Showing 54001 words to 57000 words out of 157081 words
kuke min kara idanu rufe Allah ya rufa muku asiri ya kara rufa muku asiri duniya da lahira Ubangiji ya shirya muku Yaranku da sauran na al'ummr musulmi ku yi hakuri na gode sosai da kaunar da kuke nuna min 🎉💓💕🥰*
Shafa bayanta yake yana murmushi yayi ya ce musu. "Duk abinda zaka ga ya bawa Zainab tsoro da kuka kasan yafi karfin zuciyarta ne! Duk da rashin son maganarta amma yau tana fadar yadda ta fuskanci rayuwa kasan ta ga abu!" Ya fada yana gyara mata kwanciyarta,.jan kujera yayi ya zauna yana kallonta, yaki yarda ya juya ga kowa balle har su ga hawayen da yake zuba daga idanunsa, abu biyu yake yiwa kuka ciwon da take ji, sai zafi da kishinta da har wani ya iya kallonta ya furta yana sonta, ita kanta ta ji ciwon haka balle shi. By now ya kara sanin yadda yake kaunarta itama kuma take kaunarshi da dukkan zuciyarta take son rayuwa da shi. "Ko zaku dan bashi wuri ne!" Faruq ya fada yana mai cewa su bashi wuri yasan shiru da Ubangidansa ya kuma san abinda yake, haka yasa shima ya fita ya bar dakin, bayan ya tsaya a jikin kofar, yana jin wani irin yanayi mara daÉ—i.
***
Gud'ar da Jakadiya ta rangad'a a cikin gidan ya fito da sauran matan gidan, suka fito da gudu suna tambayaarta. "Lafiya Jakadiya Iyaami?" Ijlal ta fara tambayarta, Nadiyyah da take sama ta ce mata. "Ke Old witch me kike bukata?" Ikram ta ce mata. "An samu Ikhlas ta haihu ko?" Yadda tayi maganar duk da bata sani ba, amma tasan zuwa yanzu wannan ne kawai zai tabbatar mata da cewa abinda ya tambaya gaskiya ce. Busar Algaita da bugun gangan da ake Jakadiya Iyaami ta fara rawa tana faÉ—in. "Maula ta sidi maula ta Balarabe, Maula ta Allah da Annabi, Ayiriri Fulani Babba ta haihu an samu Yara hudu, maza biyu mata biyu." Saura kiris Nadiyyah ta fado daga sama saboda tsananin kaduwa, yayinda Ijlal ta dafe kirjinta, Ikram kuwa wani irin duhu ne ya mamaye ilahirin ganinta, "ba daya ba?ba fa biyu ba? Ba uku ba? Hudu rus?" Inji Ijlal tana mai juyawa hanyar É—akinta ta haura sama, a lokacin ta isa wurin wayarta, kiran Munirah ne ya kai goma sha biyar, tana dauka ta ce mata. "Don me na biya ki, ki gaya min abinda yake faruwa da cikin Zainab?"
"Kina tsammanin saboda haukarki sai na gaya miki kome akan Kanwar tsohon saurayina? Ke ji Mijinki na turawa kudin da kika turo min, Iyayena suna da kudinsu da karfinsu, sun dauki nauyin karatuna tun daga karamar mataki har zuwa degree da master saboda ke sai na basu Kunya? Ni ba mayyar kuÉ—i ba ne. Tunda ko mijinki da na tura mishi kudin shima sadaka yai da shi, don haka idan kika kara kirana akan banza kudirinki zan hada ki da yan sanda su shiga lamarin banza mahaukaciya kin same shi da matarshi kina hauka kamar ita ce ya rabi ki da Mijinki!" Ta kashe wayar, wani irin mutum ne Salmanun Faris? Wani irin tsoronsa ya kama ta dama yana sane ya kyale ta? Me yake nufi da ita?
