Showing 273001 words to 276000 words out of 288345 words

Chapter 92 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

780

BALA I, GUMBAR MATSI, GUMBA MAI RAWANI, GUMBAR UBAN BUDURWA, IN DAI MATSI NE DA NIIMA KE KARE ZANCEN, DUK MACCEN DA MIJINTA BAI TA BA MATA KUKA BA TA ZO TA GWADA KAYAN HAJIYA FATIMA SAI TA RUFE BAKI NAI GUDUN MAKWABTA SU JI YO SU.

MACEN DA KA FAMA DA ZUBEWAR NONO KO KANANAN NONO TA ZO TA GWADA MAGANIN HAJIYA FATIMA A KWANA HUDU KACAL ZAKI FARA GANIN SAUYI.

MACEN DA KA FAMA DA RASHIN KIBA BABU HIPS BA NONO, BA MAZAUNAI TA ZO TA GWADA MAGANINMU DA IZININ ALLAH TA QARE DA WAGGA MATSALA

AKWAI MAGANIN SANYI SADIDAN WANDA DUK KIKA JARABA SHI SAI KE BASUWA TUKWICI SABODA INGANCINSA, DUK WANI DATTIN DA KE MARARKI HAKA ZA KI GA YANA FITA GUDA-GUDA

AKWAI BA KAR ZUWA WADDA KA BA KIN AIKI KAN  DA NAMIJI DUK KISSHATA KE GAMA DA TIJARAR  DA NAMIJI.

AKWAI HATSABIBIYAR MALLAKA, WANGA SET NA NA MANYAN MATA, GUMBA,TSUMI,ZUMA DA GARI NE NA MALLAKA BAN DA MAI KISHIYA.


KU NA IYA TUNTU BATA TA 08167888934, DON ALLAH IN BA SHIRYA SIYE KIKA YI BA KAR KI MIN MAGANA. MUNA GARIN SOKOTO MUNA AIKE KO INA CIKIN AMINCIN ALLAH



