Showing 234001 words to 237000 words out of 288345 words

Chapter 79 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

786

ma Dakyar ya iya yi saboda mamakin wannan al'amarin
Ganin haka yasa Engr yace"Kana mamaki ko..?
Ka daina mamaki nima jiya haka na kwana mamaki ammh daga baya sai na Fahimci Hadin Allah ne shi ne mai Tsara abunda yaaso alokacin da yaso kuma ya faru a sanda yaso"
Abba ya jinjina kai kafin yace"Hakane. Sai dai ka sani Fa'iza ba D'iyata?ta cikina ba ne..D'iyar kanwata ce mai rasuwa da muka taba zencen ka da ita ta garin mu Karofi"
Engr ya gyara zama kafin yace"Allah Sarki Allah ya jikanta na tuna wacce kace baka san kana da kanwa ba sai daga baya..?
Abba ya gyada kai yana fadin"Mganar gaskiya Fa'iza auranta shari'a ita ya bama wannan damar, sannan ta rabu da mijinta ba domin shi baya sonta ba sai kaddara"
Engr ya yi karaf yace"Kaddaran aure na ne Abba.."
Shima sai ya mayar masa da cewa"Ya'yanta Hudu fa Engr"
Shima cikin kwarin gwiwa yace"Masha Allah daman dagani sai su Taye Sweatheart Ta haifa. Ka fara fada musu ma sun samu wani Baban din bayan na su Baban"
Abba ya murmusa sanin Halin Engr kafin yace"Fa'iza ba tayi boko ba fa Engr.."
Shima mirmishin yayi kafin yace"A na addini a ina ta tsaya..?
Abba yace"ta wannan fannin Mahaddaciya ce sannan ta sauke wasu littafan"
Cikin Annushuwa yace"Good. Karatun boko! da nake da shi ya ishemu ni da ita har gaban Abada"
Sai Abba ya kasa mgana Abba yasan waye Engr da naci kan abunda yake so.
Shima kuma yasan ya san shi din Shiyasa ya yi mirmishin nasara kafin yace"Ka gama min gwajin tambayoyin..?zaka iya bani amanar rayuwar Yarka Fa'iza..?
Abba ya girgiza kai kafin yace"Fa'iza ba kamar ko wacce mace ba ce,Tana da lalura.."
Sai ya kalli Engr ya tsaya yaga yadda zai yi sai yaga yace"Lalura ai ta Allah ce Abba ko da lalura ko ba lalura ni Fa'izar nake so,kaga kenan da duk abunda ya danganceta ina son shi"
Abba ya karbe da fadin"ko da laluran kurmanta ne..? Bata iya jin mgana sai an yi mata da karfi."
Da sauri Engr yace"Alhamdulillah naji dadin haka. daman ni kadai ya Dace tarika jin muryata saboda ina da kishi kan abunda nake so"
Jaruntar Engr sai ta bama Abba Dariya sai ya kanne kafin yace"Fa'iza ba yar kowa ba ce bata da komai bata ijiye ba kuma bata bama wani ajiya ba. Ba yar kwalliya bace ba yar kyale kyalen yanmatan zamani ba ne,Ba ta da wayewar yan matan zamani balle ka yi tunanin samun soyayyar da kake Fata Engr Fa'iza yar zuhuda ce duniya da abunda ke cikinta baya gabanta ba lalle ka iya zama da ita ba,kuma Fa'iza ba fara ba ce sannan bata cikin Sahun manyan mata kyawawa burin kowani namiji"
Engr ya kura ma Abba ido har sai da ya tsargu kafin ya yi mirmishi yace"Na dauka kafi kowa sanin irin zab'ina. Kyau ko fata bai taba zama Dalilina ba."
Engr zai cigaba da mgana Abba ya taresa da fadin"bazan taba ma Fa'iza dole ba Engr ammh ina ganin kai ba sa'an auranta ba ne.."
Sai mganar ma ta basa dariya ya yi mirmishi kafin yace"Tafi karfina ko..?
Abba yace"Kai ne kafi karfinta.."
Sai kawai ya mike ya hau kan kujera ya zauna yana fadin"Naji dadi da ba ita bace ta fi karfina ba. in har ka aminta dani zan shiga layin zawaran Fa'izaa..'"
Abba ya saki baki kafin yace"Engr.."
Hannu ya dagamai kafin yace" *ENGR.ABDULBASIT ABDULGHAFFAR OLOWATOSIN..*"
Lokaci daya yana Dora kafa d'aya kan d'aya yana girgizawa.
Abba sai kwarjinin Engr ya dakesa ya kasa mgana kai Tsaye yacigaba da fadin"Engr Usman Karaye ka amince na shiga layin bazawaran Fa'iza..?
Abba sai kawai yayi kayattacen mirmishi mirmishin hango Salama da aminci in har Fa'iza ta samu miji kamar Engr.
Batare da fargaban da yaso yayi tasiri a ransa da farko ba yace"Na amince"
Cikin karfin gwiwan da yakinin cewa Engr zai karkato hankalin Fa'iza garesa.
Yana wannan tunanin ya tsinkayesa yana fadin"Ayi min mgana da ita,Daga yau zan fara zaawarci na"








