Showing 252001 words to 255000 words out of 288345 words

Chapter 85 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

707

ba,ki gurbatamin Tarbiyan yarana ba Faa'iza ba zai yuyu ba,Ki Fad'amin gaskiya nawa yake Biyan ki kina bashi jiki..."
Mganarsa tasa bata gama Fita ba na Sauke masa tagwayen maruka har guda Biyu dama da Hauni. kafin na Fashe da wani irin kuka wanda daga ji shi kasan na tsatsananin bakinciki ne da bacin rai.
Cikin kuka na nunasa da hannuna cikin ihu da Tsawa nace"Kul..Karka kuskura ka kara dangantani da barna ko datti Ishaq kada ka kuskura"
Na fad'a ina zubar kwallah shi ko duk da Mamakin marinsa da nayi haka ya watsake idanuwansa sun rufe Engr ko Daskarewa ya yi a Tsaye yana kokuwa da bacin ransa.
Dariyan wulakanci ya saka yana nunani sama da kasa daga karfi yace"Don na fad'i gaskiya shine kika mareni..?
Karya nayi nace karya nayi..?
Ba rike da juna na same ku ba..?
In ba iskanci ba ina ruwansa da cewa kin yi kyau kuma meyasa kuka kebe a gida daga ke sai shi nace Muharraman juna kuke..?
Ya karishe fad'a yana min ihu kawai sai na kasa tsaida hawayena cikin dauriya da wani Turiri dake taso min daga kasan raina nace"Gaskiya ka fad'a. Tabbas ka fadi gaskiya bai kamata a yi maka rufa rufa a kai maka Datti agidan ka ba,ballatana ta gurbata maka tarbiyan da ka kwashe shekaru kana yi ma ya'yan ka.".
In sha Allahu baza'a kai maka Datti gidan ka ba".
Na karishe fad'a cikin kuka hawaye wani na korar wani na kama Hanya zan fice Engr ya yi saurin kiran sunana"Faa'izaa.."
Ban juyo ba sai da na tsaya cikin kukan dake tasomin ina Dannewa nace"Kayi?min alfarman bazaka je ko'ina ba sai an gama Daurin auran nan..?
Ina jin muryansa cikin jarumta yace"In sha Allahu"
Ban tsaya ba na fice da Sauri ina jinsa ko kunya wai yana kiran sunana ashe da na koma ma auran Ishaq haka zan cigaba da Fuskantar wulakanci..?
Ashe a shekarun da na kwashe tare da shi bazai iya shaida ta ba?
Ina fita naci karo da Amir na tsaya ina kallonsa sai raunina ya karu na fashe da kuka da Sauri ya kariso zai rikeni na kauce na fita da gudu shima sai ya Biyo ni yana Kiran" Umma Umma"
Ina tafiya ina kuka kamar mahaukaciya ban je gidan Goggo ba. sai na wuce gidan su Yaya isa Dakin matar Yaya salisu ke bude ciki na shiga ina ta rafzan kuka sai ga Amir ya biyo bayana.
ba kowa a falon sai wayar yaya Salisun kila yana ciki ne,ita na Rarumi na shige uwar Dakin matarsa da ita na rufe kofa.
Ina ji Amir na kiran sunana Daga baya har da muryan Yaya Salisu suna kiran sunana cikin kuka da Ihu nace"Ku tafi kyaleni. lafiyata kalau bana son ganin kowa.."
Sun jini shiyasa Yaya Salisu yaja Amir suka fita daga gidan nan.
Ni kuma nan na sulale ina kuka kamar karamar yarinya.

