Showing 249001 words to 252000 words out of 288345 words

Chapter 84 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

744

gatanan zaune ya bata zabi to kusan Fa'iza kan yaran nata yasa ta amince ammh mganar gaskiya Engr Fa'iza ke so kuma shi din ta bama Dama da Farko"
Sai falon ya yi shuru aka rasa mai mgana,Mama da Anty Binta suka hada ido suna kallon juna kunya da nauyi duk ya kamasu.
Ammi ko ajikinta ta cigaba da bada Labarin irin soyayyar Engr da Fa'iza ta karishe da fadin"Wlh yana ganinta haka din ta yadda take yaji duk duniya ba wacce yake so sai ita, ku duba dai matakin abunda ya taka a rayuwarsa ammh Fa'iza ce ta masa,Daga karshe da ta zabi koma ma uban ya,yanta sai Baban Nana ya bashi Hakuri da yake shi Mutum ne mai takwalli Yace bakomai Haka Allah ya kaddara kuma Daurin auranta ya kawosa Jibi yake da Tafiya zuwa America"
Sai falon ya dau Allah Sarki Yaya Mariya tace"Tab..'
Tama kasa mgana Nana fatima tace tana kallona"Daman ke kika zabi ki koma Fa'in mu..?
Sai na kasa mgana Idanuwana sun kawo kwallah,Goggo dai sai jinjina kai take yi ta dauki saunar mganar yadda taji mganar a gari batare da Abba ya kira su ba, sannan nima ban mata mgana ba kenan Ishaq da yaran Fa'iza ya yi amfani.
Goggo sai ta Bude baki tace"Bai ko kyauta ba in dai hakane da sai ya yi mgana da ita yaji ra'ayin ta ko.?
Da Sauri Mama tace"Kar ku ga laifinsa ita Fa'izan tayi mgana da Anum ta fada'mata zata dawo,sannan ta fadama Zainab su kuma suka fadamasa to shi rudewa ya yi yasa bai nemi jin ta bakinta ba kuskuran da ya yi kenan"
Tafada cikin fargaba da abunda taji,Yaya Asiya tace"Allah dai yasa hakan ya zama alheri"
A ka amsa da Ameen ni kan ina zaune kirs ya rage ban yi kuka ba Badariya na chan gefe sai auna wasu abubuwan take yi tsakani ga Allah wannan Engr ta lura da daman irin kallon da yake bin Anty Fa'iza da shi sai da akayi mganar ta Fahinci komai.
Tana hasaso yanayinsa a Fuskarsa Tabbas babban gwaska ne,taji matukar Dadi da Fa'iza ta samu wani mai kaunar ta bayan Yaya Ishaq sai dai an ce so so ne ammh son kai yafi, bazata zabi bare a kan yayanta ba ammh da ace wani ne bazata yarda Fa'iza ta koma ba, da sai ta bata shawaran ta auri wanda ke son ta ba domin komai ba sai domin kauna Daga Allah ba wanda zai ce zai yi mata alfarma ba.
A na cikin mganar sai ga Amir ya shigo da sallama sai falon ya yi shuru,Gaishe da su Goggo ya yi suka amsa cikin Fara'a Ammi tace"Ina ka baro abokin naka..?
Cikin yanayin sanyin sa yace"suna chan gida ni an aiko ni wajen Umma ne"
Sai alokacin aka lura da abunda ke Hannunsa,wani dan karamin kwali ne mai kyau yana kyalkyali wajena ya Nufa ya mikamin kwalin na karba ina kallonsa kafin nace"Waye ya baka wannan Amir..?
Kai tsaye yace"abokin Abba ne..yace sunansa Baba shima wai baba na ne"
Yana fadin haka gabana ya fad'i nasan waye ya bashi Engr ne.
Da sauri na kara rike abun na kasa mgana shi kuma ya cigaba da fadin"Shi ne yace na kawo miki"
Kai na gyada ina kokarin maida hawayena ban damu da yadda ido ya Dawo kaina ba na tashi na shige Daki har da turo kofa..
Na zauna a saman gado na bude kwalin wani irin agogon Silba ne mai kyau da yarari daga ganinsa kamar na Diomod,yana kyalli irin na mata da na gwada shi daidai ni a hannuna kamar an gwadani.
Sai wata karamar Takarda na gani a gefe na dauko na warwareta ga abunda ya Rubuta.