*Janafty*
[7/30, 7:00 PM] Hauwa Galadima: *KNKB3011*

*Goron Tula*

*Ingantaccen maganine dake saukarda niimar mace sannan dadin dadawa fruit ne ga dadi abaki zakine dashi chakwai sannan bashi da wata illa yadda kikasan fruit haka yake*
*yana da matukar kyau da tasiri ga ma aurata daga mace harna mijin Kuma munada Syrup nasa da akataceshi sannan aka hada da ingantattun magunguna dasuke temakawa ma aurata kwarai don inganta lafiyarsu dakuma maganin matsalarsu ta auratayya yana saukar da niima sosai yana karawa mace dadi fiye dazatanku sai kingwada zak ibada labari insha Allah*

*Sannan akwai zumar kiba*
*Duk macen dake son ta murmure tayi kyau taciko tatada komad'a sosai shaf dinta yafito sosai da sosai to tasha wannan zumar insha Allah zaki gode min*

*Zumar gyara nono*
*Zasu yi kyau suciko ammanfa bawai su tsaya ba=?? zadai suciko suyi kyau sosai insha Allah*

*Zumar hips*
*Indai kinsha zumar nan to hips dinki zai bude zasu yi kyau suciko sosai zaki godemin nina fadamiki insha Allah*

*Note magungunan mu ingantattune basu da side effects kokad'an anyisu da ingantattun*
*magunguna sosai*
*Location Gombe munaturawa ko ina 08030861857*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*