******

Karfe Daya na ranar asabar din karshen mako,Dubban mutane suka Shaida Daurin auran *ENGR ABDULBASIT ABDULGHAFFAR ALUWATOSIN*
Tare da Amaryan sa *FA'IZA SIDI KAROFI* sauyin da aka same shi batare da kowa ya sani ba.
Abba shi ya yi ma Engr walicci Ya yin da Mallam ya zama waliyyina,Akan Sadaki Dubu Dari,kuma Engr ya biya da Cheque din banki tunda ba shi da Cash a hannunsa.
sannan Direban Engr ne kadai ya shaida Daurin auran sai shi Engr d'in cikin mutanensa, sai dai ya saka an Dauki komai Live ta Vedio call ga su Papa da Sweetheart da Sisters dinsa.
Daurin auran da ya faranta Zuciyar Engr sannan ya Kusa tafiya da Bugawar zuciyar Ishaq kabir karofi.
Engr gaban mutane acikin masallaci ya yi sujudul shukru kafin ya Daga ya hannayensa sama yana Fadin"Allah na gode maka. ba wayau na ba ne kuma Dubarata ba ne da ka bani Faa'iza amatsayin mata ba,Allah karka barni ni kad'ai ka yi min jagora wajen tafiyar da rikon Amanarta a tare dani"
Ba su Abba ba kowa dake masallacin nan Engr ya Burgesu ciki har da Jamal da yazo Daurin auran yayansa da ma wasu daga cikin abokansa sai sukaji Labari ya sha bambam.
Kallonsa kawai ake yi duk yayi zufa sai uban zare ido yake jamal ya taso yazo wajensa yana fadin"Yaya Ishaq ya haka..?
Sai a lokacin ya fara Nadaman abunda ya aikata duk da yayi nadaman tun ad'azu din ammh bai Taba Tunanin zai iya rasa Faa'iza a wannan gabar ba.
Ya dauka bata da wani zabi sai zabin shi da ya'yan su.
Idanuwansa sun tara kwallah dishi dishi yake hango Amir tare da Abba tun bayan da ya barsa nan bakin kofa bai kara ganinsa ba sai yanzu.
Kamar in ya gane manufar abun Amir ya fara Gudunsa kenan..?
Kenan yaji abunda ya faru tsakaninsa da Fa'iza..?
Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un
Ya fadi a zucci da Sarari kamar yadda ya saki wannan salatin haka suma acikin gidan Goggo,Mama da su Anty Binta ke salatin lamarin.
Har Labari yazo cewa ba da Ishaq aka Daura aure ba da Engr ne.





*Janafty*


[7/31, 11:43 AM] +234 803 974 5115: *KNKB3015*

*Na gaida ke,My Anty. Anty Sise&?Kyakyawan sharhin ki yasa kin gama fad'in komai game da wannan labarin,Madallah da ke,Allah ya raya Zuru'a*


*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

*AWANNI BIYU KAFIN DAURIN AURAN*.

