Showing 57001 words to 60000 words out of 185502 words
saida ya raba jikinshi da nashi kafin ya d'an bubbuga bayanshi yace "Ni zan wuce, sai munyi waya."
Da kallo Asas ya bishi har ya rab'ashi zai shiga mota Asas yace "Sheikh."
Tsayawa yayi tare da juyowa ya kalleshi, kafeshi yayi da ido saboda yana son fahimtar yanayin da zai shiga idan ya ambaci sunanta sannan yace "Me ye tsakaninka da Mimi?"
Sake zaro idonshi yayi yana k'urawa Asas da mamakin tambayar, a hankali ya had'e fuskarshi yana binshi da kallon tuhumen tambayarshi, lura da haka yasa Asas fad'in "A'a cheikh! Ba wai ina zarginka bane da wani abu, kawai dai na fahimci kamar akwai sanayya a tsakaninku, shiyasa na tambaya."
D'an d'auke idonshi yayi daga kan Asas ya bud'e murfin motar yace "Ba komai tsakaninmu, karka k'ara min tambayar nan."
Wani murmushi Asas yayi ya kallonshi har ya shiga motar, zai ja murfin ya rik'e yayi saurin rik'eshi yace "To ya maganar Ryam d'inka?"
Ba tare daya kalleshi ba yace "Tana lafiya, zamuyi magana a gaba."
Yanda ya amsa mishi yasa Asas bai da wani zab'i daya wuce yar rufe mishi murfin dreba ya ja shi suka bar gidan, saida ya ga b'acewarsu kafin ya nufi b'angarenshi dan shiryawa, yana so idan ya fara zuwa asibiti daga nan saiya wuce ya ga yanda Mimi ta kwana.
*Mim-Ma'u*
Ita maganar duniya bata b'uya ko da k'ark'ashin k'asa aka yi ta, tashin hankalin daya faru a gidansu Mimi tsaf a kunnuwan mutan gidan su Asma'u, dan dama katangarsu d'aya ne, wannan ya jawo cece-kuce har abun ya so juyewa kan maman Asma'u, dan ita kanta Asma'u saida kishiyoyin uwar suka fara yada musu magana suna cewa abokin b'arawo ai b'arawo ne, hakan ya jawo fad'a sosai a gidan suma jiya, dalilin haka kuma mahaifin Asma'u ya fad'a da babbar murya cewa ya soke k'awance tsakanin Asma'u da Mimi har abada.
Ita kanta Mimi yau data tashi sai ta samu kanta kamar bak'uwa a gidan, suna fara had'a ido da Mama kamar yanda ta saba ta duk'a har k'asa tace "Mama ina kwana."
D'auke kai tayi kamar bata ji ba ta wuce aikin gabanta, mik'ewa tayi jiki a sanyaye ta d'ora hannu akan mad'aurin gidan sangensu Yaseen zata kwance, murya a dak'ile Mama tace "Barshi zan d'auke da kaina."
Kallonta tayi zuciyarta na harbawa tace "Amma Mama..."
Kujera ta data ta d'auka ta aza ta kuma tak'ark'are ta taka kujerar ta shiga kiciniyar kwance sangen, kasa katab'us tayi tana kallo har ta kwance duka, mik'awa Yaseen tayi tace "Kai d'aki."
Karb'a yayi ya wuce Mama kuma ta fara tattare shinfad'ar, muk'ut tayi ta had'e kukanta tare da k'arasawa gaban murhun da mama ta fara k'ok'arin hura wuta, shi ma dai cikin fad'a tace "Bana so, ban sakaki ba Mimi, idan baki da abinda zakiyi ki nemi waje ki zauna, dan makaranta ma kin gama zuwanta."
Da tsananin mamaki ta kalli Mama hawayen da take rik'ewa suka gangaro, cikin muryar kuka tace "Mama ku yafe min, nasan nayi laifi amma dan Allah karku hanani samun albarkarku."
Wani tsaki Mama taja tare da k'uk'utawa ta d'auki bargon zata shiga dashi d'aki, har ga Allah bargon yafi k'arfinta amma tsabar hushi haka ta wuce dan kai shi d'aki, a daidai k'ofar shiga tsautsayi yasa mama gurd'ewa ta fad'i ita da bargon, da gudu Mimi ta tunkareta haka ma su Yaseen da suka tsaya bakin k'ofar, kamata tayi ta mik'e cikin jin haushi tace "Sakeni, karki taimaka min."
