Showing 207001 words to 210000 words out of 288345 words

Chapter 70 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

770

kasa mgana Ammi nata jin Dadi a ranta ni Abba ya kallah ina sharan kwallah Cikin Fada yace"Ni ba sakarai ba ne ban kuma Haifi sakaran d'iya ba.Meyasa,kika zauna Tsawon wannan Lokacin da wanda baya sonki..?wanda ya zabi wata matar sama dake..?
Yafad'a yana kallona Zuciyarsa har Dagawa take yi ran yan maza ya baci Tsawa ya dakamin yana Fadin"Tunda kinsan baya son ki meyasa kika yi masa afarman zama dashi..?
Ina kuka jikina na rawa nace"Abba ya'yana.."
Abba kamar zai Dageni ya tasomin yana Fadin"Ya'yan banza..Nace ya'yan banza kan ya'ya ne zaki zauna ya na wulakantaki Shi da yan"uwansa..?ki bar ya'yaan su mutu mana ai ba ke kika Haifesu ke kad'ai ba shima Uban su ne. Kada ki kara zama Saboda wasu ya'ya ana wulakantaki Jariri ma yazo duniya bai ga uwarsa ba. kuma ya Rayu ballatana yaran da suka girma"
Yadda yake mgana yasa Inno saurin cewa"Usmanu kayi mata a Hankali"
Sai a lokacin ya Saussauta mganarsa yana Fadin"Ki bude baki ki Fad'amin Tundaga farko har karshe in kika boyemin wani abu sai naci Mutumcin ki Fa'iza"
Kaina naji ya sara na kasa mgana Tsawa ya sake dakamin Cikin Hargagi yace"Ki fad'amin Hujja nake nema yadda zan ci uban duk wanda ya ci zarafin y'ata wlh"
Jin haka yasa da Sauri nace"Abba ba niyyata in tona masa asiri ba don Allah ka bar mganar nan"
Marina ne kad'ai Abba bai yi ba,Ammh sai da na samu Tsaraban kallo kafin yace"Shi ai bai Rufa miki naki asirin ba shine ke kike neman ki Rufa masa.?Tona masa kowa yasan Abunda ke Boye"
Kuka na kara Fashewa da shi har ga Allah na riga na yafe masa bana son Dawo da abun da ya wuce shima kallona yake yi alamun roko cikin lokaci daya duk ya zabge sai Zufa yake yi har Shadda jikinsa sai da ta jike da Zufa.
Mama ce tayi mgana cikin Dashewar murya tana Fadin"Gwara ki Fad'a Fa'iza ki fad'a musu komai duk da nima nasan da Laifina tunda ina gani yana wasu abubuwan ban taba Hanasa ba,sai ma kokarin Dora shi kan Hanyar banza da laifina nima"
Kukan da take yi baisa kowa yaji Tausayinta ba.
Kamar daga sama sukaji ance"Ai bazata taba mgana ba Abba.
Da zata yi mgana da ta fad'a muku ishaq ya yi ikirarin zai Daukomin yan Sanda in ya kara ganina a gidansa"
Gabad'aya muka jiya bakin kofa in da muke jin mganar Yaya mariya ne ke Tsaye tana Hawaye Gabana ya fad'i shikenan Yaya mariya zata fad'i wannan sirrin da na zata ta manta da shi.
Da sauri Abba yace"Taho nan Mariya ki fad'amin abunda kika sani kan zaman Fa'iza da yaron nan"
Da Dauri ta kariso ta zauna agabansa kafin tace"Abba ban taba fadin ma kowa abunda ya faru ba sai yau. Saboda Fa'iza Saboda ita ammh yau bazan iya shuru ba!
Ta kalleni kafin tace"Kiyi hakuri Fa'iza..'"
Kafin tamaida kanta wajen Abba bayan ta gama kare ma mutanen Falon kallo ta wani sakarma Ishaq wani kallo kafin tace"Abba ban san mganar da kuke yi ba na shigo na dade Tsaye ina jin wasu mganganu.
