Showing 180001 words to 183000 words out of 288345 words

Chapter 61 - Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

Janafty   

01 Nov 2025

711

siga na ya kare.
Kamar Daga sama naga ya fad'omin cikin daki a kaina ya tsaya a gabana kere kere,Sau d'aya na kallesa ban kara ba na cigaba da had'a kudina sai naji ya zauna gefena yana fadin"Fa'iza baki ganni ba ne..?
Kai tsaye nace"In na ganka me zan yi maka..?kai ka shigo min Daki ko Sallama baka min ba"
Sai ya gyara zama yana fadin"To Salamu Alaikun shikenan"
A tsime na amsa masa daganan na bama banza ajiyarsa na lura yana so yayi mgama ya kasa sai kame kame yake yi har da tashi yana leka band'aki da kara Duba Dakin na d'ago ina kallonsa cikin mamaki kafin nace"Hala kayi ajiya ne kake nema.?.
Sai ya fara sosa kai yana fadin"A'a ina duba dakin ne sai yau na Lura yafi Dakin yaran nan girma ashe.."
Sai na yi kasake har kofafin hancina na budewa na shaki iska a kasan makoci na kafin nace"Uhm"
Kai tsaye kuma yace"Shine sai nayi wani Tunani me zai hana ke ki koma Dakin yaran nan ita kuma Zainab sai ta zauna anan tunda yafi girma kinga ita ba rayuwar mu da'ya da ita baa,akwai Danne hakki in na ce ta zauna Dakin yaran nan yayi mata karami kinga Dakinta na Abuja?
Wlh yayi biyun wannan Fa'iza.."
Daman nasan za'a zo wajen mai Hali bazai fasa halinsa ba. meyasa nake Tunanin Ishaq zai iya daidaitani da Zainab.?har abada ta fini a wajensa matsayina bazai taba zamowa d'aya da nata ba,Nagode ma da ya sa Rud'add'en kalamansa basu Rud'eni na sake bashi kaina ba.da yanzu na fi kowa nadama.
Maganar bata D'akina ce ma ta tsaya min arai,na bude baki yafi sau biyar ina rufewa sai kawai na maida Hankalina kan kirga kudin hannuna kama kansa ya yi,sai ya durkusa a gabana Lokaci d'aya yana fadin"Kin gane Fa'iza ki Fahimceni wlh ba da wata munafa nayi wannan mganar ba. Nasan ke zan iya sakaki komai kiyi min sannan zaki zauna dani ko a dakin Bukka ne,ita kuma ba kamar ke ba ce shiyasa kikaji nace haka don Allah kada ki Daukeshi a wani abu"
Ya karishe fad'a yana min uban magiya sai kawai na mike idanuwana ne suka ciko da kwallah me na zama ne.?na tabbata har abada in dai a Rayuwar Ishaq kabir korofi ne ni Fa'iza bazan taba samun daraja ba.
Gaban Wadrope d'ina na tsaya kawai na rasa me zan yi ma saboda takaici,Ina jinsa ya mike yana fadin"Kin ji Fa'iza baki ce komai ba..?
Juyowa nayi bayan na Saita kaina Lokaci d'aya nace"Me kake so nace.?ai ba shawarata kake nema ba Hukunci ka yanke sai kuma ka ke bani Umarni,ba komai kada damu ni daman ban taba had'a kaina da matarka ba nasan tafini Daraja. Zan kwashe kayana kada ka damu ka fad'amata zan bar mata Dakina na har Abada"
Na fada Lokaci daya ina kokarin wucesa na fita Daga dakin kawai sai ya Riko hannuna a fusace na juyo ina kallonsa irin kallon da na sakar mai ne yasa ya sakeni da Sauri a Shake nace"Nace maka zan bar mata dakin nawa har abada daman ai D'ofane nake kada ka damu. Hafsah daman ba zama zatayi ba Abba na nema mata Transfer zata koma kaduna yara kuma ya'yanka ne ko a soro ka zaba musu su zauna bazaka samu matsala da Fa'iza ba"
Ina gama fadin haka na fice daga d'akin domin ji nayi iskar Dakin tamin kad'an,na rasa ina zan shiga sai kawai na shige kitchen na fara safa da marwa Anum ta shigo kawo kwanuka ban ma ji shigowarta ba sai ji nayi tace"Umma lafiya..?Da sauri na goge kwallar da suka kawomin,na juyo ina kirkiro mirmishi kafin nace"Bakomai kin gama wanke wanken.?