"Congratulation Faa'izaa. Allah ya sa ma abunda kika karanta albarka"
Ina miki Fatan alheri a sabuwar rayuwarki da zaki fara"

"Engr Abdulbasit Abdulghaffar Aluwatosin"

Haka na kamkame takardan ina kuka wannan wani irin shiga tsaka mai wuya ne..?bana duba ban kuma san wani irin zama zan yi da Engr ba, ammh ina masa kyakyawan zaton zan samun farimciki ko da ba duka ba a tare da shi Fiye da yadda na samu a tare da Ishaq sai dai ya'yana su nake tunawa bana so a wannan karon ma na kara karya musu zuciya, shiyasa na yanke shawaran komawa in dai su zasu yi farinciki na amince ko da nawa Farincikin zai samu tawaya.
Kwata kwata bana jin Farinciki ko annushuwa kan maida aurena da Ishaq,sai ma wani kunci da nake jin yana mamaye ruhina ina ji ajikina kamar zan koma gidan Jiya ne,wanda fa yace baya sonka to har abada baya sonka sai dai kila Daga baya ya Fahimci kana da wani Muhimmanci a Rayuwarsa ne shiyasa ya Damu ya kai.
Ammh nasan waye Ishaq ni ba Zabinsa ba ne bazan kuma taba samun Farinciki daga garesa ba..
Gobe ne za'a maida auran mu ammh mgana ta Fatar baki bata had'amu ba,koma ya tambayeni wani shiri nayi..?hakane soyayyar..?na fi Tunanin shima Saboda ya'yan mu ne sannan kuma da Tasirin zama tare da shi ba Domin muna da Fahimtar juna a tsakanin mu ba.
Na yarda da wani tunanin masana Soyayya,ita soyayya tana ginuwa ne tare da Fahintar juna,ban dad'e da Haduwa da Engr ba ammh ya fahinceni nima na Fahincesa fiye da yadda Ishaq ya Fahinceni shekaru kusan goma sha da auren mu nima yadda na Fahimci Engr wlh ban Fahimci waye ishaq ba. Saboda bai bani Damar haka ba abu daya kawai ya bani wanda zan Daki kirji na nuna shi shine ya maidani uwa ya bani Ya'ya bayan su a zama da shi ban san komai ba, sai Tozarci da wulakanci sai kuncin zuciya da ciremin dukkan sha'awan aure acikin raina.
A Daran ranar nayi kuka sosai kukan da bansan iyaka ba,Ina kuma kamkame da agogo da yar takarda a Hannuna ina ji ana kwankwasa kofar naki Budewa,inaga ganin halin da nake ciki yasa suka kyaleni.
har Biyu na Dare idanuwana Biyu,gajiya nayi da kukan na tashi na Dauro alwala na shiga Sallah bayan na Idar na Daga Hannuwana sama ina fadin"Ya Allah ga baiwarka nan Fa'iza kaga zuciya ka ga zabina sai dai na baka zabi. Sai ka zabamin Ishaq a karo na biyu..Ya Allah ina rokon ka da ka tabbatarmin da alheri ka bani natsuwar zuciya da kwarin gwiwa shi kuma Engr yadda ya kaunace don Allah,ka basa wacce zata kaunace sa shima domin ka,ka cire masa damuwan rashi na,ka yi masa kyakyawan Sakamako irin sakamakon da kake yi ma bayin ka Salihai masu Hakuri"
Ina addu'a ina kuka Sauran Daran da karatun Qur'ani na raya su kuma na Bude muryata har ma karatun ya tada wasu da asuba sauran kuma Dakunan su na Bisu na buga musu sannan na koma na tada sallar Raka'atul Fijir.
Ina sallamewa na Dora da Sallar asuba bayan na idar ina azkar barci ya rika Fizgata nan saman Darduma na bingire da barci ban ta shi ba sai tara na Safe kuma Daurin auran karfe Daya ne ina ta shi ba kowa a dakin, sai ni a firgice na tashi da ganin rana har ta fito,hayaniya na rika ji a tsakar gida ina lekawa naga suna ta ayyuka kamar ma sun gama abincin share share suke yi.
Nana Fatima ce ta shigo falon Goggo tana ganina tace"Amarsu kin tashi..?
Ina tura baki nace"Shine baku tasheni ba..?
Tana Dariya tace"Mu tashe ki mu yi laifi..?
