Showing 162001 words to 165000 words out of 185502 words

Chapter 55 - Matar Mutum Book 1 Hausa Novel Complete

20 Dec 2024

512

kin ce a'a, na ce zan tafi kin ce a'a."

Cikin fad'a Iya tace "Tashi d'auko kud'in ni zan je na siyo miki, amma ba zan bari ki fita ba kinji na fad'a miki."

Galala ta kalleta tace "Taya zan baki siyayyar nan mai yawa haka? Wallahi na san ba zaki iya fad'in sunan kokombre ba bare kuma su karas da mayonnaise."

Jim Iya tayi tana kallonta sai kuma tace "Ai shegun abubuwan nan naku ne na yan zamani da wuyar fad'a."

Dariya tayi tace "Yawwa to na je ko?"

A hankali ta kalleta tace "Gaskiya Mimi ina tsoron fitarki, ba wai dan ban yarda dake ba saidai kinga yanzu kamar amana ce ke a wurina, in wani abu ya faru ni za'a ce da sanina."

Marairaicewa tayi tace "Iya na miki alk'awarin babu abinda zai faru, kuma ba zan jima ba zan dawo tunda kinga ba k'asa zan tafi ba."

Sallama suka ji a farfajiyar gidan suka amsa yaron ya shigo, cikin girmamawa ya kalli Iya yace "Ina kwana Iya?"

Da kulawa ta amsa da "Lafiya lau Sadam."

Mik'o mata k'ullin goro yayi yace "Gashi wai in ji mamanmu ta ce goron Nuseiba ne aka raba."

Da fara'a ta karb'a tace "A'a masha'Allah, har an raba kenan?"

"E." Ya fad'a yana juyawa zai fita, da sauri tace "Sadam zo nan d'an albarka."

Dawowa yayi yana kallonta ita ma ta kalli Mimi tace "D'auko kud'in ki bashi ya siyo miki."

Cikin kumburo baki ta mik'e ta nufi d'akin ta d'auko kud'in, kawo tayi ta zauna ta lissafa mishi komai sannan ta ce ya shiga taxi zuwa kasuwa, cike da dattako yaron yace "A'a ki bar kud'in taxin, akan moton yaya Bello na ke."

Da jin dad'in dattakon daya mata tace "To nagode sosai Sadam, ka kula da titi kaji."

Fita yayi ita kuma ta d'auki wayarta ta kira Jamila dake kusa da gidan Iya, tana d'agawa daga b'angarenta ta fara fad'in "Shegiya Mimi amarya, sai yau kika tuna damu?"

Tsaki Mimi tayi cike da jin sarauta akan ta ta yatsina baki tace "Ke bana son iskanci, wai ku baku san inda mutum yake bane?"

Cikin dariyar mugunta Jamila tace "Ke tafi can marar mutumci, waye zai je gidanki kina kwasar amarci ke da sugar Dady d'inki."

Wani irin b'acin rai ne ta ji ya taso mata da bata tab'a jin shi ba, haka kawai ta ji ta bata masifaffen haushi, da k'unar zuci ta katseta da fad'in "E d'in, sai me? Na ci amarcin da shi da matsala ne?"

Tsagaitawa tayi da dariyarta tace "Ke ni ba masifa nake ji ba yau, fad'a min me ke labari? Zaki zo ranar k'umshina ne?"

Cikin dak'ilewa tace "K'umshin me?"

Da mamaki tace "Baki san ni zanyi k'umshin Salma ba na farko?"

Ba tare da wani kulawa ba tace "Ko? Ya akayi ta baki k'umshinta kamar ta rasa dangi?"

Cikin jin haushi Jamila tace "Ban gane ba Mimi? Wannan ai wulak'anci ne ma, yau a makaranta mun d'auka zaki zo ai shiru."

Cike da iskanci tace "Ke ni fa ba lafiya ma gareni ba, laulayi nake, ciki ne da ni."

Cike da zumud'i Jamila tace "Da gaske? Kai amma na ji dad'i, ashe dai shehinmu da saurenshi, da wuri haka?"

Wani lalataccen murmushi Mimi tayi a ranta tace "Can da yawonki, wai ciki, mtsss?"

A fili kuma d'orawa tayi da "Ke farantai nake so manya masu, idan akwai ki aiko a kawo min ina nan gidan Iya."

Da sauri tace "Da gaske? Yaushe kika zo?"

