Showing 243001 words to 246000 words out of 288345 words

Chapter 82 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

766

Yaron nan ai gwara ta koma Saboda ya'yan Dake Tsakani"
Sai ya tabbatar da ba shi kadai yaji wannan mganar ba mutane da Dama sun sani,da ya dawo yau ya tambayi Ammi kan yanayin alakata da Engr Ammi cikin Fara'a ta labartamasa yanayin Farincikin da nake ciki sai ya gano shi Ishaq bai yi mgana dani ba abaki yaran yaji mgana ya hau ya zauna kuma ya yad'a labarin batare da ni na sani ba lalle ko in hakane akwai kura ya zama Dole nasan Halin da ake ciki na kuma yi gaggawan fidda Guda daya in Engr na bama Dama z??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ai bama Ishaq hakuri in kuma Ishaq ne zai san yadda zai lallabi Engr yasan shi da Takwalli da yakana.
Ni daman nazo sanar da Abba ranar asabar zan tafi Karofi ne saboda walimar mu,sai kuma naji yace yana son mgana dani ni yanzu nauyin Abba nake ji saboda Engr,naji Abba na mgana ammh har ga Allah ban ji da kyau ba ina chan ina tunanin hirarmu da Engr na rigiman sai yazo walimarmu har karofi daganan ma sai na nunasa wajen Dangi.
Kamar daga sama naji Abba na ambaton Ishaq da mganar ya kirasa yana tambayansa Lokacin da da suka sanya na auran mu.
Sai na kalli Abba cikin wani yanayi kamar ban ji da kyau ba nace"me kace Abba..?
Sai da Abba ya kara maimaitamin sannan na gane in da aka dosa gabana ya fadi cikin rawan murya nace"Abba..Ni kuma..?
Daman ka ba shi dama ne..?
Abba ya girgiza kai kafin yace"Ke yace kin basa dama kin fad'ama yaran da Antynsu"
Sai na tuna mganar muka yi da Anum,Da mganar mu da Zainab sai naji hankalina ya yi bala'n tashi cikin tashin hankali da rawan murya nace"Ni na fad'a ne wasa nake musu Abba.."
Kai tsaye Abba yace"Zabi naki ne har yanzu Fa'iza ki yi tunani in Ishaq din kika zaba falillahil hamdu sai na sallami Engr, in kuma Engr kika zaba sai na bama Ishaq hakuri ki yanke hukunci daga yanzu zuwa ranar da zan zo Karofi yaushe ne Walimar taku..?
Cikin rawan murya nace"Sati mai zuwa"
Abba ya jinjina kai kafin yace"To kiyi tunani a tsanake kafin lokacin aranar zamu tsaida mgana in sha Allahu.
Tashi ki je, jibin Direba zai kai ki zan barma mamanku Sako ta baki."
Daga haka ya sallameni na mike jikina na wani girgiza zuciyata na rawa.
Allah ne ya kaini d'aki lafiya ko gani bana yi,gabadaya idanuwana sun yi Duhu kamar yadda zuciyata ke cikin Duhu da Sarkakiya.







*Janafty*
[7/31, 6:37 AM] Hauwa Galadima: *KNKB3013*

*Goron Tula*

*Ingantaccen maganine dake saukarda niimar mace sannan dadin dadawa fruit ne ga dadi abaki zakine dashi chakwai sannan bashi da wata illa yadda kikasan fruit haka yake*
*yana da matukar kyau da tasiri ga ma aurata daga mace harna mijin Kuma munada Syrup nasa da akataceshi sannan aka hada da ingantattun magunguna dasuke temakawa ma aurata kwarai don inganta lafiyarsu dakuma maganin matsalarsu ta auratayya yana saukar da niima sosai yana karawa mace dadi fiye dazatanku sai kingwada zak ibada labari insha Allah*

*Sannan akwai zumar kiba*
*Duk macen dake son ta murmure tayi kyau taciko tatada komad'a sosai shaf dinta yafito sosai da sosai to tasha wannan zumar insha Allah zaki gode min*

*Zumar gyara nono*
*Zasu yi kyau suciko ammanfa bawai su tsaya ba=?? zadai suciko suyi kyau sosai insha Allah*

*Zumar hips*
*Indai kinsha zumar nan to hips dinki zai bude zasu yi kyau suciko sosai zaki godemin nina fadamiki insha Allah*

*Note magungunan mu ingantattune basu da side effects kokad'an anyisu da ingantattun*
*magunguna sosai*
*Location Gombe munaturawa ko ina 08030861857*