Cikin matsanancin kuka Mimi tace "Mama me yasa ba zaki bari na taimaka miki ba? Wani ma bana jurar ya cutar daku bare kuma ku naga kuna k'ok'arin haka."
Duk'awa tayi zata d'auki bargon Mama ta fizge da k'arfi ta k'arasa dashi ciki ta aje ta fito, fitowa tayi ta samu Amir na nad'e tabarmar, Mama kuma na hura wuta zata d'ora d'umame, tsaye take saita rasa me zatayi ma sai hawaye kawai.
Bud'e gidan da suka ji yasa Mimi saurin juyawa, tana ganin Abba sukuku dashi idonshi jajir tayi saurin durk'usawa tana fad'in "Abba ina kwana? Abba ina ka tafi mun..."
Nunata yayi da yatsa hakan yasa ta yin shiru, ta gabanta ya bi zai shiga d'akin mama ta kalleshi tace "Ina kwana?"
A dak'ile ya amsa da "Lafiya lau." Su Yaseen ma gaisheshi sukayi ya amsa, nan ya barta tsugune saida ya shige sai kawai ta ja k'ugu ta jinjina a bango ta rakub'e tana hawaye, haka Abba ya fito zai shiga wanka mama ta d'auki bokiti ta zuba mishi ruwa, a yanda suka saba Mimi ke d'aukar bokitin, amma yau basu barta ba Abba ne ya lailayeshi ya kai ban d'akin, tana zaune har mama ta zubawa su Yaseen tuwon suka fara ci Abba kuma ya fito.
Gaba d'aya ta rasa ya zatayi ina zata saka kanta ta ji dad'i, a halin yanzu kam kunyar fita waje take kuma tana kunyar had'a ido da Asas, saidai gashi iyayenta ma na neman zama mata dodo su saka ta fara fatan mutuwa. Mik'ewar su Amir suka wanke hayyane suka d'auki jakunkunan makarantarsu yasa Mimi cikin shashek'ar kuka tace "Amir, lek'a gidansu Asma'u ka kira min ita kafin ta tafi makaranta."
Juyawa yayi zaai fita Mama tace "Kai." Juyowa yayi yace "Na'am."
A d'aure tace "Wuce ku tafi inda zaku je."
"To." Ya fad'a yana bin bayan Yaseen suka fita, tusa kanta tayi tsakanin gwiwoyinta ta sake fashewa da kuka, fitowa Abba yayi yana saka takalminshi ya kalleta yace "Kuka ko? Yanzu kika fara ai Mimi, ai duk wanda yasa iyayenshi kuka shi ma sai yayi marar iyaka."
D'agowa tayi cikin matsancin shid'ewa tace "Abba dan Allah dan girman Allah karku min baki, Abba ban aikata abinda kuke zargina da aikatawa ba, wallahi ban tab'a ko da d'aura niyyar fara bin wannan hanyar ba."
Tab'e baki yayi yace "Maganar banza, shi wanda ya baki wayar kenan d'an mahaukaciya da zai baki ita ba tare da shi ma ya moreki ba."
Rintse ido tayi tace "Abba ka tambayeshi kaji idan kana so, wallahi ko hannuna bai tab'a rik'ewa ba."
Zaune yayi akan kujerar katako ba tare da yace komai ba, ga abinci mama ta aje mishi amma saiya tsura mishi ido yana kallo, ganin kamar baya hayyacinshi yasa mama fad'in "Malam."
D'agowa yayi ya kalleta hakan yasa tace "Lafiya, ka ci abinci mana karka bari hawan jini ya kamaka a banza."
Girgiza kai yayi yace "Wallahi Allah ba dan girman sheikh da nake gani ba, da na mayarwa da yaron nan kayanshi ita kuma na bayar da sadakarta a masallaci."
Yanda Mimi ta k'ura mishi ido tana kallo yasa yace "E! To yaushe zamu d'aukeki gwalagwaje mu kai a wannan babban gida, bayan kasantuwar fak'irai kuma wadanni mun zama iyayen karuwar gida..."
Sake had'a kanta tayi da gwiwa ta fashe da kuka tace "Abba ka daina dan Allah, Abba ka daina babu kyau wallahi, Abba ni ba karuwa bace."
