaida masoyana gabadaya Allah ya had'amu a Aljannah Ameen*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

Lokacin da nace Direba ya juya dani,fita daga hayyacina nayi.
ya'yana kawai nake tunawa,ina tuna kukan da suke yi sanda zan tafi a raina nake jin kirjina ya matse waje d'aya,na kasa Sarrafa kaina abu d'aya zuciyata da gangar jikina suke fad'amin. Fa'iza Zaki iya ba ma auran ki wata dama Fa'iza zaki iya ko saboda ya'yanki.
Bansan Lokacin da na furta a fili ba"Zan bashi wata dama. Zan bashi ko Saboda ya'yana"
Ina fada ina shara hawayena ina kokarin bama kaina karfin gwiwa,Sai dai sai me?muna shiga layin sai naji gabbaina sun karayin sanyi kalau,zuciyata ta fara sakewa kirjina ya fara nauyi,gabana kuma na fad'i Ras! cikin wani yanayi a acikin zuciyata nake jin kamar ana min mgana da cewa Haba Fa'iza ashe kin manta irin zaman da kika kwashe shekaru sama da goma kina yi tare da Ishaq.?Ashe kin manta bai taba sonki ba?Mama bata kaunar ki ba,ko ya'yanki Rabo ne ya shiga Tsakani,kin manta da cewa wanda yace baya sonka har abada baya sonka? Sai alfarma yake yi maka kamar yadda ya fad'a"
Ya'ya ba kanki farau barin su ba Fa'iza, bazasu mutu ba in kikaga sun mutu Lokacin su ne ya yi,in kuma suka rayu Allah ne ya rayasu ko kina Tare da su,ko bakya tare da su ta Allah in yaso zata kasance tare da su,kada ki bari Tausayin ya'yanki ya hanaki cika Muradinki.
Kamar wacce aka bugi kaina,cikin kiftawan ido na dawo cikin hayyacina na fahimci shirmen da na kusa yi ma kaina da rayuwata,kamar yadda na saba a baya.
Da sauri nace"Direba. Direba juya mu koma,Mu koma kawai"
Na fada ina kokarin danne kukana,cikin mamaki Direba yaja ya tsaya sannan ya juyo yana kallona Cikin wani yanayi ganin yadda nake kuka,sai kawai ya koma ya gyara zama yana fadin"Hajiya ki tsaida Shawara d'aya in tafiya tafiyar in kuma komawa to komawar"
Sai kawai na shiga Sharan kwallah da Bayan hannuna cikin Dashewar murya nace"Muje kawai.."
Cikin jadaddawa yace"kin tabbata Hajiya?
Cikin Tabbatarwa na gyad'a masa kaina lokaci


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login