Showing 111001 words to 114000 words out of 288345 words

Chapter 38 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

724

nace"Ko ban damu saboda yana mijina kuma uban ya'yana ba.Zan nuna alhini na saboda yana matsayin Yayana wanda iyayenmu suke abu d'aya ballatana shi din Uban ya'ya na ne"
Daga haka na huce na barta,sai ta fashe da kukan nayi mata rashin kunya mgana taki ci taki cinyewa Goggo ta kashe mganar da Fadin"Haba Binta mu bar wannan ceceku cen tunda ba shi ba ne a gabanmu.Mu ji da abunda ke gabanmu don Allah"
Ammh Anty Binta batayi shuru ba sai da tace"Ai gani tayi tana kama kud'i sai ta dauka daidai muke da ita.Abunda bata sani ba komai lalacewar Daji bai kai in giwa ta mutu kiyasha ya jata ba, ko tana mace tana da Madaukakiyar Darajarta"
Dakyar mgana ta mutu sai da Wata kanwar uwa take ga Mama ta tsawarta ma Anty Binta sannan mganar ta Dakata ammh tana ta kananun mganganu a kaina niko bansan tanayi ba ina Dakin Badariya.
Washegari ya kama Sati daya kenan da labarin da iso mu,an yi an yi an shiga an fita duka labarin bai sauya ba,Hankula ko sun fara kwanciya sai su kara tashi jin ba wani labari mai Dadi.
Sai a ranar muka yi waya da Zainab da yake muna da lambar juna sai dai mukam jima bamu yi mgana ba. sai in wani abu ya taso ko rashin lafiya,Ita ta kirani ni na shafa da ita ballatana ma na kirata, mun gaisa cikin Alhini muka yi ma juna jaje,Sai dai ban wani ji ta cikin wani yanayi ba,Ita take fad'amin mganar Yaya Ishaq sai manyan Gwamnati sun shiga tunda Fitar da kudi ne na ma'aikata kuma ta Office dinsa da saka Hannun sa komai ya fita ba yadda za'ayi ya fita,Tace Babanta ya samu ganinsa sau daya ammh har yanzu ba wani mganar su bada Belinsa,Mun dade muna mgana da ita nace mata ina gidan Mama tayi ta mamakin tace ita da yara sun koma gida sai dai bata bar zuwa wajen aiki ba,Saboda sun ki bata Hutu a raina nace Mama taji kuwa..?sai ga shi tana fadamin Ko da yaushe suna Mgana da su Mama,kuma susan tana zuwa wajen aikinta nan take na Fahimci abun,inda ake raina an fi kai Hari chan bangaran.
Ranar da yammah sai ga Hajiyar su Raliya tazo,ni ina chan Dakin Badariya ban sani ba,Mama na ganinta da su Anty Binta suna ta Rawan jiki mama ta santa tunda kawancen Raliya da Badariya ba yau ba ne,Sai dai ita Hajiyar su Raliya ce bata zurfafa zumunci da Mama ba, sai kuma gashi ni jinina ya had'u da nata da zuru'arta.
Bayan gaisuwa da jajanta abunda ya faru sai Hajiyar su Raliya ta nemi ganina Mama ta tabe baki kafin tace"Kila ma bata gidan domin tun jiya take son ta koma gida dayake bata damu ba"
Hajiya batace komai ba,Da Badariya tazo gaisheta sai tace ta kira mata ni,Ina Dakinta tazo ta kirani ina jin tace Hajiyar su Raliya na mike na fita da Hijabi suna falo na duka na gaisheta cikin Fara'a ta amsa ni tana fadin"Haka ake yi Fa'iza abu ya faru haka bazaki kirani ki fadamin ba..?
Sai dai naji a bakin Raly.?
Kaina na kasa ban ce komai ba sai ta Cigaba da fadin"ba'a haka Fa'iza irin wannan sai ki kirani ki fadamin ko ba a Uwar kika Daukeni ba..?Goggon karofi ta karbe d'iyarta kenan.?
Goggo na gefe tayi dariya kafin tace"Ba ruwana Hajiya ke da Diyar ki"
Kaina na kasa na shiga bata Hakuri sai tace bakomai su Mama haushi duk ya cikasu kallona tayi tana fadin"Ya abun ya faru ne ina so na sani saboda naji in zan iya taimaka wa"
Kafin nayi mgana Anty Binta ta karb'e da bayanin yadda ake ciki Hajiyar su Raliya,ta gyada kai kafin tace"Akwai Kanina yana aiki da Hukumar EFCC din achan Abuja, bari na nemesa naji ko zai iya taimaka mana"
Nan da nan bakin Mama ya washe a gaban mu ta kirasa suka gaisa ta rattamai bayanin komai sai ya nemi sunansa da inda yake aiki Anty Binta ta fadamata sai ta turamai yace ta bashi nan da zuwa Dare zai bincika mata halin da ake ciki.
Bata wani jima ba, tayi ma su Mama sallama,akan yadda akace in sha Allahu gobe zata dawo ita da sauran yaranta Mama godiya kamar zata kwanta mata Hajiya ta kalleta kafin tace"Bakomai kada ki damu babba ne a wajen zai binciko komai..Zan iya yin komai saboda Fa'iza kamar diya take a wajena Ahalina Ahalinta?ne,zan iya bakin kokarina bazai gagara ba insha Allahu"