Dayake mai taxi d'in yasan gari kuma Engr ma ba baya ba.
cikin lokaci kankani sai gamu a kofar Apartment din Su Anty Fadila kamar suna jiran mu ko nace suna jin Dirin mota suka fito gabadayan su harda yaran.
Anty Fadila tundaga nesa take faman washemin baki ni ma haka ina ta so na karisa gareta da Sauri ammh Engr yaki sakin hannuna,Sai da na kallesa da wani irin duba da muka kadai muka san ma'anarsa sannan ya saki Hannuna yana min mirmishin nan nasa mai narkan min da zuciya.
Da sauri sauri muka tari juna mu da Anty Fadila muka rumgume juna kamkam muna murnan ganin juna mijinta kuma suka yi hannu da Engr,Mai taxi din na jiran mu tunda Drop ne zai kai mu har gidan Yaya Ishaq ne.
Dagoni Anty Fadila tayi cikin tsananin mamaki tana karemin kallo kafin tace"Fa'inmu ce wannan kuwa..?
Sai ta bani dariya har kara tattaba kumatuna take yi,ina Dariya mijinta na tayamu Engr kuma na faman mirmishi ya kame fuskarsa kadan.
Kallon Engr tayi tana fadin"Engr ranka ya dade a enging aka saka mana Fa'in namu aka sauyata?
Ya yi dariya kamar bai zai yi mgana ba sai daga baya yace"Ni ne enging din kenan Anty Fadila.."
Sai da ya fad'a sannan taji kunya taja hannuna muka wuce Engr da Babansu Falaq suka tafa kamar sun shekara da sanin juna Suka bi bayan mu su da yaran dake ta gaishe da Engr.
Allah sarki dan'uwa mai Dadi abubuwa na musamman Anty Fadila ta shiryamana,A falon gidan muka fara yada zango aka gaggaisa,su falaq sun zo wajena suna gaisheni na jawo su na rumgume ina tambayan su makaranta,Engr da Babansu falaq ko kamar sun shekara da sanin juna sai Hira kawai ta Tsarke a tsakanin su tunda ma in ka kallesu zaka iya auna shekarun,saboda yanayin jikinsu sannan kuma dukkansu suna da Ilimi da wayewa shiyasa saurin sabo bai yi musu wahala ba,ballatana Engr da na sani ko a akan hanya ne sai ya bar wanda ya san shi Tsabar mganarsa da iya mu'amala da Mutane.
Kiran sallar mangariba ne ya tashe su suka fita masallaci su da yaran maza ni kuma Anty Fadila tajani Bedroom dinta domin nayi sallah.
Bayan na dauro alwala ta bani Sabon Dogon Hijabi nayi sallah,ita kuma ta fice inaga dakin yaran taje tayi sallah ina zaune ina azkar sai gata ta dawo.
Gefena ta zauna muka kara gaisawa cikin matukar jin dadi kaga wani naka alokacin da bakayi Tsammani ba.
Kallona kawai take yi tana karawa kafin tace"Ikon Allah Fa'i ko dai su Ahmad sun samu kani ne..?
Mirmishi nayi kafin nace"Ko d'aya Anty Fadila kawai kwanciyar Hankali ne na samu shiyasa"
Anty Fadila sai ta rumgumo gefen kafadata tana Fadin"Am happy for u Fa'in mu. Wlh ganin ki kawai da nayi sai na kara jin Hankalina ya kwanta na Tabbata kin yi dace Engr mutum ne nagari mai nagarta da har ina jin Haushin baki komama Ishaq ba,ganin yadda ya susuce akan ki,ammh daga baya sai na Fahimci wani abu duk sanda Allah ya baka abu ka yi wasa da shi to fa in ya subuce maka ba lalle ya iya dawo maka ba"
Kai tsaye nace"Hakane Anty Fadila".
Kumatuna taja kafin tace"kinga yadda kika koma..?kin kara fari kin kara kiba kin kangi kuwa.?kin zama yar gayu Fa'in mu..?Wlh tallahi in ba wanda yasan ki ba in zamu yi ta kwana muna rantsuwan kina da Saurayin yaro ba mai yarda damu ikon Allah"
Dariya nayi kafin nace"Ni kaina ina mamakin chanzawata"
Anty Dadila ta karbe da fadin"Haka ake so. Allah ya kara zaunar daku lafiya da soyayya duk da naga akwai ta,Sai kuma Allah ya kawo rabo na alheri ina so naga danku ko yar'ku ke da Engr"
Cikin raina na amsa mata ban iya amsa mata a bayyane ba nan muka zauna muna ta hiran mu ta kira Abba ta fad'amai gamu a gidanta har ta bani shi muka gaisa ina jin kunyarsa shi ko ajikinsa faman tambayanta? yake yi mun dawo lafiya..?
Yana gida Lokacin har Ammi sai da ya bata muka gaisa tana min tsiya da fadin"Ina fatan kin kara kiba kin zama lukuta yanzu.?
Na kasa amsa ma Ammi sai Anty Fadila ne ta karbi wayan tana zuzuta kyan da nayi Ammi sai hamdala take yi,har Nana Fatima sai da ta kira ai tana jin muna Lagos ta daka Tsalle tana Fadin"To wlh nima zan duba Hanya saura ayi min danwaken zagaye"