A lokacin da na shige dakin Matar Yaya Salisu Zulaihat,bana cikin hayyacina zuciyata gabadaya tayi Duhu tare da wani irin kuncin da na jima ban jini cikin yanayin ba.
Kuka nake yi da hawaye? da sautin muryata ina tuna kalaman Ishaq gareni da ya kirani Datti gaban Mutum mai karamci irin Engr.
Tunani nayi cewa har abada bazan yi kima a idon Ishaq ba,baya sona kuma bazai taba sona ba,ba abunda zai iya sauya wannan abun kawai dai akwai wani gibi ko bangaran da ni zan cike masa ne shiyasa yaso komawata garesa.
Ammh daga yanzu na fahimci komai kuma bazan kara bari rayuwata ta kara shiga wani hali ba,ya'yana na wa ne har kuma gaban Abada ba su da uwar da ta fini a wajen su,ko da sun Raunana na dan Lokaci ne zasu dawo daidai da yardan Allah.
Da wayar Yaya Salisu nayi amfani na kira Abba ina kuka daman na Haddace lambarsa sai da na saka naga shima ashe yana da lambarsa.
Jina cikin kuka da Damuwa yasa Abba yace na zauna a inda nake ga su nan zuwa shi da mallam bayan na fad'a musu ina gidan su Yaya isa.
Sai da naji muryan Abba na bude kofa ina kuka gabansu na zube na had'a Hannayena Biyu ina fadin"Abba in nace na fasa komawa gidan Ishaq ran ka zai baci..?ba zaka kalleni a wacce ta maida kai karamin mutum ba..?
Sai Abba ya saka Hannu ya Dago ni Cikin wani yanayi muka isa har falo kan Daya daga cikin kujerun falon ya zaunar dani su ma duka suka samu gefena suka zauna cikin Tausasawa Abba yace"Bazan taba cewa ba Fa'iza daman ai zabin naki ne ba namu ba ko ba haka ba Mallam..?
Sai ya jinjina kai yana fadin"kwarai da gaske"
Cikin kuka na zayyane ma Abba komai da ya faru tsakanina da Ishaq na karishe da fadin"Abba ko waye ka auramin shi ni dai ka taimaka kada ka auramin Ishaq Saboda yace ni Datti ce bazan je ce na gurbata masa Tarbiyan ya'ya ba'
Na karishe fad'a cikin gunjin kuka Abba ya yi shuru ransa ya baci ya kasa mgana Mallam ne yace"Subhanallah shi kuma ya zai yi haka..?Ana mganar aure kuma zargi na shigowa ciki"
Abba ya yi huci kafin yace"Ai shikenan bakomai daman zabin na baki da kaina ban miki katsalandan ba ne, saboda watarana ko bani ki iya sanin abunda ya dace dake. tunda yace haka ya gama mgana ba kwantai kika yi ba Fa'iza ke yar baiwa ce in yace ke Datti ce wani a Dattin zan bashi auranki kuma ya karba tashi ki je ki wanke Fuskarki ki kwantar da Hankalin ki insha Allahu bazaki ji kunya ba Allah zai nuna miki Ribar Hakurin ki tun a duniya."
Kalaman Abba suka sanyayamin rai duk da ban kawo ma Engr a lokacin ba, na riga na yanke hukunci gwara na auri koma waye da na koma ma Waye da auran Ishaq,bayan tafiyar su Abba ba jimawa sai ga Ammi ashe Abba ya yi mata waya yace tazo ta zauna dani.
Alokacin su kan su su Goggo ba su san abunda ya faru ba, ita kanta Abba bai yi mata bayani ba yace dai ina gidan su Isa taje ta zauna dani bayan tazo ne na zayyane mata komai..
Kyafci ta fara kafin tace"Uhm komai akayi da jaki daman sai ya ci kara mutum mai kima irin Engr ya yi ma wannan cin zarafin..?