Basa kaunar su ji an ambaceni kuma basa kaunar alfarma ta barayina har waje na rakata ni da Badariya,Direba ya zo da ita ta shiga mota tana ce min sai zuwa gobe,Ta tambayeni su Amir nace suna cikin gida,na dawo cikin gida naji ana ta maimaita zencen nidai a raina ina fatan Allah ya kawo mafita.
Washegari da wajen yammah sai ga Hajiya ta dawo ita da Raliya da yayyin Raliyan suna zuwa ni suka nema daman suna zuwa gidana,Ita kuma Hajiya ta nemi su mama ta gayamusu halin da ake ciki,Hukumar ta na bincike ne,sannan akwai yuyuwar komai da ya fita da saka hannun Yaya Ishaq saboda haka in sun gama Bincikensu zasu yi mgana, sannan sun hana Belinsa saboda cases din na da girma Hankula sun kara tashi tace dai a Dage da addu'a komai zai daidaita.
Wasa wasa har an shud'e Sati Biyu shuru dai mgana d'aya sai sun gama Bincike,Gajiya nayi da zama na Tattara na koma gida na da yara Goggo ma ta koma Karofi mama an barta da Anty Hure ne mutum yamai suma sun koma kowa ya Saduda yasan Allah ke yi,Mama ta saka ana ta Sadaka da Saukan Qur'ani ni kuma agida banzauna ba ni da yara muna ta kai ma Allah kukan mu,Ban kara bi ta kan Zobo da kunin aya ba,Saboda Halin da nake ciki ko makaranta yaran basu koma ba Hafsa ce ta koma makarantar ta tana zuwa.
Wajen wata da'ya da Tsare Yaya Ishaq aka bama yan'uwansa Daman ganinsa Su Yaya Isa dai suka koma Abuja mgana ta tabbata ba yadda Yaya Ishaq zai fidda kansa saka hannunsa da yardansa aka fidda kudad'en,zai biya taran kudaden gabad'aya da tsabar kudi ko Kaddara.
Lokacin da labarin yazo mana Sai murnan kowa ta koma ciki kudi ba kadan ba wajen Million 70,ina Yaya ishaq yaga wannan kudin ko Kaddara..?su Yaya isa sun dawo suna mganar ya lissafa abunda ya mallaka, gida biyu nan katsina d'aya sai na Abuja sai mota sai gidan mahafinsa,Sai tsabar kudi miliyan d'aya da rabi asusun bankinsa sai fili a nan katsina,Hukumar tace zata zo ta Duba duka kaddarorin zata kwace zai zama karkashinta.
Sai naji na rude ina ta maimaita innalillahi acikin raina Hankali tashe na kalli Yaya isa ina fadin"Aikin sa fa Yaya isa..?
Ya kalleni cikin Tausayawa kafin yace"Ba mganar aiki Fa'iza ya samu ma ya fito lafiya"
Su mama sai kuka Daman a gidan ne ake maida zencen,Agidan muka kwana Dagani har yara saboda ana saka ran dawowar Yaya ishaq acikin Satin.
Haka ko akayi hukumar tazo ta Duba Gidajen da Yace kada a saka gidan Mama,Mama ta saka kuka miye amfanin gidan in bashi a Had'a dashi,Sannan akwai tsabar kudi a wajenta na sana'arta miliyan uku Anty Binta ma ta saka miliyan Biyu,suka tura ta asusun bankin Ishaq,Saboda kudin su rage nauyi.
muna ji muna gani Hukumar ta kwace gidan da muke ciki da gidan Mama da filin da ya siya acikin gari chan ma Abuja ta karbi wanda zainab ke ciki da motar hawansa, sannan sun bamu Notice Wata daya mu tashi Saboda wajen ya zama mallakin Gwamnati
Lalle mun ga tashin Hankali mai suna tashin hankali,Wannan labarin sai dai mun Dauki Dangana tunda zasu sake sa,Bai amsa laifinsa ba ya riga ya rantse bai da hannu akan lamarin, zasu sake sa ammh ba su kyalesa ba in bukatar wani Binciken ya shigo zasu kara nemansa,Shima da taimakon ????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
manya acikin lamarin mijin Hajiyar dala da Kanin Hajiya dake hukumar tare da Mutanen Mahaifin Zainab Dr.Lawal bako.
Mama ta tsine ma duk wanda ya saka Danta cikin bala'i tayi mugayen addu'o'i akan sa,Ta ce tunda ya jefa Rayuwar d'anta cikin bala'i shima bazai ga rayuwa mai kyau ba.
Watan Yaya Ishaq biyu a Hannun Hukuma suka sakesa,Daga Abuja tare da Dr.Lawal da Zainab da yara, sai su Yaya Isa da su Jamal suka iso da shi katsina ko da suka iso karfe goman Dare ne an so ya kwana sai gobe yace Zai je yaga Mama yasan tana cikin Damuwa.
duk da Dare ne, gida cike yake da masu dakon dawowarsa.
Mama na jin Dirin motarsu ta Fice da gudu ita ta bude masa Mota ya fito Allahu akbar Duk wannan fafan da kyau da nasabar ta Yaya ishaq ta tafi cikin wata Biyu.
ya rame ya fita Hayyacinsa sai sumar kai da kasumba ta rufe masa fuska, yayi duku duku kamar ba d'an kwalisa Ishaq Kabir Karofi ba.