Ikram kuwa Aojanah ce ta bayyana mata a madubi. "Me yasa baki gaya min abinda yake faruwa ba? Me yasa kika yi shiru? Kin ga azabar da ya bani?" Wani dauke kai tayi tana faÉ—in. "Ke ba mace bace? Taya zaki kasa samun kasan? Wannan shagon da kike gani ni kaina ba zan iya samun damar tab'a shi ba, domin akwai wata wuta da take fita a jikinsa ko sau daya kika yi sanadin da wutar ya daina fita a jikinsa zan baki mamaki, yana wata irin abu da duk lokacin da na isa gare shi nake ji kamar zan kone, shi wannan ba gama garin mutane ba ne, ko wannan da yake yawo a bayansa bazan iya cutarwa ba balle ita Awatif din. Don haka ki nutsu da kyau ki nimo mana wata mafita da hanyar."
Tsaki Ikram tayi tana faÉ—in, "Ya zan yi yanzu? Ya fara gano wani abu kuma ina kyautata zaton idan ya gano manufar da yasa nake tare shi zai kashe ni da hannunsa, duk da shi din bai kai abinda Malam Junaid yayi min ba, ashe amfani da ni yayi ya cimma kudirinsa da na yarsa!" Murmushi ta jikin madubin tayi tana faÉ—in.."Dama taya zai tsaya miki har ki samu mijin yarsa? An ce miki baya kaunarta ne, kamar yadda kika yi amfani dashi ya shigo dake haka yayi amfani da ke ya kafa yarshi kamar yadda ake kafa kusa a jikin bango. Haka ya kafa ta babu wanda zai iya cire ta cikin sauki, karin dadden shine ya kara bawa yarshi mafitan da kowa zai ji tausayina. Balle kuma yanzu da ta haifi maza biyu!" Murmushi tayi tana kallon Ikram.
Shiru dakin ya dauka domin dai hankalin kowa ya tashi.
***
Karfe uku na yamma na farka ina sauke ajiyar zuciya, tare da kallonshi yana zaune a gabana. Shafa hannuna yayi yana faÉ—in.."sannu zaki shiga ban daki ne?" Gyada kai nayi, sannan ya cire min karin ruwan da na gani, ya dauke ni zuwa ban daki hada min ruwan zafi ya taya ni na cire kayana sannan na shiga ruwan zafin yana mai gasa min jikin da towel yana min sannu. Har ya gama min na kama ruwa bayan nayi fitsari, fita yayi ya dauko wasu kayan ya kawo min na saka, sannan ya dauko ni cak ya dawo da ni dakin ya gyara ban dakin,.sannan yayi alolanshi ya gabatar da sallah la'asar domin tayi, ina kwance yana Sallah, Maluma ta shigo Faruq da Umma tare da mai babbar daki suka shigo da Yaran, sai lokacin na tuna da su wallahi. Ashe har xan iya mantawa da su. "Mun ga ta kanki kike baki tunanin su, shine muka kawo miki su ko kin tuna inda Uwarsu take mu kai mata?" Murmushi nayi nace musu. "Tow mai xan basu?" Motsin da Yaran suka yi yasa ni jin wani irin motsin da nonona yake yi, mika min Ayaat Faruq yayi yana faÉ—in. "Little Hajjah sai kuka take tayi fa." Amsarta nayi ina kallon ta. Damkar collar din Faruq Yayi ya kai shi waje yana faÉ—in. "Wuce ka ba wuri." Dariya ya saka bayan ya ja kofar dakin ya rufe. Ya gaida Maluma yana kallon mai babbar daki ya ce mata. "Kin tafi gida kuwa?" "A'a ban tafi ba ina jiran idan ka gama barci ka zo mu tafi!" "Taya ni da Aminiyata Tarasulu kace ba zan shiga ba? Yan Umaru Faruku kana son ganin Annabi kuwa? Wannan ita ce Tarasulu Aminiyata ce ya kutdakut gaskiya Sarki Salamanun faransa bai yi dace ba don ka sauya halinka!" Ta tura kofar tana jan hannun Tarasulu. "Yawwa ai ko naji ashe Salamanun faransa yana nan, tow Allah ya maka albarka, ai naji yadda kayi ta niman yar nan! Ja'ira sannu kin ji ya kika ji da hakurin rashin Ibrahim Tauhidinki dai an kashe miku shi ranar da kika b'ata, ai mutanen nan azzalumai ne babu irinsu, wallahi suka zarge Yaron nan waye ya sani.ko uwarsa ce. Tunda ba mutunci ne da ita ba!" Salatin da Umma ta saka na fado daga gadon daga ni har babyn, Allah ya takaita Babyn Ubanta ya tare ta, ina ga da ta mutu a yau din, jini ne ya balle min. BakiÉ—aya sarkewar hakori ya kamani, haka Mai Babbar daki ta saka aka ciro wani cokalin roban da yake cikin gwangwanin madara aka hada da audugar pampas aka tusa min a bakina domin na taune harshenta. Haka aka kira Doctor Munirah suka tsaya a kaina.