Muka yi ta dariya mun manta da mazan har sun dawo suna falo sai da Babansu falaq ya leko yana fadin"Sai a gaya mana yan'uwanta ka,an wani shige daki to muna dai mun zama abokai"
Dariya muka yi gabadaya sannan muka fita saman Dining din su muka had'u gabadaya mukaci abinci Shinkafa Fara da miyar albasa,sai Pepe Chicken,da kebbab sai Lemun arbarba mai apple,ina kusa da Engr bai ji kunyar su Anty Fadila ba. ballatana yara sai ya bani abinci a baki kamar yadda ya saba na rika nokewa sai ya kalli Anty Fadila yana fadin"Kin dai ga kanwarki ko..?
Mun saba tun a gida da kaina nake ciyar da ita kuma yau kawai Saboda ta ganki ta fara sauya hali"
Babansu Falaq ne yace"To ka sani an fa kule acikin daki"
Anty Fadila ta mintsi hannunsa tana Fadin"Kasan dai bazan hana ayi ma Engr love ba ko..?
Kawai nasan kunya take ji kasan kanwar tawa da kunya da kun koma gida zaka ga ta saki"
Kai tsaye Engr na kallona yace"Tabbas nasan ko tana da kunya ammh ma fara kokarin yaki da wannan kunya tsakani ga Allah tana hanani kara'i na yadda nake so"
Kunya kamar na nutse don ma yara suna gefe ne kuma hankalin su baya kanmu Anty Fadila suna ta Dariya ni dai dakyar na iya cin abincin nan shima kadan bada yawa ba,Engr ma ganin ban wani ci ba shima bai ci da yawa ba nasan Halinsa bai iya sakin jiki yaci abinci a waje sai ya Dawo gida mun ci abincin tare.
Bayan mun gama cin abincin mun dawo Falo ne,Anty Fadila ta kalleni tana Fadin"Ammh nan zaku kwanar mana ko..?
Ina rufe bakina Lokaci daya ina Fadin"Kwana kuma..?A'a gobe zamu tafi kano yanzu nan ma daganan yaran nan zamu je mu gani,kafin mu koma masauki."
Engr na jin mu bai sakamana baki ba,Anty Fadila ta rike baki tana Fadin"Shine baku zo da wuri ba Fa'iza.."
Engr ne yace"To kisan amarcin ne har yanzu bai sakemu ba"
Dariya tayi kafin tace"To kun sanar da su kuna tafe..?
Sai Engr ya kalleni Saboda bai sani ba ko na kira su ni kuma sai nace"Ban fad'a ma Zainab din ba, ammh bari na kirata yanzu"
Kiran sallar isha'i yasa suka tashi zuwa masallaci mu kuma muka muka shiga ciki.
Bayan mun idar da sallah ne na Kira zainab tana tsokanata da Amarya amarci yasa bata samuna a waya kai tsaye nacemata"Ba ma kasar ne ni kuma ban ce ya siyamin wani layi ba. wayar tana kashe ne sai da muka dawo na kunnata"
Zainab ta fara fadin"Uhm su Maman Amir to ya amarcin..?
Allah yasa an samo mana d'an Honeey moon"
Ina dariya ban biye mganarta ba nace"Kina gida ke da yaran ne..?
Kai tsaye tace"Ina gida yau ma ko aiki ban fita ba,bana jin dadi.
Yaran kuma suna Falo tare da Honey da Mama"
Cikin zolaya nace"Ko dai ko dai..An sama ma Islam.."
Kafin na rufe baki ta tareni da fadin"Ba Ameen ba. Haba Maman Amir ai haihuwa mun bar ma sabbin Amare irin ku"
Kalamanta suka sakani Dariya ita da tayi uku ni hudu gareni ammh take tunanin haihuwa sai irin mu Allah Sarki nima ina so Allah ya bani ko Domin Engr dake son ya'ya a rayuwarsa.
Kamar daga sama Zainab taji nace muna nan shigowa anjuma.
Cikin mamaki tace"Bangane ba..?
Kina lagos din ne..?
Kai tsaye nace"Tun shekaran jiya ai ta nan muka sauka,gamu gidan Anty Fadila zamu kariso"
Sai ta saka Ihun murna nayi dariya ina fadin"Kada ki fad'ama yaran nan fa so nake kawai su ganni. Kuma.. kuma ni da shi ne,ki fad'ama megidan naki"
Ban jira cewarta ba na katse kiran nasan Halimta ihu zatamin ban damu da address din gidan ba tunda nasan Anty Fadila tasan gidan ko ita zatayi ma Mai Taxi din kwantance wajen.
Karfe tara saura muka yi shirin Tafiya bayan naje na dauko musu ledan Tsaraban su na bama yaran suna ta Godiya Anty Fadila ta bani wata Gumba mai shegen dadi tace haka nan zan rika shanta nasan Darajan gyaran jiki yanzu shiyasa ba na wasa da shi yanzu.
Babansu Falaq ya yi ma Direban Taxi kwantancen gidan nan da nan ya gane wajen mun rabu cikin jin dadi,Engr da Baban Falaq suka karbi lambar juna har muka kule suna d'agamana Hannu.