*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*


Ko gani bana yi haka na fad'a kan gado yaraf kamar kayan wanki. tunanina ba shi a tare dani ya tafi wani waje mai nisa na tunanin yadda zan iya kara zaman aure da Ishaq..?tuna Engr kawai in nayi sai naji gabana ya amsa kaina da zuciyata suna amsa kuwwar Rugugi a lokaci daya.
Tsakani ga Allah ina son Engr a lokacin da ban sani ba,na fara son shi batare da na sani ba,Sai dai na amince da kyawawan hallayarsa da barkwancinsa da kuma yadda yake sona batare da shi ya yi tunanin alfarma ya yi min ba,shiyasa na ba shi amanar duka rayuwata gabadaya.
Saboda Tsabar Rudanin da na shiga har bansan ana ta kiran wayata ba sai da Hafsatu ta shigo ta kawo min nata wayar tana fadin"Yaya Asiya ce tace tana ta kiran wayarki baki dauka ba"
Idanuwana har sun yi ciki ciki Tsabar Tashin Hankali na mike a kasalance zaune kan gado ko Hijabin jikina ban nemi cirewa ba, na karbi wayar ina gani tana kallo na kasa kasa nazarina take yi ganin yanayina,ammh bata ce komai ba ta juya ta fice ta bar min Daki.
A amsa kuwwa na saka wayar kamar yadda na saba,Sallama nayi Yaya Asiya ta amsa muka gaisa kamar yadda muka saba jin muryata a chunkushe yasa tace"Ya na ji muryan ki ta yi ciki ne ko Mura kike yi..?
Na rasa amsar da zan bata sai nace"Uhm'
Sai ta min fatan samun sauki kafin ta zarce da fadin"Ashe kuma zaki koma gidan mijin ki Fa'iza naji dad'i wlh.
Gwara ki koma ko Saboda yaranki"
Wani irin Dum!naji a tsakar kaina nama kasa mgana saboda bakina ya yi nauyi sosai kamar ma miyau ya kasa tsirgamin saboda yadda naji harshe na ya nad'e waje daya.
Ina jinta tacigaba da fad'in"Gwara da kika yi wannan tunanin Fa'i komai lalacewar Ishaq dan'uwanki ne kuma akwai zuru'a a tsakanin ku,tunda kuma yayi nadama kema ai kin kwatarma kanki yanci na tabbata kika koma kina da Darajan ki"
Ni da yake ma ko Goggo bata fadamin ba Gidan Halisa naje jiya kinsan ta kara samun bari Anty Binta ta kirani tace naje na dubata, ita ke min zencen daga gani suma sun ji dadin komawar da zaki yi,Da farko mamaki nayi tunda ban san mganar ba sai da na Kira Mariya tace itama haka taji baku yi mgana a waya ba dai gaskiya"
"Uhm"
kawai na samu kaina da Fadi Saboda yadda harshe na ya Nad'e waje daya,mgana ta cigaba yi tana tunamin manufa da alherin komawa gidan Ishaq jin yanayina yasa bata neme ni da wata mgana ba. muka yi sallama na rude zufa kawai nake yi kenan mgana ma ta shiga bakin yan'uwa ban sani ba..?
Zufa ya jikamin jiki tunda ga Hijabi na har jikina, Tsabar shiga wani yanayi,kenan har su Goggo suma sun ji labari ni ina nan bansani ba..?
Dole na zare Hijabin jikina ina Fifita da shi zufa har kasan wuyana,sai lokacin na tashi na Dauko wayata kira ne ba adadi kuma nasan duk na Engr ne domin tun safe da shi nake fara mgana.
Wayar na hannuna ina Tunanin kiransa ammh kuma kamar an hanani saboda ina ganin ban kyauta ba in na cigaba da yaudaransa,kila ni tawa kaddaran kenan yin aure har Abada batare da naji dadin auran ba.
Zama nayi na tasa wayar a gabana ina gani Engr na kira ammh na kasa Dauka Idanuwana suka cika da kwallah Hirarmu na dawomin a cikin kaina bansan Lokacin da naji hawaye sun cikamin ido ba a fili na Furta"Allah Sarki Tosin"
Kiransa na katsewa sai ga kiran Badariya sai da gabana ya fadi daman mun kwana Biyu bamu yi mgana ba. kamar bazan dauka ba saboda nima bana cikin yanayi mai Dad'i sai dai na Daga kiran Tuna fa Badariya ce.