Ban ce mata komai ba na juya na koma Daki har ga Allah naji zuciyata ta samu natsuwa kuma na samu saukin Al'amura naji na samu natsuwa Dari bisa Dari,wanka nayi tunanin na fara yi na shirya kafin mutane su fara taruwa duk da ni ban yi gayya ba ammh nasan Goggo tayi gayya kuma wasu mutanen arxukan ko ba gayya sai sun shigo.
Bani da wani zabi sai na Ubangiji kuma Tunda ya zabanin Ishaq to bazan yi Butulci ba na karba Hannu Bibbiyu.
Ina wanka Abba ya shigo gidan saboda ta bayin ne tsakar gida ina jin mganarsa,har yana tambayana shiyasa da na fito na shirya a gurguje cikin,less riga da zani ko kallabi ban saka ba na zumbuda hijabi na fita Falo muka gaisa da Abba da Mallam Sai Amir da ya taho wajena yana Fadin"Umma ina kwana"
Ina shafa kansa na amsa masa chan ya kwana wajen babansa.
Zama na yi a kasa Mallam ya bamu waje tunda kamar Abba na son mgana dani ne.
Cikin dattakonsa ya kalleni yana Fadin"Ya kuka yi da shi Ishaq din kan mganar tafiyarki..?
Kaina na kasa Amir na gefena nace"Ni bamu yi wata mgana ba Abba"
jinjina kai Abba ya yi kafin yace"Shikenan in an Daura auren sai ku yi mgana in zai wuce dake ne sai na baki kudin kayan Dakin ki yar'uwanki ta rakaki ki siya abunda kike so. ina Tunanin kila tare zaku koma"
Gabana na fadi ammh na cije sai kiran sunan Allah nake yi acikin raina,Abba ya yi ta min nasihan da suka kara sanyayamin jiki,haka Inno da Baba ati suna ta bani Hakuri da Nasihan zamantakewar aure.
har Abba zai fita ya tuna ya Dawo da baya yana fadin"Kin ga na manta ki kira Engr ki yi masa godiya 300thousand ya turomin yace a baki,ko kuma ma kije chan gidan ku gaisa ki yi masa Godiya,Engr mutum ne mai kirki har ga Allah a zuciyarsa komai ya wuce, yace ke ba Rabonsa ba ne"
Kai na kasa na Daga ma Abba kai,ina son tashi ammh na kasa bani da kwarin gwiwan Fuskantarsa yasa nayi zama na Badariya da Nana Fatima ne suka jani Daki suka tasani gaba da tsiyan sai nayi kwalliya
Gajiya nayi na kyalesu suna min kwalliyar a waje kuma Yaya Asiya ke fadin ko kayan gyara ban sha ba, Ammi naji batace komai ba saboda Ishaq ne yasa bata bani komai na shafa ba, ammh da Engr ne da an ga Ruwan gyara kuwa.
Yaya mariya ne tace tana da wasu sai a bani na sha Goggo kuma tace kwanaki ai ta bani na tsumi na sha da tace na mganin sanyi ne achan Daki kuma sai da sukamin kwalliya suka min Dauri sai ga shi na fito ras dani Allah yasa daman kaina ya Tsefe yake Kunshi ne ban yi ba.
Badariya sai fadi take"Kina gyara wasu amaran ammh ko yar Dilkar nan bazaki kwama kan ki ba..?
Nana Fatima tace"Ba kuma turarren kamshi? ta kuma iya had'a ma wasu ammh ita ko na goga ma jiki bata da shi"
Duk ina jin su ban ce musu kala ba ina da Turaruka suna cikin kayana ne ban fito da su ba, Tunda ba amfani zan yi da shi ba kuma ma ina da Zallar madaran Turaren ban dai hada ba ne.
Tunawa nayi da mganar Abba yasa nace musu zan fita Amir ya fice tun dazu kila yana wajen babansa.
Sai kuma na rasa yadda zan yi na fita sai na ari wayar Hafsah na kira Abba na tambayeshi suna tare da Engr ne..?
Abba yace basa tare sun fita da mallam Shi Engr na gida naje nayi masa godiya.
Kunyar zuwa ni kadai yasa naja Nana Khadija nace ta rakani,na saka Dogon Sabon Hijabina mai ruwan madara da takalmi,goggo kawai na fadama inda zani ta kalleni cikin wani yanayi kafin tace"Yakamata kam sai kin dawo"
Suna ta faman tambayana ina zani nayi musu banza domin haushin su nake ji suma.