Kai ta dagamin kafin tace"Yanzu zan wanke tsakar gidan ko Umma..?
Sai na jinjina mata lokaci daya ina fadin"Gama ki tayani zuba zobon nan in ya wuce kada su kawo wuta bamu saka ba"
Sai ta amsamin da toh Umma,Falo na koma shi kuma daidai ya fito ina ganinsa sai na juya na fita wlh bana son ma ganinsa,a kwanakin baya sai naji kamar Burina zai samu Rauni na fara Tunanin sauke kudurina,ammh yanzu na ji na samu karfin gwiwan da zan iya tunkaran komai menene tabbas ina Bukatar Sabuwar rayuwa ina son na shaki iskar yanci nima.
Gabadaya yini yayi son kara min mgana ni kuma ban yarda mun had'u ba,ga shi dai nace na amince ammh kuma Fuskata ba fara'a Da Daddare na kira Abba muka gaisa sai na masa mganar Hafsah cikin barkwancin sa yace"Ina ta kokarin nema mata Transfer Fa'i..Wlh tallahi ko kuma ba domin aure ba,da gabad'aya zan tattaraku a gidana"Sai nayi dariya ina Tambayansa Ammi yace"Tana chan ta na kwalliya kinsanta gayu gayu dai Mamam Nanah taki ta bar ma yara"Da Sauri nace"Abba ta bar ma yara ka kyallo wata yar caras"
Sai ya fara Dariya yana fadin"Fa'i Laala..aiko baku isa ku hanani kara aure ba.ku gama shafa dai jan bakin da hoda sai nayi ehe"
Ni dai sai Dariya nake yi tuni Abba ya mantar dani Damuwar da nake ciki mun jima muna mgana,Sannan muka yi sallama,Mun gama wayar kenan sai ga Kiran Nana Fatima itakam sai da taji yanayina ba Dadi tace"Fa'in mu ya ya ne.?naji ki wata so silent ne"
Sai nayi saurin ce mata kaina ke ciwo sai tace na sha mgani na kwanta da Safe zamu yi mgana da haka muka yi sallama sai kawai na kira Goggo ita har ta Tsorata cikin Tsoron tace"Fa'iza lafiya kuwa.?goma saura na Dare fa"
Ina dariya nace"Lafiya lau Daman na kiraki mu gaisa ne naga kwana biyu kin manta da D'iyarki"Sai goggo tayi dariya kafin tace"Kina raina Fa'i nasan kina lafiya ke da yaranki,hidima tayi miki yawa Fa'iza kinsan sana'ar hannu tana da wahala nasan sai hankali yanzu"Gyada mata kai nayi kamar tana ganina kafin nace"Na saba goggo ba matsala ga Anum kinsan tana gida sannan in Hafsah na gida tana taimakamin,haka ma yaran ma in sun dawo. Amir kinsan san shi sarkin aiki su shara har girkin su taliya ya iya Goggo"Sai goggo taji dad'i har sai da ta bayyana min cikin Murnan ta tace"Masha Allah Dakyau.Dama iyaye su rika tunani irin naki Fa'iza su rika koyama yaransu, aikace aikacen gida tun suna da kananun shekaru, saboda taimakon iyaye da kuma taimakon kansu a duk inda Rayuwa zaata kai su Allah yayi albarka Allah ya shirya miki yaranki,Allah ya Daukaka su alfarman Annabi muhammadu salallahi alaihi wasallam"
sai na samu kaina da Hawaye sun cikamin kwarmin idanuwana, ina amsawa da Ameen Ameen cikin jin dad'in da ya bayyana har a murya ta. kafin nace"Goggo Baba ati tana kaduna abunta..?
Goggo tace"Tana ko chan Fa'iza ta samu hutu,Inno tace bata son ta dawo ta samu abokiyar zama ai ma ginin Abban naki an kusa gamashi kila in ya kammallu ta dawo"
Kai tsaye nace"Kila ta dawon to.nima Hutu nake son nazo miki Goggo
"Dariya tayi ina jin ta Dauka Zolaya ce sai tace"Ina maraba da Fa'iza Allah ya kawo ki lafiya"na amsa mata da Ameem daganan ta tambayeni megidan da Yanayin zaman mu da Mama nace lafiya lau kamar bata gidan.
Goggo tace'"Nima naga duk tayi sanyi.Rayuwa ta gara Saudatu daman na fad'amiki watarana sai tafi ruwa sanyi a wajenki"na jinjina kai ina Tunanin yadda Mama ta zama kamar kankara yanzu,Duniya ce da mutanen cikinta suka maida ita haka.