ABBA.."
yaji muryan Engr ya kira sunansa cikin taushin murya. ya riga ya yi nisa cikin Tunaninsa yana juyowa yaci karo da Engr gurfane a gabansa ya sadda kai kamar me neman gafara cikin mamaki yace"Engr..!"
Kallonsa yayi kafin ya yi mgana ya cigaba da fadin"Haba ranka ya Dad'e.."
"ABDULBASIT.."
Eh ka kirani da sunana Abdulbasit Abba ni ai surukin ka ne,nema nake a wajen ka y'arka zaka auramin fa"
Yafad'a har yana sosa kai alamun kunya Abba baisan sanda kyattacen mirmishi ya kubce masa ba.
Duk da bai san Engr tun yana matashinsa ba. ammh yasan shi Lokaci mai tsawo shine zai iya ba da Labari da shedar nagartan sa.
Yana kallonsa zuciyarsa na bud'ewa da wani farinciki yana kuma fatan Fa'iza ta karbi tayin Engr.
Mganarsa ne ta katsesa cikin gyara zama yana fadin"Nagode Abba na yi maka alkawarin in sha Allahu bazaka yi nadaman bani amanar Faa'izaa ba.."
Zan rike maka ita amana bisa gaskiya da aldalci"
Abba ya murmusa kafin yace"Na fad'a maka tun farko bani da Hurumin yi ma Fa'iza zabi duk da ina matsayin Uba gareta, bazawara ce Shari'a ta bata Damar yi ma kanta wani zabin a karo na biyu"
Ya fad'a yana dan dakatawa yana nazarin fuskar Engr da tayi wani haske da Haiba,wanda yaga ya karu na yau kada'i.
Maimakon yaga sarewa a tare da shi sai yaga Jarumta da Kwarin gwiwa daman ya sani Engr ba shi da Tsoro ko Fargaba. ko karaya kan abunda ya saka ma gaba.
Cikin irin Taushin lazafinsa yace"Ai nima ban ce ka yi mata Dole a kaina ba. Ina son Fa'iza kuma zan nemi soyayyarta ina fatan ta bani Dama har takai mu ga aure, in kuma hakan bai Faru ba ni musulmi ne na yarda da Allah zan rumgumi kaddara a madadin Allah ne bai yi ba."
Yana mgana Abba najin yana kara Burgesa ko daman yasan shi mutum ne mai hankali da Takwalli yana ma Fa'iza fatan samun Engr a matsayin abokin Rayuwa.
Mikewa Abba ya yi yana Fadin"Shikenan bari naje na saka Maman Nana tayi mata mgana."
Da sauri Engr yace"Allah ya saka da alheri Abba"
Abba ya kara kallonsa yaga ya ma gyara zama ne cikin gyaran murya yace"Ammh nake ga da kaje ka shirya ka dawo ko..?lokacin itama an fad'a mata ta shirya..?
Kai tsaye yace"kirawota kawai kaji ni da zamu gina auran gaskiya ina ruwan mu da wani kyale kyale..?
Ya fad'a yana kara tankwashe kafa sai kawai Abba ya girgiza kai ya fice Daga Falon shashen Ammi ya shiga su Hafsah na Falon suna kallo kowacce da Hijabinta alamun bayan sun idar da sallah ne suka fito gabadayan su suka Duka suka gaishe shi ya amsa yana tambayan su yau ba makaranta ne sukace sai 9am zasu tafi.
Bedroom din Ammi ya shiga tana zaune tana duba wasu kayanta da aka karbo wajen dinki,Abba ya shigo daman tana ta zencen zucci na zuwan Engr sai ta mike ta tare shi tana Fadin"Baban Nana lafiya..?ina Engr din..?Abba ya riko hannunta zuwa bakin gado suka zauna yadda taga ya yi ne sai da gabanta ya fadi daman Ammi akwai rudewa cikin Rudanin ta Dafe kirji tace"Ba dai wani abun ne ya faru wajen aikin naku ba Baban ko Nana..?
Mirmishi ya yi kafin yaace"Kwantar da Hankalinki abun alheri ne zan ce ya faru"
Ammi ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Har na samu salama me ke faruwa ne..?ya tafi ne..?
Abba yace"yana nan..Ina Fa'iza..?
Ta tashi.?
Ammi cikin mamaki tace"Eh yanzu ta bar nan tazo mun gaisa ka sakani a duhu meke faruwa ne Baban Nana. ?
Ganin ta fara rud'ewanta ne yasa ya rike hannayenta yana Fadin''Ki natsu mana..Bafa wani abu ba ne Engr ne jiya da yaga Fa'iza.."
"Eh sai yace Fa'izan ta masa me..?
Ammi ta katseshi cikin Firgici har acikin Idanuwanta.
Yanayinta yasa sai da ya yi Dariya kafin yace"Ba abunda yace ta yi masa sai abu d'aya"
Ammi taji wani ras! fad'a da masu gwammati da yarbawa ai bala'i ne Cikin Kara rudewa tace"Mun shiga uku me yace ta yi masa..?
Abba na kanne Dariyan sa yace"To laifin D'iyarki daya da ta sace mai zuciya"
Kyam Ammi ta tsaya da kifta idanuwan da take yi tana auna mganarsa kafin kwakwalwarta ta hasaso mata zencen Abba ai sai ta ware ido kafin tace"Wai kana nufin Yana son Fa'i?
Sai Abba ya jinjina kai yana Fadin"Haka yace"
Nan ya shiga bata Labarin abunda ya faru Tsakaninsa da Engr a falo yanzu ai Ammi bata jira komai ba ta kwace hannunta cikin na Abba ta mike ta rike Hanci ta Rangada kyakyawan guda,Sai da Abba ya saki baki yana kallonta kafin yace"Aziza me ye haka kuma..?
Juyi tayi a gabansa kafin tace"Bar ni nayi gud'a babban gwaska fa Irin Engr yaga d'iyata yana so..ah ban ga ta zama ba kai Allahu akbar,wani Hanin ga Allah baiwa ne sannan KANA NAKA Allah ya riga ya gama nasa Baban Nana kaji Rabo ko..?
Take fad'a bakinta kamar ya tsage tsaki yaja yana kokarin yi mata bayanin yadda suka yi taki Tsayawa ta Fahimta tunda taji Engr na Falo yana Jiran Fa'iza ta fice tana Fadin"Bari naje na sakata ta kimtsa taje ta same sa"
Yana kiranta ammh bata dawo ba sai dai Fadi take yi"Ina zuwa Baban Nana"
Kai kawai ya Dafe a fili ya furta"Yaushe Aziza zata girma ne..?
Bai ga ranar ba, tunda takai ga jika bata Sauya ba,kila sai? cuta mai Tsanani da ba'a fata shi kanshi a hakan yake tsananin kaunarta mace ce tagari son kowani namiji mai kima.
Ammi na shewa ta fito falon su Hafsah ganin yanayin ta yasa Nana Khadija tace"Ammi hala Abba ya biya miki Umra ne..?
Ammi na Dariya tace"A'a Abban ku ai ya gama kaini Umara yanzu fanni na Surukai ne. in da rai da rabo bana ai dani za'a keta Hazon hajji ya'yan nan haihuwa mai Dadi"
Take fada tana Dariya sun san Halinta yasa suka saka Dariya Hafsatu na fadin"Ammi mijin Anty Fadila ko Anty Fatima ne zai biya miki..?
Ta wuce tana fadin"Kash kuna da gajen hakuri ku jira mana Lokaci ya gaya muku"
Murnan da take yi ya isa yasa su san wani abu na faruwa. Abba kuma kin fitowa ya yi saboda ya bama Fa'iza daman sakewa kada ya koma ya takura musu yana suruki guda duk da yar kunya Tsakaninsa da Engr ammh ya Lura daga yau da Safe ya sauya mai matsayi da suna daga baban Nana engr ya koma Abba,baban Fa'iza.

