Showing 1 words to 3000 words out of 157081 words

Chapter 1 - Royal Politics Book 2 Complete Hausa Novel

Ramlat   

07 Nov 2025

10

[8/26, 5:39 PM] Ramlat Manga41: 🌲🌳🌿☘️

*DA MAGANI A GONAR YARO!!*

*08089965176*

*07084653262*

*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*

*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*

*07084653262 ko*

*08089965176*

*SIYAN NAGARI!!!!!!*

*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*

01

Idan na ce Parlourn bai rikice ba nayi karya , domin tunda nake a rayuwata ban tab'a ganin mai babbar daki a haka, sauran matan gidan rayukansu a b'ace yake, idan nace ban muzanta ba nayi karya. Matsawa wurin mai babbar daki nayi cikin wani irin gigita, ta janyo ni jikinta tana kallonshi a karo na babu adadi, wani irin kallo take mishi wanda uwa ce kaɗai zaka samu da wannan fahimtar, tunda ya haɗa idanu da ita zai kamar an zuge mishi bakinsa,ya taune lips dinsa, yana jin yadda kukan Nadiyyah ya cika parlourn ya kuma kalle ni yadda na kifa kaina a kan cinyar mai babbar daki, nayi lumo tana shafa bayana. Duk sai ya ji ranshi yana kara tunzira. "Ranka ya dade, kafin ka yanke hukunci ka fara nazarin abinda zai faru, don Allah kada ya yi abinda zaka yi danasani, wannan shine sauran binciken da ka saka ni yi akan abincin da na kitchen din Fulani Babba da na kuma wurin Nadiyya da ta ci, sannan ga wanda Ijlal tayi, sannan evidence na karshe da na kawo ita ce, Wildat!" Ya turo ta ciki ta zube akan gwiwarta. "Me ya faru?" Cikin shashekar kuka ta ce mishi. "Barazana suka min idan nayi magana zasu kashe ni!" Kurawa Wildat idanu nayi kafin na koma na rufe fuska na a kan cinyar mai babbar daki, "ina jinki!" "Talatulle ce ta saka ni na dibo kayan girkin Fulani Babba ta amsa ta kuma ce sai ta kashe ni idan nayi magana, ba iya nan ba duk abinda yake faruwa talatulle ke sakawa ana yi, wnada da a binne ko wnada da zuba a wuri takawa ya tsallake."

Kallon Faruq yayi, shi kuma yayi kasa da kai ya ce mishi. "Talatulle ba daya daga cikin gidan nan take ba, shigowa take cikin gidan nan wurin Madam Nadiyyah, ita take kawo mata kome da sauransu. Sannan na saka ayi bincike akanta."

Duk azabar da take ji na hannunta sai gashi ta bude idanun tana zaresu kamar zasu fado. "Ni kuma Faruq? Idan kana son Zainaba da Ubangidanka na cancanci ka yi min sharri?" Table tap din hannunsa ya ware ya ciro drive ya isa gaban tv parlourn. Ya haɗa sannan ya koma gefe ya kunna, shigar talatulle gidan, da abinda ta bayar Nadiyyah ta shiga cikin gidan da shi, da lokacin da talatulle ta bada abu Nadiyyah ta shiga bangarenshi da shi, da lokacin da ta kara kawo abu a kwalli aka yi bangaren Zainaba da shi.

Kallon kowa yayi a parlourn yana jin wani irin abu a ransa, ya kalli Mahaifin Nadiyyah. "Matar da na sani bata da wannan nufin ashe wata rana zaki iya wannan kasadar? Waye ya kawo miki abincin da kika ci?!" Wani irin kuka ta sake tana nuna ni, kasa magana nayi na nuna kaina. "Ita ce ta bawa Ijlal ta ce ta kawo min!" Dafe kirjina nayi na ce mata. "Ni ce na kawo miki abinci? Nadiyyah ni zan kawo miki abinci?" Cikin hargowa ta ce min. "Waye ya bawa Ijlal?" "Ijlal ce ta dibi abincin a wurin Fulani Babba, sannan ta amshi kayan girkin da na bawa Talatulle, wannan iya bin na sani!" Wani irin cafkar kafarta Ismaha tayi da ƙarfi, sai da ta saka ihu tayi wani doro, kamar zata cinye Wildat, "Isma!" Na kira sunanta, da gudu ta haura cinyata, tana lashe min hawayen da yake zuba a idanuna. Sannan ta kwantar da kanta a kan cinyata.."Girkin da nayi iya shi da Ilham na zubawa, ni da Wildat ko ci bamu yi ba na mana sabon girki, Nadiyyah a baya ban baki guba ba sai yanzu?"