Sallamar Gambo tasa su dakatawa suka amsa, wuri mama ta bata ta zauna suka shiga gaisuwa cike da alhini, kallon Mimi tayi da ko d'agowa ba tayi ba tace "Abban Mimi ba dai har yanzu maganar nan bata wuce ba?"
Kallonta yayi yace "Wucewa? Haba dai yaushe?"
Girgiza kai tayi ta gyara zama tace "Abban Mimi, a gaskiya abinda kayi jiya baka kyauta ba ko kad'an, tabbas laifin Mimi ya isa ya hanaku nutsuwar zuci, amma kuma ai komai yana son sirri, yanda ka tozarta kimar yarinya a idon k'awarta da babban malami da kuma mijin da zata aura abin sam baiyi dad'i ba, ka fa sani duk lalacewar da Mimi zatayi wallahi ba zaka iya cireta a 'ya'yan daka haifa ba. Gashi yanzu kuna ta zargin yarinyarku a banza yarinyar da ko yatsa bai iya wucewa ta gabanta ba, kun d'auki alhakinta sosai gaskiya, dan zaku iya yin komai a tsanake."
Kallon Mimi tayi tace "Kamar yanda na fad'a miki jiya Mimi ki ci gaba da rik'e mutumcin kanki, wannan d'in shi ne darajarki a wannan k'arni, iyayenka ma suna wofantar da kai idan ka zubar dashi a waje."
Kallon Abba tayi tace "Idan baku yarda ba ku kaita wata asbitin, amma ka sani duk tozarcin da zaka jawo mata kanka ka jawo ma, dan kafin a nunata sai an nunaka da yatsa tunda kai ne namiji mai fita."
Mik'ewa tayi tare da fad'in "Sai anjimanku, ina sauri dama zan wuce asibiti nace bari na tsaya dan cika alk'awarina."
Babu wanda yace mata k'ala harta fita a gidan, jiniyar kukan Mimi kawai suke ji amma babu mai sauke ko da numfashi da k'arfi. Da k'yar Abba ya sauke numfashi ya kalli Mama yace "...
*Alhamdulillah*
06/08/2021 脿 11:54 - Mme Ishaq馃拑馃グ: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*NA*
_SAMIRA HAROUNA_
*SADAUKARWA*
_GA DUKA_
*'YAN AMANA TA*
馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃
鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
*20*
Da k'yar Abba ya sauke numfashi ya kalli mama yace "Kina ganin gaskiya ta fad'a?"
Zuru ta masa da manyan idonta tana kallonshi ba tace komai ba, kallon Mimi yayi tare da fad'in "Tashi shiga ciki."
Mik'ewa tayi tana kuka kamar ranta zai fita ta shiga d'aki, kallon Mama ya sakeyi yace "Ni fa sai naga kamar gaskiya ta fad'a."
Saida mama ta d'aure fusja tace "Ko da gaskiya ne bai kamata mu sake sakar mata fuska ba, ai ta yaudaremu ta munafurcemu, shi kuma wannan laifin fa?"
Jinjina kai yayi yace "Hakane, a gaskiya ban tab'a kawo faruwar haka a raina ba, uwata? Uwata ita ce ta aikata wannan babban kuskure."
Ajiyar zuciya kawai mama ta sauke ba tace komai ba, abincin ya ci gaba da ci yana idawa ya wanke hannu ya fita a gidan. Yana fita kuma malam ya sallamo gidan, jiki na rawa mama ta shiga amsawa tana k'ok'arin d'auko mishi kujera, ta tabbata abinda ya faru ne ya kawoshi gidan, dan ko haihuwa tayi malam ba gidan yake zuwa ba, ai kuwa ciki ya shigo fuskarshi a had'e tsabar b'acin rai, dan har gida Gambo ta biya yanzu ta sanar dashi abinda ya faru jiya, ita tausayin Mimi da ganin yanda ta sameta a gidan yasa ta zuwa ta fad'a mishi.
Kanta k'asa ta durk'usa tana fad'in "Malam ina kwana."
Cikin fad'a yace "Kwanan lafiya? Ina Mimi?"
D'aki ta kalla tace "Tana ciki."