Ina Dauka sai jin guda nayi a cikin kunnuwana sai da na matsar da wayar Cikin Ihun murna tace"Lalle Anty Fa'iza irin wannan kome na ban mamaki ba Labari.?
Wayata ta lalace tun last week Mama ta fad'amin da muka yi waya sai yanzu nan Yusuf ya kawo min sabuwa ina saka layi ke na fara kira. Ina murna Anty Fa'iza yayan dai nawa In sha Allahu"
Salati na saki a raina kafin naji na tsinke da al'amarin itama kenan taji Labari,ni dai bayan Badariya na amsa wayoyin mutane da dama ciki har da Anty Fadila a bakinta nake jin har kayan dakina da ita akaje aka siyo an gama shiri dawowata kawai ake jira naji ina kuka ne batare da nasan hawaye na fitomin ba
Anty Fadila na fad'amin irin murnan da su Anum suke yi zan dawo har a makaranta sun gayama yan ajinsu, suma Umman su zata dawo hatta da Zainab da Mama suna farinciki da dawowata,har muka gama waya hawaye nake ina sharewa a matsayina na uwa ban isa na Karya ma ya'yana zuciya ba.
Zan koma ma Yaya Ishaq ba domin ina son shi ba sai domin Ya'yana da Farincikin su,bazan iya karya musu zuciya a karo na biyu ba,barin ma da Na kira jamal saboda shima naga kiransa shima zencen yake yi min,jikina bai kara saki ba sai da yace a wayar wani dan ajin su Amir shi Amir din ya ara ya kirasa ya fad'amai haka na zauna na hada kai da gwiwa ina ta kuka kamar raina zai fita,kukan rasa wani abu da nake so kuma ya yi min nisa.
Kamar kuma yan gidan sun sani ba wanda ya nemeni da Hafsatu tazo karban wayata baya na juya bata ma ga Halin da nake ciki ba,bakin kowa sai dai yace na koma ma Ishaq Saboda yarana ba wanda ke tunanin shin in na koma zan samu Farinciki ko bazan samu ba..?meyasa mata da dama ake kokarin Danne musu hakki Saboda yara da an yi mgana sai ace ki koma Saboda yaran ki babu wanda ke tunanin ya mace zata yi in ta koma..?Shin zata yi farinciki..?ko zata Dauwama cikin kunci Allah Sarki Uwa uwa itace wacce zata Sadaukar da Duka Farincikinta Saboda Farincikin ya'yanta.
in dai ko hakane naji zan Sadaukar da farincikina saboda Farincikin ya'yana na. Na Tsaida mgana zan koma gidan Yaya Ishaq saboda yarana Engr kuma bansan ya zan yi da shi ba,Sai dai ko sunan shi na tuna sai naji kuka yazo min na san yana sona ya zai yi in nace na fasa auran sa..?wlh da nasan hakane da tun farko ban basa Dama ba da tun farko ban karya masa zuciya ba.
Ammi bata a gida diyar kawarta ta haihu sun je barka,shiyasa na yini a Daki ina kuka Engr ya kira har ya gaji yayi sakonnin ammh saboda na riga na yanke hukunci yasa ban bude Sakon ba,Ina son na bama kaina karfun gwiwa abincin ranar bai shiga Cikina ba sai ruwan Tea sai yammah Nana Khadija ta lekoni tace Inno na Cigiyata,sai nace tace mata bana jin Dadi ne zan shigo da Daddare.
Bayan sallar mangriba Abba ya Dawo gidan tare da Ammi kila sun biya ne sun D'auketa,ina daki Hafsatu tazo ta kirani In ji Abba sai da gabana ya fadi amnh sai ban razana ba na riga na yi zabi kuma bazan sauya ra'ayi na ba.
Cike da kwarin gwiwa na tafi falon Abba ammh duk wanda ya ganni yasan bana cikin natsuwata.
Suna tare da Ammi Lokaci duka na duka na gaishesu.
Ammi ta kalleni idanuwana sun kumbura tace"lafiya naga idon ki sun tasa..?
Cikin Dishewar muryata da yanayina nace"Lafiya kalau Ammi inaga ciwo suke"