Wlh Abba Fa'iza ta sha wahalan rayuwar kaskanci da wulakanci a gidan wannan mutumin,Fa'iza bata da daraja ko Kima a wajensa da wajen uwarsa gata nan da Yayarsa Abba ni fa uwa d'aya uba Daya muke da Fa'iza ishaq ya bata Sakon ta gayamin kada na kara zuwa Gidansa da bata gayamin ba ranar da ya iskeni Abba koran kare ya yi min Fa'iza na kuka tana rokonsa ammh ya rantse in ban fita ba sai ya Had'ani da yan Sanda Abba"
Gabadaya suka saka Salati Abba yace"Good..'
Yaya mariya na Hawaye ta kalli Goggo tana Fadin"ai kin tuna Lokacin goggo. Lokacin da kuka barni wajen Fa'iza sanda tayi ciwon nan kikace nayi mata kwana Biyu to kwana D'aya nayi yayi min tozarcin da har na Mutu ba??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????zan manta ba dalilin da yasa har yau ban kara taka inda Fa'iza take ba. sannan ban kuma taba gayama kowa ba,sai yau shima din naga in nayi shuru Fa'iza zata iya koma ma Wannan rayuwar data bari"
Da Sauri Abba yace"Bazata koma ba. Bazata taba komawa ba indai ina Raye mari"
Yafad'a idanuwansa jajir Goggo na Sharan kwallah tace"Nasan dai daga Lokacin indai zamu gidan Fa'iza sai ki zille na Dauki Saunan wani abu sai dai yadda baki ce min komai ba, Fa'iza ma ban ji tayi mgana shiyasa sai na dauka tsiyar ki ne ya tashi kika dauke kafa."
Baba Ati tace"Ko ba domin Darajan Fa'iza ba,ai ya Duba zumunci"
Yaya Mariya tayi mirmishi kafin tace"Ke kika san wannan Baba Ati, tunda Fa'iza ta zama banza a wajen su zaki san ba su damu da wannan zumuncin ba"
Kai Tsaye Abba yace"Ki fara sanar dani abunda kika sani"
Ina kuka ina girgizama Yaya Mariya kai bata Saurareni ba ta fara zayyana ma Abba abubuwan data sani akan zamana agidan Ishaq da yadda ya rabani da su da auran sa da wulakanci da Anty Binta tayi mana. da yadda na kara zama banza bayan auransa da Zainab Saboda ita mai kyau ce kuma yar gata ce,da yadda har mahaifiyarmu ta rasu bamu gana ba,kunci rayuwar da na cigaba da Fuakata kafin samun sana'ata da duk irin cin kashin da Mama da Anty Binta suke min ta fadi iya abunda ta sani kafin ta gama gabadaya su Inno sun fara kuka saboda Tausayina.
Ammi tace"innalillahi lalle Fa'iza ta ga Kunci rayuwa"
Abba ko Ishaq da Mama yake kallo ji yake kamar ya saka a kulle masa su har sai sun daina Numfashi,shuru falon ya Dauka sai mganganun su Baba Ati cikin Tausayawa ni ko kuka kawai nake yi cikin kunar rai abubuwan da suka faru suna Dawo min Daki Daki.
A fusace Abba ya mike yana fadin"Ba anfanin wannan zaman. Ka rubuta ma y'ata takardan saki tunda ba'a Dole. kuma kwatankwancin yadda ka Wulakantamin Fa'iza wlh nima sai na wulakantaka"
Kokarin Fito da wayarsa yake yi ganin haka nayi wuf na rike kafafun Abba ina kuka nace"Abba kada kayi mai komai don Allah nice daman baya so to ya sakar maka y'a
Abba da gaskiyansa ni Nakashashiya ce ina da Raunin ji,sannan ni ba Fara bace bani da kyau Abba sannan ni bani da ilimin Boko kuma ban iya Turanci ba,sannan ni bani da gata bani da kowa ni ba yar kowa bace sai Diyar Bebiya,Abba da gaske ne ni nayi kutse cikin mafarkin sa ni ban Dace da Mutum irin sa ba,Abba ka Dubeni baka mara kyan Fuska wacce batajin Turanci bata kuma da gata Abba dole yaji kunyar nuna ma Duniya ni a matasayin matarsa in kuma yaji kunyar nuna ya'yansa shima bai yi Laifi ba ,Abba bai so a haife su ba Karfin Rabo ne ya samar da su na fi shi sanin zafinsu shiyasa na zauna Domin na kare su Abba.