Bayan munyi sallama da Goggo na jima ban yi barci ba,Hafsah tana Dakin yara tana karatu sun kusa fara Jarabawa Ni da Anum me muke kwance ita har tayi barci ni kuma ina faman sake sake a daran nan na yanke ma kaina abunda zai fissheni bayan na roki Allah kada ya barni ni kad'ai ya yi min jagoranci.
Da Safe wasai na tashi,Duka aikin gidana ni nayi abuna. Abun kari kawai Hafsah tamin,Sai aya data wanke ta mikamin nika kafin ta fita,ni kuma sai ta barni da Dafa zobo,Ganin yadda nayi ne ko da Safe saboda a gaban yara ne muka gaisa na Sakar mai Fuska suna watsewa na had'e raina gim ko fara'ata bai gani ba.
Mama ta aiko Anum ta kirani ina zuwa na durkusa na kara gaisheta ta amsa cikin kallona Lokaci d'aya tana fadin"Ishaq ya same ni da wata mgana. Wai zaki koma Dakin yara Zainab zata zauna a dakin ki? nace kin amince ne yace eh! shine nace sai na tambayeki"
Kai tsaye nace"Eh Mama yau zan fara ma Tattara kayana. yaran kuma duk inda ya ijiyesu daidai ne a wajena"
Sai ta muskuta tana fad'in"yaran ba matsala ga daki nan su zo mu zauna damam xaman kada'ici ya isheni kece bana so mu kara yi miki wani rashin adalci kamar yadda muka yi miki a baya,Shiyasa nace sai naji ta bakin ki,ki fad'amin in hakan bai miki ba to bai isa ba"
Sai nayi mirmishi takaici kafin nace"Bakomai Mama na amince ni daman ba mazauniya ba ce.Dakin daman ai jingina ne, Zainab ce ke da wajen zama na har abada"
Nasan bata gane kan mganata ba, sai dai nauyin baki yasa ta kasa min mgana har na fice,ina komawa Daki bayan mun gama hada zobo mun zuzzuba agoruna Anum ta jera a Frezee,kunin Aya ne zan had'a shi jira nake nepa su kawo wuta.
Anum na bar ma sharan Falo da gyaran kitchen, ni kuma na shiga Dakina na fara had'a kayana a waje daya duk abunda nasan nawane na Daukosa babban ghana d'aya gareni itama sakon kayan sallar yara aka kawo aciki daga kaduna kuma tamin kad'an sai na kira Hafsah nace in ta shiga kasuwa ta siyomin manya guda biyu
Kafin dare wardrope dina kaf ba kayana aciki Hafsah ta siyomin manyan ghana guda biyu sun isheni na dura komai nawa,aciki akwai wasu kayan da ko di'nka su ban yi ba. na Ishaq ne ban kara dinka kayan da ya siyamin ba,tun bayan auransa da zainab hatta kayan da Anty Binta ta bani na Fad'an kishiya suna nan suma na Had'a masa kayansa waje daya.
Gadajen yara daman duk ya b'abb'alle,sai nayi tunanin na basu na Dakina da wardrope din ya ishe su saka kayan su,nasu? kuma a gyara ma Anum tunda ita macece ni ba zama zan yi ba,so kayan basu da amfani a wajena.
Da dadadre suna falo da shi yana musu karatu,na fito ina kallon Amir kafin nace"Amir ku fara had'a kayanku waje daya,ka taya kannen ka su had'a nasu .Anum na fara had'a miki naki kema kije ki karisa in kun gama"
Da mamaki suke kallona ammh sai na juya zuwa kitchen ina ji suna tambayanta Umma ina zamu..?
Sai na bar mishi ya basu amsa sai kuma ya kasa ina kitchen din ya Biyoni yana fadin"Fa'iza bafa yanzu ba ne naga kina ce ma yara su had'a kayansu'
Ina juya tumatur din da Hafsah ta Dora Tafashensa akan wuta nace"Eh gwara su fara had'awan tun yanzu kada sai lokacin yayi kuma basu samu sararin had'awa ba. gwara tun yanzu kowa yasan matsayinsa"
Na fad'a ina kokarin rab'asa na bar kitchen din sai ya bake hanyar yana fadin"Fa'iza.."