Sai ta faramin fad'an meyasa ban yi mgana ba da sai aje asibiti Abba na gefe yana jin mu bai ce komai ba.
Ni nace ma Ammi idon fa ba sosai ba ne duk Abba na jin mu bai yi mgana ba sai da aka kira wayarsa bai Dauka ba Ammi ta kallesa tana fadin"Ba kiran ka ake yi ba Baban Naana..?
Kai tsaye ni ya kallah kafin yace"Engr ne yau ban san adadin sau nawa ya kirani akan Fa'iza ba"
Ammi sai ta zaro ido kafin tace"Topha lafiya ba su yi waya da Fa'in ba ne..?
Abba yace"Gata nan kiran da nayi mata kenan ya kirani a rude baki ji sa ba, yace tun safe bata daukan wayansa kuma ya tura mata sakonni bata bude ko Daya ba,yanzu ma kiran da kika ga ya yi min nace mai ne ina Office ya bari na koma gida"
Ammi mamaki ya kamata ni ko sai sharan kwallah Abba ta kallah kafin tace"To me ya faru.?
Ke Fa'i meyasa baki daukan wayansa kada fa ki rikita bawan Allah kinga yana son ki"
Sai kawai na Fashe da kuka Abba Da Ammi suka tasani suna kallona cikin mamaki yi nake yi harda shessheka daganan Ammi tasan akwai matsala.
Cikin Sausauta Murya tace"Fa'iza bar kukan nan fadamin meke faruwa..?
Ko kun samu Sabani ne..?
Abba na gefe yaki cewa komai ammh Tabbas ya fahimci wani abu.
Fa'iza na son Engr ammh Ishaq ya sakata cikin Tsaka mai wuya.
Wayar Abba aka sake kira sai ya Turo wayar gabana yana fadin"Ina jin nauyin Engr Fa'iza ki dauka ku yi mgana kada yaga kamar ina masa yawo da Hankali ne"
Kaina na kara shigarwa cikin Hijabi ina kuka Abba bai nuna ya damu da kukana ba,ya cigaba da fad'in"Dauki mana Fa'iza"
Sai na dago kaina cikin kuka nace"Abba bazan iya ba. Bazan iya mgana da shi ba"
Na fada ina rufe bakina saboda ji nayi zuciyata na wani harbawa saboda yanayin da nake ciki.
Ammi ta kalleni a tsorace kafin tace"Wai ban gane ba..?
Mgana da Engr ne bazaki iya ba ko mene..?
Abba kuma shuru yayi bai yi mgana ba ammh kukan fa'iza ya gama tadamai Hankali Cikin kukan na cigaba da fadin"Abba ka bama Engr Hakuri.."
Gabadaya da shi da Ammi suka kafeni da ido shi yana min kallon Tausayi ita kuma Ammi na Rudani da mamaki.
Kafin tayi mgana Abba ya rigata da fadin"Hakurin me..?
Kai tsaye ina kokuwa da Numfashina nace"Na zabi Ishaq. Zan koma gidansa Saboda ya'yana Abba ka tayani ba ma Engr hakuri wlh ba da son raina ba ne
Bansan haka zai faru ba Wlh bansani ba"
Na karishe fad'a cikin gunjin kuka Abba yaji jikinsa ya yi sanyi Tausayin Fa'iza da Engr ya gama kassara Sauran kuzarinsa kaunar da Engr ke yi ma Fa'iza daga Allah ne, Ubangijine ya hada wannan soyayyar ba ta mutum ba ce.
Ya tuna kalamansa dazu da ya kirasa kan bata amsa wayarsa fad'i yake yi"Baban Nana ina son Fa'iza ina jin ta a raina yadda ban taba jin wata y'a mace ba, ka fad'amata tayi hakuri in Laifi nayi mata ta bari in nazo sai ta Hukuntani ammh ta yi ma Girman Allah kada ta hanani jin muryanta"
A yanayin yadda yake mganar zaka Fahimcin yanayin da yake ciki sannan zaka san mganar daga karkashin zuciyarsa suke fitowa.
Ammi kuwa mgana ma kasawa tayi baki ta bude kafin tace"Bangane ba..?
Baban Nana meke faruwa ne..?
Ta fada tana kallon Abba na neman karin bayani.
Shi ko Abba ni ya ke kallo na wani Lokaci kafin yace"Kin tabbata..?
Bana so ki yanke hukunci cikin gaggawa kina da Sauran Lokaci"
Kai Tsaye nace"Ban yi gaggawa ba Abba. Na yanke shawaran zan koma gidan Yaya ishaq"
Na fada ina kokarin danne yanayina ammh fa hawaye bai? bar idanuwana ba.