"Zaki ce haka mana, tunda kina jin haushina don Allah ya bani haihuwa ke ya hanaki!" Wani irin kuka ne ya zo min, na ce mata. "Shi wannan cikin kuma da yake jikina ya zaki yi da shi?" Ba ita ba hatta Fulani Kubra, Fulani Balkisu, Fulani karamar, Jakadiya Iyaami da take bakin kofar, wani irin rangad'a gud'a tayi domin tun da Zainaba ta biya mata umara ta dawo, ta zama hannun damar Mai Babbar daki, abu ba abu ba zata fara kod'a Zainab. Yadda na mike tare da tsayawa a gaban Nadiya da na taka, na kamo hannunta na daura akan cikin nace mata. "Kin gamsu ba zan iya cutar dake akan kin samu ciki ba? Kin yarda ba zan cutar dake ba? Ni ba zan tab'a cutar da kowa ba, hatta barin muku Yaya da nayi don ku saka a ranku bani da lokacin fada akan shi, daga lokacin da na juya akan shi baki isa kome ba, Nadiyyah da nasan zaki iya min irin wannan abin da na jima da yakarki amma ba kome ki je Allah yana nan, ya kuma baki wani rabon ni dai ban bude ki da sharri ba ke da kika nufe da shi Allah ya sakawa duk wnada aka zalinta! Na godewa Allah da bai rufe lamarin ba sai da ya kawo mafita!" Na juya tare da barinta nan a zaune rike da hannun da ya kumbura sumtum, wani irin tashin hankali zukatar mutanen da suke parlourn suka shiga rud'ani, tashin hankali. Firgici, da wani irin yanayi da ya kasa boyewa akan fuskar wasu Ni kan daki na wuce na zauna suna kuka me yasa ni nake fuskantar kalubale daga wajen mutanen da na kyautata musu? Gyara murya yayi cikin natsuwa ya ce

"Ni Salmanu Faris Attahiru Shehu Yayari, na saki Nadiyyah Jamil Chiroma, saki ɗaya Zainab kuma ta koma gidansu sai na gama binciken abinda ya faru!" Yana fadar haka ya juya zai bar parlourn, Mai Babbar daki ta ce mishi. "Idan har da gaske adalci zaka yi, ka fara daga kanka, tambaya ɗaya nake da da shi akanka, Malam Salmanu Faris, ita mata ta ukun meye makomarta?" Juyawa yayi cikin girmamawa ya isa gare ta sannan ya durkusa a gabanta. Ya daura hannunsa kan nata. "Duk abinda kika yi fata ni xan aikata?" "Ban ce ka sake ta ba, ban kuma ce ka mata kome ba. Amma yana da kyau ka kula da kanka da rayuwarka domin kada tarihi ya maimaita kansa." Juyawa yayi ya kalli kofar dakin. A hankali ya mike ya bar parlourn, Nadiyyah kuka take tana jin wani irin ciwo da kishi. "Dad ka ce ya dawo ni, nima cikin zai kara min." Ko ba kome yau daya Salmanu Faris ya goge takaicinsa a zuciyar Umminsa. Gaban mai babbar daki ta nufa tana faɗin. "Ummi ki yafe min abin da nayi don Allah ya dawo da ni!" Murmushi tayi ta ce mata. "Ni ba zan mishi dole ba, domin ina matuƙar son ganinshi cikin halin lafiya da kwanciyar hankali, kece Babba don ya kula da sauran matan alfarma kika musu, duk wacce zai so a bayan ke ce, duk wacce zata zo a bayanki ce. Idan da kanki yana ja yadda zainab take watsi da lamarinsa da haka kika yi da kin barwa sauran matan hauka akanshi amma bakiɗaya kika nuna ke karamar mace ce, ke ba zaki iya gani ki dauke kai ba, ke ba a tab'a miki abu ki yi hakuri ba, kune mata gorin haihuwa Nadiyyah ina cikin yake? Ita Yar da kike tare da ita kin san lafiyarta? Cikin gidan nan da muke kowacce mace tana kiyayye kanta da Yaranta, domin tsoron kada a cutar mata da su, ai na gaya miki satin da ya wuce yayyatawa da faɗin cikin namiji ne da ke an gaya miki za a ganki a bar ki ne?" Wani irin tsoro ne ya kara cika mata zuciya. Ta fashe da kuka tana faɗin. "Zainaba ta ce na kula da bakina mai yasa haka?" "Allah ya baki lafiya!" Daga haka mai babbar daki ta bar parlourn, ihun Nadiyyah ya kara jefa ni cikin tashin hankali mara iyaka, na tsinci kaina da yi danasanin bayyana cikina, amma ganin yadda Isma take dungure a jikin cikin, sai naji zuciyata ta samu kwarin gwiwa, yadda magen ta makalewa cikin kamar da ita na same shi. Shigowa dakin Mai Babbar daki tayi, ta zauna a gabana bayan ta ja stool. "Ki yi hakuri!" "Ba kome Ummi!" Na fada ina share kwalla. "Gobe xan tafi unguwar Malamai na gaya musu halin da ake ciki kada su ji labari daga sama." Gyada mata kai nayi ina shafa Isma, "ita dai magen nan , tana tayaki kishi dazun na ga yadda take hararan shi. Tabbas ya ce zai miki wani abu zai, ba zai kwashe ta dad'i da ita ba." Kamar ta ji abinda mai babbar daki take fada, ta sauko daga cinyata ta nufe ta, tana wani mata dungure irin na jin dad'i din nan, daukarta mai babbar daki tayi, tana shafa bayanta. "Kiyi hakuri ki yi hakuri shi rayuwar Aure kana ganin abubuwa dayawa amma idan kayi hakuri gaskiya zata yi ranar ta, sannan nayi wani tunani zan cire Wildat a daga ɓangarenki, akwai jikar Iyaami, Nana Asma'u sai ki zauna da ita ko miko min wani abu yi zaka, domin bana son ki koma wancan gidan sai an gama ginin tsohuwar ganuwa. Lokacin kin sauka lafiya."