Ni kaina nasan na wahala a rayuwata amma ban kawo zan rasa aminina dan uwana, ban tab'a ganin inda ka ayi irin wannan zaluncin ba, ita kanta Hajjah da tasan ban san da labarin ba, na rantse da Allah ba zata gaya min ba, bata sani ba sai abin ya dame ta. Wasa wasa sai da na kwashe kwana uku masu kyau kafin na dawo hayyacina, da wani irin ciwon kirji. Wanda tun farkon sumar da nayi Doctor Andrew ya gaya mishi. "Ka kula sosai da ita domin zuciyarta ya tab'u sosai. A guji abinda zai sakata damuwa ko kunci a nisantata da b'acin rai ko damuwa, sannan tayi ta shan magani in sha Allah zata samu sauki kuma zata iya rabuwa da ciwon!" Lokacin da na farka da kuka na farka ina kuka ina karawa nace musu. "Wallahi bai mutu ba, yana nan ku ce min karya ne, ku ce ya dawo xan bashi dukka abinda na mallaka ba iya dubu ashirin ba, Yaya ka bashi kome yake so. Maluma ku kira min Tauhid bai mutu ba!" Sai a lokacin mutuwar ta dawo sabo fil nayi kuka nayi kuka na ji tausayina Mommy Turai domin yadda take son Tauhid ko Iram albarka, lokacin da Iram tazo tana daga bakin kofar tana kuka itama, mika mata hannu nayi Yaya ya shiga tsakaninmu.
"Ki yi hakuri don su Abba nake barinta zuwa nan, amma bayan nan bana kaunarta. Tana sane da abinda ya faru amma tayi shiru don zalinci, yaushe zaki yi hankali da mutanen nan? Basu kaunarki basu sonki kowa good opportunity yake jira akanki yayi amfani da shi. Please yadda na bar kome dominki, ki yarda ke nake bukata a rayuwata please ki goge kome ki kula min da zuciyarki domin ita ce abar bukata a Yanzu ba kowa ba!" Sannan ya koma ya rufe kofar ya dawo ya dauko abin sukar nonon, haka yayi ta zuka har ya saka su acikin wani boxs, ya saka a jikin Charge, bayan minti goma ya cire ya buÉ—e kofar ya mikawa Maluma suka kai can inda Yaran suke."Yaran suna tare da Isma taki barinsu, sannan akwai masu kula da tsaron kofar da suke. Yaran suna cikin halin lafiya da kwanciyar hankali, burina ki yi hakuri da kome."
Kunun madara ya zuba min ya saka cokali yana bani harshena har lokacin bai warke ba, jikina da ciwo amma na zuciyata tafi koda yaushe ciwo, yadda yake bani labarin abinda yaran suke yasa hawayen da nake yi ya tsaya, sannan ya cigaba da bani kunun,a takaice sai da na shafe kwana goma a gadon asibitin kafin aka sallame ni,zuwa gidan Iyayena a wannan karon Maluma ta bukaci haka domin kuwa ita É—aya tasan yadda take tsoron masarautar Zanzabira, tunda muka shigo gidan da aka kawo ni a kan keken marasa lafiya, sabo Yaya ya saya min domin ya taimaka min da yadda zan na dan yawo a dakin, don har lokacin kafaffuna suna ciwo. Ashe wai gagarumin suna suka shirya, haka yasa aka cigaba da shiri sosai gidan mu har jami'an tsaro aka saka, Yeemar ita ce a kan kome sama da kasa ba zama.