*03/07/2023*
*Janafty*

*KNKB2002*

*Ki biya ki karanta cikin salama,Kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta min littafi,Sannan kada ki yad'amin shi,Pay N500 regular ko kuma VIP N1000, Via Jamila Umar Gt bank 05521790550,ban da tsarin kati wannan karon. a turo ta POS, Shaidar biya ta wannan lambar 09069067488*


Mama ta rikesa cikin Fitan Hayyaci,da Dimaucewa ta furta"Ishaq.."
Ashe zan sake ganin ka..?
Sai ta rushe da kukan da ta Dade tana yin sa ammh na yau na Dabam ne, cike yake da tsantsan farinciki sannan hade da fargaba da fidda tsammani.
Rumgumeta ya yi shima cikin wata murya mai cike da laushi da sanyi yace"Mama.."
Sai ya kasa mgana gabad'ayan mu muna kansu,mu kanmu Tausayin ya kamani dole ka tausaya ma uwa indai ta bangaran abunda ta haifa ne. Dakyar Mama ta bari aka shigo da Yaya ishaq gida,ko kan kujeran da ya zauna tana kusa dashi kuka take yi tana Sharb'ewa fadi take yi"Duk wanda ya yi sanadiyar shigar ka wannan Halin Ishaq Allah ya Dai'Daita sa,ya hana sa zaman lafiya a cikin wannan duniyan"
Sai ta kara fashewa da kuka tana cigaba da fad'in"Tsakanin mu da shi Sai Allah ya isa bazamu taba yafe masa ba"
Shi ko yana ta faman lallashinta Fadi yake yi"Ba ga shi na dawo ba Mama? don Allah ki daina wannan kukan hakanan"
Su Goggo kuwa sai sannu Ishaq kawai suke ce masa yana amsawa Hajiyar Dala tace"Sannu Ishaq ka auna arziki Allah ya kyauta gaba"
Cikin yanayin Sanyi jiki yake amsawa Badariya da Anty Binta suka rumgumesa suna koke koke yana mirmishin karfin Hali yace"Kuka dai..?ba ku gani ina lafiya, Daddy ka fad'a musu ba wanda ya Dake ni fa"
Dr.Lawal bako na zaune a gefe ya murmusa kafin yace"Tun muna Abuja nake fadama Jamal haka,ammh bai bar kuka ba kamar wani mace"
Sai aka juya ana kallonsa yana ta sharban Hawaye Ishaq yamika masa hannu yazo kusa da shi Cikin karfin Hali yace"Kun gani ina lafiya basu dake ni ba in baku bar kuka ba,Mama ba zata bari ba"
Ni ko ina gefe daya ban tusa kaina ba Farhan ne a sabe a Hannuna yana ganina ya kirani"Umma.."
Ni kuma na Chabesa da yake har Hutu an taba kawosa wajena kuma indai suna garin to yana wajena sosai yaron ya saba dani.
Sai dai nayi hamdala da godiya acikin raina da ya kubutar da shi Lafiya,duk da an rasa aiki da dukiya sai dai an gode Allah Yaran dake d'akin Badariya basu san abunda ke faruwa ba,suna tare da Halisa,Su na kyalla ido su ka gansa sai suka nufesa suna kiran sunansa "Daada.."
Da sauri duka ya Tare su Anum ce akan gaba sai musty da Ahmad Amir dai a gefensa ya zauna yana fadin"Alhamdulillah Daada ya dawo"
Mirmishi ya saki ya shafa kansa yana fadin"na dawo Baba na"
Anum ta fashe da kuka su Ahmad na tayata Ishaq ya fara lallashinta sai ta tsagaita tana fadin"Daada.."
Sai shesshekan kuka ya tareta sai ya rumgumeta yana fadin"Ina fatan baku yi kuka da baku ga Daada ba ko..?
Anum tace"Bamu yi ba da mun fara Umma zata hanamu sai tace mu yi maka addu'an Allah ya kubutar dakai,mu addu'a muka yi ta maka"
Amir ya karbe da fadin"Umma nata karatun Qur'ani ta d'aga hannu ta na ta maka addu'a Daada nima nayi maka sosai"
Gabada'yan falon sai yayi tsit ana Sauraran yaran Yaya ishaq jikinsa ya karayin sanyi kaunar ya'yansa ya kara kamasa ya kamasu duka ya Rumgume yana Dagowa muna Had'a ido ina shirin na gaisheshi tare da barka da arziki karo na farko a Rayuwata tun da na san Yaya Ishaq da ya taba ambaton sunana cikin Tausasawa.

"Fa'iza.."