Tsaki tayi tace "Ban sani ba, idan zaki aiko min to, in kuma babu ki fad'a min."

Dariya Jamila tayi tace "Zan kawo miki da kaina ma, zan zo gidan yanzu dawowata kenan daga makaranta."

Tab'e baki tayi tace "Wato kuna zuwa kuyi shik'a ou dawo ko? Ai kunsan yanzu ba'a fara komai ba."

Dariya Jamila tayi tace "Ai ki bari kawai, in fad'a miki PC (Physique Chimie) ma wallahi saida ya tambayeki, Lariya ma tana ganinmu ke ta fara tambaya, ga su Sadiq da su Omar, ke kowa fa bakinshi a Mimi."

Wata shak'iyiyar dariya tayi kafin tace "Allah sarki Mimi mai masoya dayawa."

Cike da izgili Jamila tace "Kamar aljanna ba."

D'auke wayar tayi a kunne tace "Sai kin zo." K'it ta kashe kiran tana dariyar saboda tuna rayuwarta ta makaranta, a gaskiya zata sake lallab'ashi dan ta koma makaranta, tana son rayuwar nan sosai saboda rayuwa ce mai cike da 'yanci da nishad'i.



*Bayan kwana biyu*



Dke yammacin alhamis ne aiki take tuburan wajen had'awa sheikh abun bud'a bakin da ita ta saka kan ta ba tare da saninshi ba, 04:30 ta gama da komai ta saka a basket d'in da Jamila ta kawo mata ta ajiye jug d'in lemu gefe ta shiga wanka, wanka ta tsala ta fito ta shirya cikin doguwar rigar leshe wacce ta mata masifar kyau, kwalliya tayi sassauk'an mai ban mammaki ta kashe d'aurin d'an kwali, turare ta shafe jikinta da shi kafin ta d'auki mayafinta mai d'an girma ta rufe duka jikinta da shi ta saka saka da takalmi ta fito.

Kallo Iya ta k'are mata cike da jimami tace "Mimi kina ganin shirin nan baiyi yawa ba kuwa?"

Kallon kanta tayi tace "Iya wane yawa kuma? So kike na je a hargitse ne to ina wari."

Jinjina kai tayi tace "Ba haka nake nufi ba, Allah ya kiyaye hanya."

Dariya tayi tace "Yawwa Iya ta, sai na dawo."

Cikin zolaya tace "Kuma ki tabbatar kin karb'o min na wa abun bud'a bakin a wurinshi."

"To." Ta fad'a tana kallon Jamila dake shirin d'aukar basket d'in kwanukan da sauri tace "To uban wa zai d'aukar miki jug d'in?"

Hararanta Jamila tayi tace "Ban sani ba, ke uban me zaki d'auka bayan jakarki?"

Juyawa tayi ta kalli Iya tace "Iya dan Allah ba gabanki likita aka ce na daina d'aukar abu mai nauyi ba?"

Da mamaki Iya tace "Yaushe? Akan wane dalili kuma?"

Dariya Jamila tayi tace "Iya rabu da ita raina min hankali ne zaatayi."

Matsowa tayi daf da ita tace "Nima dai na kusa auren nan na samu ciki."

Hararanta tayi tace "Kafin kiyi dai ai har cikina yayi k'wari."

Iya dai na jinsu har suka fita suna wannan cacar bakin bayan Mimi ta karb'i basket d'in ta b芒 wa Jamila jug d'in lemu, suna fita kam basu sha wahalar samun taxi ba suka d'auki hanya, wayarta ta ciro a jakarta ta dannawa lambarshi kira.

Yana tsakiyar masallacin dake ma'aikatarsu duk yan ma'aikatar sun zagayeshi suna d'aukar darasin daya zamar musu saurare dole, ba komai kullum yake fad'a musu ba sai rik'o da amana da kuma yin aikin domin Allah, sannan nuna musu mahimmancin aikinsu da tuna musu al'umma suke ma. Wayarshi na fara vibration ya laluba aljihu ya cirota dan ya kashe kiran, sai dai? Wacce take kira tafi k'arfin ya katse kiranta, hasalima mamakin ganin kiran na ta ya shiga yi sanda sunan daya saka mata a lambar ya bayyana da *yan matana*.

Kamar wani marar gaskiya ya saci kallon mutanen dake gabanshi sannan ya d'aga wayar ya d'ora a kunne, cikin rad'a yace "Salam, ina darasi ne, zan sake kiranki."