Kai Tsaye na kallesa ina fadin"Na'am Ishaq"
Sai mamaki ya hansa mgana,Girata na Daga ina fadin"Bani hanya na wuce"
Ba musu ya matsamin na fice ina jin wani irin Tukuki acikin kaina Amir ne ya taso yana fadin"Umma ina ZAMU KOMA..?Ko zamu yi tafiya ne.?
Ban kallesa ba nace"Ku yi abunda nace Amir kaji"
Sai ya amsamin da Toh ammh sai jikinsu duka yayi sanyi,nan na barsu na shige Dakina ina Sauke numfashi,Adaran na saka Hafsah ta taimaka musu suka had'a kayansu itama ban bata ikon mgana ba sai dai ta tambayi yaran Anum tace"Umma bata ce mana komai ba"
Sai itama bata kara mgana ba, ammh ta kara tsorata da ganin na kara had'a kayana a karo na biyu wannan karon bata san kuma me zai iya Dakatar dani ba.
Lalle kana naka Allah na nashi Washegarin jumma'a da Safe Ishaq ya samu wayar Dr.Lawal inda yake sanar da shi an gano saka hannun nan ba nasa ba ne, kwaikwayo ne na wani abikin aikin su.Mr James mutumin osun State ne Daga office din sa sai na Ishaq,da shi aka had'a baki aka kwaikwayi saka hannu Ishaq Daga office dinsa aka fitar da wad'anan kudaden,yanzu Mr james din ya tafi gida chan Osun,abu d'aya ya rage bangaran Cibiyar Bincike ta EFCC ita zata ba da umarnin a kamo James ya fad'i gaskiya sannan ta wanke shi Daga zargi.
Da murna ya fito yana fad'a mana,ni da Mama da muke tsakar gida ita tana shan iska ni kuma ina Dafa zobo,sai na manta da abunda ke tsakanina da shi na mike ina fadin"Alhandulillah. Ka kira Abba kira Abba ka fadamasa"
Mama ko sai da tayi sujuda tana godema Allah sai kuka shi ko Jiki na rawa yace"Shima Daddyn haka yace na kira Abba..yayi ta kiransa bai same sa ba'
Kiransa yayi sau biyu bai Dauka ba nima na Ruga daki na Dauko wayata na kirasa bai Dauka ba.
Sai na Kira Ammi bayan mun gaisa na tambayi Abba tace ya tafi Office ina fad'ama Ishaq yace"kila ya shiga meeting ne. mu basa Lokaci"
Anum na gefe tace"Daada me ya faru..?
Cikin farinciki ya dagata sama yana Fadin"An gano gaskiya Anum.angano bani da hannu a satar kudin ma'aikanmu"Sai itama ta washe baki tana fadin"Congratulation Daada"
Sai da yagama juyi da ita sannan ya sauketa yana kallona Lokaci da'ya yana Fadin"Fa'iza kinga abun Allah ko..?
Sai na jinjina kai ina fadin"Allah yasa karshen wahalan kenan"Mama ta amsa da ameen ta mike tana fadin bari ta kira Binta Yaya ishaq ya hanata da fadin"ki bari mu yi mgana da Abba tukunnah"
Da sauri nace"Eh Mama gwara labarin ya kamallah Tukunnah"Sai ta gyada kai yini mukayi Duba waya ko Abba zai kira sai Dare ya kira Yaya Ishaq,kafin shi yayi masa mganar ya fara yi masa. yace sun yi mgana da Dr.Lawal yanzu nan ya kira Engr sun yi mgana shima ya ce Mr ABDULGHAFFAR ABDULBASIT BABATUNDE ya dawo Office satin daya gabata,zuwa gobe ko jibi ya sauraresa"
Nima Abban ya kirani yayi min bayanin komai ya karishe da fadin"Last friday ai muna Abuja da ni da Maman Nana mun je duba Hajiya Kudirat olamide,itace kakar Engr sun dawo gida bayan an yi mata Dashen koda,da mukaje mun samu Engr din a gida sai na kara tunasar da shi mganar aiko yana masa mganar yace a tuna masa in ya shiga office sai fara Duba Case din,balle da Engr ya fad'a masa Ishaq Inlow ne a waje na,ya? tabbatar min da ba matsala mu jira cewarsa kawai"
Da wannan labarin mai Dad'i muka kwana sai dai na Tsananta addu'a na Allah ya kawo mafita da karshen al'amarin.
Har yara na saka suka yi ta addu'an Allah ya kawo ma Daada mafita shima nace yayi ta addu'a da ikon Allah sai an wanke sa daga wannan zargin.