Idanuwana a bude na dago ina kallonsa shima ni yake kallo, ba ma shi kadai ba.kaf mutanen dake falon sai kallon su ya dawo kaina,mamaki da al'ajabi basu bar ni na iya amsa mai ba, sai ya kara shayar dani wani gumbar mamaki cikin karin Laushin da yayi ya sake fadin"Nagode..Nagode sosai da baki bari ya'yana sun yi kukan rashi na ba.ko achan in na Tunasu nakan shiga damuwa ammh da zarar na tuna kina nan sai naji sanyi a raina ina da yakinin zaki Kula da su fiye da yadda zan kula da su'"
Ya karishe fada yana kallona da zurmamun idanuwansa da suka zurma Saboda wahala abun mamaki baya karewa har da mirmishi yayi min na Daskare a tsaye na kasa mgana Sabon Ishaq nake gani a gabana ko kuwa dai tsohon ne wanda na sani..?
Ni kaina baki na yayi nauyi,Nauyin da dakyar na iya fuzgo mganar dake bakina sannu da arziki nayi masa, sannan na hada da Allah ya kyauta cikin yanayina nace"Allah ya baka ikon cin wannan jarabawar Allah kuma yasa a mizani"
Cikin Muryansa mai cike da sanyi da Haiba ya amsa min da fadin"Ameen Fa'iza Ameen Ameen"
Tare da su Goggo suma da suka amsa ni Ni dai tsabar mamakin da nake ci bai sakeni ba naji ana cewa ya kamata a barsa yayi wanka yaci abinci ya huta zuwa gobe da Safe.
Mama da kanta ta rakasa har dakin Jamal ita da su Anty Binta,Mazan kuma fita suka yi Hotel zasu kama su kwana,Sai alokacin muka gaisa da zainab muna ma juna barka da arzikin Farhan na wajena ya makaleni tana Dariya ta bar min shi ta shige Dakin Mama inda ta saba sauka.
Ni kuma daman ba ni da wannan gatan Dakin Badariya ne wajen saukata nan muka shige ni da yaran,basan ya suka kare ba ni dai daganan bayan na gama shirya yara sun kwanta nima na kwanta,Kafin nayi barci na dade ina tunanin Yaya Ishaq da Sabon Tausasawarsa gareni, wata zuciyar ta ankarar da ni da cewa kada na sakankan ce kada na manta Hukuma ce ta tsare shi na tsawon Lokaci yana cikin firgicin da bazai yin wani abu ba kada hakan ya rud'eki daganan na watsar da wannan Tunanin na kwanta barci,ammh sai da na tashi wajen uku na Dare na Dauro alwala nazo na yi nafilfilun godiya ga Allah.
Washegari da na tashi,na riga na saba da aikin da jikina bazai iya zama haka ba,Hafsat bata nan tana Hostel wajen wata kawarta ta kwana tun jiya,Mun dai yi waya da asuba na fada mata Yaya Ishaq ya dawo sai tace ma ta gani a waya Badar ta saka,Sai da nayi sharan duka Dakunan na gyara nayi abun karyawa sannan na kama yaran nan duka nayi musu wanka, Goggo nata min sannu da kokari Su Anum nata Tambayan Daada Hajiyar Dala tace yana Hutawa ba'a so a damesa.