Da sauri jin zai kashe wayar tace "Abdul."

Sam ba da son ranshi ba ya dakata saboda sunan Abdul data kira, cikin shagwab'abb'iya kuma siririyar muryarta tace "Gani nan fa tafe wajenka, zamu had'u a gidan nan ne ko kuma na zo ma'aikatar?"

Zabura yayi yana nufin tashi tsaye sai kuma ya kalli mutanen gabanshi ya dakata, ture hularshi yayi ta gaba ta koma baya yana tsatsare mutanen da ido da suma dayawa shi suke kallo, gyara zamanshi ya sake yi da kyau ya rufe bakinshi da tafin hannu cikin rad'a yace "Ryam ban gane gaki nan tafe ba? Munyi dake zaki fita ne?"

Cike da shagwab'a tace "To ba kai ne ka fad'a min kana azumi ba, shiyasa na maka abun bud'a baki, ni kawai ka fad'a min inda zan zo na sameka kaga fa ina cikin taxi ne."

A hankali ya lumshe ido ya furta "Hasbunallahu wani'imal wakil."

Bud'ewa yayi fes a kan mutanen dake gabanshi yana jin kamar ya fashe da kuka, ba wai fitowar babu izininshi bane matsalar, tunanin yanda ta fito daga gidan shi ne yake masa yawo a kai, shin ta rufe jikinta da hijab ne? Ta saka nik'ab da safar k'afa? Ko kuma dai yanda ya santa a haka ta fito kowa da komai ya gama kalle masa halalinsa?

Zunbur ya mik'e tsaye yana fad'in "Ku gafarceni, kira ne na gaggawa."

Da sauri ya juya inda jami'anshi suka rufa masa baya da sauri su ma, suna shiga mota yace "Gaggauta dan Allah, Tallague zamu je."

Yana maganar ne yana kiranta a waya, tana d'auka hankali tashe kamar wanda aka shaidawa iyalinsa na d'akin nak'uda yace "Ryam kina ina yanzu?"

Cike da rashin damuwa a tare da ita tace "Yanzu muka baro gida."

Da sauri yace "Hakan na nufin bakuyi nisa da gida ba?"

"E." Ta fad'a kan ta tsaye, wata ajiyar zuciya ya sauke mai k'arfi yace "Ryam ku dakata, ku dakata dan Allah gani nan tafe sai mu tafi tare."

Kallon Jamila tayi dake gefenta tace "Amma fa ba ni kad'ai bace, tare da k'awata muke."

A sanyaye yace "E, har da ita d'in."

D'aga kafad'a tayi alamar shikenan sannan tace "Ok."

Yanke kiran yayi ya mayar da wayar aljihu, maida kan shi yayi ga kallon gabanshi sai sukayi ido hud'u da dreba dake tuk'i fuskarshi d'auke da mamaki, matse bakinshi yayi ya feso wani sanyayyen iska yana tsare dreban da ido yace "Yarinya ce, wahala take bani, amma dai nasan na d'an lokaci da ta k'ara girma zata bari."

Murmushi dreban yayi yace "Hakane." Ci gaba yayi da aikinshi sai sheikh daya sake fad'in "Kana ga na ci gaba da lallab'ata a haka? Wani lokacin kamar mahaukaci nake zama wallahi, ban san ya zanyi ba."

Satar kallonshi dreban ya sake yi a ran shi yana fad'in "Allah ya sauk'ak'a maka sheikh, abun ya ta'azzara kam."

*Bakin* titi aka aje su suka gyara tsayuwarsu dan jiran tsammani, duk da suna cikin unguwar ne amma sun d'an yi nisa, suna tsaye sun aje kayan hannunsu a k'asa motar ta tsaya a gabansu.

Mugun bugawar da k'irjinta yayi yasa ta dafe k'irjin dan tsaf ta san motar waye, bata gama tsurewa ba saida Muttak'a ya fito a gadarance har ya tsaya gabanta k'ik'am yana k'are mata kallo daga sama har k'asa.

Bata tab'a jin haka ba sai gashi tana kallonshi a mugun tsorace bakinta bud'e tana had'a yawu da sauri sauri, hannu ta d'ora a kan cinyarta tana ta cumimiye rigarta, wani sakaran murmushi ya saki yace "Mimi kenan, ashe kina nan?"