G
*Janafty*



[7/19, 2:47 PM] Hauwa Galadima: *KNKB2019*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

Allah maji rokon bayinsa kwana Biyu Tsakani. ranar Litini da misalin wajen sha biyu na rana ya samu wayar Abba in da yace maza ya taho kano yanzu zai had'u da Abdul'Ahad a Airport din Aminu kano zasu hawo jirgi zuwa nan Abuja.
A na nemansa a Office din Chairman na EFCC,daganan bai yi mai wani karin bayani ba. shiyasa sai ya Rude,ya fito daga daki yana fad'amin cikin wani yanayi kafin ya kara da cewa"Gaba na ta fad'i Fa'iza. Allah yasa ba wata matsalan ce ta sake kunnowa ba"
Cikin son kwantar masa da Hankali nace"Haba ba komai abunda muke fata ne jeka ka fad'a ma Mama,bari na saka maka ruwan wanka ka shirya kada ka b'ata Lokaci"
Bai min gaddama ba ya wuce Dakin Mama ya fad'a mata ni kuma na je na kunna gas na saka mai ruwan wanka Tuna murhun gawayina yana waje girki na d'ora akai,sama sama ruwan yayi zafi na sake mai nice har bayi sai da na kai masa.?
Da kuma ya shiga wankan na Lalubo masa kayan da zai saka,yana wankan sai ga yaya Abdul'Ahad ya kirasa ni na d'auka muka yi mgana yace yana kano yana Jiransa, daman ya kawo Raliya ta gaida su Hajiya ne, sai ga kiran Abba so in ya taso ya kirasa yadda zasu hadu a Filin jirgin kawai.
Ko da ya fito wankan mun gama wayar,Sai rawan jiki yake yi ya kasa natsuwa fad'i yake yi"yanzu a chan kano zamu hadu da Abdul'Ahad din?
Kai Tsaye nace"Eh mana yanzu ma ya kira wayarka na d'auka muka yi mgana,yace in ka taso ka kira sa"
Sai ya amsamin da toh fita nayi na basa waje ya shirya nasan ba shi da kudi cikin kudad'en sana'ata na kirgo Dubu Biyar na bashi Saboda nasan in dai suna tare da Abba bazai rasa kudi ba in yaje koda na dawowa ne, har ya shirya cikin shadda fara riga da wando,Sai Hula daya sanya ina shigowa yace"Ba sai na dauki wasu kaya ba ko.?
Kai Tsaye nace"Me zakayi da kaya kuma? in ma kwana ya kama ka kana da Muhalli da wasu iyalan achan ka manta ne"Sai ya sauke ajiyar rai kafin yace"Wlh duk na Rud'e ne Fa'iza"
Ina mika masa kudin Hannuna Lokaci daya ina fadin"Ka kwantar da Hankalinka babu abunda zai faru ai Yaya Abdul'Ahad yace Abba na chan shima in kaji zuciyarka bata natsu ba kayi ta ma Allah kirari da Hailala, yafi ka zauna kana wannan zullumin"
Cikin gamsuwa ya gyad'a min kai kafin ya karbi kudin da nake mikamasa Lokaci d'aya yana fadin"Wannan fa na menene..?
Nasan ya rude ne, kila ya Dauka haka zai tafi ba kudi sai na juya ina fadin"a kasa zaka je kanon.?
Sai ya Dafe kansa yana fadin"Shaa..Fa'iza wlh na manta"ina jinsa yana bin bayana har Tsakar gida Inda Mama ke jiran fitowarsa.
Sallama yayi mana ya tafi mama na sakamai albarka da fatan Allah yasa mu dace. ni kuma mun rabu kan sai ya kirani naji yadda ake ciki.
Mun yi masa fatan sauka lafiya tare da Fatan Allah ya tsaresa ni da mama Anum bata san tafiyarsa ba taje kai min nikan Aya,sai da ta dawo nace tayi ma Daada addu'a ya tafi Abuja.
Tafiyarsa ba Dad'ewa Yaya Abdul'Ahad ya sake kirana na fad'a masa ya kama Hanya sai yace ya yi ta kiransa bai Same shi ba,yana ga network ne, bari ya Saurareshi.
Mu dai ya tafi ya barmu da zullumi,bayan ya isa kanon mun yi waya yace suna Filin jirgi yanzu zasu tashi zuwa Abuja .
Daganan shuru bamu kara jinsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login