Abba ka kyalesa yana da gaskiyansa ni Fa'iza bani da wani amfani Abba ni ba macen data dace da namiji kamar Ishaq ba ne,ba ya so na ne Abba Kuma gaskiyan Mama data sha Fad'in bauta ya Dace da Mata irina. Abba na zauna na wahala da ya'yana Tunda ya zabi wata matar sama dani Abba sai mu kwana mu yini ni da yara bamu ci abinci ba Abba,Abba ba tun yau ba Mama da tab'a so ta koreni Anty Binta ta taba zuwa har gidana ta min watsi da kayana akan sai na bar gidan kaninta Abba..!
Sai kuka yaci karfina na rika rusa kuka sai jikin kowa ya karayin sanyi Abba ya Duka ya rikeni jin hannayensa yasa na cigaba da Basu labarin irin zaman da nayi da ishaq irin yadda na fuskanci tozarci da wulakanci a wajensa da wajen mama yadda suke zuwa da Zainab ina musu wahala kamar jaka yadda yake tafiyar ya barmu da yunwa ni da ya'yansa,Yadda mahaifin? matarsa da shi kanshi suka taru suka wulakantani Saboda bani da gata ni kaina ban san ina mgana ba Idanuwana a Runtse nake maida musu komai ina ganin shi a idona yana wucewa kamar a majigi.
Ina basu labarin taimakon Hajiyar su Raliya gareni tare da taimakon Badariya da kudin da Kungiyarsu tabani kafin fara koyan san'ata da yadda muka yi da ishaq da zaman mu da shi bayan haka.
Na Damke hannunwan Abba ina Fadin"Bani da abunda zai so Abba. Shiyasa na yi zaman ya'yana Lokacin da na yanke shawaran barinsa sai ya rasa aikinsa sai na janye kudirina Abba har zuwa wannan Lokacin"
Kuka yaci karfina ammh ban yi shuru ba na cigaba da gaya musu yadda muka fara Sabuwar Rayuwa da duk abubuwan da suka Faru da Lokacin da ya nemi na bama aurammu wata Dama.
D
Da sauri Abba yace"Allah yasa baki bashi wannn damar ba Fa'iza..?
Ina kuka nace"Na kasa Abba..Na kasa dalilin Ishaq yasa na Tsani aure da maza Gabadaya auren ya fita a raina. Don girma Allah Abba ka saka shi ya Sakeni ina jin kamar zam mutu in na Tuna da auren sa a kaina"
Na karishe Fada ina wata jijjiga Saboda kuka Inno na sharan kwallah tace"Tabbas ya wajaba a raba wannan auran Usman zaluncin ya yi yawa"
Abba yaji gabadaya bai son ganin Ishaq da mahaifiyarsa dake kuka shi ko Uban gayyar kansa na kasa jiki na rawa.
Cikin Daga murya Abba yace"Sai ya saketa..?ai wannan auran ba shi..Duk da ban da zurfi a sanin wasu hukunce hukuncen addini,nasan matsayin ka jingine auran ka a musuluci wata Hudu ne in baka Waiwiyo ba, ta nemi manya su Raba auran ita ko ta haura shekaru mganar ma yayi saki ko kar ya yi ya Rage nasa mgana D'ayace daga ita na gama Bilhil azim ko kusa da Y'ata Ya sake kusantowa sai na saka an Dauremin shi"
Ya fad'a cikin bacin rai yana kokarin mikewa da Sauri Mallam yace"AlhaJi don Allah ka koma ka zauna ina da karin bayani kan wannan al'amarin"
Girman Mallam yasa Abba ya koma ya zauna ina jikinsa ina kuka Yaya Mariya ma sai sharan kwallah.
Kowa ka gani jikin ya yi sanyi Ishaq ko bakinsa ya yi nauyi ya kasa ma mgana.
Mallam ya gyara zama yana fadin"Matsalace ta Ila'i wannan mganar ma'ana rantsuwa a shari'a,kamar kace kayi ramtsuwa ka iyakan cewa bazaka kara kusantar matarka ba har na tsawon Lokacin da ka Dib'a ma kanka.