Ba tare data d'auke idonta a kan shi ba ko ta rusuna su ta ci gaba da kallonshi, wani mayen kallo ya mata yace "Mimi na fad'a miki idan ban sameki ba babu wanda zai sameki, na yarda wannan karan an fi k'arfina, Sheikh ko aljanun kaina suna kunyarshi bare kuma ni kaina."

Daf da ita ya sake matsowa yana kallon fuskarta yace "Kinyi kyau fa, amma ki sani baki dace da zama matar tsoho ba, babu abinda zai iya yi miki."

Baya ya ja ya bud'e murfin motarshi yace "Ki kula da kanki, hakan ba yana nufin na hak'ura bane."

Shigewa yayi ya tashi motar yayi baya baya sai kuma ya tsaya, Mimi da har wata zufa ta keto mata sauke numfashi tayi da k'yar ta kalli Jamila dake kallon Muttak'a da bai gusa a wurin ba, dafata tayi cikin b'arin murya tace "Mu tafi kinji, mu matsa gaba dan Allah."

Sunkuyawa Jamila tayi tana d'aukar kayan tace "Waye shi kuma waccen mahaukacin?"

Yatsina baki tayi tace "Rabu dashi kawai, d'an k'waya ne."

Sun fara takawa kenan ta hangi motar sheikh tsaye ga dukkan alama kuma tsaye suke a nan watak'ila sun jima, takawa ta shiga yi a hankali sai Jamila data tsaya tana kallonta dan ta tabbatar su d'in ne, Muttak'a na ganin haka shi sam bai ga motar su sheikh ba sai ya sake murd'awa motar giya ya taka da k'arfi ya nufi Mimi gadan gadan wanda hakan yasa Jamila kaucewa da sauri har tana sakin jug d'in hannunta.

Sheikh da ke hangen komai a cikin mota zufa ta jik'eshi sharkaf sakamakon ganin Muttak'a na wani shigewa jikin matarshi kamar zai tab'ata, ga mugun wankan da ya ga ta d'auka, yanzu kuma da yake ganin motar da wani matsiyacin gudu tana nufi kan Mimi yasa shi bud'e motar da sababin sauri ya fito takalminshi d'aya irin babush d'in nan k'irar Rusia mai sunan MisTsar ya baroshi a motar sai d'aya a k'afarshi ya tako da mugun sauri har da gudu gudu ya fizgi hannunta hakan yasa shi ya tsaya ta inda motar ke tahowa ita kuma ta koma baya.

Kallon juna sukayi saidai kafin wani cikinsu yayi wani yunk'uri Muttak'a ya taka birki da iya k'arfinshi saboda gaba d'aya ya razana saboda ganin sheikh, duk da haka saida motar ta daki gwiwan sheikh daya bada baya yana kallon fuskar Mimi. Sanda motar ta dakeshi lumshe ido yayi amma sam bai motsa ba, da sauri yayi baya-baya ya ja motar ya d'auki titi da gudu ya bar wurin a tunaninshi sheikh bai ganshi ba.

Numfashi ta shiga saukewa gaba d'aya fuskarta ta nuna yanayin tsoro, ba tare daya saki hannunta ba ya juyar da ita ya shiga takawa da ita da k'arfi suka nufi mota, saida ya fara takawa yana jin lallausan k'afarshi na taka tsakuwa ya fahimci babu takalme a k'afarshi, turata yayi cikin mota ta shiga sannan shi ma ya shiga ya zauna, tayar da motar sukayi suka bar Jamila nan tsaye ta rasa me zatayi? Ina zata nufa? Ya zatayi da d'an sauran abinda ya rage musu? Tunda jug d'in ya fashe kasancewarshi na kwalba sanda ta sakeshi abun ciki ya zube.

Gidan daya kaita ranar suka je kai tsaye ya bud'e da makulli suka shiga, a falon ya zauna kan shi a k'asa hannayenshi a jimk'e, ita ma jiki a sanyaye ta zauna kan kujera tana kallonshi, shiru d'akin babu wanda yace wani abu a k'alla minti talatin, gajiya tayi da zaman shirun kawai ta muskuta tana ci gaba da kallonshi tace "Abd..."