Abinda bai tab'a yi ba a rayuwarshi, sai gashi yayi yau dan kuwa wucewa kawai yayi d'akin yana cire takalmi ya sake yin sallama, da mamaki mama ta bishi da kallo dan ita dai tasan baya haka. Mimi na jin sallamarshi ta sauko daga kan gado ta sake fashewa da kuka, a hankali ta d'ora kanta a k'irjinshi tana sake sako wani kukan, cike da tausayinta ya dafa kanta yace "Amaryata yi shiru kinji, ki rabu da mutanen gidan nan, yau ba zaki kwana a gidansu ba sai nawa, dan na basu amanarki har na gama k'era miki gidanki, shi ne za'a ci min amana haka."
K'wafa yayi a hankali Mimi ta fara jin sanyi a zuciyarta ta ji tana neman yin murmushi, d'aga kanta tayi saidai bata kalli fuskarshi ba saboda kunya tace "Angona ban aikata ba, ban aikata abinda suke zargina ba, kawai dai ina karb'an kud'i ne idan aka bani amma ban tab'a rok'a ba da kaina, ko waya ma dana rik'e bani nace a siya min ba, kawai anga rashin dacewar ace bana da waya ne yasa aka bani, ni kuma na sa hannu na karb'a, amma wallahi kakana ban tab'a zubar da mutumcina ba kafin a bani wani abu."
Kama hannunta yayi suka zauna kan kujerun robar yana kallonta yace "Na sani Mimi, ni ban tab'a ji a raina ba damaa zaki iya aikata wannan mummunan aiki ba, laifinki kawai karb'an abun hannun kowane gara da wawa, ta hakane wata rana wani zai zo miki da buk'atarshi, dan wani in ya baki dan Allah wani kuma wani abu ya hango a tare dake da yake son mora, dan haka saiya fara siye zuciyarki da kyaututtuka marasa anfani."
Numfashi ya sauke yace "Naji dad'i da yaron nan yace bai fasa aurenki ba, hakan ya tabbatar min shi namiji ne kuma d'an halak."
Cikin share hawaye tace "Kakana kunyar Asas nake ji, da wane ido zan kalleshi bayan abinda ya faru? A gabanshi komai ya wakana kakana."
Sake dafa kanta yayi da babu d'an kwalin sai tarin sumar mai yawan gaske da tsayi saidai bai wuce iya wuyanta ba yace "Karki damu kinji, idan ya zo shi ma ki nemi gafararsa, sannan ki fad'a mishi abinda kika fad'a min yanzu, zai k'ara fahimtarki har ma ya sake miki alk'awarin aure."
Jinjina kai tayi alamar to, cikin rarrashi yace "Zan tashi na tafi kasuwa yanzu, me kike so na taho miki da shi?"
Cike da kunya ta sunkuyar da kanta tana d'an murmushi, hancinta ya lak'ace yana fad'in "Kaga ja'ira ko? Yaushe aka fara tausayina haka har ake tsoron ragargaza min aljihuna?"
Fashewa tayi da dariya mai sauti har hak'oranta suka fito, sosai yaji dad'in ganin wannan annuri na ta, dan haka yace "To fad'a min me zaki ci?"
Girgiza kai tayi tace "Bana son komai, kuma ma ai wannan tsohuwar matar taka ta hanani cin kayan yaji yanzu."
Kumatunta ya shafa yace "Kenan da abu mai yaji zan siyo? To ai naji dad'in haka."
Mik'ewa yayi hakan yasa ita ma ta mik'e tsaye, kama hannunta yayi yace "Fad'a min yanzu zaki zauna anan? Ko kuma kina so idan na dawo daga kasuwa na biyo mu tafi tare dake? Dan naga a nan cutar min ke a ke yi."
Shiru ta d'anyi tana tunanin abun yi, ji tayi ya shafa kumcinta data sha mari jiya yana fad'in "Ga shaidar sawun hannu a fuskarki, wannan jar fata ai bayan sabulu da ruwa ban yarda komai ya tab'ata ba."
Dariya tayi tace "Kakana zan fara tambayar izinin Abbana, idan ya amince sai naje."
Jiijina kai yayi yace "Shikenan to, sai anjima."
Jinjina kai tayi ta bishi da kallo cike da k'aunar kakan nata har ya fita a d'akin, mama na ganinshi ta sake sunkuyawa tace "Allah ya tsare malam, a dawo lafiya."
A dake ya amsa mata da "Allah yasa." Ya fice a gidan, haka kawai ta samu kanta da sakin murmushi, wato duk abinda Mimi tayi ba tayi laifi ba d'an hukuncin da suke son yi mata shine su har sun aikata laifi, mik'ewa tayi ta ci gaba da kai da kawonta.