A can fada ma manyan dattawan fadar sun zo har gidanmu, gaishe shi da kyaututtukan ban girma da daraja. An kawo musu Yaran sun gani kamar su sace su. Haka suka tafi suna min ta'aziyar da ko yaya ka tuna min sai nayi kuka. Ina jin kamar laifina ne da ya mutu ni ce ma sanadin mutuwarshi.
Ahalin Yayari sun zo barka, kowa ya zo da burin ya dauki Yaran amma Isma ta haka sai dai a kawo gadonsu ka gansu amma ba dai ka tab'a su ba,, wannan yasa hankalin kowa ya kwanta ranar da na cika kwana biyu da dawowa, Ijlal da Ikram suka zo tare da jagorancin Faruq, ya kawo su ina zaune a parlourn ina shan ruwan zafi, aka kawo tunda suka zo Isma taki zama sai zagaye gadon yaran take. "Me yasa take haka?" Murmushi nayi da harshena da ya cika min baki na ce mata.."kin san idan bata yarda da kai ba haka take, sannan idan akwai abinda yake ranku, ku ajiye shi domin zata iya kaiwa mutum farmaki!" Na fada ina cigaba da kallon tv parlourn, Faruq da yake ta hawa jikinshi tana tsalle ta dirka akan gadon.."Kina nufin haka zai hana ayiwa yaran wani abu ne?" "Ai suna cikin kariyar Allah, tun suna cikina nake musu addu'a duk abinda ya faru da su Ijlal dama can rubutacciyar al'amari ce, ban haife su don na boye su ba, amma idan hauka tasa mutum ya tab'a min Yara zai gane Allah da girma yake, domin xan dauki kome amma ban da wasa da Rayuwar Yarana, tunda ban shiga rayuwar kowa ba!;" "Fulani Babba zamu tafi ya ce a gaya miki za kawo sha biyu da ragu huÉ—u, Yarima Salim Attahiru Shehu Yayari ya bada raguna hudu, Mai Bauchi ya turo da guda biyu, Alhaji Mamman Abba yayari ya turo da saniya, sai dattawan fada sun sayi shanu biyu wai ina za a saka miki idan kuma za a kawo duka ne sai ki gaya min an jima a kawo!"
"Ina zan kai waÉ—annan dabbobin, kace ya san.yadda zai da su don Allah kada a kawo mana kome sai ana jibi naji zai su yi babu sai a yanka saniya daya da ragonan hudu, sauran ya kai gidan gonarshi. Sannan kace ya ambaci sunan Allah ya kai mun su can!" Daga haka na koma cigaba da zamana, jikin Ijlal har wani rawa yake jin irin wannan abin duniyar da aka tarawa Ikhlas da Yaranta, kai Innalillahi wainnalihir rajoun, haka suka bar gidan zuciyarsu cike da mugunta, suna shiga cikin gidan Ijlal ta gayawa Nadiyyah abinda aka yi ihu tayi ta rufe ijlal da mugun duka domin ita ta mata sanadin cikinta sai yanzu abin zo mata. Tayi ta kuka tana faÉ—in. "Yarona kika min sanadin shi bakar munafuka kin zo kina gaya min abinda zata samu sai na kashe kowa wallahi!" Dakyar aka raba su, tana shiga bangarenta ta kira shi tana kuka tare da tambayarshi abinda ta ji, ya share ta sai tayi......