A shari'ance Wata Hudu ya bama mace dama ta zauna in bai Sauya ra'ayi ya Dawo ba ta saka manya Cikin mganar, ko ta kai kara Alkali ya raba auran,ita kuma Fa'iza ta Shafe wasu shekaru tana jingine bi masala ta addini auran su bai saku ba, sai in har shi da kansa mijin ya Saketa ko kuma ya bayyana mana matsayin jinginarsa gareta na saki ne ko ba na saki ba ne.? Ammh Shari'a ta bata damar ta Nemi Saki in har bazata iya zama da shi ba"
A fusace Abba ya ce"Ai ko yanzu zai sakarmin y'a don mai garin su.."
Kai Tsaye ya maida kallonsa kan ishaq kafin yace"Zaka sakar min y'a ko sai na gwada ma ka nima d'an tasha ne?
Abba ya fad'a yana Zare mai ido Lokaci daya kamar D'an tashan daya ambata.




*Janafty*


[7/26, 10:00 PM] Hauwa Galadima: *KNKB3005*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWOWINRL ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY*



Ba domin halin da ake ciki ba, da abunda zai hana mutanen Falon Darawa da kalaman Abba.
Ammh yadda zukata ba sukuni yasa ba wanda ya bi ta kan mganar ni dai kuka kawai nake faman yi gabad'aya ji nayi zuciyata ta rufe ba sarari ko kad'an shi ko Ishaq sai da Abba ya kara Dakamai Tsawa sannan ya Dago a Firgice yana rawan bakin fadi'n"Don Allah Abba kayi hakuri. kace zakayi min adalci wlh nasan nayi kuskure ammah na dade da yin nadama ita Fa'iza ta sani na nemi afuwarta da amincewar ta bama auran mu wata Dama Abba.."
Abba ya katseshi a Fusace Lokaci Daya yana Fadi:n"ai baka sonta. ko ba haka ba ne..?
Rantsuwa ya kwaso kamar ya yi kuka Cikin rawan murya yace"Da ne Abba ban da yanzu wlh ina son Fa'iza ita ta sani ina Sonta.."
Ina jikin Abba na rika girgiza kai ina Fadin"Bani kake so ba. Bazaka taba sona ba saboda ba'a sauya Fa'iza ba,ni ce dai Fa'iza bakar nan mummuna, mai raunin ji mara gata yar talakawa wacce bata jin Turanci ba ni kake so ba.
So kake na koma saboda ya'yanka da kuma yi maka gadin gida kamar yadda na Saba, tunda daga kai har matanka ba masu zaman gida ba ne kuna fita aiki"
Na karishe fad'a hawayena suna shata shata kamar an Bude Famfo Goggo tace"Kibar kuka haka Fa'iza wannan ai sai hawayen naki ya kare"
Inno tace"Na yaushe kuma?ku barta tayi kukanta na samun salama ne yarinya ta jima cikin kuncin rayuwa ba'a sani ba irin shi ke sa jini ya haye yayi sama kaji an ce mutum ya Fad'i ya mutu,kayi ta mamaki to shi kadai yasan irin bakincikin da ya rika Hadiya shi kadai"
Kalaman Inno suka kara Tunzura Abba ya kara dagama Ishaq murya yana Fadin"Da baki zaka Fad'a ko sai an kawo maka takarda..?
Rawan muryansa ya kara Daukowa Abba ya Dakatar da shi cikin Kaushin murya yace"Kada ka sake kirana da sunan Abba kirani Usman karaye na. Ishaq ni uban Fa'iza ne kad'ai"
Ya karishe fad'a cikin kaushin Murya har ya nuna sa da yatsa Yaya mariya na gefe ta gyad'a kai cikin jin Dadi Ammi ma ranta fes,Daman tasan Baban Nana bashi da wasa.
Cikin kankantar da kai yace"Kayi hakuri Abba ammh bazan iya sakin Fa'iza ba"
Abba ya kallesa a wulankance Baba Ati tayi karaf tace"Tunda har baka sonta ka saketa mana..?fiye da shekara goma kana cutar da yarinyar nan bata taba mgana ba sai yau kayi mata adalci kaima mana"
Inno ta karbe da Fadin"Ahto mganar Sulhu ai batama taso ba. Mganace fa ta Shari'a Atika haba ai ya cutar da ita abun sam ba adalci aciki."