Ina hawaye na kasa mgana saboda ni kaina kunyar kaina da abunda Ishaq ya yi ma Engr duk ya kamani,Ammi ta rika fada kamar zata ari baki tana fadin"Daman wata Daraja naki ya sani..?dan renin wayau ne fa Jaka ya maidake wacce bata da yanci ki koma ki cigaba da gadin gida da kula da mahaifiyarsa da ya'yansa da matarsa. to ai kuma yaci taliyar karshe ya'ya in bazai rike ba ya baki zaki hada ki rike abinku kuma na tabbatar da Engr wlh ko duka duniya kika haifa bazai gaza ba wajen rike miki su ba'
Ina tsiyayan hawaye nace"Ammi ni fa ban ce Abba ya auramin Engr ba. Cewa nayi ya bani duk wanda yaga Dama"
Ammi ta min dakuwa kafin tace"Kaji min sakarci in ya je ya aura miki wanda baki sani ba fa..?an rabu da bukar kuma sai a haifi Habu"
Ina kuka ne ammh sai da nayi dariya a raina nasan Abba uba ne na gari bazai taba min zabin da zai zama Cutarwa gareni ba, shiyasa ma ban damu ba ni dai tunda na sahale ma kaina Ishaq sai naji kamar an saukemin wani katon dutse mai nauyi daya tokaremin zuciya.
Cigiyata suka fara yi dagachan Gidan Goggo,tunda an ce ina ko tare da Abba ne sai aka kira Ammi tace tana tare dani,Yaya Salisu kuma na tare da Amir yana lallashinsa Domin yaga yaron ya shiga damuwa shi ko Amir kalaman Daada ne ke masa yawo a kwakwalwa tare da Kukan Umma sai yaji ya tsani Daada ta ya zai kira Umma da wannan sunan mara kyau..?
Kuma ya sakata kuka.?
Kawai don yana Da dauriya ne yasa bai yi kuka ba ammh duk yayi zuru zuru.
Abba da Mallam suka tattauna mafita batare da sun yi zencen da kowa ba. Engr na gidan inda Ishaq ya Fice ya barsa cikin kogin nadama,Hankalinsa ya tashi Tunanin abunda ya aikata kuskure? ne bai zo mai ba sai da ya aikata wani kishin Fa'iza ne ya taso masa da yasa ya kasa iya Sarrafa kansa. kishin ta samu wanda ya fisa komai yace yana sonta shi ya Dauka bayan shi ba kuma wani namijin da Fa'iza zata Burgesa,yana da yakinin in ba shi ba,Fa'iza ba ta da kowa kuma yana takamar cewa shi da ta gujen ma wa bata da kamarsa sai ga shi Allah ya nuna masa Isharan sa da cewa ita Daukakan Allah ba ta zaba ba ne, Daukakarsa ta kowa da kowa ne koda kai ba kowan kowa ba ne in ya tashi zai Daukaka domin nuna izina ga maza ire iren su ishaq masu Tunani irin nasa.
Har ga Allah shi kan shi Engr bai san da Sauyin mganar ba sai da suka shiga masallaci Abba ya karkata ya ce masa ya kawo sadakin Fa'iza ya bashi auranta Engr sai yaji kamar bai ji da kyau ba, sai da Abba ya maimaita masa bashi da Cash sai cheque ya rubuta ya bada sannan ya kira Sister dinsa kafayatu Vedio call Papa na gida tunda Weekend ne ya bama Direbansa ya Daukan musu Daurin auran Live suka kallah duka duka Lamarin ya faru gaza da mintina talatin ne. sai akalan Fatan alherin ya koma ga Engr a madadin Ishaq da aka barsa baki Bude.
Engr bakinsa kamar zai Tsage daman ga shi ma'aboci mirmishi da Fara'a haka jama'a ke ta ba shi Hannu cikin masu hannu da shi har da Dr.Lawal bako. yazo Daurin auran Abba ya fad'amai Ishaq ma haka shi kan shi da yaga Engr sai da ya rankwafa Aiko a gidan giya akwai babba shi kan shi yasan yanzu ko yarsa zainab bata isa ta Dagama Fa'za kai ba,Tafita komai na Duniya Tunda ta samu miji a gefenta kamar Engr da ya taka matakan Rayuwa masu girma.