"Ummi ya ce zai dawo da ni ne? Cewa yayi na tafi sai ya nime ni?"

Murmushi tayi tana faɗin. "Ai ba zai tab'a sake ki ba, domin ba zaki saku ba ke matar rufin asiri ce, idan ya sake ki sai yayi yawo hannu a kai!" Ta fada tana murmushi, "ku huta!" Ta fada min, a shagwab'e na ce mata. "Taya xan huta ina jin yunwa?" "Wannan cikin da alamu akwai matar sarkin noma ko shi kanshi Sarkin noma, amma wannan cin banda Mijina jarumi ne ya koya min jarumta da nace a wuri gidan Hajara da Asma'u ba zan iya da ku ba, haka gwamnatin Zanzabiran ba zata iya rike ky ba, sai gwamnatin tarayya." Dariya na saka mata ina faɗin. "Ummina Mijinki jarumi, itama kishiyarki jaruma ce idan ta zo zaku ganta!" "Tow Uwar zamani!" Rufe fuskana, tana fita sai ga Sailuba da tiren abinci, ta ce min. "Uwar dakina, Allah ya kad'e na gaba ya sauke ki lafiya, ki yi hakuri." Ta zauna tana buɗe min kwanon, isma kuwa ta shiga zagayeta tana shafe jikinta a jikin Sailuba na ce mata. "Isma tana miki godiya da ciyar da Mamanta!" "Ai ban tab'a ganin mage mai hankali kamar isma ba, bari na kawo mata nata!" "A'a barshi ga kwanonta!" Na dauko yar karamar bowl da nake saka mata abinci tana gamawa zan wanke na ajiye mata tow ko da na koma can na ajiye mata kwanon nan idan nazo da ita nan zata biyo ni, kuma zan bata. Fitowarmu na barta a gida, amma da aka hautsine parlourn na ga shigowarta. Zuba mata abincin nayi, ta fara ci kafin ta kalle ni ta cigaba da ci, nima na fara cin abincin ba sai na ji kamar an shake min wuya na, wani irin tsalle magen nan tayi tare da hawa kaina ta tsaya cak. Tana wani irin mikewa da doron da tayi a kaina, na ji kamar an sake min kaina, ta sauke ta zauna tana cin abincin, yadda na cirewa Isma dan kwalli shine goran ruwan tayi ta zagayawa alamar na dauka na sha, dauka na sha itama ma zuba mata. Ina jin hawaye na shirin zuba min.."Isma na gode da zama a tare da ni!" Na fada ina sha bayanta, har muka gama cin abincin sannan ta fita zuwa kitchen tana ta zagaye Sailuba, nufo dakin tai ta samu ai mun gama ne. "Kin san magen nan kirana tayi? Ta je kitchen sai zagaye ni take shine nace ban sani ba ko kirana kike?" "Isma kenan,mun gama cin na yanzu sai an jima kuma!"