*08130269641*
5921536136 ramlat Abdulrahman Manga Moniepoint 500₦
[8/26, 5:37 PM] Ramlat Manga41: 21
Bai da niyyar shiga cikin tsohuwar ganuwa, amma yadda Nadiyyah take mishi ihu ya hasala shi, har shi zata kira ta gaya mishi wani abu akan Matarshi, dama cike yake da ita yadda ta wulakanta mishi Zainaba lokacin haihuwar Princess shine don bata da kunya zata kira shi ta mishi tana zancen banza. Lokacin da ya isa gidan tana can tana cika ita a tunaninta yadda bai kulata ba, idan ya zo ai hakuri zai bata ya ce mata wani abu, sai gashi yana fada kamar zai rufe ta da duka har da gaya mata gori da kiranta butulu sannan ya gaya mata dukkansu, yasan dalilin zamanshi da su, ya kara da cewa.."akwai ranar da zaki yi kuka da abinda kike aikata, kowa ya je ya mata barka, amma ke dake zuciyarki akwai ciwo a cikinsa shine kika ko zuwa ina sane dake kyale ki nayi kawai akwai ranar da zaki yi kuka da idanunki!" Banza tayi mishi ya fita yana fada har yana gaya mata."idan akwai garken dabbobin da zan mallaka sai na bawa Zainab da Yaranta, hakurin da tayi Allah ya saka mata da abinda baku tab'a tsammanin ba, wallahi na rantse da Allah wata rana zaki yi kuka da idanunki zaki yi kuka sosai, ki kuma saka a ranki Allah ba azzalumin sarki bane sai wnada ya zalunci kansa!"
Daga haka ya bar parlourn, washi gari, bangaren Zainaba masu aiki suka zo suka yi gyara tare da saka kayan jarirai, Bilqis da Daulah suna kai tare da Kubrah aka gama, Ilham ta kira su tana ihu an bata zata zo. Kowa sai murna yake, gashi sunan da zaman wankar ana ta rokon Maluma ta barta ta dawo dakinta, ita dai bata ce kome ba, shima Angon karnin sai bin Hajjah yake tana gaya mishi ya kwantar da hankalinsa. Daga karshe Maluma ta kira Mai Babbar daki, ta gaya mata dalilinta na rike Zainab tayi arba'in, kuma bata ga illar haka ba, asalima ta nuna ita wacce da ta san zafin nata, don haka ya bashi hakuri ayi sunan a fada ana gobe sunan za a kawo Yaran da uwarsu ayi sunan bayan suna a mai da su gida wanka. Maluma ta amince kuma ta yarda.
Yaran da yake har riga-kafi anyi musu, abinka da Yaran gwani. Gwajin lafiyarsu sai da aka yi, ga wani irin kulawa da suke samu.
***
Ana jibi suna aka zo aka min gyaran jikina, ko ina sai wani sheki nake. Sannan aka yarfa min ƙananan kitso irin na yan Borno, washi gari da safe mai lalle ta zo ita da yara yan mata shida daga shagona, aka fara min bakin lalle a hannu, wasu nayi kafa ja, na sha zama sosai. Ina zaune sai ka sakon 3M ban san daga waye ba sai daga baya ya turo min sakon cewa. _Ina sonki Maman yan hudu, ina sonki Zainaba _
Goge sakon nayi ina jin wani irin ciwo a raina, daurewa kawai nake ina jin wani irin kuka yana tawo min, Tauhid ne ya dawo min raina lokacin da ga hiranmu da Uwais, wani irin kewarshi nake ji ban san lokacin da nayi ta kuka ba, suka yi ya rarrsshina. Domin sun san Tauhid tunda ya tab'a bina shagon yana faÉ—in wallahi sai na bashi 20k, haka nayi ta kuka dakyar Maluma tayi ta rarrsshina domin haka kawai ma idan na tuna shi kuka nake ji nayi ta kuka kamar raina zai fita ni kaÉ—ai nasan yadda nake kewar Tauhid, "Maluma yanzu ba zan kara gashi ba kenan?" Shafa kaina tayi tana faÉ—in. "Allah da ya fimu son shi ya dauke shi, kin ga ba yadda zamu