*******

Tsakanin Mama ko Anty Binta an rasa mai iya mgana ballatana su fahimci yadda aka samu wannan Sauyin haka bangaran su Goggo ma suna ta jimamin garin yaya aka samu Sauyi ba tare da kowa ya sani ba..?Sai dai ba amsa tunda mazan duk ba su dawo ba,ni kuma ina gidan su Yaya isa Nana Fatima ta kira Ammi tana fad'a mata Halin da ake ciki da sauyin da aka samu.
Ammi ta rangada guda ta yi rawa tayi juyi ina zaune ina kallonta Sai da ta katse wayar Fatima sannan ta kalleni tana fadin"Aure ya Dauru murna muke ta yi. Kin Zama Amaryan Engr igiya uku har Abada"
Kamar an zaremin wani mutuwar jiki haka naji,sannan na ji gabbaina da suka yi sanyi sun tashi daga suman da suka yi,Naji dai yanayina ya sauya kadan ammh kuma bana bakincikin sai ma wani boyayen ajiyan zuciya da na saki batare da na sani ba,Ina da yakinin zan samu farinciki ko ba duka ba ammh zan samu ko da kad'an Daga cikin farincikin da Sauran mata suke samu a gidan auran su.
Sai da mukayi sallar Azahar Ammi ta sani gaba muka koma gidan Goggo ba wasu jama'a sosai sai na gida,Muna shigowa Yaya Mariya ta saka gud'a tana fadin"Shi daman alkawarin Allah baya tashi"
Daman ita bata wani so Yaya ishaq ba,tun da farko da bata yi? da shi yasa har yanzu sama sama sama ne,ni dai daki na wuce,Su Mama na falo duk jiki ba Dadi,Badariya ce kadai ta biyo su Nana Fatima zuwa dakin wajena ita kuma Ammi ta tafi wajen Goggo Abba ya kirata suna bukatar abinci da abun sha.
Duk da Jikin Badariya ya yi sanyi bayan Nana Fatima ta rumgumo ni tana fadin"Ina tayaki murna yar'uwata. Allah ya sanya alheri"
Na amsa mata da Ameen kasa kasa Sai Badariya itama ta kariso tana Fadin"Ina murna Anty Fa'iza Allah yasa gwara da akayi"
Na amsa mata ina kallonta tana so mu yi mgana ammh sai taga idanuwan mutane shiyasa ta juya ta fice Su Raliya ne da su Yaya Asiya tare dani suna ta tattauna yadda lamarin ya sauya ni dai ina jin su ban ce komai ba zan yi mgana ammh ba yanzu ba.
Abinci su Abba Nana khadija da Hafsatu suka kai musu,Sai wajen uku na rana muka samu kebewa da Badariya shima din tazo fad'amin su Mama na shirin zasu koma katsina ne..
Cikin mamaki nace"Yau kuma..?Na sha sai gobe..?
Cikin damuwa tace"Mama tace kunyarku take ji bazata iya zama ba. taji abunda yaya ishaq ya aikata Jamal ya kirani a waya duk ya fad'amin yace Yaya ishaq nata kuka yana bama Abba hakuri, shi kuma yace bakomai tunda dai kin auri wani shi ba da shi za ayi masa rufa rufa akai masa Datti ba.."
Kai na sadda kasa ban yi mgana ba sai ta Dafani tana fadin"Don Allah ki yi hakuri Anty Fa'iza"
Ina kokarin maida hawayen da suka kawomin nace"Bakomai rayuwa ce Badariya"
Nama kasa mgana sai kawai na saka kuka,sai ta rumgumeni tana Lallashina itama tana cikin damuwa ammh kuma bazata iya gayamin ba ganin yanayin da nake ciki.
Tare da ita mukaje wajen su Mama,Anty Binta dai ta kasa mgana Mama ce ke ta bani Hakuri nace bakomai Anty mahma tace"Shi ma dai Ishaq kamar wani yaro..?
Ai ba haka ake nuna kishi ba"
Yake kawai nayi ban yi mgana ba Halisa nake kallo duk ta rame ta lalace kamar ba Halisa ba Daga gani dai tana ji ajikinta a raina nace Allah ya kyauta.
Anty Binta ke tambayan ina shi Ishaq din.?Badariya tace"Jamal yace ya wuce kano ta chan zai siyi ticket na komawa Lagos. tunda yasan tsiyar da yayi"
Mama tace"To ina shi Amir.?
Sai da akayi mgana na Tuna da Amir cikin Damuwa nace"Ko dashi ya tafi ne..?
Badariya na shirin mgana sai ga Jamal da Amir sun shigo tare,yana ganina ya Rugo ya rumgumeni yana kiran"Umma."
Mu kadai ne afalon su Goggo suna ciki,Ammi ta gama warware musu komai kowa yaji sai yace gwara da ya rasa Fa'iza bai chanchanta ba.
Mama har ciki ta shiga tana basu hakuri tana sharan kwallah Goggo tace bakomai kansa yayi mawa ga shi ya rasa Fa'iza ita kuma Allah yasa gidan arzikinta ne.
Ganin yanayin sa yasa nasan Amir na cikin damuwa sai najashi Daki bayan mun gaisa da Jamal shima hakurin yake bani nayi yake,nace bakomai a raina ko nace shi ke da Hakuri kuma yanzu ammh har abada bazan taba yafe masa da kazafin da ya kullamin ba sai mun yi Hisabi a gaban Ubangiji ranar gobe kiyama.
Tambayan Amir na yi da yaci abinci sai ya dagamin kai kafin yace"Naci ai ina tare da su Abba ne a sabon gida"
Sai nayi shuru na kasa mgana saboda nasan yaji mganganuna da na Babansa kuma wasu kalmomin masu nauyi ne a Tunanin yaro karami kamar Amir.
Ba zato kawai naji ya riko hannuna kafin yace"Umma ki yi hakuri"
Sai hawaye sharr da sauri na rikosa ina fadin"Kai Amir menene yasa kake kuka..?
Sai na rumgumesa ina Lallashinsa cikin shesshekan kuka yace"Umma ki yi hakuri kin ji ko.?
Sai naji kaunar d'ana ta kara ratsani na Dago fuskarsa ina share masa hawaye,ina fadin"To shikenan na hakura kai ma ka daina kuka"
Mirmishi nayi masa shims ya maidamin kafin yace"Umma gwara da kika auri Baba baki auri Daada ba. Tunda yace miki ke datti ce"
Cike da mamaki nake kallonsa kafin na samu bakin mgana yace"Baba yace yana son ki Umma. Muna yace yana son mu"
Sai ga hawaye sharr sun zubomin rike hannayensa nayi ina fadin"Nima ina son ku ya'yana ka kula da kannen ka Amir kuma kada ka kuskura ka fada musu abunda ya faru kaji ko..?
Sai ya gyad'amin kai alamun bazai fada ba,kansa na dafa ina fadin"Yauwa Sannan ka lallashesu in zasu yi kuka saboda ban dawo ba kaji ko..?
Nan ma kai ya gyadamin nima sai na jinjina kaina kafin nace"Allah ya yi muku albarka gabadaya"
Ya amsa da Ameen,mun dade muna Hira da shi yawancin labarin rayuwar su a lagos ne ina jin sa ina mirmishi gefe daya?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ina sharan kwallah Haka Allah ya kaddara bazan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login