Muna fita waje muka hadu da Yaya isa da su Yaya Salisu muka gaisa suna ta zolayata mun wuce kenan sai ga Yaya Ishaq da Amir,har ga Allah ni ban gan su ba ance hankali ke gani ni kuma ina chan tunanin haduwata da Engr suna ta mana mgana ban ji ba hatta Nana khadija bata gan su ba tunda suna ta gefen hanya ne.
Shi kuma yana ganin mu mun nufi gidan Abba sai yayi tunanin ko shi nake nema sai suka biyo bayan mu.
Tunda tun safe suna tare da Engr suna ta Hira mutum ne mai ilimi ba ruwansa ga sakewa da mutane. tun a jiya Abba ya yi masa bayanin shine Ishaq din da ya kirasa kan mganarsa da EFCC har yasa mahaifinsa ya shiga ciki,Engr na ta mamakin daman shine mijin Fa'iza kenan..?
Ko a fuska bai nuna masa komai ba suka cigaba da tattauna mganar aiki Sai Ishaq ya Fahimci Engr mutum ne da yake da ilimin rayuwa da wayewa ga shi bai da girman kai duk ko da matakin Rayuwar da ya samu ya yi mamakin da yaji sunansa ashe bayarbe ne..?ko a kama ko a mgana ba shi da kama da yarbawa Allah mai hikima kenan..
Dayake gidan shashe biyu ne shashin da aka bude na Abba sai nayi Tunanin yana ciki muna kokarin shiga Nana Khadija tace min wai fitsari take ji nace mu shiga tayi tace a'a bari ta koma gida tayi ba'a son raina ba ta koma tana fita suka hade da Ishaq a Hanya shine yake ce mata ya gansu yana ta mgana basu ji ba..
Nana khadija tace"Laa bamu lura dakai ba dayake muna ta sauri Anty Fa'iza tace na raka zata je wajen Engr"
Gaban Ishaq ya fadi bai gane zata je wajen Engr ba..?
Bai gama tunaninsa ba Nana Khadija yace"Tana chan ni zan koma gida ne na Dauki wani abu"
Fitsarin ne ya matseta sai ta wuce da Sauri bayan tace Amir yazo ya rakata sai ya noke wajen Babansa.
Ishaq kasa gaba ya yi ballatana baya haka kurum yaji shakku a ransa.
Sai da Amir yaja hannunsa yana Fadin"Muje Daada Umma na chan na jiran mu"
Kamar an jasa haka ya shiga Binsa har gidan.
Suna bakin kofar falon sukaji Muryan Engr na fadin"Faa'izaa..Son da nayi miki daga Allah ne. Don kuma na rasaki sai na butulce masa..?
Sai kafafun Ishaq suka fara rawa jin kalaman Engr,sai dai kuma bai jin mganar Fa'iza ba, abun mamaki sai Amir shima ya Tsaya cak kamar ubansa.
Ji sukayi cikin tattausan murya ya Cigaba da fadin"Ni daman bana so nayi miki Dole wajen aurena. Tunda kika zabi komawa gidan mijin ki i will Support u Faa'iza ni masoyin ki ne masoyi na Hakika"
Sai a lokacin yaji muryata cikin sanyi ina Fadin"Duk da haka nagode Abba ya fadamin abun alheri Allah ya biya da Aljannah"
Kai tsaye ya amsa da Ameen Ameem.
Duk kokarinsa na kada ya kalleni ya kasaa sai da ya kuramin ido yana daga zaune kan kujera ni kuma ina zaune a kasa ne sa da shi, daman sanda na shigo anan na samesa.
Sanye da Farar shadda har da babban Riga sai kwarjinsa ya karu a cikin Idanuwana mirmishin nan nasa bai bace ba.
Cikin kauda shurun yace"1pm ne Daurin auran ko..?
Kaina na kasa saboda kallon Engr Daidai yake da Ruguza duk wani kwarin gwiwata.