Mita dai suka fara yi nasu na Tsoffi,Goggo dai tama kasa mgana Domin bata da abun cewa mganar gaskiya auren Fa'iza da Ishaq akwai tarin zalunci in akace Fa'iza tayi hakuri matuka an danne mata Hakkinta da shari'a ta bata.
Mama ce tayi karfin Halin matsowa tana Fadin"Alhaji don Allh ku yi hakuri. Ku yi hakuri ku yafe mana gabadayan mu.
In sha Allahu hakan bazai kara faruwa ba,Alhaji a Duba ko domin yaran nan a bama Fa'iza Hakuri tabi mijinta"
Abba ba domin girman shekarun Mama ba,Tuna baya yaso yayi wato ya mulmulamata ashariya,ammh girman shekarunta yasa bai zageta ba. ammh fa sai da ya auno wata mganar cikin bacin rai yana fadin"Su ya'yaan sun ci kaza kazan su. shekarun ki nake dubawa Hajiya shiyasa na raga miki,Shi ai ba duba Darajan ya'yan ba ya Tozartata kema ai baki duba yaran ba sanda kike Cin mutumcinta,sannan ki saka D'anki shima yayi,yaran ai ba son da ranshi suka zo Duniya ba Tunda ba zabinsa ba ne .Bani da damuwa da yara in suma bai kaunar su ya had'o min duk zan iya Hada su da uwar su na rike in sha Allahu bazan gagara ba ammh Wlh tallahi ba mai maida ma Ishaq Fa'iza ko tace zata kuma. ni Usman karaye sai nayi shari'a da d'an ki wajen karban ma Y'ata Hakkinta.
gwara tun muna ganin darajan juna ki sa kashi ya saketa kafin mu yi mara kyau ni da shi"
Ya fad'a yana Huci ransa gabadaya ya gama baci da wannan renin wayau na uwa da D'anta.
Mama ta kasa mgana sai matsar kwallah yau ga ranar nadama bata taba zaton akawai wannan Ranar ba ta dago tana kallon Goggo wacce ta kauda kanta alamun bani da ta cewa sai ta kalli Ishaq kafin tayi mgana yayi saurin ta shi yana cewa"A'a mama kada ma ki rokeni bazan iya sakin Fa'iza ba. Wlh bazan iya ba..!
Fa'iza! Don Allah ki saurareni"
Ya fada yana kokarin Tunkaro ni Abba ya mike ya taresa cikin wani Kallo na gargadi yace"Kada ka fara. Kada kuskura"
Kaina na Tusa cikin gwiwata ina Cigaba da kuka sai ga Ishaq ya Duka gaban Abba ya rike kafafunsa yana Rokonsa Abba ya kwace kafarsa ya matsa gefe yana Fadin"Ka riga ka bata komai da kanka Ishaq. shi kan shi Dr.Laawal din da yazo har gida ya wulakantamin y'a sai naji Dalilinsa ka bani Takardan Fa'iza kaje ka zauna da wacce ka zaba ya'ya ko zan kara maimaita maka in bazaka rikesu ba ka dawo ma da uwar da su, ita zata rike su tunda tasan Darajan su"
Abba ya fad'a yana kauda kai Ammi Daga gefe tace"Shikenan kuwa Baban Nana mgana ta kare masu cewa ayi Hakuri saboda ya'yaa an kashe bakin su"
Ta fada tana kallon Mama tana Hararanta,duk sai ta zama kamar Mujiya acikin mutane,Ina kuka nayi Saurin Tsaigaitar da kukana na Dago ina Fadin"Abba ba ruwan Zainab da Mahaifinta wanda ya ijiyeni ne ya nuna musu matsayina. In da ace ya nuna musu ina da Daraja abunda ya Faru bazai Faru ba,Mganar gaskiya Zainab bata taba kyamatata ba ta rikeni ni da ya'yana tsakani ga Allah kuma ta kaunace ni shiyasa nima na kaunaceta domin Allah,Wlh ba ruwanta nayi zaman amana da ita da Daraja fiye da yadda mijinta ya Darajani taga kimata fiye da yadda wanda ya ijiyeni ya gani, ka kyalesu Abba mahaifin Zainab ba shi da Laifi kwata kwata.
Abba sai faman Huci yake yi Falon ya yi Shuru Ishaq ya Dake yana ma Abba magiya shi kuma yace ya gama mgana ganin Haka yasa ishaq ya mike ya kalleni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login