*****

Ni ko ban san wainar da ake toyawa ba,Tsakani har ga Allah nima cikin wani yanayi na kwana abun mamaki da Haushi mafarki na yi ta yi masu cike da Engr a cikin su,sannan ko yaya na yi zurfi a tunani sai na hango kamilalliyar Fuskarsa na min mirmishi gabad'aya sai na tashi a jagule na rasa gane kaina Na tambayi kaina Fa'iza daga ganin mutum baki san komai a kansa ba sai Tunanin sa..?
Abunda ban taba yi ba ko zamanin Ishaq wlh tallahi bana zama nayi Tunanin sa to basai da kwanciyar Hankali da so da kauna kake tuna mutum ba..?ba auran soyayyah nayi ba shiyasa ban san kallon so ko mirmishin soyayyah ba,ni bani da sani ta wannan bangaran a bangaran auran ma akwai ta bangaran da ni Fa'zan ban san komai ba.
Na idar da sallar asuba ban d'aga daga kan Darduman ba ina ta azkar dina daman kuma jiya da daddare sai uku na kwanta nayi istikara,sai kuma na ga akasin haka maimakon naji na samu natsuwar Komawa gidan Ishaq a'a sai mafarkan Engr nake yi acikin barcina.
Kuma in bude baki in fad'ama wani wannan iftila'in daya sameni abun kunya ne to abun kunya mana Daga ganin Sarkin fawa ni Fa'iza sai miya taki zaki...? Da hannu bibbiyu nayi Taguni ga Uban Hijabi ga carbi ina ja har bata lissafi nake yi saboda Tsabar Tunani ana ta ma kiran wayata ban ji ba sai daga baya ina Dauka Zainab ce sai dai ba muryanta ba ne na Anum ne na Tsorata ganin bakwai saura.
Cikin tashin hankalin daya bayyana har amuryata nace"Ke Anum lafiya kuwa..?ina Antyn naku..?
Sai naji ta saka Tsalle da Ihu tana Fadi"Eyee Umma wai da gaske zaki Dawo gidan Daada gabadaya ki zauna tare damu da Daada da Anty..?
Sai da gabana ya fadi Zainab ta gama dani daga ce mata zan yi Tunani har ta Yadani na kuma san gabadaya yaran ta fad'a musu har da uban gayyan.
Kafin na bata amsa naji hayaniyan sauran yaran suna ihu suna kiran sunana dakyar na iya tambayanta su Ahmad ne tace min"Eh Umma kowa nata Murna zaki dawo har da Yaya Amir baki ga Daada ba,yace yau zamu fita shopping gabadayan mu zamu gyara miki daki Umma don Allah ki Dawo.."
Miyau na naji ya kafe nama kasa hadiyewa,saboda rudani ni yaushe nace zan dawo..?
Ina jin hayaniyar yara kamar zan kashe wayata ammh Anun taki bari fadi take"Umma don Allah ki dawo kawayen mu fa kowa gidan su Umman su daadan su na waje d'aya sai mu ne Umman mu bata nan,Sannan Umma Daada yace shi ya yi miki laifi mu tayasa bashi hakuri don Allah ki yafe masa.."
Tafada cikin wani yanayin da yasa sai da Hawaye suka kawo cikin Idanuwana,Anum da iya zencen Amir ne daman mara Hayaniya.
Damuna tayi da fadin"Kin ji Umma ki yafe ma Daada don Allah ki dawo"
Sai na samu kaina da fadin"Na yafe masa tuntuni Anum"
Sai ta saka Ihun murna tana fadin"To Umma zaki dawo din.?
Da gaske ne..?
Kasa ba ta amsa nayi ina fadin"Yau ba makaranta ne..?
Da sauri tace"Umma muna shiri ne..Ni ki fad'amin zaki dawo..?
Da kai na daga mata kamar wacce aka zare ma lakka naji jikina ya yi min nauyi kafin nace"Ehh.."
Kamar ashe a amsa kuwwa a ka sakani ina jin ihun yaran gabadaya Da mganar Anum tana fadin"Umma Umma yaushe..?gobe..?
Don Allah ki dawo gobe.?
Kaina na Dafe da naji yana Saramin kafin na samu damar mgana naji sallamar Ammi da shigowarta yadda naga tana hanzari ne yasa na katse wayar na mike da sauri kafin ma nayi mgana tajani gefen gado muka zauna tana Fadin"Fa'i albishirin ki..?