Sai bayan na natsa na kira Yaya Asiya na gayamata sai da tayi hamdala,ta nuna alamun murnanta ammh Yaya Mariya ko ajikinta cewa kawai tayi Allah ya kyauta da nace ko zata zo ne..?sai tace min zaria zata tafi suna, kanwar mijinta ta haihu ban ja mganar ba, sanin bazata zo din ba Yaya mariya akwai kafiya da riko Daman sau d'aya tazo shima ba wai jaje tazo ba,Goggo ce ta dinga mata fada yasa tazo kuma har tatafi Allah ya kyauta bata iya ce ma Mama ba, Da Yaya Asiya ta mata fad'a bude bakinta sai cewa tayi"wani Jaje kuma Yaya Asiya..?Alhakin Fa'iza ne fa ke bibiyan Ishaq da danginsa"
Bige mata baki Yaya Asiya tayi ta na mata fada sai bata kara mgana ba, kuma tunda tatafi bata Dawo ba.
Chan da rana sai ga su Anty Nasara da mutanen karofi gida ya cika da yan Taya murna kamar Biki kawayen Mama har da yan'uwanta na yamai da suka yi sammakon tasowa da makota ammh Yaya Ishq din na barci har alokacin bai tashi ba, ana ta dai yi ma Mama barka da arziki bakinta Har kunne Hajiyar Dala tun safe ta bi mijinta suka koma Bayan Mama tayi ta Godiya,Kuma duk wanda yazo sai ta nuna Zainab tace ayi mata Godiya mahaifinta ne ya tsaya ma Yaya ishaq har aka sako shi,sannan sai ta zauna ta bada labarin sharri a ka kulla ma Danta,kawayenta na tayata mugayen addu'o'i ga wanda yayi sanadiyar haka.
Ni dai ina gefe ban tusa kaina ba,Da kaina na kira Hajiyar su Raliya na fadamata tace sun yi mgana da kaninta ya fadamata an sakesa tace min zata shigo in ta samu sarari yanzu harkokin sun yi mata yawa ne,muka rabu bayan nayi mata fatan alheri da nasara,Yaya Ishaq bai tashi ba sai yammah ya rama Sallolin dake kansa yaci abinci Lokacim Tuni Goggo da iyalanta sun wuce Karofi sai ga Mama nayi mata godiya Goggo tace bakomai an yi ma zumunci ne.
Ya iske Dangin mama da makota da kawayen mama da su Anty Binta,ana ta yi mai barka da arziki,yana amsawa kayan Jamal ya saka riga da wando sai naga yana yawo acikinta ahalin yafi jamal cikan namiji a baya sai dai zama waje d'aya da Tunane tunane yasa duk ya zabge.
Ni aikina shine Saukewa da Dorawa da an yi baki Mama tace a kawo abinci da ance ya kare sai tace ina nake da bazan sake dora wani abu ba? ko meye amfani na.?daman nasan ba ni da amfani shiyasa ban damu ba Zainab kuwa yar gatace tun safe tana ciki tana hutawa tace min Kanta ke ciwo saboda tafiyar Mota Fadil ma ni ta bama shi nayi mai wanka na goyasa duk wanda ya ganni da goyo sai yayi mamakin sanin Tunda Ahmad ya girma ya wuce Goyo,Sai na juya aga Fadil ne,ni renon yara bai dameni ba kafin ma nasan zafin Haihuwa na iya kula

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login