Ban ba shi amsa ba sai ya yi mirmishi kafin yace"Abuja zan wuce ana gama Daurin aure nan, sanadin ki yasa cikin wattanin nan ina ta tafiyan Mota Faa'iza"
Muryata a shake nace"Allah ya kiyaye hanya'
Ya amsa da Ameen kafin yace"Tafiya ta a America ranar Tuesday ne fa,sai nayi wajen 1month achan kafin na dawo tunda aikin daga nan Ma'aikatarmu ta Edo ne suka turani"
Ni dai ina jin bayaninsa na ko kasa motsi kamar yadda Shima Ishaq ya kasa motsi Amir kuma tunani yake Umma zata auri Daada na biyu ammh me take yi da wannan mutumin kuma ..?
Gani nayi na kusa rasa jarumta ta ga Khadija taki dawowa yasa na mike ina fadin"Zan tafi"
Shima sai ya mike yana fadin"Tun yanzu Faa'izaa..?
Yadda yaja sunan Faa'izan ne ya karyamin Lago na sai da na Dago ina kallonsa sai ya wani sakarmin mirmishinsa mai kassarani lokaci daya yana Lumshe idanuwansa..
Ji nayi kamar zan fadi ammh bai lura da haka ba kai tsaye yace"Kin yi kyau Faa'izaa.."
Yau dai kad'ai Ki bari Tosin ya yaba faa'izarsa"
Yanayin mganarsa yasa na kwashi Saurin zan fice Tsautsayi yasa na ci tuntube da Cafet din dake Tsakar Falon sai nayi gaba zan fad'i da azama da wani karfin gwiwa ya rikoni sai gani na Dawo baya Dumu Dumu a acikin kirjin Engr.
Sai na ganni yar karama dani a saman hammatansa tsabar yadda bani da Tsawo da girma
Cikin Sanyin muryansa yace"Subhanallah sannu baki dai ji ciwo ba ko..?
Kamshin Turaransa ne ya cikamin Hanci yasa na kasa mgana ina shirin kwace jikina daga rikon da yayi min, kamar daga sama mukaji an bankad'o labulen Falon an shigo.
Gabadayan mu a tare muka juya sai idon mu ana Ishaq.
Gabana ya yi kwance kwance yace Ras!
Ban ga Amir tare da shi ba ashe shi kuma sai yaki shigowa. ya tsaya daga bakin kofa bai so ya shigo yaga wani abu da zai saka yaga bakin Umma.
Engr bai damu ba sai ma sakina da yayi bayan ya tabbatar da na Tsaya Daidai har yana fadin"kin tabbata kina Lafiya..?
Kai na d'agamai jikina na rawa ganin irin wulalakantattacen kallo? da Ishaq ke bin mu da shi kamar wand'anda ya kama suna wani abun assha.
Engr ko Ishaq ya kallah yana Fadin"ko ka biyota ne kaji ta shuru..?
Sallama ma muke yi zata tafi"
Cikin kallon reni ya ke kallonsa duk da ya gani bai damu ba, ni ko jikina na rawa na kama Hanya zan fice sum sum sai ji nayi Ishaq yaja hijabi na ya Dawo dani ta baya kee da karfi ya yi jifa dani har? na kusa fad'i wannan karon ma Engr ne ya rikeni yana Fadin"Sannu"
Lokaci daya yana kallon Ishaq kafin yace"Ka yi mata a hankali mana..?
Ai cikin tsawa da Fusata yace"Kace nayi mata a hankali mana tunda abokiyar shashancin ka ne.."
Dagani haar Engr a rude muka kallesa baki bude shiko kishi da rashin sanin Daraja yasa idanuwansa ya Rufe gani yake yi raina masa wayau nayi ina tare da wani zan kuma koma gidansa.
Cikin Dariyan renin wayau yace"Ku ke kallona kamar baku gane manufa ta ba ko..?karya nayi ba shashancin kuke yi ba..?Abun naku ma bai isa ba har sai a ranar da za'a Daura mana aure shine kika lallabo kikazo a yi abunda aka saba, achan kaduna duk watsewar da kuka yi bai isheku ba ya sake biyo ki nan. Anan din ma a filin Allah na kamaku rike da juna saboda Lalacewa Fa'iza me kike nema.?
Me kika rasa..?
Oh na gane kudi ko..?yana sakar miki kudi ke da iyayen shi shiyasa kike sakar masa jikin ki Tir dake Fa'izaa. wlh kin yi asara idan har kin san kin Fara watsewar ki a waje tun wuri ki yi min bayani domin duk yadda nake so ki koma gidana bazan kwashi datti na kai gidana


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login