Tuni na manta da wani mutum wai mun yi rigima da shi. Zama nayi na jingina da allon gadon, wayata tayi ƙara kiran Bilqis ne dauka nayi. "Fulani Babba da gaske ne?" "Idan baki yarda ba ko ki gani!" "I can't wait Fulani da ciki!" Dariya nayi mata, kusan kira babu wanda ba ayi min ba, haka har wurin isha ina kwance a daki muna chat da Yeemar nake gaya mata batun cikin dariya tayi sosai sannan ta ce min. "Sannu bari zan zo na ga cikin nan tunda na fita takaba!" "Har kin yi wata huɗu da kwana goma?" "Hmmm wata hudu da sati uku nake nima!" " Ke watannin cikin kusan daidai da rayuwar Yazid ne fa, nima next week zan cika 5month amma kin ga cikin kamar ba cikin fari ba, kuma na ga cikin Ammy bai miki girma haka ba!" "Alhamdulillahi Ubangiji yasa ki haifa masa yan biyu!" "Ke dai!" Na fada ina jin tsoron cikin yan biyu wasa ne, da sallama ya shigo dakin lokacin ina cin apple, ni fa cikin ya hanani zaman lafiya da bakina, domin ko me nake akwai abin tab'awa a gefena. Wata yar rigar shan iska ne a jikina, ya ja stool ya zauna. Yana kallon yadda gashin kaina ya sauka a kafadana, shima kalaba ce wanda nayi da kaina kafin faruwar lamarin. Shiru ne ya maye gurbin shigowarshi, amsar wayar yayi sannan ya danna wayar ya kashe yana kallon yadda na nutsu ina cin apple. "Ke ba zaki tab'a zama baki ci wani abu ne?" Kallon Isma da take kwance nayi na shafa kanta na ce mata. "Tashi ki kira min Sailuba idan ta gama ta kawo min ina jiranta!" Sai da tayi kamar bata ji ba, kafin ta yiwa wani mika sannan ta sauka a gadon, ta nufi waje. Wayarshi ce tayi ƙara ya duba tsaki yayi ya mai da aljuhunsa. "Tun yaushe cikin nan?" Sallamar Sailuba na amsa sannan nace mata ta shigo, a tire ta saka abincin, dumamen tuwon dawa miyar auki ne, shi nasa aka kara dumammin. Tana ajiyewa na ce mata.."Na gode tunda na ga Isma nace nasan kece kika aikota!" Murmushi nayi nace mata. "Na gode sosai yar albarka akwai hankali!" Shi kanshi yayi mamakin yadda take iya isar da sakon da zan gaya mata, haka na zuba mata abincin ta juya ta koma wurin kwanciyar ta zauna tana kallonshi. "Ki cewa magen ta bar kallona!"

"Isma bar kallon Abba!" Ka fada mata, kwantar da kanta tayi , ta rufe idanu. "Ba tambayarki nayi ba?" Sai da na barbad'a yaji, na zuba loma mai kyau na ce mishi. "Kayi lissafi yaushe ne haduwarmu na last!" Na kara zuba loma da kyau, ina jin yadda cikin yake wani irin juyi. Shafa cikin nayi cikin yanayin farin ciki na ce.."Isma mutanen ki suna murnan na kawo musu tuwo!" Mikewa tayi ta dirko tare da hawa cinyata ta daura kanta a jikin cikin. Wani juyi cikin yayi itama kuma ta juya da ƙarfi, har zata fado, na tare ta "Zainab mai kika mai da ni ne?" Ban kula shi ba na cigaba da cin abincina, ina gamawa na mike da kyar na wanke hannuna a toilet, juyawa da zan yi na ganshi a bayana. Gabana ne ya fadi. "Malam bani hanya Please!" Na fada ina matsawa gefe. "Ba zan matsa ba sai kin gaya min me yasa kika boye min cikin jikinki?" "Saboda haka nayi niyya!" Na fada ina murmushi, don yanzu babu abinda Yaya zai yi ya bani haushi. "Zo ka fita a dakin!" Daga ni har shi mamaki muka yi ya aka yi Mai Babbar daki ta san da yana dakin, Isma na gani tana wani goga jikinta a kayan mai babbar daki, sake baki nayi ina mamakin anan take kwace yaushe ta fita? Mikewa yayi yana faɗin. "Ummi taya tana da ciki bata gaya min ba har da gudummawar boye min? Ko!" "And so what don ba a gaya maka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login