Cikin kallonta nace"Goro Fari kal Ammi"
Tana Dariya tace"Sauya Hijabi kije falon Baban ku ki dawo sai na baki albishir din"
Cikin mamaki na kalleta zan yi mgana ta dora yatsa a bakina tana fadin"Ba yanzu ba sai kin dawo"
Da kanta ta mike ta zabo min wani hijabi sea green cikin kayana Sabo ne ban ko taba sakashi ba.
Ta bani na cire na jikina na saka bayan ta sakani na sauya kayan barcin jikina na saka wata bakar Abaya,ta kuma saka na goga Turaren Humra cikin mamaki nace"Ammi bana son kamshin turare,kuma fita zan yi fa"
Ammi tamin dakuwa tana Fadin"Kuma kike had'awa kina Saida mana amnh ke kice baki so..?ai ko baki isa ba yarinya ba turare yanzu kika fara son shi da saka shi"
Dariya nayi ban yi mgana ba,haka ta sakani gaba muka fita ina tafiya ta shiga gabana tana nuna min wai irin Salon Tafiyar da zan yi in na Shiga Falon Abba baki na bude kafin nace"Ammi waye ya zo wajena..?
Ko baki Abba ya yi.?
Fadin haka yasa sai da gabana ya amsa ko dai ko dai Engr ne..?
Na juya nayi ma Ammi mgana naga Tuni ma ashe ta koma Shashenta ta barni nan tsaye sai na fara waige ina jin wani yam acikin jikina.
Kamar najuya zuwa shahshen Inno daman ban shiga mun gaisa ba da Safe,Sai kuma na kasa bazan iya komawa ba tunda Ammi ce da kanta ammah jikina ya bani wani abu.
To ko dai ishaq ne..?in shi ne kuma da Anun ta fad'amin.."
Ni dai kafafuwana suke ja na zuwa Falon Abba ga yanayin mganata ga Sanyin murya shiyasa da nayi sallama ban sani ba ko yaji,ni kuma sai naji kamar gyaran murya shiyasa na shiga falon kaina na kasa.
Kafafunsa na fara gani zuwa kansa yana tsaye ya juyamin baya yana waya ammh kuma abun mamaki wani yare yake yi kamar yarbanci yarbanci na kasa dai ganewa saboda ina Rude ne.
Dagowa nayi in kallesa dakyau karaf ko kamar juyin waina naga ya juyo muka hada ido hud'u da shi jiri ne yaso ya kwasheni na kame kaina da jikina ammh a wannan karon ma jikina da gabana sai da suka amsa wannan kamilaliyar Fuskar da wannan mirmishin da yaki b'acemin yau ma da su ya jefeni kafin ya yi mgana ashe wayar na makale a kunnensa bai kashe ba naji yana Fadin"Is ok Papa i will call u later"
Daga haka ya katse kiran kacokan kuma ya maida Hankalinsa kaina ni ko ban saba ganin irin wannan kallon ba, kaina na kasa ina rawan jiki Lokaci daya ina faman cikwikwiye hijabina ta gaba.
Ina ga fahintar haka ya yi yasa ya yi mirmishin sa dake dimautani kafin ya matsa yana nuna min saman d'aya daga cikin kujerun falon Abba yana fadin"Barka da shigowa sarauniyar mata Hv a sit.."
Sai kuma daya fada haka yayi yayi sauri gyarawa da fad'in"Ki zauna bismillah"
Yafad'a duka a tare ai da sauri na samu gefen kujera na zauna ina kara Dukar da kaina sai kawai naji yace"Kada mu fara haka dake Fa'izaa kan kujera zaki hau a matsayin ki na Sarauniyar mata,ni kuma na zauna a kasa a gabanki tunda nine zan mika kokon barata."
Da sauri na dago muka hada ido sai na Dirirince zan yi mgana ya yi saurin cewa"Kada ki fara da min gaddama Faa'izaa ni mutun mai son ya yi mgana Daya ajisa. kuma a Sauraresa"
Yafada kai Tsaye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login