Ban dauka zan ji fad'uwar gaba ba sai da nasan mun d'au hanyar zuwa gidan Yaya Ishaq sai naji gabana na fadi ina rasa natsuwata Engr ya lura da haka ko daga yadda Hannuna ya jike da Zufa dake cikin nasa.
Matse hannu nawa ya yi sai da na juyo ina kallonsa sannan yaa jinjina min kai alamun kada na damu sai na samu natsuwa naga mai zai Dameni gani kusa da Engr in har indai ina kusa da shi to na kaddara sai dai Kuduran Allah zan iya neman wani abu na rasa sai na dora kaina kafad'ansa ina Sauke ajyar zuciya shi kuma sai ya kara rikeni Cikin Salon kulawa irin ta shi.
Ba jimawa sai gamu a Anguwan Apapa,Dayake kuma Gidajen suna Tare ne waje d'aya bamu sha wahalan ganewa ba,tunda daman Anty Fadila tace 16 ne lambar gidan.
Sai da muka fito daga Taxi din sannan na Kira Zainab ringing daya ta Dauka da Sauri tana fadin"kun kariso ne Maman Amir?
Sai da na amsa mata kai kafin nace"Eh muna waje"
Sai tace bari su fito kafin mu yanke kiran a tare,gefe na koma gabana na Tsananta fad'i sai Engr ya matso gareni ya rike hannuna cikin nasa na Dago ina kallonsa sai ya sakarmin Mirmishi nima na maida masa.
Mun kurama kofar gidan ido a kan idanuwan mu Zainab ta fito,Sanye da Doguwar Riga na wani yadi maroon ta yafa wani siririn bakin mayafi bayanta kuma Yaya Ishaq ne cikin Jallabiya mai ruwan madara.
Zainab na ganin mu ta saki mirmishi nima sai na sakar mata ta fara taku zuwa garemu muma sai muka fara takawa Hannuna gam cikin na Engr. muna tafe jiki na gugan jikin juna.
Idanuwana Zainab suke kallo ammh bansan ta yadda akayi ba idanuwana suka sauka kan Yaya ishaq ba,ido hudu muka hada da shi,Mirmishi nayi masa sai yayi kasa da idonsa ammh bai dauke ba gabadaya,shi kuma ni yake kallo tare da kallon hannuna cikin na Engr dake Sarke da juna.
Gabana ya yi wani ras!har sai da takalmin kafata ya turgud'eni zan fad'i Engr ya yi saurin rikoni yana kallona nima shi na kallah cikin sanyin muryansa yace"Are u ok..?
Da kai na amsa masa sannan ya sakeni ammh bai yarda ya saki hannuna ba.
Sai da muka kariso gabda juna sannan ya sakeni ganin kuma Zainab ta bude hannuwanta bakinta kamar Gonar Auduga tana fadin"Oyoyo Oyoyo ga maman Amir"
Nima sai na bude hannayena muka Tarbi juna cikin fara'a muka rungume juna.
Kafin mu saki juna muna bin juna da kallo cikin fara'ar da taki barin fuskokin mu dani da ita.
Yaya Ishaq ko hannu ya mikama Engr cikin jin nauyi suka yi musabaha tare da gaisawa Engr ko a fuska bai nuna masa da wani abu ba.
shima ya tarbesa cikin Fara'a kamar wani abu bai taba shiga tsakaninsu ba
Zainab ta rike hannuna tana gaishe da Engr ya amsa mata cikin fara'a da Tambayan yara.
Tace duk suna lafiya tana kamkame da Hannuna tace"Bismillah mu shiga ciki"
Sai muka yi gaba,ni da ita su kuma suka bi bayan mu duk sai naji na takura na kalli Ishaq ta gefen idanuwana sai da gabana ya fadi da ganin irin ramar da yayi kamar wanda ya shekara yana jinya.
Shima duk da ban sani ba ya kalleni sannan nasan yana mamakin sauyawata.
Zainab ke min mgana kasa kasa da cewa"Kin ganki kuwa maman Amir..?ko dai an samo mana bby Honeymoon ne?
Dariya nayi ban yi mgana,ita ta shiga gaba tana janye da hannuna har cikin Falon,yaran duk suna falon Har da Mama da Shema'u.
Zainab na kan gaba ta kareni tace"Anum.."
Anum dake zaune kan kujera tana duba littafan makarantar ta yan SS1 ce,First time,musty na zaune a kasan Cafet ya na zanensa na fama Ahmad Kuma na gaban Tv shi da Farhan suna kallon Mbc3,Amir kuma na daga chan gefen Mama wani Novel din Turanci ne a hannunsa yana karantawa Fadil na kan jikinsa ya lafe kamar mara lafiya.
Kiran sunan Anum da Zainab tayi yasa duka yaran suka dago suna kallonta Batayi mgana ba illah kaucewa da tayi na bayyana afalon. ina saka yarana a ganina naji idanuwana sun cika da kwallar Farinciki da wani irin kewa da ban taba ji ba.
Gabadayan su suka mike har da Amir kuwa da naga ya kara zama wani Zabgege ga tsawo ga jiki irin na Ubansa Dukkansu bakin su ya kasa motsi mamakin ganina suke yi,Ahmad ne ya bude murya kafin yace"UMMAA..!