Ammi fadi take yi"Ke baki da Hankali ne..?Engr din fa..?
Ina Abba bai bi ta kanta ba zama ya gyara yana fadin"To Alhamdulillah. Allah yasa hakan shine mafi alheri zan yi mgana da Engr zan basa hakuri goben zaki tafi karofin.?.
Ina kokarin Dauke hawayena na daga mai kai sai yace"Allah ya kaimu lafiya tashi kije kin ji ko..?Allah na tare da ke Fa'iza"
Jikina na rawa na mike na fice ina Kare Fuskata Saboda kukan daya tasomin,haka na koma Daki na kulle kaina ina ta kuka wayata ma kasheta nayi gabadaya..
Sai bayan fitar Fa'iza Abba ya yi ma Ammi bayani ashar ta zuba kafin tace"Wlh wannan mugunta ce ya za'ayi bai yi mgana da Fa'iza ba sai ya kama yad'a mgana haka ake yi baban Nana..?Saboda yasan Fa'iza kan ya'yanta shiyasa yayi mata haka Engr fa ya zaka yi da shi..?
Abba ya lumshe ido kafin ya bude yace"Muna namu ne Allah na nashi kuma na Allah shine Daidai. Komawarta gidan Ishaq ba laifi ba ne Aziza,Duk kyan Sabon gini gwara Tsohon yabe"
Ammi ta karkace kai kafin tace"Wlh da Tsohon yaben nan na Ishaq gwara Sabon gini irin na Engr ko baka lura itama Fa'izan na son shi ba..?Fin karfi yayi mata kuma kana gani kai bazaka yi mgana ba"
Abba ya girgiza kai kafin yace"Ai zabi na bata kuma ta zaba ni bani da wani abu zan yi mata. Ba Hurumina ba ne"
Ammi ranta ya baci tace"Sai kayi shuru yarinya ta cutu Baban Nana..?
Wannan ba zalunci ba ne"
Abba yace"Komama Uban ya'yan nata ne Zalunci..?
Ammi ta mike ranta ya gana baci kafin tace"Eh Saboda bai dace da Fa'iza ba"
Fuu kamar iska haka ta bar masa Falon kai tsaye shashen Inno ta wuce su Hafsah na wajenta idanuwanta sun rufe ta shiga karanta ma Inno Abunda ke faruwa sai Inno tayi shuru kafin tace"Kin san shi aure rai garesa Azizatu..Gwara da Usman bai saka baki ba,in har Fa'iza ta amince da komawa gidan Uban ya'yanta shikenan Aziza abu ne mai kyau hakan suna da ya'ya a tsakani,sannan ga zumunci kuma ko Allah ma muna masa laifi ya yafe mana ballatana mu d'an adam..?mganar wannan bawan Allah kuma ai ba nisa yayi ba sai Usman ya bashi Hakuri haka Allah ya tsara kuma mu bamu isa muja da hukuncinsa ba"
Sai bakin Ammi ya mutu ganin Inno ma bata goyo bayanta ba ammh tasan wannan komen na zalunci ne,Sai ta yi fushi da Abba ta shige dakinta tana kunci tasan da Baffa na da rai shi kadai ne zai gayama Abba yaji,Ga tafiyar Fa'iza ga abunda ya faru ko siyayyan komai ma bata samu yi ma Fa'izan ba. sai da Safe da ta shigo gaisheta ta bata kudin da Abba yace ta bata ita kuma ta hada mata kayan kwaliya da atamfa da less da Hijabai wadanda bata dinka ba.
In ta tuna Fa'iza zata rasa mutun kamar Engr sai taji ma Fa'iza takaici har sai da ta mata mgana da cewa"Ke yanzu gidan wanda baisan Darajan ki ba zaki koma Fa'iza..?kada fa ki yi gaggawa kizo ki yi da kin sani"
Sai na fashe mata da kuka shiyasa ta kyaleni tare da Nana khadija da Hafsatu zamu tafi zasu weekend achan Abba na gida bai fita da wuri ba Direban sa zai kai mu har karofi.
Naje yi ma Inno Sallama ta rika yimin nasihan hakuri da rayuwa Daga karshe tace"Ki yi hakuri ki kuma barma Allah, Zabin nan da kika yi in sha Allahu Hairan ne"
Mganganunta suka d'an sanyayamin rai ammh muna mota na makure kaina a gefe ina kuka Hafsah na gaba Nana khadija na baya sai na sanya Nikab ina ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login