Jajayen idonshi da jar fuskarshi da k'arara ta nuna b'acin rai ya d'ago ya kalleta kafin ta k'arasa, da sauri ya mik'e kamar an mintseneshi ya cire hularshi ya aje kan kujerar, tattara babbar rigarshi yayi ta malamai ya aje gefe ya nufo kan ta, yana tsayawa gabanta ya rik'o hannunta tayi tsaye ba tare data shirya ba, hab'arta ya tallabo ya zuba idonshi cikin na ta cikin muryar b'acin rai yace "Waye shi?"

Muryarta na rawa tace "Tsohon...saurayi..."

Bata gama fad'a ba ya saki hab'arta yace "Shi ne kuka had'u dan ku gaisa?"

Da mamaki ta kalleshi tace "Kamar ya? Kasan me kake fad'a kuwa? Kai fa ka tsayar damu a hanya ka ce kana zuwa."

A mugun tsawace yace "Amma na ce ki kula wani d'an iska ne? Ba ma wannan ba ni na fad'a miki ina buk'atar abun bud'a baki ne? Da izini na kika fito daga gida? Me kika d'aukeni ne Ryam? Nema kike ki mayar dani wani sakarai mahaukaci, akan wane dalili?"

Yanda ya rufe ido yake mata masifa a cewarta yasa ta yin zaune kan kujerar tana had'e hannayenta, da mamaki ya kalleta sai kuma ya d'auke kallabin kan ta hakan ya bayyanar da yalwataccen gashinta yana fad'in "Wannan shirin fa? Wai ke baki da hankali ne?"

Da sauri ta kalleshi idonta taf da hawaye ta mik'e tsaye, cikin zubo da hawayen idonta tace "Ni ce ma marar hankalin? Saboda ina ganin nayi abinda zan birgeka."

Juyawa tayi kan kujerar ta d'auki jakarta da kallabinta ta juya a fusace zata fita ita a la dole ita ce yanzu aka b'atawa rai, rik'e k'ugu yayi shi ma yana kallonta har ta fita yana jin shi ma fa shi aka b'atawa dole ma a bashi hak'uri.

Tana fita taxi ta shiga aka nufi gida da ita shi kuma zaune yayi a falon ran shi a b'ace kamar zai ciji wani, banda tsaki da dukan iska babu abinda yake yi yana ta tunanin lamarin yrinyar nan, ya yarda akwai k'uruciya saidai a lamarin Mimi har da wauta da hauka ma.


_(Dan Allah ku fahimce ni, ba labari ne da nake rubutawa dan daidai da son ran kowa ba, abunda nake da tabbacin zai iya faruwa ga duk wanda hakan ya faru dashi nake rubutawa, ma'ana zahirinmu ba wai abinda ba zai yiwu ba, idan mukayi duba da shekarun Mimi da bud'ewar idonta, da kuma shekarun Sheikh dole hakan ya b'ata masa rai, sannan ita ma dole ta ji kamar tsuntsuwa ce da ake neman cirewa pika-pikinta dan hanata tashi sama.)_



*Alhamdulillah*
06/08/2021 脿 11:59 - Mme Ishaq馃拑馃グ: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�
*MATAR MUTUM*
_(K'abarinsa)_
馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈�

*NA*


_SAMIRA HAROUNA_


*SADAUKARWA*


_GA DUKA_

*'YAN AMANA TA*


馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃

鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔�

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


*54*




*Kwana biyu* kenan da faruwar abun nan amma babu wanda ya kula wani ko a waya, Sheikh ya zuba ido ne ya ga tana da wayon da zata tuntub'eshi har tayi k'ok'arin bashi hak'uri, amma shiru kake ji kamar malam ya ci shirwa yasha ruwa, hakan ya d'ugunzuma hankalinshi wajen tashi sosai, dan shi fa ba haka Hafsat ta koya mishi ba, ba haka ta raineshi ba, shiyasa rainon na Mimi yanzu yake neman dagula masa lissafi gaba d'aya.

Gashi a daren ranar kuma shi da uku daga cikin wasu malamai suka tafi k'asar Abuja dan gabatar da wani babban taro na malaman k'ungiyar ahlul-sunna wal-jama'a, duk da yana wurin amma kuma hankalinshi yana kan wayarshi yana saka ran ganin ko da flashing d'inta ne, gashi muguwar kewarta na damunshi, har yau idan ya tuna darensu na farko da sauren dareren da yake wasa da ita sai ya ji yana buk'atarta a kusa da shi, wasu lokutan yana d'aukar wayar dan ya kirata amma kuma saiya dakata da niyyar ya d'an hukuntata ta gane ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login