Sai na gyada mai kai sai hawaye sharr na Farinciki suka zobomin na zube gwiwoyiyina a kasa na bude hannayena ina fadin"Umma ce Ahmad di'n Umma"
Ai da gudu ya rugo ya fada jikina sai ya fashe da kuka Musty ma ganin haka ya watsar da Abun da yake yi ya iso gareni yana fadin"Umma..!
Sai kuka shima nima kukan nake yi,Farhan ma ya kariso yana kallona yace'Umma..'
Kamar yana tamtama sai na jawosa jikina na hada da su Ahmad na Rumgume ina fadin"Farhan din Umma ina Fadil..!
Sai kawai naji an chakumeni ta baya ashe Fadil ne bakina yaki Rufuwa ina kuka ina Hawaye ina Dariya Lokaci daya ina fadin"Fadil..Fadil d'in Umma"
Yana Dariya yace"Umma umma..Ina kika tafi bana ganin ki?
Ya fad'a yana shafa Fuskata kamar yana Tantamar ni ce ko ba ni ba ce.
Ni ko kuka ya hanani mgana Duka na hadasu na rumgume ina Hawaye ina Dariyan jin dadi raina nake jin wani salama da kwanciyar Hankali suna shigata
Amir da Anum sun kariso gabana ammh sun kasa bin ayarin yaran,sai da na ji Anum na fadin"Umma mu kin manta damu..?
Tafad'a idanuwanta taf da kwallah sai na mika mata hannuna Daya ta kama ina Hawaye nace"Ina ni ina mantawa da Anum din Umma"
Amir dake gefe yace"Umma ita Kadai..Ita k'adai..kika gani"
Yafada muryansa tana wani irin rawa,da kuma wani kewa a cikinta.
Na dago ido na ina kallonsa sai na mika masa Dayan hannun ina fad'in"Babana bazan manta dakai ba kaima zo. kuzo wajen Umma"
Gabadayansu suka taho atare suka Duka suka bi bayan kannensu a tare Amir da Anum suka fashe da kuka nima kukan nake yi kasa kasa har yana bayyana ammh na farinciki.
Mama dake gefe ta Dauke kwallarta tana mirmishi,Dazu taga Zainab tazo ta kira Ishaq kila zuwan Fa'izan ta shaida masa Allah sarki Uwa. ita uwa tana da girma girman da Ubangijine kadai yasan iyakarsa.
shema'u ta kalli Mama kafin tace"Maman Innar su Anum ce..?
Mama ta gyada kai batayi mgana ba Ranta ya cika da wani nauyi da ta rasa ko na menene tasan dai na kunya da nauyin Fa'iza ne sannan da Tausayin yaran nan.
Ba ita kadai ta share kwallah ba Hatta Ishaq sai da ya juya baya yana goge kwallar da suka cika kwarmin Idanuwansa. Engr na kallonsa sai ya nuna kamar bai gani ba. yana Daga baya ya sagale hannayensa a bayansa yana kallona ni da ya'yana wani irin kauna da soyayya da baisan yana yi min yaji ya kara sarkeshi, ya tabbata ba karamin kaddara bace ta fidda ni daga gidan mijina sannan ya kara Godema kaddara data kaddara auran mu.
Zainab ma sai da ji kwalla sun kawo mata,sai daga baya baya ne aka samu sauki ammh ko da yaushe yaran cikin kiran Umma suke Fa'iza ba a iya Rayuwar ya'yanta take da tasiri ba har a rayuwar su Farhan domin mai kulawa dakai baya bace maka aranka har abada.
?Zainab ce ta matso tana Fadin"To ku saki Umman naku ta zauna ta Huta mana"
Jin haka yasa su Amir suka tashi da Musty Ammh Ahmad da Fadil makalemin sukayi kamar zan gudu haka na mike suna rike da hannayensu Ahmad bakinsa ya bude fadi kawai yake yi"Umma nan zaki kwana..?
Fadil kuma"Umma ni zan biki gidan ki"
Ina Dariya nace"Yaran Umma duk sun kara girma"
Na fada ina kara ganin girman Ahmad da Musty Farhan da Fadil har mamakin girman yaran nake yi mutsy fa ya kamo tsawo na Amir ko in muka jera sai ace yayana ne ni daman gani ba Tsawo kuma ba wani jiki ba yar Firit don ma na kara kumari da a baya ne kila sai dai ace nice karamar su sai ko in anga Fuskar ta manya.
Engr ne yayi gyaran murya kafin yace"Umma kad'ai kuka sani ko..?
Sai alokacin su Amir suka gansu kunya ta kama Anum baki bude tace"Laaa Baba.."
Amir ma yace"Baaba.."
Sai su Ahmad suka tsaya suna kallon su,Amir yace"Sannu da zuwa Baba.."
Makale kafad'a ya yi kamar yaro kafin yace"No..Oya nima hug irin wanda kuka bama Umman ku"
Sai suka tafi a tare suka fada jikinsu ya Rungumesu cikin Fara'a.
Ahmad da Musty suka kalleni sai nayi mirmishi na gyada musu kai ganin suma yana mika musu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login