Da k'yar ya samu yaron daya turo ya shigo cikin gidan da sallama, mama ce ta amsa tana kallon yaron da alama almajiri ne, cikin girmamawa yace "Ina kwananku? Aka ce wai ana sallama a waje."
Da mamakin maganar yaron tace "Waye?"
A nutse yace "Yace wai Ashraf ne."
Numfashi ta sauke mai nauyi kafin tace "Ka ce ya shigo ciki."
Da sauri ya mik'e ya fita dan isar da sak'on, jim kad'an ya shiga doka sallama mama na amsawa har ya shigo ciki, har k'asa ya durk'usa suka gaisa kafin ya ajiye ledojin hannunshi yace "Mama dama wannan sak'on Mimi ne na jiya, Hajia da kuma aunty Hafsat ne suka bata, shi ne nace bari na kawo mata."
Cike da kunya da kuma rashin farin cikin ganin sak'on tace "Harda wahala haka? Wallahi da ma ka barshi ai, a halin yanzu bana jin mahaifinta zai yarda ta karb'i kayan nan."
Ba tare daya kalleta ba yace "A daure a karb'a mama, tun jiya kayan ke hannu na, idan na mayar musu yanzu ba zasu ji dad'i ma suma."
Jim tayi alamar tunani sai kuma tace "Shikenan angode, Allah ya biya."
"Ameen." Ya fad'a da fara'a, mik'ewa mama tayi ta nufi d'aki tana fad'in "Tana ciki ai."
Tana shiga zaune ta samu Mimi tana jin komai dake waknaa a wajen, cikin d'aure fuska tace "Kije ku gaisa, amma karki yarda ki wuce minti biyu."
Jiki a sab'ule ta mik'e tana d'aukar hijabinta na makaranta, yau kam Mimi bata bi ta kan duba madubi ko shafa turare ba haka ta fita, tunda ta fito kanta k'asa bata so su had'a ido, amma tana jin yanda idonshi ke yawo a jikinta, saida ta tsaya d'an nesa dashi a fargajiyar gidan kamar zata duk'a mishi tace "Ina kwana."
Da murmushi a fuska yace "Lafiya lau maah, antashi lafiya?"
Bakinta kawai ta iya motsawa ta amsa amma bata fito da sautin ba, wani murmushi ya saki ganin yanda take ta wasa da hannayenta a cikin hijabi, saidai ta bashi tausayi ssoai ganin yanda fuskarta ta wahala dan kuka da marin da ta sha, numfashi ya sauke yace "Maah ni zan wuce, dama kayanki na zo kawo miki."
Sake sinne kanta tayi, duk da kuwa bata so amma ba zata iya d'aga kanta ta kalleshi ba bare ta fad'a mishi, a sanyaye ya sake furta "Sai anjima, nan da jibi zan dawo insha'Allah."
Jin ya juya zai tafi yasa Mimi d'aga kanta ta bi bayanshi da kallo, kamar yasan ta d'ago kai sai kuma ya tsaya ya juyo hakan yasa idonsu sark'ewa a juna, hawayen dake mata ambaliya ne yasa shi saurin matsowa yana fad'in "Maah lafiya? Me ya faru kuma yanzu kike kuka?"
Cikin fashewa da kuka tace "Kayi hak'uri Asas na cuceka, ka yafe min dan Allah kaji."
D'an tsakin nan yayi irin haba ke ma tare da fad'in "Naanah, tun jiya na fad'a aurena da ke babu fashi insha'Allah, gaskiyarki tasa nake k'ara sonki, kuma wannan gaskiyar yanzu haka gata nan ina hangowa cikin idonki, dan haka ki kwantar da hankalinki kinji."
Jinjina kai tayi tana share hawaye tace "Nagode, amma ina jin kunyarka da ahalinka da iyayena da kowa da kowa, Asas ya zanyi da abun kunyar nan?"
D'an matsowa yayi kusanta kad'an yana murmushi yace "Maah le, na ce ki kwantar da hankalinki kinji, karki damu da komai dan Allah, kinji."
Jinjina kai tayi alamar to, wani murmushi ya saki yace "Yawwa ko ke fa, dan Allah karki bari damuwa ta samu muhalli a zuciyarki har tayi tasiri a shagulgulan bikinmu, ina so